Showing 201001 words to 204000 words out of 363280 words

Chapter 68 - DUNIYATA BOOK 2 COMPLETE

HUGUMA   

11 Nov 2025

1427

ta zauna daga bayanta kadai ya qawatar dashi gami da tafiya da hankalinsa. Ya dora yatsunsa a hankali saman fatar wuyanta,inda wajen ya danyi jajaja. Hannunta ta dora saman nasa tana dan danne wajen,guri kusan uku duka haka sukayi,yasan kuma shine sila,zare hannun nasa yayi yana juyo da ita tana fuskantarsa.

Idanunsa ya lumshe yana kuma budesu duka samanta.

"You look so gorgeous" Ya motsa labbansa yana furtawa da wani irin sassanyan yanayi yana duban qirjinta da yayi redness shima guri uku. Yatsantsa yakai wajen yadan taba sannan yace

"Does it hurt?" Fuska ta kwabe masa cike da shagwaba kaman zata sake masa kuka,sai ya yarfar da hannunsa yana fadin.

"Ayyah.....sorry,bari na fanshi wannan ciwon" Ya fada yana ja da baya fuskarsa da murmushi. Luggage dinsa ya kwantar ya bude,ya ciro wani dan mitsitsin box ya tako gabanta.

"Qaramim gift ne....for you duniyata" Ya fada yana ciro wani siririn agogo dake zuba qyalli. Koda bakasan meye ba kasan abune me matuqar daraja,kallo daya zakayi masa kasan abune me tsadar gaske,bashi da girma ko fadi amma yana daukan ido sosai. Matsowa yayi kusa da ita sosai,ya miqa mata hannunsa yana kallonta da ido. Ta fahimci me yake nufi amma saita noqe,bai wani tsaya jiranta ba yasa hannunsa ya kamo hannun nata sannan ya fara saka mata agogon.



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

5?? 5?? 5?
? 5?? 5?? 5?? 5?? 5??
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D? D? ?

5?K?5?

103


"Ya subhanallah" Ya fada yana juya hannun cikin tafin hannunsa. Ya mata wani irin kyau kaman saboda ita aka qirqireshi,ya zuba idon hannu yana jujjuyashi kafin a hankali yace.

"Our latest wrist watch...2025,kin masa kyau duniyata.....nayi accepting wannan design din saboda ke,koda baiyi daidai da ra'ayin dealers dinmu ba,i love it for the sake of you" Ya qarasa maganar a tausashe yana kai hannunsa yayi kissing hannun nata,still idanunsa a kanshi,ya zura hannunsa a aljihunsa ya fiddo wayarsa ya laluba wata number ya kira. Bugu daya aka dauka,da hausa taji yana magana.

"Mun siya design dinnan......sannan madam ta ninka price din da wasu dollars din akai ainihin price din". Ya fada a nutse da alama yana magana da wasu ne

" Alright " Taji ya sake fadi yana katse kiran,yana maida wayar aljihunsa tana dubansa idanunta a warwaje,sai daya daga kai sannan suka hada ido,fuska ta narke

"Wacce madam din?" Ta tambaya da siririyar muryarta dinnan,miskilin murmushi ya sake mata

"Akwai wata bayan ke?" Saita sake fidda idanun

"Ban da kudin siya fa....thought dai bansan nawa bane"

"Amma kina da muhammad jadda ko?" Ya furta yana ja baya kadan idanunsa a kanta. Yana jin dadin kallonta sosai,sai yakejin duk wata tsohuwar kewa ta rayuwarshi tana sulalewa,yana jinsa wani sabon mutum na daban.

Duban hannun nata tayi,haka kawai taji kaman ya saka mata wani abu me daraja da yawa,sai takejin hannun ya mata nauyi.

"Na gode.....na gode sosai" Ta samu kanta da furtawa a sanyaye. Wani tsadajjen qaramin murmushi ya saki yana girgiza kansa.

"No.....no need duniyata.......ba irin wannan godiyar nakeso ba.....the only one i want........" Sai bai qarasa ba ya mata nuni da shimfidadden gadon. Da sauri ta juya masa bayanta tana kasa hada ido dashi,ta fahimci yana bawa abunnan muhimmanci tamkar baisan kayan kunya bane?.

A nutse taji ana yafa mata abu ta baya,ta daga kanta sai taga wata baqar sassalkar abaya ce,manal alhammadi shine tambarin da yake maqale a hannun rigar,ta fidda idanunta tana jin wani abu yana girmamarta,ta taba jin company din,wanda dukka abayas da yake fitarwa luxury ne masu tsada da aji sosai,ta sansu ne saboda ita din masoyiyar abayar ce.

"Ba wani kunya tsakanin muhammad fu'ad da duniyarsa......ba kunya tsakanin muhammad fu'ad da matarsa......abinda kawai yake buqata......madawwamiyar soyayya da zata mamaye rayuwarsa.....ta bashi wani farinciki da nutsuwa daya rasa a rayuwarsa.....duk da cewa ina zaqewa da yawa.......amma wannan abun nake bara" Ya rigata fada kafin ita ta fada. Boyayyen murmushi ya subuce mata,wato daga jiya zuwa yau ya fara haddace irin kalmominta kenan da take yawan maimaita masa?.

Juyo da ita yayi yana zura mata hannayen rigar ya furta

"Fatabarakallahu ahsanul khaliqeen.....komai saikin masa kyau?" Yayi maganar yana dage girarsa.

"Komai saina masa kyau?.....ko komai sai yamin kyau?" Ta tambayeshi tana mamakin yadda yake juya maganar daga qarshe ta koma farko.

"Kece kike musu kyau basu keyi miki ba.....don dama kedin me kyau ce.....you're not ordinary duniyata" Yayi maganar sanda ya dago daga tsugunnan balle mata button din da yayi har qasa. Mayafin ya warware yayi mata lafiyayyen rolling tana tsaye tana kallon ikon Allah,ya kama hannunta zuwa gaban mirror yayi tsaye a bayanta.

"Duk wani abu me daraja rufeshi akeyi a killaceshi" Ya furta a nutse yana duban kyakkyawar fuskarta ta cikin madubin,yana jin yadda zuciyarsa ke bugawa saboda ita,kishinta yana sake ratsashi da kyau,yana sake jin tabbas......lallai ba wanda zaisha ba kuma wanda zaici bulus daga cikin mutanen dake hannunsa a yanxu.......tun daga kansu mashkur har zuwa kan zuwaira da bibo.

"Ga aro nan na baki.....idan munci abinci mun dawo zaki bani kayata" Ya fadi wannan karon yana dan sanya seriousness saman fuskarsa. Dan dubansa tayi kadan,sai ya gyada mata kai alamun tabbatarwa. Yanaso ne yayita kallonta,yanason wucewar kowacce daqiqa tayishi bisa idanunsa,yanaso yaci gaba da kallon baiwa da ni'imar da Allah yayi masa,yanaso su kasance a haka shi da ita......da zaiyiwu su qare rayuwarsu cikin irin wannan yanayin na dagashi sai ita.

Yana maqale da hannunta suke sauka zuwa bangaren cin abinci,private ne wanda ya dauko musu cook dinne musamman saboda iya su biyun. Sun samu dining room din cike da cima kala kala,abincin Africa da wasu na Nigeria. Macace da batace ga daga qasar da take ba,ta tarbesu cikin haba haba sannan ta fara serving nasu cikin kulawa,lokaci lokaci tana magana da fu'ad da hankalinsa ke waya cikin yaren Dhivehi,har ta kammala ta juya ta fita tana basu guri.

Juya spoon din take kawai a plate din tana hadiye wani abu a qirjinta. Batasan meye ba amma ya tsaye mata a wuya. Bai ankara ba,sai daya gama uzurinsa da waya sannan. A mamakance yake dubanta.

"Start mana madam....banason wasa da abinci fa?".

"Itama fareedan ce?" Ta tambayeshi da wani salo daya sanyashi karantar zallar kishin dake kwance a idanunta,saidai kuma a sarari qwalla ce kwance saman oily eyes dinsa,sai suka qara wani sheqi.

Dariya yakeson mata saboda wani irin farinciki yaji yana lullubeshi,tun daga saman zuciyarsa yana sauka ta kowanne sashe na gangar jikinsa. Har ya fara winning haka da wuri? Ya tambayi kansa yana taya kanshi murna,amma a bayyane sai ya lanqwasa fuskarsa alamun tausayi.

"Me kuma nayi?". Muryarta na rawa kadan tace.

"Kunata magana da yaren da banaji.....tanata maka hira kana amsawa?". Wannan karon kam kasa boyuwa dariyarsa tayi,abinda ya tunzurata kenan.

" Karki wuce gona da iri sabreen,karki rudu ki fada soyayyar abinda ba yafi qarfin ajinki.....abinda yafi qarfinki,abinda baki da tabbas a kansa.....shin kin Manta maamah tana nan?". Tambayar data tarwatsa duk wani qwarin gwiwa da take qoqarin tattarawa kanta,taji kuma komai ya tsaya mata cak.

Dab da ita ya dawo ya zauna,ya kama hannayenta ya saka cikin nasa yana matsawa a hankali.

"Kin taba ganin mutum ya canza DUNIYARSA?" ya mata tambayar kai tsaye,qasa tayi da kanta don sai takejin tana son jefa rayuwarta cikin hadari ne kawai,muddin ta sakewa zuciyarta ta fada sonshi to ba shakka ta fada babban tarko......babban tarkon da zai bawa maamah daman walagigi da rayuwarta yadda taga dama.

"Amsar itace aah......ke duniyata ce,babu daman na sauyaki ko na hadaki da wata ko wani abun......ni muhammad jadda naki ne ke kadai,don ke kadai aka halicceni.....ki rubuta wannan ki ajiye"

_to zamu gani,anya hajiya maamah zata qyale kuwa???_


*ANNI*


Tun a jam'in sallar asuba da sukazo yi taga bata ga fu'ad ba.....still da tace farouq ya turo mata shi komin dare baizo ba,har suka gama waya da abba Alhaji hamza kibiya dake tashi umrar ta kwanta amma ba fu'ad din ba dalilinsa.

Sanda suka kammala sallar sai tayi zaune kawai tana lazimi,tunaninta yana rarrabuwa,bataga fu'ad ba......bataga sabreen ba,duka ina suka shiga?. Ta wata fuskar sai takejin relief na rashin ganinsu su duka biyun,don zuciyarta na qissima mata wani abu,ta wani bangaren kuma bataso ta sake jikinta akan hakan,saboda tasan wace mariya din.

Takwas saura farouq ya shigo gaidata. Yana daga zaune gabanta ya dan dubi amna dake kwance tana shirin komawa bacci

"Ta duba qur'aninta kuwa?". Kai anni ta daga masa

" Ta duba" Sai ya jinjina kai. Wani sabo ne da raino data musu dukkansu,dole kowacce safiya....komai uzurinka ko meye kakeyi ka fara duba qur'ani kafin komai.

"Kiramin fu'ad.....ka gwadamin dukka layukansa" Anni ta fadi tana gyara zamanta.

"Na gwada wani tun jiya a kashe,amma bari na gwada sauran" Farouq ya fada hankalinsa kwance,don shi kam ya gama hasashen inda aka haihu a ragaya ma. Baya tunanin ko maamah ta yiwa fu'ad farin sanin da shi yayi masa.

Daya bayan daya yabi layukansa yana kira amma kowanne gaya masa ake a kashe yake,sai ya daga ido kawai yana duban anni da fuskarta ta shiga damuwa.

"To ina ya shiga?,ina kuma sabreen?". Dariyarsa ya danne yana dan saka alhini a saman tasa fuskar shima

"Karki damu anni in sha Allah jikina yana bani suna tare,bari na tura masa email da SMS duka" Ya fada yana fara rubuta saqonnin ya kuma aike masan kaman yadda yace,duk da yasan zai wahala ya gani a kwanakin nan,lallai indai ya samu nasarar dauke sabreen ne tofa sai baaba ta gani.


*MAAMAH*

Idan tace hankalinta a kwance yake daga daren zuwa safiyar tayi qarya. Ta kirashi ta kirashi har batasan adadin sau nawa ba. Tabbas ta sani,a yanxu duk duniya idan ameenatu tace itace mahaifiya ga fu'ad,kuma tana tuhumarta batan sabreen ba wanda ya isa ya hana a daureta,ba wanda zai fiddata idan ba fu'ad din ba,da sauran mutuncinta,bataso wasan ya qare a haka,saidai hakan ya sake ninka qiyayyar anni sosai a ranta. Ita daya taketa shawa kanta alwashin saita yiwa ameenatu abu mafi munin da ba zata tabawa mantawa da ita ba,idan don tayi wannan ne don ta nuna mata iyakarta ne ganin suna qasar da ba tasu ba.....to tabbas ita kuma zata bar mata wani babban tabo a rayuwarta da ba zata taba mantawa dashi ba.

Musaddiq ta kira ta sanyashi nema mata fu'ad din,saidai shima kiran duniya wayar sunqi tafiya.

"Maamah wayoyinsa a kulle suke" Maganan data sake sakata a taraddadi da tunane tunane iri iri.

"Kada fa ya zamana ameenatu ta salwantar mata da yaro ne takeson tayi garkuwa da ita akan batun haka da wuri?" Wannan shine tunanin daketa mata kai kawo.

"Ya kamata ki xama cikin shiri.....ki xama a ankare.....karki nuna mata tsoronki,ki tabbatar mata da.naki zargin kema" Abinda zuciyarta take nanata mata kenan,wanda shine kuma ya bata qwarin gwiwa.

Cikin kwanakin sai ya zamana wani irin zama ake a gidan,kallo kallo kawai akeyi tsakanin maamah da anni din. Duk da maamah tana cikin d'ari d'ari da tunanin inda fu'ad da sabreen dinma suke......amma ta azawa ranta wani dakiya. Ta fannin annin kowanne taku na maamah din saman idanunta yake,ba komai take dubawa ba sai idanun yaransu da suke rayuwa guri daya,zai zame musu wani abu na daban kuma na tashin hankali idan suka ga wani sabani muraran a tsakaninsu,banda hakan a shirye anni yake akan maamah wannan karon.....duk da tana danjin relief idan farouq na bata tabbacin fu'ad da sabreen din suna lafiya.

Farouq din ya fahimci abinda ke faruwa,saidai bai nuna musu komai ba,yayi ma kaman bai sani ba,saidai time to time shima yana neman fu'ad din ta waya,amma dif kakeji ko sau daya bai taba katarin samunsa ba.....a haka sannu a sannu sai gashi an kwashe sati guda cif ba wanda yaji motsinsu ko yasan inda suke.

Zuwa sannan hankalin anni ya tashi sosai,kusan kullum sai tasa farouq ya kira mata shi,mafi qaranci sau biyu a rana,saboda kwanakin barinsu Maldives kusan za'a ce yayi,kwana uku ko hudu suka rage musi,gashi babu shi ba sabreen din.

Tun tana yiwa maamah din kara har abun yaci tura,ranar daya rage kwanaki uku subar qasar,da wani yammaci suna parlor. Amna ke mata kalba saman dogon gashinta da tafi masa kalba akan kitso,maamah tana daga gefe zaune tana kallo cikin tv. Ta tsiri wannan zamanne kawai don ta nunawa anni ba abinda zai tsoratata,hakanan itama me cikakken iko ce,duk da cikin rashin cikakkiyar nutsuwa itama take. Ba sabreen ce ma damuwarta ba danta shine damuwarta,idan tana da damuwa akan sabreen din bazai wuce na yadda take gudun kada anni ta fake da wannan ta tozartata a idon duniya ba.

Farouq ne ya shigo da sallama,kaman yadda suke koyi da tarbiyyar anni da umarninta,ya yiwa maamah barka da gida,ta amsa masa a d'age kaman yadda ta saba. Mugun haushinsa takeji.....tana ganinsa a asalin tantirin munafuki tun daga quruciyarsa kawo yanzu,kai tsaye zata iya cewa shine kanwa uwar gami da yaja mata yaro cikin gidansu ya hadashi da mayun iyayensa da suka kasa sakar mata kurwar d'a,suka hanata taci arziqin d'anta yadda ya dace. Ko a yanzun gani take cutar fu'ad kawai yakeyi yana amfana da arziqinsa,yana tatsarsa ne shima.....ba wani tare da suka samo arziqin,ba kuma wai iya harkar noma da kayan abinci yake wannan fantamawar ba,dukiyar gold da diamond din d'anta ce.

"Farouq......kwanaki uku suka rage mana mubar Maldives.....ka samomin 'ya'yana?" Tayi maganar cikin salon son isar da saqo ga maamah.



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

5?? 5?? 5?
? 5?? 5?? 5?? 5?? 5??
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D? D? ?

5?K?5?

104


Kalmar 'ya'yana din kuwa ta daki zuciyar maamah da wani matsanancin kishi. Wato har fu'ad dinma ya tashi daga sunan dan riqo ya koma danta?.

"Aah anni....inata dai qoqari" Ya amsa mata yana fahimtar inda saqonta yasa gaba. Kai ta jijjjiga

"Zan sabawa fu'ad kuwa muddin qafafunsa yasa ya tafi bai sanarwa iyayensa ba.....idan kuma wani keda hannu kan hakan....na rantse da Allah ko waye bazan barshi ba.....tashi kaje,tsakanin yau da gobe nakeso ka lalubomin shi" Kai kawai kada mata yana tashi,maimakon ya koma daki sai ya juya yana sake ficewa a gidan.

Yau din Jordan ya nema kai tsaye,shima ya gaya masa tun randa suka fita tare bai sake ganinsa ba. Ci gaba yayi da bibiyarsa ta waya amma a banza,sai ya koma ya lalubi system dinsa da yakan ajiye schedule nasa da komai. Yasan password nasa da komai don haka kai tsaye ya bude ya shiga. Zallar aminci ne da yarda da kuma dawwamammiyar qauna,shima iya abinda yaje nema ya shiga ya duba kawai ya fito. Bai samu bayanin komai ba,hasalima bai ajiye inda zashi ba banda ranar da sukayi zasu fita din satin baya daya wuce ranar daya bace kenan.

Awa daya ya bawa ransa zai sake kiransa,idan bai sameshi ba kuwa aikin safa da marwa ya sameshi cikin tsibirin Maldives,wala'alla sai yayi hayar boat ko skis ya gewaye tsibirin Maldives ya nemowa anni 'ya'yanta.

"Oops.....wannan soyayya taku nima ta jefani kwale kwale.....where are you?.....anni ke kika jawo,da kin damqa masa matarsa salin alin dani kaina ban tsinciki kaina a halin da nake ciki ba" Ya fada yana furzar da iska daga bakinsa gami da yin relaxing jikin kujera yana lumshe ido. Murmushi ne kuma ya qwace masa saboda hango fuskar maamah da yayi,tayi wani laushi da yaushi ba tare data fahimci hakan ba

"Wato anni kema kinsan takan tsiya?" Ya fada qasan ransa yana komawa ya kwanta sosai saman sofa din.


&Gaba daya ya wani narke saman sofa din bayan ya miqe qafafunsa saman table din gabansa daya dora system dinsa. Tun dazun ya kunna system din amma ya gaza saka mata password ya budeta. Sai yau yakejin ya kamata ko farouq yasan inda yake,don yayi imanin ko kowa bai nemesa ba anni zata nemesa,zata kuma damu da rashin ganinsu.

Gilmawarta kadai a gabansa yana debe hankali daga gangar jikinsa,a kwanakin nan shi kansa yasan mahaukacin so yake mata wanda baisan adadinsa ba. Idan ya kebe yana salla,yana yawan tuhumar kansa wanne irin so yake mata wannana?,abu daya ke sanya masa relief addu'o'in daya debe tsahon rayuwarsa yana yi akan.

"Ya Allah,idan ka tashi dasamin soyayyar wata 'ya mace.....ka jarabceni da soyayyar da zan iya.....ka dasamin soyayyar macen data dace dani ta dace da rayuwar 'ya'yana,macen da zata soni itama sama da yadda nakeson kaina....macen da ni karan kaina takeso ba abinda na mallaka ba.....macen da zata fifitani sama da kowa da komai....tsaftatacciyar mace.....kamila aaqila....aabida,ya Allah,kada ka jarabceni yadda ka jarrabi mahaifina......ubangiji ka azurtani nida dan uwana da matayen da zasu rufe ciwukan da suke cikin zukatanmu kaman yadda kayi mana baiwa da samun anni". Idan ya tuna wannan addu'ar sai yaji son da yakewa sabreen din ba komai bane.....yayi imanin


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login