Showing 213001 words to 216000 words out of 363280 words

Chapter 72 - DUNIYATA BOOK 2 COMPLETE

HUGUMA   

11 Nov 2025

1453

wa ni'imannasir". Da kallo maamah ta bita sanda take takawa tana barin wajen. Ta aje mata shakka sosai cikin ranta,ta sani itadin kuma shaida ce,ba kasafai murmushin yarinyar yake xama alkhairi ba,so amma koma meye wannan karon ta shirya kawar da ita me gaba daya idan ta kama ayi hakan.

Amna ce ta rugo da sassarfarta ta kawo mata runguma,abinda ya kusa sabbaba faduwarsu gaba daya,Allah ya kawoshi ya sanya hannu ya tareta ta fada hannunsa.

"Ki kula" Ya fada adan dake sannan ya maida dubansa ga amna.

"Be soft with her amna" Kai ta gyada a sanyaye kunya tana kamata. Kwanaki ne kadai tayi bata ga adda sabreen din ba,amma sai taga ta canza mata gaba daya. Wani ajiyayyen kyau na musamman,qamshinta da komai nata ya zama wani na daban


*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

5?? 5?? 5?
? 5?? 5?? 5?? 5?? 5??
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D? D? ?

5?K?5?


109



a nutse amna ta riqe mata yatsu,duk da yadda ta fahimci fu'ad din kaman yafi so tabar masa kayansa,to amma itama sabreen ita ta naniqewa,saboda bataso yayi wani abu daban da zai sanyata jin kunya gaban anni. Tayi imani kuma dukka hankali da idanun maamah yana a kansu,nunawa ne kawai ba zatayi ba. Abu guda daya daya tsaye mata a rai,ya gaza barin kwanyarta ta huta duk da yadda takejin jikinta shine dariyar maamah din. Ta gama karantar kowanne taku da motsi na matar......ta kuma sake sallamawa al'amarinta daga labarin fu'ad din. Ta tabbatar ba wata halitta da bazata iya cutarwa ba tunda har ta iya cutar da mijinta da kuma d'anta. Directly or indirectly tana farautar rayuwar 'ya'yanta ne ba tare da tasan hakan ba. A ranta taji dole ta qara takatsantsan da ita fiye da baya,sai taji kaman a baya ma kulawa da kiyayewa al'amuranta da takeyi kaman tayi sakaci,tabbas inda tasan wacece ita har haka......inda tasan wacece ita irin sanin da tayi mata a yanzu lallai ba shakka zata kiyaye komai nata fiye da yadda tayi a baya.

"Hannunki dumi adda.....kaman akwai zazzabi a jikinki" Amna ta fada cikin kulawa dab da zasu qarasa kusa da anni. Kai ta girgizawa amna din tana sanya murmushi saman fuskarta

"Ba wani me yawa bane......zai sauka in sha Allah,karki gayawa anni ki daga hankalinta" Dan jim tayi kaman ba zata amsa ba,don bataga dalilin da mutum baida lafiya ba kuma sannan yace kada a fadi.

Hannu anni ta miqa mata sanda take shirin durqusawa ta gaidata.

"Dawo nan ki zauna" Ta fada qasan ranta wasai da farinciki. Iya yadda taga fu'ad din ya koma a 'yan kwanakin da baya kusa dasu kadai ya bata tabbacin lallai komai yana tafiya daidai,ba fu'ad kawai ba.....hatta sabreen din ta canza mata gaba daya. Fatarta wani glowing kawai takeyi,hakanan idanunta sun qara haske da kuma girma.

Tsananin kunyar anni takeji kaman zata nutse......ko kusa ko alama yadda takejin nauyin anni yana kamata batajin koda kusa da haka akan maamah,bata ce kuma ga dalili ba.

"Sai kuma ka buge da sacemin diya ko?" Anni ta fada tana duban fu'ad daya gaidata. Karon farko shima kunyar anni ta kamashi,tattausan murmushin nan nasa da anni ta jima bata gani ba ya subuce masa,yasa hannunsa ya shafi baqa sidik din sumarsa da kudin da take lasa yayi jarin mutane da yawa.

Matsawa amna kadan tayi kusa da anni tana rada mata sabreen din zazzabi takeyi. A nutse amna ta dubi fu'ad

"Me ya samu ameenatu?" Fararen idanunsa ya sauke kan fuskar sabreen din sannan ya dubi anni.

"Dan zazzabi ne dazu da zamu fito ya sauko mata......nace ma muje ta karba magana but ta dage wai zatayi managing" Kai anni tadan kada kadan.

"Manage da ciwo?......to Allah ya sawwaqe,idan muka sauka dubai bai tsaya ba sai taga likita,ba kyau zama da ciwo ai"

"Ameen" Ya amsa yana satar kallon sabreen din. Jinsu kawai takeyi,amma wani sabon amanne suketa kokawa dashi.

"Bani ruwa amna" Ta fada a hankali tana tunanin idan tasha ruwan zai fada mata. Motsin bakinta kadai ya kalla ya fahimci me tace,ya matso a hankali bayan ya karbi gorar ruwan hannun jordan dake nesa kadan dasu,ya bude mata ya tako inda take yana tsugunnawa saman qafafunsa yakai robar bakinta.

Tsam maamah ta dauke idanunta tana kullesu gaba daya,qirjinta na sake bugawa sosai tana jin kaman haki yanason kamata. Zazzabi?.....wanne irin zazzabi bayan ba'a Nigeria ake ba ballantana ace malaria ce?,wannan tsugonnan bata ruwan......ko ita da take uwarsa ba zata iya tuna ranar daya tsugunna haka gabanta yana bata ruwa ba......lallai dole ta batar da yarinyar nan bat daga duniya.

Kai ta girgiza masa alamun xata iya sannan ta karba da kanta. Kurba uku tayi taji kaman ya isheta,sai ta miqa masa robar.

"Is okay?" Ya fada yana motsa labbansa a nutse idanunshi a kanta kaman me tsoron kada ta bace masa. Kai ta gyada a kunyace tana saka kanta cikin mayafinta,bataso batason wannan kallon,halakata yakeyi gaba daya.

"Kai Muhammadu" Maamah data gaza jurewa ta qwala masa kira,tana jin ya kamata ko yaya tayi wani abu da zata shiga lamarin ciwon don samun report da zai bata daman aiwatar da duk abinda ya dace da gaggawa.

Tsam ya miqe yana amsa mata,sannan ya fara takawa gabanta sanda farouq ya iso yana gaya musu lokacin tashinsu yayi.

"Sakamin takalma na......bazan iya durquso ba" Ta fadi tana qoqarin saisaita fushinta. Baice komai ba ya tsugunna gabanta yana tura mata takalman,ta fara saka qafafunta a ciki qirjinta a quntace.

"Ita matar taka me ya sameta da ni bani da mutuncin sanin komai saidai naji daga bakin bare?". Daidai sanda ta gama zura takalman sai ya zare hannuwansa yana shirin miqewa.

" Zazzabi ne kawai......shima din dazu ne yazo bawai a kwance take ba".

"Zazzabi?,tana iya cin abinci?" Kai ya gyada mata a nutse don baisan me zaice mata ba,ita sabreen idan ya sakata sahun masu cin abinci ma ya zalunci sakamakon da zai gayawa.me bincike.

"Akwai tashin zuciya?" Ta sake tambaya cikin bin qwaqwafi da son tabbatar da zarginta. Kai ta girgiza mata alamun a'ah.

"Ciwon mara ko ciwon ciki fa?" Ta sake tambaya tana kafeshi da idanunta. Kansa ya mayar gefe kafin ya dawo da dubansa kanta.

"Ban sani ba maamah.... Duka duka zazzabin na awa daya ne".

" Eh dama da irin sakacinnan naku sai ciki ya shiga ya fice abinsa ma baku sani ba......banason ganganci da rayuwa shi yasa nake tambaya,dama wani aikin ai sai uwa ita data damu da rayuwar 'ya'yanta damuwa ta haqiqa.......tana yin amai ne?" Tambayarta ta qarshe da yaji yakai bango,hannuwansa suna zube a aljihun wandonsa sai kawai ya zubewa maamah kallonsa. Karon farko kenan tun bayan shudewar shekaru ashirin kusan da hudu rabon daya kalleta tsakiyar qwayar ido irin haka. Komai daya danganceta yaji yana dawo masa.......gaba daya tambayoyin nan nata basu zama komai ba face suna sake bude masa wani abu da yake zargi a kanta.

Duk yadda ake maganar kwarjininsa bata taba yarda da gaske yana da wani irin kebantaccen kwarjini ba sai yau. Idanunsa sukayi mata wani irin nauyi,sai taji tana daburcewa.

"To Allah ya kawo sauqi,sai a bincika ai aji meye,ko tsohuwar malaria ce" Ta fada tana miqewa tsaye,wanda hakan bai sakashi dauke kallonsa ba a kanta,har sai da yaji muryar farouq

"Dude....." Waiwayawa yayi yana dubansa,sai ya nuna masa agogon dake daure a tsintsiyar hannunsa,wannan shine ya ceci maamah daga irin kallon nasa ya juya yana nufar farouq din.

"Wai......ka jini da yaro?,haka yakewa mutane?......muje zuwa,na rantse har da Allah muddin abinda nake zargi ya tabbata ga yarinyar nan bazan taba aminta na hada jini da ita ba......muddin wani me rai ne a jikinta ni mariyatu bazan bari ya taka duniya ba" Ta fadi tana cike da fatan ya zamana ma ba abinda take tunani bane.

Amna najin takunsa a bayansu ta zame hannunta daga na sabreen din ta qara sauri zuwa gaba ta cimma anni abinta suka jera tare. Matsowa yayi yana daidaita tafiyarta da tashi,ba zato y dauki hannunsa ya aza saman kafadarta yana jawota zuwa jikinsa.

"Kinga yadda kike tafiya kuwa?,you need my support......dont reject it" Ya qarasa fada yana furzar da iska.

"Inajin body temperature dinki kaman yana hawa......you need medical care........banaso komai ya tabaki duniyata" Ya fadi yana waiwayawa ya dora mata qwayoyin idanunsa. Nauyin nan dai taji,sai tadan basar tana dauke kanta gefe

"Zafin kaman na dazu ne,bai wani qaru ba" Ta fadi saboda batason yace zaa kaita asibiti. Idan tayi ciwo a Maldives ba zata damu ba......amma ciwo tsakanin makka da madina bata son hakan ta kasance,saboda qashene da take da burin xuwa a rayuwarta kafin ta koma ga mahaliccinta.....qasa ce da ta tara tarin shigifar addu'o'i take kuma kuma son tayi bajakolinsu a nan.....ba zataso wani abu ya kawo.mata tsaiko ba. Tana da tarin buqatun da batasan adadinsu ba,batasan kuma kwanaki nawa zata shafe kafin ta gama jerosu ba.

Ba idanun wanda sukayi masa nauyi,a haka suka jera suna taka steps na jirgin har suka isa ciki. Suna shiga din matuqin jirgin yayi salute nashi sannna ya bashi hannu sukayi musabaha ya buqaci magana dashi,wannan ya sanya ta zame jikinta suka jera da amna suna wucewa ciki don samun seat din zama.

Tuni maamah ta yiwa kanta mazauni a executive suit,a nata zaton shine guri na qarshe da yafi kowanne tsari,batasan sam da VIP suit ba,wanda wada dama mazauni ne na fu'ad din shi kadai,saidai idan yaso wani ya shigo ya zauna.

A Aminitiy anni tayi zamanta,zaman jirgi ba baqonta bane,amna ma a nan ta zauna sai sabreen ta zauna kusa da ita suna taba hira abinsu,saidai komai ya tsaye mata a wuya,hatta ruwan da tasha.

Yana takowa ta tsakaninsu xai wuce VIP suit zazzafan aman ya taso mata,ta saka hannu da nufin tareshi ta miqe da saurin don wucewa lavatory.......saidai inaaa,wani karo da tayi da fu'ad din take aman ya qarasa fitowa ta kuma soma kwararashi tun daga qirjinsa saman lafiyayyar suit dinsa har saman qafafunsa. Ba wannan bane damuwarsa.......yadda take kakarin amai duk jikinta yana kyarma shi yafi daga hankalinta,ya bita da sauri a rude yana fadin.

"Subhanallah......ya salam......sannu.....am sorry" Kaman zai sake mata kuka. Yadda ya kanainaye abarsa su anni sai baya suka tsaya suns jera mata sannu tana ci gaba da yunquri kaman zata fidda kayan cikinta.

Kafin ta gama kanta ya fara sarawa da wani irin ciwo,zazzabi jikinta kuma ya sake ninkuwa akan nada.

Shi ya karbi ruwan daga hannun daya daga cikin crew din ya bata tasha saboda yadda take haki,ya saka hannu ya dagata suka wuce lavatory.

Da idanu take binsa kawai sanda yake qoqarin gyara mata jikinta ba tare da ya damu da qazantar data zuba masa a nasa jikin ba. Idanunta ta lumshe a hankali a kansa sanyi yana ratsa gabbanta. Ta dauka zaiyi mata fada,ko zai nuna fushi saman fuskarsa,ko yayita hargagi idan ta kama ya tureta ma,amma sai taga sabanin hakan. Gaba daya ya bata attention dinsa,tanaji anni na cewa amna ta biyosu ko xata tayashi da wani abun yace "no need.....zauna kawai".

Wani irin abu taji yana ratsata a kanshi,ta zuba masa ido sosai sanda yake goge mata saman qafafunta da takalminta daya dan baci,saita miqa hannu ta zaro napkins dake ajiye a lavatory din ta tsugunna a gabansa tana daidaita tsahonsu. A nutse ya dago suka hada idanu,fararen zagayyun idanuwansa sun qara haske wanda suke sauya launi nan da nan da wani abun ya taba zuciyarsa,sai ta langabe sannan a nutse ya dora napkin din saman qirjinsa tana cewa.

"Am sorry" Ta furta a hankali. Labbanta yabi da kallo yana jin suna qara burgeshi,murmushi ya subuce masa wanda ya sake qara fidda kyansa,hannuwansa duka ya saka ya daga kafadunta suka miqe tsaye,idanunta yake kalla

"Sorry for what?" Shima ya tambayeta muryarsa can qasan maqoshi. Idonta ta janye tana nuna qirjinsa da yatsarta,sai shima ya maida dubansa wajen. Murmushi ya kuma saki,ya kamata yana jinginata da jikin mirror din gurin,sannan yaja da baya ya soma balle button din suit din farkon,ya xareta ya ajiyeta a gefe,ya sake balle button din ta biyun itama ya ajiyeta a gefe,sai ga shirt din cikin ta ukun ta fito fes ba abinda ya tabata. Idonsa ya sake dagowa ya kalleta sannna ya daga mata kafadunsa gami da watsa hannuwa alamun ba abinda ya sameshi. Murmushi ta saki itama abinda ya kusa narkar dashi kenan,fararen jerarrun haqoranta sun fito reras tamkar adon lu'ulu'u,har qasan ranta taji dadi da dayar rigar bata baci ba,ya sunkuya a nutse ya zare takalman qafarsa sai socks kawai daya rage,sai ya miqa hannu ya kama hannuwanta,a hankali yace

"Kinga abinda nake gudu ko?,zazzabin nan ya dawo sosai".

" Ba matsala......zai"

"Da matsala mana......bakisan yanzun nan sai na rasa nutsuwata ba saboda wannan zazzabin?" Ya tambayeta da dukka idanuwansa a kanta suna kuma karanta gaskiyar abinda yake fadi daga qasan zuciyarsa ne. Wani abu na daban takeji,wai yau ita ake damuwa da ciwonta?,matar da saidai ta damu da ciwon wasu amma nata ciwon dai damuwar qannenta ne kurum?.

A nutse ya riqe mata hannu suna takowa har xuwa bakin wani dan box,yasa hannu ya danna ya budeshi,saiga loafers masu kyau ya ciro ya saka a qafarsa sannan ya kalleta



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

5?? 5?? 5?
? 5?? 5?? 5?? 5?? 5??
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D? D? ?

5?K?5?


110


"Zan iya daukarki mu qarasa?" Kai ta girgiza masa da sauri,sai ya dauke kai bai sake cewa komai ba.

Qafafunta takejin kamar ba zasu iya daukarta ba sanda daya daga cikin crew din ke gyaran wajen aman haka taja jiki tana komawa gurin ta. Xarginta yana sake qarfi da kowanne motsi na yarinyar,amma jikinta da zuciyarta sunqi aminta da cewa coki zai iya kasancewa a jikinta. Ita ta kawo yarinyar rayuwarsa kuma har yanxu bata manta da fafatawar da akayi dashi kafin ya karbeta ba......to mene haka yayi sautin sauya masa ra'ayi game da yarinyar idan ba sihiri bane?. Wannan abun yafi qarfin bariki......ta samu kalar kulawa da damuwar da ko amernatun bata sameta ba. Har yanzunda take zaune idanunta suna iya gane mata yadda hankalinsa yayi mugun tashi da aman da takeyi din,baya jin kunyar kowa dake tsaye a wajen,kamarma ya manta da wanxuwar kowa a wajen saishi da ita kawai....dole ta lalubo musabbabin ciwon nan da dukka iyawarta,musaddiq ne kawai kuma zatabi ta kanshi ta samu information din da takeso hankali kwance.

Tayita zuba idanu ta gansu ta inda su anni ko maamah suke amma sai tsintar kanta tayi a VIP suit. Ta yita maimaita sunan bayan ganin wajen,wajen yaci sunansa dari bisa dari,zama rantse da Allah ba cikin jirgi kake ba,don ko windows sai ka danne wani abu sannan zai yaye maka su. Akwai mini bed da sofas masu tsananin kyau da taushi a gurin,tamkar kana cikin wani qawataccen madaidaicin parlor maras tarkace da hayaniya,harda office area da aka yiwa gurin daya ajiye tarkacen kayan aikinsa kamansu system dinsa da wasu documents nashi.

Gadon yaso tayi kwanciyarta amma taqi,sai ya ajiyeta saman recliner,ya jawo foot setter din dake qasanta ya dora mata qafanta akai sannan ya lullubeta da wani sky blue din blanket sannan ya juya a hankali yana fita a wajen ta wata qaramar qofa.

Numfashi taja sosai tana saukewa,tana yawo da qwayar idanunta cikin wajen. Wani nutsatsen guri ne da yaci sunan VIP suit din,daga ita saishi a wajen,guri ne da idan kana nan bazakasan meye yake faruwa cikin jirgin bama. Tabbas duniya girma gareta kuma fadi gareta,sannan ta sake yarda ta sallama kuma rayuwa mataki!mataki ce. Daga shigarta family din jadda taga abubuwa masu yawan gaske da idan a baya akace mata akwaisu a duniya hankalinta bazai dauka ba,da gaske ne kudi ba wasa bane.....arziqi kuma ba qarya bane......kudi nada wani irin power......suna mallakawa mutum girma da fadin ikon da baisan iyakarsu ba. Wani lokacin idan ta kalleshi sai ta dinga jin yafi qarfinta nesa ba kusa ba......ya kuma tserewa ajinta.....wani lokacin saita dinga jin kokwanto da shakkar sake masa dukka gaba daya.....kada a gaba ya samu dukkan komai ya kuma zame ya barta tunda tabbas ita ba ajinsa bace,saidai kuma wucewar kowacce daqiqa da second yana sake bata dukkan wani dalili na soyayyar gaskiya a aikace ba wai a baki ba. Maida idonta tayi ta rufe tanajin yadda zazzabin ke ratsa qasusuwanta,gefe guda kuma tana jin irin tababar da akeyi tsakanin bangarorin zuciyarta dukka akan MUHAMMAD FU'AD JADDA.

Motsinsa taji kafin taji sautin nutsatstsiyar muryar nan tasa da sautari takan mata gizo.

"I'd appreciate it if everyone could stay where they are,am looking for some peace and quite,i need some


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login