Showing 228001 words to 231000 words out of 363280 words

Chapter 77 - DUNIYATA BOOK 2 COMPLETE

HUGUMA   

11 Nov 2025

6482

cikin salon tsokana don yadan bata wani nutsuw??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????ar zuciya.

Harara ta jefa masa tana dan murmushi kadan kafin ta amsa masa

"Kafi kowa sanin ameenatu ba raguwa bace.....ameenatu ba matsoraciya bace.....fitina ce kawai ameenatu bataso,ita din me son nutsuwa da kwanciyar hankali ce".

"Na shaida hakan" Ya fada yana murmushi sannan ya sakar mata hannunta.

Miqewa tayi tana cewa

"Muje na dubata.....saika samu kadan zauna da ita,ka kwantar mata da hankali ka fahimtar da ita har ta samu nutsuwa". Murmushi kawai ya saki yana zube hannayensa a aljuhun rigarsa. Anni tana wasu abubuwan kamar batasan halin maamah din ba,kamar ita din baquwa ce a dabi'unta.

A zaune suka sameta saman gadon,har sun zare ruwa da alluran da suka saka mata. Ga oxygen din da suka cire mata a gefe. Dakin shuru,banda qarar ac bakajin komai,musaddiq da saddiq na zaune saman kujera suna zaman kurame su da ita.

Kallo daya tayi musu shida annin ta dauke kanta daga sashensu,don ci gaba da kallon nasu bazai iya Haifa musu da me ido ba,hasali ma jarumtar da take jin zatayi tsaf zata iya kwaranyewa tayi nata wajen.

Shigowarsu ya sanya musaddiq da saddiq ficewa,don dama shikam musaddiq zaman ya gundureshi,hanya kawai yake nema.

"Ya jikin?,Allah ya sawwaqe ya qara afuwa" Ido maamah kawai ta runtse,batason jin sautin muryar anni sam sam. A halin da takeso ta ganta kenan,ta kuma ganta,saidai tana bawa kanta da kanta tabbacin wannan shine gani na qarshe da zatayi mata a haka,next time lallai zai zamana annin ce kwance saman gadon asibiti kamar haka......wannan alwashin saita cikashi koda numfashinta zai qare.

Juyawa anni tayi ya fita tana basu waje,ya matso gabanta kadan yana mata sannu da jiki. Idanu kawai ta zuba masa na wasu sakanni,sannan a hankali ta bude bakinta.

"Ci gaba da qirqirar sabbin kurakurai suma kuskure ne.......yayin gyaran kuskuren kuma komai yana iya faruwa da kowa ma......kasa a maidani gida.....jibi nakeso na koma nigeria" Iya abinda ta fada kenan tana yunqurin sauka daga saman gadon. Baice mata komai ba ya bita da kallo,saidai kowacce kalma data fita a bakinta ya rubutata tsaf ya ajiyeta,ya juya ya taka a hankali yana fita a dakin don cika umarninta.

Tsaye sukayi a farfajiyar asibitin sanda motar da jordan ke tuqawa da maamah din a ciki tana barin cikin asibitin. Musaddiq ya motsa don komawa ciki bayan bacewa ganinsu da motar tayi.

Caraf fu'ad ya damqo hannunsa,musaddiq ya waiwayo da sauri yana duban idanun fu'ad din. Ko sau daya bai kalleshi ba,yaci gaba da riqe hannunsa yana takawa dashi a hankali har zuwa gaban motarsa,yana isa abdulgafar ya bude masa ya tura musaddiq ciki sannan shima ya shige abdulgafar ya rufesu.



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

5?? 5?? 5?
? 5?? 5?? 5?? 5?? 5??
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D? D? ?

5?K?5? ______________________________
_kin dade kina cizon yatsa kan yadda ake kacalcala suturun yaranki da dinkuna marasa ma'ana?_

_HUGUMA na miki albishir da wajen zazzafan dinki na MS KIDDIES WEARS,irin dinkunan yaran da kike gani a Instagram TikTok suna burgeki kuma bakisan inda zakikai ayi miki ba ko kina tsoron tsada_

_Zafafan dinki na gayu da ado kiga yaranki sun fita dagwas dagwas_
_ready

_MS KIDDIES na nan kano gwammaja_

*TRUSTED AND TRUSTED mun gwada mun gani*

_Maza tuntubeta a nan_

+234 708 865 2858

Ko Instagram account dinta

https://www.instagram.com/ms_kiddies_wers_by_nafs?igsh=MTljZWQwM2FsaXlxaA==
____________________________


116


Wadannan tsumammun idanun nasa da ya saba hukuntashi dasu tun yana qanqaninsa ya zuba masa. Wani irin kallon qurilla me dauke da tarin ma'anoni da suka sanya jikin musaddiq yin sanyi tun kafin fu'ad yace komai.

"Wanne irin tsoro nake gani cikin idanunka musaddiq?" Fu'ad ya jefa masa tambayar yana nuna qwayoyin idnunsa da yatsunsa. Tambayar tadan daburtashi,har ya rasa me zaice masa.

"Ashe kai maqaryacin masoyi ne?......bakason soyayya batason ragwantaka ba?,bakasan mata basason ragon namiji ba?,bakasan soyayyarka bata cika soyayya ba sai ka amince zaka iya fuskantar dukkan wani qalubale da hatsari akan masoyiyarka ba?,bakasan soyayya bata amsa sunanta ba sai ta samu sadaukarwa tsananin kulawa da jure duk wani tsanani ba?........you're very stupid musaddiq muddin baka xama tsayayyen namiji ba akan amna......na aura maka amna don ubanka saboda ka kula mana da ita.......ban tsaya a matsayin waliyyinka ba saboda amna ta samu wani uban bayan abba.....ni waliyyin amna ne da bazan lamunci duk wani rashin kulawa daga gareka ba a kanta......ka riqe musu yarinya da kyau.......ka xama jarumi a kanta koda kai rago ne.......wallahi wallahi bazan daga maka qafa ba idan har naga ko naji wani abu mara kyau dangane da ita a kanka ba......yiwa auren amna riqon wasa ko ka bari tsoronka ya jagoranci igiyar aurenta dake hannunka.....to kasa a ranka baka taba sanin wani me sunan muhammad jadda ba".

Gaba daya jikin musaddiq yayi laushi tubus......yana tsananin qaunar amna,irin qaunar da bai taba yiwa kowa irinta ba,to amma kuma tsoron fitinar maamah yana neman dakushe masa komai,duk da yaji cikin ransa ruwa da iska.....ko zaa saka kanshi gabas a yanka bazai iya rabuwa da auren amna ba.

Qofa yasa aka bude masa ya nuna masa hanya,musaddiq ya kalli fu'ad din sai ya sauka salin alin daga motar,yasan ba lallai a yanzu ya wani bawa ban haqurinsa muhimmanci ba.

Abu guda daya tak daya tuna yaji ya kwaranye masa duk wani bacin ransa.....cikinsa dake kwance cikin mararta wanda ita kanta batasan dashi ba,murmushi ya subuce masa ya sauka a hankali daga cikin motar yana komawa asibitin.

A hankali ya tura qofar falon yana shiga,idanunsa suka fada kan anni. Tana tsaye da takarda a hannunta tana dubawa,shigowar tasa ya sakata daga kai ta kalleshi.

Wani kwantaccen farinciki me ban mamaki ya gani saman fuskarta wanda bai taba ganin irinsa ba. Ya zare idonsa yana duban takardar sosai. Takardar dazu ce da maamah ta saki,take ya fahimci dalilin wannan murmushin,kawai sai ya shafa sumar kansa,karon farko yaji kunyar annin ta saukar masa,ya taka da dan hanxari yana wucewa cikin dakin.

Sosai murmushi ya subuce mata,ta saki sassanyan ajiyar zuciya tana jin zuciyarta na wankewa daga dukkan wata fargaba da bacin rai.

"Ubangiji ka rabasu lafiya,ka yiwa abinda aka samu albarka" Ta furta a sarari tana ninke takardar.

Wani sanyi ne yaji yana ratsa zuciyarsa sanda yayi ido hudu da ita. Tana zaune tsakiyarsu huda......haneefa tana gefanta a zaune hannunta cikin nata. Hira sukeyi irin hirar da kana kallon fuskarsu zakasan qauna da soyayya gami da shaquwa irinta 'yan uwantaka ta huda su. Murmushi ne kawai ke fita a fuskarta,wani irin murmushi da yake sake qawata fuskarta da wani irin lallausan kyau me daukan hankali.

Jingina jikinsa kawai yayi da jikin qofar,ya langabar da kansa yana qare mata kallo. Kallo yake mata irin kallon da mutum yakewa DUNIYARSA a sanda tayi masa dadi.....irin kallon da mutum yakewa ruhinsa a sanda yake tsananin buqatarsa da kuma sonshi. Duniyarsa rayuwarsa dama nutsuwarsa gaba daya yake gani tattare da ita.

Daren jiya yake tunawa,wani irin dare me tsayawa a tsakiyar zuciyar masoyi,ta shayar dashi wani zazzaqan abu da bai taba hasashe ko mafarkin akwai irinsa ba sai a lokacin.

Cikin jikinta ta dinga jin kamar akwai wani ido na musamman dake kallonta. A hankali tayi slow da hirar tana watsa idanunta cikin dakin,sannu a hankali ta hango fuskarsa a tsakiyar qofar yana qare mata kallo. Murmushi ya sakar mata wanda ya qara mata nauyinsa,sai ta danyi qasa da kanta,shi kuma ya tura qofar gaba daya yana shigowa.

Tsam momma ta miqe tana fadin

"Qaraso mana......dama masallaci nakeso mu wuce ai,ita ta riqemu wai lallai zamu barta ita kadai,tunda gaka kazo alhamdulillah" Momma ta fada cikin yanayi na surukuta tana maida takalmanta.

A nutse ya qarasa gaban gadon ya bawa haneefa dake zamowa tana sauka daga saman gadon hannu fuskarsa qunshe da murmushi yayi bump din hannunta data miqa masa yana kuma amsa gaisuwar huda da basu hadu da ita dazu ba

"Muna da meeting anjima" Ya fada yana dubansu,sai suka sanya dariya suna bin bayan momma bayan sun amsa masa da

"Yes hamma". Shi da ita duka da kallo suka bisu har suka fice,shine ya fara dawo da dubansa kanta kafin itama a hankali ta maida duban nata kanshi.

"Karki ma fara cewa zaki tambayeni akan mene" Ya rigata fadi,sai murmushi ya qwace mata tayi qasa da kanta.

Idonsa ya lumshe a kanta sannan ya taka a nutse ya jawo kujera zuwa gaban gadonta. A hankali ya zauna yana sake matsowa kusa da ita har gwiwoyonsu na gogar na juna,ya saka lausasan tafukan hannayensa a nutse ya kamo nata cikin nasa yana murzawa a nutse.

"Ameenatu" Ya kirata a tausashe murya a karye kaman wanda baison kowa yaji sirrinsu. Kiran da yayi mata har cikin tsokar naman jikinta,ya kuma aike mata da saqo ta cikin jinin dake gudu a jijiyoyin jikinta. Labbanta ta motsa kadan tana amsa masa da
"Na'am" Sai ya lumshe idonsa labban nata suna daukan hankalinsa.

"Ina dauke da wani albishir ameenatu,yayi girma da nauyi sosai a qirjina" Ya qarasa fada yana zame hannunsa daga cikin nata,sannan ya maida kansa ya kwantar saman cinyoyinta kamar wani qaramin yaro.

A hankali ta daga hannunta ta dora saman sumarsa tana nutsa yatsunta a ciki,laushin sumar da santsinta suka ratsa yatsun nata,sai suka sauke ajiyar zuciya lokaci guda shi da ita kowa yana jin soyayyar dan uwansa tana keta jininsa.

"Ameenatu wannan zuciyar da wannan gangar jikin duka naki ne.....kulawarki take buqata kici gaba da bata muddin kinaso ta rayu yadda ya dace" Ya fada yana jin yadda bugun zuciyarsa ke daduwa daga yadda take yamutsa sumar kansa kawai.

"Zaka samu sabreen fiye da yadda kake fata.....zaka samu dukkan wani cikar burikanka a tattare da ita.....harma abinda tunani bai taba baka ba". Maganarta ta tsumashi sosai,ta kuma sakashi daga kanshi daga cinyarta. Idanu ya zuba mata sosai yana kallon qwayar idanunta,sai itama ta samu kanta da mannewa kallon nasa,kafin ya miqe a hankali tsaye a gabanta.

Hannuwansa ya miqa mata,sai itama ta aza nata ciki ya tashe tsaye sannan ya buda qirjinsa ya sanyata a ciki ya maida hannuwansa ya lullubeta da kyau.

Ajiyar zuciya ce ta subuce masa,ya kwantar da kansa saman kafadarta.

"Sabrrrrr........kinsan kin bani wata kyauta da ba wani dan adam daya taba bani makamanciyarta?" Ya soma da jefa mata tambayar data kasa gane ma'anarta. Shurunta ya fahimtar dashi cewa ya sanyata a duhu,don haka ya zare jikinsa a hankali sannan ya juyata ya rungumeta ta baya yana sake nutsata sosai cikin jikinsa. A tausashe ya dora duka tafin hannunsa saman mararta,ya dora habarsa saman kafadarta yana saka tausasan labbansa saitin kunnenta.

"Sabrrrrr......you're pregnant......ciki ne dake,cikin muhammad jadda......zaki zama uwar 'ya'yana ameenatu". Wani irin abu ne ya tsarga mata tun daga tsakiyar kwanyarta har tafin qafarta,bugun zuciyarta ya qaru sosai. Samun kanta tayi da saka nata tafin hannun saman nasa dake mararta tun dazun,ta kasa fadin komai,don duk kalmar data kamo sai taji ta qwace mata,tana ci gaba da sauraren saukar numfashinsa cikin kunnenta.

"Are you happy sabrrrrr?" Ya tambayeta a raunane yana fatan ya sameta cikin irin yanayin da yake jin kansa shima.

Kai ta gyada a sanyaye,tanajin wani irin yanayi yana ratsata,mamakin yau itace wai dauke da ciki?,itama zata zama UWA?,zata haifi d'a ko 'ya a cikinta?,abun kamar cikin mafarki.

"Alhmdlh" Ya fadi yana sauke mata tattausan kiss a wuyanta,a hankali kumya ja dawo da ita tana facing dinsa sai ya rungumeta tsam a jikinsa.

Shuru ya ratsa tsakaninsu na sakanni,tana jin yadda zuciyarsa ke bugawa ta cikin kunnuwanta dame kwance a qirjinsa,sosai kaman akwai wani abu dake taba zaman lafiyarta,kusan minti biyu sannan ya sauke sassauqar ajiyar zuciya a sanyaye sannan ya dagata daga jikin nasa yana kallon fuskarta. Qwayar idanunta ya laluba ya saka nashi a ciki,da wani irin coolness ya sake kiran sunanta.

"Kinji yadda zuciyata take bugawa ko?" Ya jefa mata tambayar yana lalubar tafin hannunta ya matse gam cikin nasa. Kasa amsa masa tayi da baki sai kai data gyada mass,saboda cikin idanunsa abubuwa ne masu yawa ta gani suna yawo.

"Sabrrrr.....na gode da kika karbi ajiyata da sauri haka......inajina kaman ni kadai nake rayuwa cikin duniya......ashe rashin haduwa da tawa DUNIYAR shine sila......sabrrrr......bansan dame zan saka miki ba......bansan kuma da meye zan gode miki ba....kome na kalla sai naga kamar yayi kadan,alfarma daya kawai nakeso ki yiwa rayuwata.

Kallonsa da kalamansa gaba daya qara kashe mata jiki sukeyi,mamakin irin tsananin son da yakewa yara ne yake sake kamata,ta motsa labbanta a hankali

"Tame?"

"Kiyimin alqawari zaki rayu dani....kiyimin alqawari ba zaki taba rabuwa dani ba.....kiyimin alqawari zaki zauna dani,da dadi ko babu.....cikin wadata ko talauci.....sabrrrr kiyimin alqawari ba zaki taba tafiya ki barni da yara ba.....zaki zauna dani dasu a duk yadda nake ko suke,mu rainesu tare.......kiyimin wannan alqawarin sabrrrr cikin wannan garin me tsarki". Idan ba qarya idanunta sukayi mata ba hawaye ne kwance cikin idanun muhammad jadda din......taja numfashi sosai har kaman kayan cikinta zasu hade waje daya. Ita daya ce mutum na farko a duniya data taba ganin wadannan tsadaddun hawayen da suke zuba SILAR QAUNA daga idanun me jadda......tana fata ta zama mutum.na qarshe da zata gansu,kuma ta zama sila na goge hawayen daga idanunsa gogewa ta har abada.

Abu daya ta lura dashi har yanzu yana da tsoro game da halin mata......har yanzu wannan ciwon da maamah ta dasawa rayuwarsu yana masa zugi da radadi.....har yanzu yana jin kaman abinda ya faru da abbansu zai faru dadshi,a yanzu haka a shirye take ta goge masa dukkanin wannan fargabar da shakkun,don haka ta zame hannuwanta daga nashi,ta sulale tana duqawa saman gwiwoyinta,sai ya gaza tsaiwa ya silale shima ya bita.

Hannuwansa ta riqe da kyau tana kallonsa cikin tsakiyar idanunsa.

"Allah ya zama shaida.....annabin Allah ya zama shaida,ni ameenatu sabreen na shirya rayuwa dakai da dukka abinda zamu haifa......na sadaukar maka da dukka rayuwata sadaukarwa ta har abada......dadi ko wuya sunyi kadan su raba tsakaninmu.....zan zauna dakai tamkar dominka kadai aka halicceni,bazan barka ba muddin bakai ka buqaci hakan......". Ai bai iya barinta ta qarasa fada ba ya hade bakinsu guri guda.

Sai daya tabbatar ya kwashe ragowar maganar tass daga bakinta sannan ya zare bakinsa daga nata yana kallonta da birkitattun idanunsa.

"Ta yaya zan iya rayuwa ba'a duniyata ba?.......ta yaya dan adam zai rayu babu duniyarsa?,indai babu ta yadda hakan zata kasance....to ki sanya a ranki ni Muhammad jadda don ke kadai MAAMAH ta haifeni". Batasan sanda ta zube saman kafadarsa ba tana jin wani irin alfahari yana ratsata,tana jin tabbaci da yaqini suna ratsata.....ashe akwai sauran maza irin muhammad jadda din?.



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
5?? 5?? 5?
? 5?? 5?? 5?? 5?? 5??
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D? D? ?

5?K?5?

117


Guri kawai ta samu ta zauna cikin dakin daya kasance ita daya ce qwallin qwal a ciki. Duk yadda taso ta cinye ta kuma jure ta kasa,bata ankara ba kawai taji ta fashe da kuka.

Ta yaya haka zata kasance?,bata tsira da komai ba sai hawan jini?. Wanne irin kafaffen yaro ta haifa?.....aure tsakanin musaddiq da amna?,wacce irin asara ke bibiyarta har haka?,da gaske kamam yadda boka ya gaya mata taurarin nasararta ke bacewa?,taurarin nasararta ke dakushewa?,ina dukka kaifin hankalinta da zallar iya takunta suka tafi?(ta mance cewa shi Allah gwanin hikima ne,yana iya yiwa bawa talala,yayi shekaru aru aru yana zalinci,a nasa hangen da tunanin nasara ce,sai Allah ya barshi da wayonsa da tunaninsa,ya turo.masa nasara a gabansa,plan dinsa yayita tafiya daidai,kwatsam idan yaso kamashi zai da damqeshi a tsakiyar wannan plan din da shirin nasa da yake tunanin sune mafita a gareshi,sai ya zurma yayita bundum bundum. Idan yana da rabo sai ya gane zunubansa da kuma kusakurensa yayi gaggawar tuba....idan baida rabo kuwa,zaiyita ganin INA DA SAURAN DAMA,INA DA SAURAN LOKACI yana tsaka da wannan lissafin sai ubangiji yayi ram dashi,dauri gaba dauri baya,me kwanceshi kuma sai ubangijin daya qulle abinsa. Duk runtsi.....duk tsanani,duk yadda za'a je a dawo karka yadda ka cuci kowa,daka cuci kowa gwara kowa din ya


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login