Showing 210001 words to 213000 words out of 363280 words

Chapter 71 - DUNIYATA BOOK 2 COMPLETE

HUGUMA   

11 Nov 2025

6463

sumarta. Wani dadi ne ya kusa sumar dashi,duk da qoqarin boye masa ruwan sumar nata da takeyi amma tuni shi ya gama fahimtar inda karatun ya sanya gaba. Lallai tarkonsa yayi kamu......tarkonsa ya kama kurciya. Yanason tabbatarwa da gaske fushi tayi don ya barta saman hanya?,don haka ya qara taku biyu gaba zuwa inda take yana kuma sake ambatar sunanta.

"Sabrrrr" Idanunta ta sake lumshewa gami da budesu,saidai har yanxun dai bata motsa ba bare ta amsa masa.

"My world" Ya sake kiranta yana qara rage tazarar dake tsananin su har yanxun yana leqen fuskarta.

"Duniyata" Ya fada da wani coolness daidai sanda ya isa bayanta ya kama qugunta ya riqe yana mannata da jikinsa.

Duk wata tsiga ta jikinta sai daya tasheta da iya haka kawai,to amma duk da taji haka hakan baxai sanyata saurin bada kanta ba,don haka ta hada qarfinta duka tana qoqarin turashi gami da cewa.

"I need to get dressed"

"No....you don't" Ya amsa mata yana juyo da ita gaba daya suna facing din juna,sannan ya juyata zuwa yana hadata da bango gami da ajiye mata wani zazzafan kiss.

Ta fahimci so yake kawai ya birkitata ya sake tafiyanshi kaman daxu,itakam wani irin sanyi takeji yana ratsa mata qasusuwanta da kyau kaman ana hura mata ac.

"Am cold" Ta fada tana sasssuta muryarta saboda yadda yake qara kashe mata jiki.

"I'll keep you warm" Ya bata amsa muryarsa can qasan maqoshinsa,a zafafe ya soma aje mata kisses masu dimauta nutsuwa.

Kamo hankalinta tayi da qyar tana kauda fuskarta,jikinta nema yake ya fara shaking,matakin da tasan indai takai ba zata iya qwatar kanta ba.

"Am not wearing anything under this towel" Da bugaggun idanunsa ya saki murmushi yana dafe bangon da dukka hannayensa

"I know" Ya fadi yana daga girarsa sama. Sosai taja numfashin daya aike mata da sassanyan turaren nan nasa dake kasheta,yadda ya sakata a tsakiyar???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? yana baza mata qamshinsa da dumin numfashinsa tana jin kaman zata sume ne.

"Please" Ta fada da raunanniyar murya. Batason yaga faduwarta ko lagonta gaba daya,amma ta karanci kamar ya shiryawa hakanne.

"Don't fight it" Ya fada yana qoqarin maida bakinsa cikin nata.

"Am in towel fa...." Ta fadi tana qarasa narke masa gaba daya.

"I don't care" Ya fada kaman me rada yana jin yadda shima ya fara kunnuwa,ya sanya hannunsa yana mayar mata da gashin kanta daya rufe fuskarta baya gami da saka idanunsa sosai cikin nata kaman bazai daina kallonta ba,wani irin sassanyan kallo yake mata kaman zai hadiyeta,abinda ya sanya taji qafafunta kaman zasu watsar da ita.

"Yau zamu fita a muraaka......still Muhammad fuad anata tunanin hukuncin da za'a yanke a kansa?". Kasa bashi amsa tayi,daidai nan wayoyinsu suka dauki tsuwwa lokaci guda kaman hadin baki.

" Farouq ne,wallahi nasan farouq ne" Ya fada a wani jigace. Sosai dariya ta taso mata,amma bata da qarfin yinta,saidai wani mamaki ya kamata da taga daya daga cikin masu kiran farouq dinne.

Kiran farouq din ita ya ceceta,sai yaja baya ya zauna yana daga wayar,ita kuma ta kwashi kayanta ta koma toilet din.

Sanda ta fito ya gama hada komai,ya bita da kallo kafin ya daga yatsansa yana karkadawa. Luggage dinta ya sauke,ya birkitata da kyau ya ciro wata oversize abaya,ya hado da wani Malaysian hijab ya miqa mata.

Bata musa ba ta karba,zata koma ciki ta sauya ya bake ko ina gami da mata nuni kan ta shirya a nan. Bata tsaya jan dogon magana ba,tunda ta fahimci makara suke gab dayi,ta shirya tsaf ya kama igiyan rigar dana hijab din duka ya daure mata sannan yaja baya yana kallonta.

"Ya salam.....How can i disguise you?" Yayi Maga nan da gaske yana jin da zai yiwu ya hana kowanne ido kallonta kome wahala zai iya bin tsarin.

"Oho nima ban sani ba" Ta fada tana tura baki gaba don da gaske tana jin haushin abinda ya matan,duk da tana qoqarin nuna bata damu ba.

Dariyarsa ya danne yasa hannu ya jawota baya yana basarwa.

"Karmu fita ki canza......if not.... I'll be open about my feelings for you....i won't feel ashamed of anyone...." Idanunta ta fidda warwaje,a yadda ta shaida rufewar idanunsa akan duk abinda zuciyarsa ta karkata akai,tasan zai iya aikata komai da komai,tana kuma tsoro da nauyin hakan. Hancinta yadan matse yana gane tsoronta.

"Don hana hakan faruwa......Handle me delicately....fine"

"Ya salam" Ta fada tana jin fargabarsa yana kamata. Hannu ya miqa ya riqe hannunta yana fadin

"Ki barshi,Jordan zai kula da komai da muk....." Bai qarasa fada ba dumin hannunta ya ratsa sassan jikinsa,sai ya dakata da maganar yana kai hannunsa goshinta da sauri.

"Ya salam......fever?,when?" Ya fada a rude. Idonta ta kada kadan,ita ta dauka ma zafin jikin bai fito ba,iya ita kadai takejinsa a qashinta.

"Bai dade ba......i will be fine" Kai ya girgixa yana yana azawa kansa laifin,yana ganin kaman maidata ruwa da yayi da sanyata zubawa kanta ruwa shi ya jawo hakan.

"No.....mu tsaya ki samu relief,zansa farouq yayi magana da......" Hannunta ta dora da sauri saman nasa hannun.

"I'll manage". Dan jim yayi yana kokwanto kafin yace.

"Really?" Kai ta gyada masa duk da yadda taji kanta yana sara mata. Bataso ace duk jama'ar dake can suna jiransa jiran ya tashi a banza saboda ita kadai,hakan sam baiyi tsari ba,sannan ita kanta bata qarfafashi yayi abinda ya dace ba.

Yadda yake riqe da ita kaman zaiyi mata tafiyar da qafafunta ya sanya mata Tsananin jin kunya,saidai gurin ta sake fahimtar na masoya ne,kowa sabgar gabansa yakeyi,a haka suka iso private boat din da iya ita dashi kawai zai fitar zuwa Conrad island su ruski motarsu su wuce airport,don ko Jordan wani boat din daban ya biyo ba nasu ba.


*MAAMAH*

Kaman wadda bata da aikinyi haka ta dinga bin diddigin shudewar kowanne awa da minti na zamansu a gurin da delay din fu'ad na qarasowa gurin. Ba shakka banda idanunsu ameenatu a wajen ba abinda zai hanata komawa gefe tayi kuka koda na minti ashirinne,wataqila ta samu sassaucin abinda takeji cikin zuciyarta.

Yau ita mariya ta wayi gari karyar farautarta ta farauto abinda take da muradi ta sakashi a gaba tana wasa dashi yadda taga dama?. Yau ita mariya ita ke zaune tana jiran dakon isowar yaronta?,wata macen bariki ta riqeshi tsahon wasu kwanaki?,a yau da take jiran qarasowarsa kuma sai time din da taga daman ganinsa kowa zai ganshi?,ita kuwa idan batayi taba rayuwar mutanen nan biyu ba ai tayi asarar zuwanta duniya.

Guda gudan baqinciki haka ta dinga hadiyarsa tana korawa da yawun bakinta,tana sake tsarawa da shirya yadda zata gigita rayuwarsu duka su biyun idan sun sauka Nigeria. Tana jin kamar idan ta jira su koma ya mata nisa,don haka ta koma gefe ta zaro wayarta tana duba wata number tana jin gwara ta shirya komai tun yanzu,ta yadda komai din zai fara da wuruwuri. Sauran ma'aikatanta dake hannun yanzu haka dukansu bata da wata damuwa a kansu,tasan akwai babban aiki a kansu daba wanda ya isa ya furta sunanta da sunan toxarci ko tona asiri.

Tana qoqarin kira wani kiran ya shigo. Matsanancin mamaki ya kamata ganin sunan fareeda yana yawo saman screen din,bata tsaya jinkiri ba ta daga wayar tana kiran sunanta.

"Na'am....ya kike?" Tayi namijin qoqarin tausar kanta ta karya harshenta ta tambayeta.

"Ina kika shiga fareeda?,bayan kinsan babban aiki muka tunkara?" Sake hadiye wata guduma da taxo kan harshenta tayi,tasani cewa banda tana tausar kanta ta samu isa ga dalilin kiran da tuni ta jima da daddannawa mariya zagi.

"Kowanne aiki ma yazo qarshe......kowacce magana anzo qarshenta......kowanne al'amari dadinsa da wuyarsa sun qare..... Kedai kawai turamin date din da zaku iso Nigeria,da airport da zaku sauka,kano ko Lagos ko abuja". Daga kai tayi tana duban musaddiq dake nesa kadan da ita.

"Musaddiq" Ta kirashi tana sauke wayar,waiwayowa yayi sannan ya fara takawa a hankali har ya iso gabanta,a tsume ta danna kan number ta miqa masa wayar.

"Kayi confirming na date din komawarmu da airport din da zamu sauka ka rubutamin a nan ka tura". Wayar ya karba yana kalla,number ba suna,hakan yadan saka shakka cikin ransa,amma ta wani sashen kuma daya tuna kalmar UWA UWA CE sai ya rubuta kaman yadda tace din,ya tura bayan ya gama kalle numbers din tsaf sannan ya miqa mata yana barin wajen.

Details din daya rubuta take kalla

"Me fareeda zatayi dashi?" Taji tambayar ta tsargo mata. Cak ta tsaya tana son laluba amsar amma kuma saita kasa. Wani sashe na zuciyarta sai taji yadan shiga fargaba kadan,sai kuma daya sashen ya taso ya danneshi yana gaya mata.

"Fareeda masoyiya ce....wataqila akwai mafitar data samo mana,zatayi abinda ni na kasa yi wataqila"
(Ni kuwa nace ummm inji me ciwon haqori......ba girin girin ba tayi mai dai,maji ma gani wai an binne tsohuwa da ranta).

Aje wannan tunanin tayi tana tureshi gefe,ta kashe wayar tana ajeta da zummar ci gaba da lissafin sai yaushe zata bar fu'ad din ya qaraso?,sai kuma idanunta sukayi mata kyakkyawan gani.

A nutse suke takowa da wani irin qyallin da idan ka kirashi na amarci bakayi laifi ko kuskurr ba. Kanta yana aje saman kafadarsa wanda tayi hakanne bisa dole saboda jiri jiri data fara ji. Da farko taqi ganin zasu shiga jama'a ne,amma daga baya dole ta kwanta din saboda indai batayi hakan ba tana iya faduwa ko ya dagata ya dauketa in ya tabbatar hakan zata faru. Tsakiyar qirjinta kuma wani abune ya dunqule mata,tana jin kaman amai ne yake taruwar mata,saidai bata gasgata hakan ba ganin lafiya qalau take ai,bataci wani abu daya bata mata ciki ba bare tace.

"Na shiga uku......la haula wala quwwata" Maamah ta fada tana jin yanayinta yana hautsinewa gaba daya.......

"Anya.....anya.....anya?" Ta dinga maimaitawa cikin zuciyarta tana tsoron furta abinda ke cikin zuciyarta.

"KINYI KUSKUREN ZABOTA" Maganar bokan ta sake maimaita kanta cikin kwanyarta.

"Bazai faru ba.....saidai ita tayi danasani" Ta fada tana furxar da iske me qarfi daga hunhunta zuwa bakinta.


_uhmmmmmmmmm_




*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

5?? 5?? 5?
? 5?? 5?? 5?? 5?? 5??
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D? D? ?

5?K?5?



108


Idanunta ta dan lumshe kana ta budesu,tana iya hangen maamah dake farko,farouq daga gefanta kadan yanata amsa waya,anni daga can gaba ita amna. Musaddiq da saddiq ne bata hango ba,ko kuma yadda amai din yaketa faman mata kai kawo tsakanin cikinta da maqogorone ya hanata ganinsu oho

"Amai nakeji" Ta fada qasa qasa kanta a kafadarsa,don ta tabbatar zai iya kufce mata tsaf kafin sukai wajensu. Hannunsa yasa ya riqe hannayenta sosai,kafin ya sake riqe tafin hannunta da kyau yana cewa

"Ga can hanyar washroom,zaki iya qarasawa?" Ya tambaya a tausashe. Kai ta jinjina masa

"Oya.....be fast" Ya fada yana mata riqon da zataji dadin tafiyan da kyau,duk da ba haka ranshi yaso ba,yaso ace ta bari ya rage mata wahalar tafiyar kawai.

Murmurshi farouq ya saki,daga inda yake yana kallonsu,duk kuma da bayajin abinda suke fadi amma yadda yake kaffa kaffa da ita ya tabbatar masa dude dinsa ya qarasa zarewa......hauka tuburan na soyayya yasan ya sameshi,baisan kuma ya za'a qare da lamarin kula da gold da diamond ba,lokaci yayi na daukan sabbin ma'aikata kenan amintattu na kusa kusa dasu.

Ta bangaren maamah kuwa ta shaqa iya shaqa,wannan karon kasa riqe ashar dinta tayi sai data furtata,ta furzar da iska tana dan dukan gefanta. Ta yadda duk macen data taba bariki.masifa ce,abune a jininsu da komai dadewa sai an saida hali. A nata tunanin sabreen tana sane tayi hakan,tunda ta ganta,tayi ne kawai don kada su hadu da fu'ad din kai tsaye,tayi ne kawai don ta nesantata dashi,daga qarshe kuma tayi ne kawai don ta gwada mata tata iyakar.

"Zakiga taki iyakar a sanda kika qare a gidan tabbabbu mahaukata" Ta fadi a fusace tana qoqarin danne abinda takeji. Tanajin kaman ta saka hannu aka ta fasa ihu,tana jin kaman yanzu yanzu ta bude ido taga babu sabreen an shafe babinta daga tarihin rayuwarsu.....akwai lokaci abinda zuciyarta keta nanata mata kenan. Ta yarda da hakan,to amma shi lokacin yaushe xaixo?,amsar tambayar da bata santa ba kenan.

A nutse ya koma baya yana qare mata kallo bayan ta gama aman tana wanke kyakkyawar fuskarta da take wani fresh da ita. Ta kammala ta gyara hijab dinta sannan ta juyo,saidai ba zato ba tsammani ta sameshi tsaye yana qare mata kallo kamar yau ya fara ganinta.

Qaramar harara ta watsa masa da fararen idanunta,sai ya daga hannayensa sama alamun surrender sannan ya hade tafukan hannayensa alamun ban haquri kafin ya sauke yace.

"Kinci wani abune da yake baki reaction?" Ya tambaya da yanayi na seriousness. Dan shuru tayi tanason tunawa,saidai kuma iya saninta ba wani abu da taci din. Kai ta girgixa masa tana tsane hannunta da towel din daya miqo mata. Taku biyu yayi ya matso gabanta,ya cire hannunsa a hankali yana taba fuskarta kafin ya xare ya xurashi ta qasan hijabinta yana tattaba dogon wuyanta. Abinda ya dauke mata numfashinta kenan na wucin gadi,don bayan jin temperature na jikinta sai daya hada da tsokanota har sai da taja baya tana ture hannuwansa. Jirin da taji yasa ta tsaiwa tadan dafe kanta,kaman walqiya yakai gareta tana riqota jikinsa.

"Idan bazai yiwu ba mu wuce Seychelles......ki qara hutawa a can saimu samesu......xatafi burgeki akan Maldives" Ya qarasa maganan cikin kulawa. Fararen idanunta ta sake watsa masa. A abinda take gani cikin idanunsa ba hutawa zai barta tayi ba,saidai ya qara mata lalura ne kawai. Batasan inane Seychelles ba.......iya Maldives ma ya suka qare ya kaita qasan ruwa?,ita kuma Seychelles ai qila cikin cikin kada(crocodile)xasuyi rayuwa. Ta fahimci a son ranshi kowa ya mutu a barsu su rayu su kadai.

"Muna sake makara" Ta fadi a shagwabe kaman xata narke. Abunda yayi masifar qayatar dashi,har sai da yaja baya yana gwada yadda tayin. Dariya taso qwace mata amma tayi hanzarin kauda kanta,sai kawai ta dauki wayarta ta soma takawa zata tafi ta barshi.

"Ganganci ma kenan" Ya fada yana zaburowa ya daidaita tafiyarshi da tata.

Wannan karon farouq suka fara taraswa,suns hada ido da farouq din dai ya wani basar,yana dauko wannan tsohon dabi'an nasa na miskilanci wa mutane ya azawa fuskarsa.

"To waye ya damu dakai?" Farouq ya fada yana jifansa da harara,ya maida kallonsa ga sabreen da kunya ta fara mata qawanya. Tanaso ta zame hannunta ne daga nashi amma yaqi bata damar hakan

"Madam barka da zuwa......inajin xamu iya wucewa ayi miki screening,minti arbain ya rage lokacin tashin yayi dama" Farouq ya fada a girmame.

"Izinin wa ka nema da xaka kama yiwa mutane magana da mata?,if kana da wani important issue da kakeso lallai kayi magana da ita a kai ba gani ba?,dani zaka fara magana na nema maka izini ai ko?" Fu'ad ya fada sounding seriously. Dariya ta kama farouq sosai,yaja da baya ya kama kabbara kafin yace

"Dole ne kam,dole ne na nema izini ai.....don ko bugeni kayi na fadi ai ba'a shari'a da wanda ba cikin hayyacinsa yake ba......madam kiyi haquri kinji......wannan zama dashi sai me haquri".

" Na rantse harda Allah farouq kana qarawa kanka da kanka kwanakin bikinka ne" Fu'ad ya fada da gaske gaske,abinda ya sanya farouq ya fara shiga taitayinsa kenan. Yasan halinsa,idan har yace abu yasan ta yadda zai maida abunnan yadda yace din,shi kuwa wannan ruwan madarar soyayyar da yaga ana aiwatarwa shi a haramta masa wanzuwar tasa ai anyoshi......gwara yaje ya dandana shima kam.

"Nif bance komai ba.....daga welcoming naku?.....madam ki qarasa ciki"

"Ba ruwanka......banason kana min magana da mata fa,kana takurata,banaso kana sata magana.....she's sick".

"Sick?" Farouq ya tambaya,daidai sannan taji xamanta tsakanin drama din farouq da fu'ad ba nata bane,ta sabule hannunta ta qarfi ta soma yin gaba tana barinsu.

"Dude......ba sake lahani kayi mata ba ko?,wallahi wannan karon anni ba zata barka ba". Harara ya wurga masa

"Wai sa'anka ne ni farouq?"

"Inafa.....mutumin da yaje inda ni banje ba?" Murmushi ya saki,yasan da gaske farouq ya damu dashi da lamarinsu ne gaba daya,kowacce tambaya yana yinta ne don tabbatar da lafiyar kowannensu.

"Juts a fever" Ya maida masa a taqaice idanunsa suna kan sabreen data iss gaban maamah ta tsugunna tana gaidata.

"Allah yasa qwallonka ne ya fada a raga......zanso naga first born na gold runner" Sosai maganar taja hankalin fu'ad,sai ya kasa cewa farouq komai yadai bishi da kallo. Zuciyarsa bugawa takeyi so fast amma yanason dakatar da ita. Bayason maganan farouq ta masa tasiri,ya tasirantu da cewa shine kuma bashidin bane.

Sautin dariyar maamah a sanda take tsugunne gabanta tana gaidata shi yaja hankalinta,ta daga kanta a hankali ta kalleta. Qaqqarfan murmushi takeyi da gaske wanda yafi kama da dariya

"Kin gama naki......ni kuma zanyi nawa" Abinda tace da ita kenan kawai tana maida kanta ga wayarta.

"Tashi kije yarinya" Hakanan ta samu qwarin gwiwar aje mata murmushi itama sannan ta yunqura ta miqe tana fadin

"Hasbunallahu wani'imal wakeel,ni'imal maula


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login