Showing 246001 words to 249000 words out of 363280 words

Chapter 83 - DUNIYATA BOOK 2 COMPLETE

HUGUMA   

11 Nov 2025

1356

iyayensu.....irin sadaukarwar dake sanya kowanne yaro cikin alfahari da kasancewar iyayensa su suka haifeshi". Wani irin nannauyan abu kalamanta suka sauke mata......ta kuma isar mata da saqonni masu yawan gaske da.maganganunta masu harshen damo.

"Ki huta lafiya" Magananta ta qarshe kenan da ita tana yanke kiran.

Maya???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?r da dubanta tayi kan huda dake zaune a gabanta. Tun dazu da abba yazo asibitin yace bai gamsu suci gaba da zama ba,Dr mubeena ta sallameta bisa alqawarin zata dinga zuwa ganinta kullum don samun cikakken kulawa fiye da asibitinma.


*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862
5?? 5?? 5?
? 5?? 5?? 5?? 5?? 5??
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D? D? ?

5?K?5?


124


"Zaku wuce kaman yadda ani ta buqata.....komai bazai fasa faruwa ba huda....komai kuma bazai sauya ba sai abinda qaddararmu ta tanadar mana". Hawaye sosai huda keyi,duk da yadda take qoqarin riqe kanta daga aikata hakan a gaban sabreen.

"Zamu tafi adda da ciwo da firgici.....zamu tafi ba tare da taqamaimen masaniya akan ina hamma yake ba......yadda ya kula da lamarinmu muma ba zamuyi qasa a gwiwa ba wajen addu'ar bayyanarsa........da kuma tonuwar asirin duk wanda keda hannu wajen kitsa komai da zai illata rayuwar kamilin mutum me taimako irin hamma fu'ad".

Ba qaramin jarumta sabreen din ta nuna ba a sanda suke sallama dasu nadra din da yammacin ranar,sai takejin kaman zata sake tabbatuwa cikin kadaici,ta dinga jin kamar ita daya ta rage a duniyar zata ci gaba kuma da rayuwa ne ita kadai.


*11:30 pm*


A hankali ta farka daga wani nannauyan bacci daya saceta saman abun sallah bayan ta kammala sallar nafilfilu da dukka addu'o'inta,ta kuma cika da sallar nan me matuqar fa'ida da kuma alfanu wato sallar wuturi.

Hijabin da dardumar dukka suna jikinta,alqur'aninta yana ajiye a gefe yayin da tasbahar hannunta ta sulale ta fadi a qasa ba tare data sani ba. Ta qarasa bude idanunta da fadin

"Alhamdulillahi ala kulli hal" Cikin kowanne lokaci idan ta bude ido tsammani takeyi zata ga komai ya wuce tamkar cikin duhun mafarki ne da hasken rayuwa da idanu biyu ya ratsata,saidai duk sanda zata farka din tana samun komai a inda ta barshi,komai yana nan yadda yake.

Fitsari ne ya cika mata mararta,ta sanya hannu ta zare hijabin jikinta idanunta yana sauka saman tray din dake table din gefanta. Komai an shiryashi akai,tasan kuma wannan aikin ma'u ne bisa umarnin anni.

Hatta da dakin suna dawowa annin ta saka aka shiryashi yadda ya dace saboda jin dadinta.

Qafarta tadan riqe saboda yanayin zaman da tayi a wajen na wani lokaci,ta miqe a hankali tana nufar toilet. Ba jimawa ta fito daure da sabuwar alwala,tun daga sanda ta fahimci muhimmancinta ta daina zama babu ita,musamman ita din da tasan akwai mutum irin maamah dake gefe tana farautar rayuwarsu ta kowanne fanni. (Koda baka da masaniyar takun saqa tsakaninka da wani wanda kake kyautata zaton yana 'yan biye biyen shirkarsa,ka tabbatar baka zama ba tare da alwala ba,koba komai ita din haske ce a gareka,ga kuma kariya da zata baka daga dukkan sharrin me sharri).

Wani sauqi sassauci da kuma rangwame take ji duk sanda ta tuna ta sakarwa maamah wani tsoro da firgici,don tana zaune ta shiga shafukan sada zumunta,kai tsaye ta dinga cin karo da labarin yanata trending,ga 'yan qarawa miya maggi da gishiri sunata qawata topic din da kalar qarairayinsu. Har ta gama shawagin ta sauka labarinne ta kowanne handle na bloggers da gidan jaridu mujallu harma da celebrities.

Har zata koma ta zauna taji qishirwa sosai ya kamata. Koda ta duba tray din ba zam zam ma'u ta saka mata ba,ruwan gora ne,tana kyautata zaton kuma batasan ba kowanne ruwa take iya sha din ba sai zam zam shi yasa,don haka sai kawai ta maida hijab dinta ta zura flipp flops dinta ta nufi qofar.

Sanda take takawa zuwa parlor din sai ta dinga jin wata kakkaurar murya tana magana,kaman tasan muryar,kafin ta qarasa tunaninta kuwa tuni ta fusgo mata cewa muryar abdulgaffar ce.

Sunan fu'ad da taji an ambata ya sanya gabanta wani mummunar faduwa,qafafunta suka fara slow suka gaza ci gaba da tafiya da ita,sai kuma suka tsaidata cak qirjinta kaman zai fito waje.

"Mun samu nasarar gano inda yake.......farouq da pilot dinsa sun fitar dashi daga qasar.......suna taipei capital na taiwan,asibitin taipei wellness hospital and resort,mun samu magana da farouq,saidai na lokaci kadanne ya datse kiran,alamu sun nuna bayason kowa yaji.....kuma haka mukayi dashi,ya bani information dinne nima na through waya ba,yace idan zaiyiwu kada kowa ya sani sai abba" Muryar anni rawa takeyi sosai,yayin da sabreen taji wani murdewa da mararta tayi,tanaso taji ya fu'ad yake......tanaso taji halin da yake ciki,muddin ta bayyana ba zasu fadi komai a gabanta ba ta sani.....muddin sukaji motsinta kuma nan ma ba qarasa maganar zasuyi ba bare tasan me ake ciki,don haka salin alin ta sulale tayi zaman dirshan a nan tana dafe hannuwanta jikin wata kujera qwaya daya da aka ajiye a wajen.

"Me ya samesu abdulgaffar.....kada kace zaka boyemin komai" Shuru abdulgaffar yayi yana sadda kansa qasa,har sai da abba ya qagu shima yace

"Zauna ameena.....kaima zauna abdulgaffar....." Dukkansu suka zauna sannan abban yace.

"Dani da ameena bana jin muna cikin mutanen da zaka boye mana komai,shi kansa farouq din nasan bazai taba lissafamu a ciki ba,koda zaice kada a fada din zai fada ne saboda matarsa......tana cikin lalurar da ba komai dama ya kamata a gaya mata ba".

"Ba gatan da zakuyimin abba sama daku gayamin halin da hamma yake ciki" Sabreen da jikinta ya soma daukan wani yanayi ta fada cikin zuciyarta,tana jin kamar ta jawo abdulgaffar ya gaya mata komai da gaggawa.

"Haka ne,sun hari boss ne,a sannan yana tsaye suna magana da jordan,ya kauce basu sameshi ba,yana daga kai kuma ya hangi wanda yayo harbin,baice da kowa komai ba ya soma dosar inda yake hangoshin,daga can sama ne wani guri da ba kasafai aka fiya amfani da wajen bama,ganin ya hangoshi kuma ya nufeshi sai ya sake yin harbin a jere har sau biyu don kada ya samu isa gareshi,to amma kuma baiyi nasara ba,don harbin daya ne ya sameshi a damtsansa,dayan ya sake wuceshi,harbin bai hanashi qoqarin cimma mutumin ba,ganin yana dososhi da gaske kuma dab yake da riskarsa,jordan da farouq na biye dashi a baya sai ya fara hade kayansa zai gudu. Har yayi taku biyu ana ukun ya damqeshi yanason cire hular fuskar daya saka ya rufe idonsa,juyowar da zaiyi kawai sai ya shaqa masa wani abu a handkerchief din hannunsa yana qoqarin zamewa ya gudu,saidai kafin abinda ya shaqa masan ya kama jininsa su jordan sun qaraso,qarasowar tasu kuma yayi daidai da zubewarsa a wajen,basusan waye da waye a wajen yake tare dasu ba,basusan kuma waye ya aikoshi ba,wannan ya sanya kawai suka yanke shawarar komawa dashi su fitar dashi daga qasar,shi kuma mutumin sun sakashi hannun hukuma,He's unconscious har yanzu,wannan dalilin ya hana oga farouq bayyana ko bayyana komai".

"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun" Shine kawai abinda anni ke maimaitawa. Komai jinsa sabreen tayi kaman tana saman gajimare ko iska yake faruwa,ta dinga kokawa da numfashinta tanason kamoshi ta kuma kama ayoyin Allah da zasu taimaketa,saidai ta gaza hakan har sai da sautin muryar anni ya bayyana.

"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun!!!" Tabi bayan ta anni tana maimaitawa,saidai tata da wata madaukakiyar murya ce data fusgo sautinta da qyar daga maqoshinta,sautin kuma ya iske anni dake zaune tana maimaitata. Cak anni ta dakata tanaso taji sautin daga inda yake fitowa,jin daga inda sautin yake ya sakata waiwayawa tana duban fuskar abba wanda shima ita din yake kalla.

"Innalillahi wa inna ilaihi rajiun!!!!" Kalmar data sake maimaitawa da wani irin gunjin kuka shiya ankarar da anni daga inda sautin yake fitowa.

Da wani gudu anni ta miqe tana nufar wajen hankalinta yana tashi,bai kamata sabreen taji wannan mummunan labarin ba,bai kamata ba,labarin da aketa boyonshi ta yaya ta jishi?".

A zaune ta sameta tanata maimaitawa,wasu irin hawaye sun wanke fuskarta,jikinta kawai rawa yakeyi,durqusawa tayi a gabanta tana kamata yayin da Alhaji hamza ke tsaye a kansu shima yana tayata maimaitawa.

"Me kika fito yi sabreen?,me yasa kika fito?" Anni ta maimaita a gigice tana riqeta cikin tsananin tsoron abinda zai iya faruwa da ita. Numfashinta yana wani iri,ta tabbatar kuma tana da asthma ne irin nata,tana tsoron kada ta sarqeta cikin wannan daren.

Zuciyarta taketa qoqarin bawa dakiya da juriya.......tanata qoqarin maido wannan qwarin gwiwar juriya da jarumtartata,tanason dawo da old version of sabreen dinta. A yanzu bata da wani buri daya wuce ta bude idonta taga fu'ad din,ko a yaya yake......ko a wanne irin yanayi yake sai yafi mata nutsuwa akan zamanta a nan.

"Ruwa zan sha anni" Ta fada muryarta tana rarrabuwa.

Da kansa Alhaji hamza ya koma ya dauko mata ruwan,ya miqawa anni ta bude ta bata sannan yace.

"Maidata daki ameena,muje na bude miki qofa". Riqeta anni tayi har yanzu suna maimaita hasbunallahu wani'imal wakeel tare.

Saman gadonta ta ajiyeta tana jingina mata pillow

"Anni" Ta kira sunanta kai tsaye tana jin wani jarumta yana shigarta. Kai kawai anni ta tada ta kalleta,don bazata iya tuna yaushe ta kira sunanta haka ba.

"Kunason nutsuwata da kwanciyar hankalina?" Ta tambayi anni still tana dubanta. Alhaji hamza dake tsaye daga bakin qofa anni ta kalla,sai ya gyada mata kai,tasan umarni yayi mata sai ta dawo da dubanta kan sabreen.

"Sosai sabreena.....sosai". Idanunta da takeji hatta su sun mata nauyi a jikinta ta lumshe sannan ta bude.

"Abu daya nakeso anni da zai bani wannan nutsuwar......abu guda daya take nake da buqata....." Ta fada tana daga yatsanta daya,idanunta nayin wani iri kaman wadda tasha abun maye ta maku.......



*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

5?? 5?? 5?
? 5?? 5?? 5?? 5?? 5??
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D? D? ?

5?K?5?


125


"Mene sabreen?" Anni ta sake tambaya tana zama gefanta,tana jin kamar an salube qashinta daga cikin tsokokin jikinta,tana fata ba abinda bazai yuwu bane sabreen xatayi magana akai.

"Anni ku kaini wajensa" Ta fada a taqaice hawaye suna cika fararen idanunta da tuni kalolinsu na fari da baqi ya jima da sauyawa daga idanunta.

Da hanzari anni ta kalleta,kai ta dan girgiza mata.

"Kiyi haquri ameenatu......ta yaya kina cikin irin wannan yanayin zaki tafi ki ganshi a yanayin da yake ciki?,ba abinda yafi buqata illa kiyi masa addu'a ki kuma kula da abinda yake cikinki......bazai taba iya mantawa ba muddin kika kasa riqe abinda yake cikinki kika kasa rainan masa su....."

"Bazan iya rainonsu ba anni muddin babu shi a kusa dani.......zan fara lissafin yankewar numfashi daga gangar jikina daga yanzu zuwa fitarsa na qarshe" Ta qarasa maganar hawayen da take tarewa suka gangaro saman kuncinta.

Wani abu ya ratsa anni da Alhaji hamza tun daga saman kansu zuwa tafin qarfinsu. Tsahon rayuwarsu zasu iya cewa basu taba ganin zazzafar soyayya irin wannan ba.....soyayya da qauna me wani irin zafi da radadi,soyayya da qauna ta gasken gaske......soyayya ta a mutu da kowanne motsi da yanayi na abokin soyayya ya tsayema dan uwansa a rai.

Rasa bakin magana anni tayi,ta daga kanta tana duban Alhaji hamza da shima ya gama sallamawa. Kai kawai ya jinjinawa anni sannan ya dubi sabreen.

"Indai don wannan ne ki kwanta kiyi baccinki sosai,daga gobe zuwa jibi in sha Allah zan siya mana tickets na fita taiwan......zakije ki ganshi....amma sai kinyimin alqawarin daga yanzu harmu tafi ba zaki sake damuwa ba......kuma zaki sakeyimin alqawarin idan munje ba zaki daga hankalinki ba.....ko a yaya kika sameshi zaki sawa zuciyarki nutsuwa da kwanciyar rai har ya samu lafiya kamar yadda muke kyautata zaton hakan". Kai ta shiga jijjigawa a jejjere.

"Nayi maka alqawari abba.....nayi maka in sha Allah". Kai ya gyada shima,wani irin tausayinta yana kamashi,ya yiwa anni alama da hannu sannan ya juya yana fita.

Saida anni ta tabbatar ta kwanta ta kuma nutsu,sannna ta saka mata karatun qur'ani qasa qasa kusa da ita,ta kira mata ma'u suka kwanta tare sannan ta fice.

Tana jin fitar annin,saita runtse idonta tana jin wani rauni yana saukar mata,kuka takeso tayi wanda batasan iyakarsa ba,amma kuma sautin qur'anin da yake shiga kunnenta ya bata wata irin cikakkiyar nutsuwa,a hankali ta sake maida idanunta ta rufe,saita dinga jin kaman wani tabbaci take samu daga zuciyarta na samun nasara da sauqi a dukka al'amuranta,ta sake imani da wannan ayar da take cewa.
(Ku saurara,da ambaton Allah kadai zukata suke samun nutsuwa).

A dan gaggauce anni ta qarasa dakin Alhaji hamza,ta dubeshi,waya yakeyi yana daga tsaye a daren,batasan koda waye yake wayar ba duk da dare ya soma nisa,sai ta zauna tana jiransa ya kammala. Ba jimawa ya kammala din,ya dubeta yana aje wayar

"Na saka su dubamin tickets ne xuwa taiwan.....na gobe ko na jibi,ina zaton kuma sai jibi ma za'a samu".

"Amma abba.....kana ganin ya kamata mu dauketa mu kaita ta dinga ganinsa cikin engine da tashin hankali?kasan tabbas sai muhammadu yafi son rayuwar yaran nan da nashi rayuwar?,kasan sai yafi qaunar ta kula da kanta da lafiyarta akan tashi?." Dan murmushi ne ya subucewa abban,sai ya zauna gabanta yana dubanta.

"Ameenatu.....zuciya da ruhin soyayyarsu ba gama gari bace irin ta kowa.....karatun da na yiwa soyayyarsu shine.....suna sake qaunar juna da tsananin son kasancewa da junansu a sanda jarrabawa ko musiba ta samu daya daga cikin su,sunfi qaunar duk tsanani su kusanci juna akan suyi nesa da juna......sabreena ba zata taba samun nutsuwa ba.....ba zamu taba samun yadda mukeson gani ba muddin bamu sadata da barin ruhinta ba.....xakisha mamaki idan kikaga tafi nutsuwa a can fiye da anan din duk da unconscious yake?" Ya qarasa maganar da tambaya yana duban idanun anni. Shuru annin tayi tana juya maganar abban. Ta jima bataga soyayya me zafi jini da hanta da zuciya harma da b'argo irin tasu ba.

Kanta ta gyada a hankali bayan ta gama nazarin,ta kuma yarda da maganganun abban dari bisa dari don itama taga hakan.

"Allah yayi mana jagora,ya taqaita dukkan wahala da sharrin masu sharri"

"Allahumma ameen" Ya amsa mata yana miqewa.


_TAIWAN_
_TAIPEI_
*_Taiwan Taoyouan international airport_*


Yammaci ne sosai sanda suka sauka a taiwan,misalim qarfe hudu na yammaci,wanda yayi daidai da qarfe sha daya agogon nigeria.

Da yake tafiya ce bata shiri ba,cikin motocin da gwamnati ke ajiyewa saboda baqi da wadanda ke buqatan hayar da zaiyi driving da kansa,ya gama adadin kwanakin ka maida inda ka karbo ita suka karba.

Abdulgaffar ke driving din,yana yi yana duba map da address din da ya samu da zai sadashi kai tsaye da asibitin.

Duk yadda garin yakai ga kyau tsaruwa da daukan hankali ba wannan bane a gabanta,bama kasafai take iya fahimtar inda suke wucewar wa,burinta kawai.shine su isa asibitin,burinta kadai shine ta ganta a gabanshi,burinta ta ganshi a gabanta ta daina jin cewa yayi mata wannan nisan da kowacce rana zuciyarta da gangar jikinta suke jiye mata.

Tafiyar mintuna arba'in suka fada ainihin titin asibitin,ba wani wanda yake iya cewa da danuwansa komai. Saddiq musaddiq abba da anni......ballantana sabreen da take ganin kaman laqai laqai kawai abdulgaffar yakeyi bawai tuqi ba,kaman tafiyar kunkuru yakeyi,kamar ma bayason ya sadasu da asibitin.

Mintina sha biyar map ya nuna musu suna daidai asibitin,suna shiga titin shine gini na farko daga hannun dama.

Idonta ta daga a hankali tana kallon tsararre kuma ajiyayyen ginin asibitin,wanda ko ba'a gaya maka ba kasan cewa gurine me cike da tsari da tsananin kulawa,guri ne kuma da lafiya ke tsaye da qafafunta.

Karo na farko data soma yarda da gaske ko a qasashen waje akwai rayuwar masu hannu da shuni akwai ta tsaka tsaki akwai ta talaka. Tun kafin sukai ga shiga asibitin checking nasu da akeyi kadai ya isa ya tabbatar maka akwai tsaro sosai cikin asibitin. Checking da ya sanya ta dinga jin kaman wani salo ne na hanata isa garesa.....kafin yafi tsaye mata a rai sama da zaman da sukayi cikin jirgin kafin isowarsu taiwan.


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login