Showing 282001 words to 285000 words out of 363280 words

Chapter 95 - DUNIYATA BOOK 2 COMPLETE

HUGUMA   

11 Nov 2025

1450

zuwan bane. A rana ta biyu ne akayi zaman ajo,wanda a wannan zaman kudi sukayi rana.....dukiya tayi kuka da idanunta,ya nunawa BB dinsa qauna irin wadda ta sanya farouq tara hawaye sosai a Idanunshi.

"Karka yadda kayi mana kuka gaban mata da tarin mutane,idan kayi hakan bamu yafe maka ba.....wannan kukan ka riqeshi sai sanda kuka kebe......idan ba haka ba za'a dauka lusari ta aura" Ya fada kadan a kunnen farouq bayan ya gama zazzage pound cikin abinda aka ajiye saboda zuba ajo din,don yana gama zubawa aka dauke abun,ya riga ya cika sai wani aka sanya.

Tofa......nan idanu dama hankulan 'yammata dama zaurawa masu lokaci yayo kan FU'AD din,taron mayu bawai na maita ba......mayun mata.....ma'abota son kyakkyawan namiji me abun hannunsa hankulansu ya tashi. Kowacce isassace me aji tana jin takai,don me qaramin class ma baya suka dinga ja suna rufawa kansu asiri,saboda sunsan kalar zaren ba kalar yadin bane......saidai su kansu isassun sai rab'e rab'e,an rasa zaqaqura me qarfin halin tunkarar me jadda din.....kwarjini yanata aikinsa.

Mota ya koma yayi zamanshi suns hira da duniyarsa,video call kaman ko yaushe,ta daga masa hannuwanta da sukasha wani irin jan lalle,tun daga tafin hannun har zuwa bayan hannun nata.

"Ya salam" Ya fada yana jin wani abu ya harba a jikinsa.

"Nawa me qunshin nan takeso a bata?".

"Anni ta biya mana ni dasu amna.....beside ma ai ka ban kudin da zai isheni kalar kowacce hidima".

"No....kudin dana baki ban bakishi bane don kiwa kanki komai ba,na baki shine don ki wata hidimar daban,zan saka miki a dollar account dinki,saiki cire".

"Allah yabarmin kai jadda na.....Allah yajamin da ranka uban 'ya'yana" Ta fada tana jin kanta yana fasuwa,bada komai ba kuma,da zallar kulawa.....da kalar mijin kuma data samu.

Sanda suka koma guest in dinsu farouq shine qarshen shigowa,bai kuma tashi shigowa ba sai daya na dare. A sannan FU'AD yana zaune saman abun sallah yana addu'o'insa,wanda duka ta neman dacewa da alkhairai ce duniya da lahira shida 'yan uwansa dama dukkan wani masoyinsu(harda ku fans na DUNIYATA=??>???
Ido suka hada FU'AD ya janye idanunsa yana hade rai.

"Wanne irin abune wannan?,zaka ajiye.mutane kuma ka tafi,baka tashi shigowa ba sai tsakiyan dare kaman wani barawo?" Wani dariya sosai Farooq ya saki yana qoqarin cire babbar rigar jikinsa.

"So sorry dude.....kasan abinka dame iyali kuma farin shiga.....inacan ina lallashinta wai yatsunta sun gaji......ga tafiya kano gobe donma flight ne.....".

" A gidan ubanwa ta zama iyalin naka?" Ya fada adan fusace,don ya kira sabreen yaso suyi hirar dare bai sameta ba.

"Ka rabo mutane da iyalinsu kuma kazo ka ajiyesu?". Ido farouq ya fiddo,yanason fashewa da dariya amma ya danne

"Ikon Allah....to ni me zan muku idan nazo din?,qarqari muyi hira fa?,kuma yanzu tsakani da Allah saboda rashin imani wanda keda sabuwar amarya ai abun a masa uzuri ne ko?.....to kuma ma naga wancan lokacin naka daurin auren.....qasarma ka bari kaqi dawowa ka barni da amaryar da abokan gaba daya.....wannan rashin adalci ne dason kai dude".

"Farouq....gori zaka yimin?....gate out please ka barni naji da damuwana" Wannan karon duk yadda yaso boye dariyar ya kasa,sai kawai ya saki abarsa yana nufar toilet.

"Bani nakar zomon ba.....ratayar ma ba'a bani ba.....iyali me dadi.....ashe haka lamarin yake dama" Ya qarasa fada yana shigewa gami da turo qofar.

Qwafa fuad ya saki,sai kuma murmushi ya qwace masa. To meye ma laifin farouq a ciki?,ita kanta sabreen din bata da laifi tunda tace masa zata aje wayarta dama,kawai dai iya shegensa ne ya motsa,da alama kuma ramuwa yakeson yayi masa.


*_ALQAWARIN ALLAH baya tashi_*


"An daura auren umarul farouq hamza kibiya,da fannah maisharif babaghana......jama'a kun shaida?". Sautin daya sanya fu'ad sakin tattausan murmushi yana furta.

"Alhamdulillah......alhamdulillah"


*_DUNIYATA LITTAFIN KUDI NE(PAID BOOK),KAI TSAYE KI TUNTUBI WANNAN NUMBER_*
08187255862

5?? 5?? 5?
? 5?? 5?? 5?? 5?? 5??
_Zafafabiyar_

6B6O6O6K 62

g,D? D? ?

5?K?5?

*_Bgawo's KITCHEN AND APHRODISIAC_*


*_WATA KILLATACCIYAR MASARAUTA CE,WADDA KE QUNSHE DA DUKKAN NAU'IKAN ABINDA KUKESO_*


*_GIRKE GIRKE NA ZAMANI_*

*_KAYAN MAQULASHE DA NAU'IKAN DRINKS KALA KALA_*

*_INGANTATTUN TSUMAMMUN MAGUNGUNAN GYARAN MUTUNCIN 'YA MACE......GYARA IRIN NA IYAYE DA KAKANNI DA INGANTATTUN MAGUNGUNAN DA BABU DUNGUSHE KO KOKWANTO A KANSU_*

*_KALAR MAGUNGUNAN DA SAO WAJEN IYAYENMU NA DAURI.....INGANTATTUN SAUWOYI DA SAQE SAQI DA AKA SARRAFASU ZUWA MAGANIN GYARAN DIYA MACE_*

*_BIKI KUKE DASHI KO SUNA?_*

*_SAUKAR KARATUN QUR'ANI?_*

*_KO KUMA WALIMAR AURE QARIN MATSAYI A GURIN AIKI KO KUMA WANI QWAR QWARYAN TARO?_*

*_KO YAU DIN BAKIJIN SHIGA KITCHEN?,TSAFTATACCE KUMA INGANTACCEN ABINCI KIKE BUQATA A CIKIN WARMERS DINKI KO FOOD FLASK?_*

*_HAIHUWA KIKAYI?_*

*_KO GYARA ZAKIYI KAWAI A MATSAYINKI MA CIKAKKIYAR MACE?_*

*_BGAWO'S KITCHEN SHINE MUHALLIN DAYA DACE DA DUKKA WADANNAN BUQATUN NAKU_*

_Maza garzaya ki tuntubesu ta wannan number wayar_

08104553105
08127084190

*_zaki godemin qwarai da haduwa da BGAWO'S KITCHEN_*


*_BGAWO'S KITCHEN_*
*MATATTARAR BIYAN BUQATUNKU*



140


Daga nan inda yake yana hangen sadakin fannah dake bada tabbacin ta zama ta farouq dinsa halak malak......hakanan yana iya hango farouq dake tsakiyar abokansa wanda shigarsa bata da maraba data jikin fu'ad din,sak da sak kaman yadda sukayi a bikin fu'ad din.

Lafiyayyen walima aka gudanar a gidan gwamnatin jihar borno bayan kammala daurin auren da tarin abokansu masu jini a jika,wanda kowannensu wani ne shi ta fannin ilimi da abun duniya.

Ana gamawa fu'ad ya wuce masauki yabar farouq da tarin abokanshi,don shi bazai iyama wannan iya shegen nasu ba,sun sanyashi a gaba sunata abubuwansu daya tabbatar sai yayi trending a social media. Tunda akayi hotuna wajen reception din yayo gaba,don akwai shirin da yakeso yayi.

Ruwa ya fara watsawa ya fidda wayarsa,kai tsaye ya kira duniyarsa. Daidai lokacin tana zaune suna kallon reception da daurin auren da ko awa guda ba'ayi da yinsu ba amma har an warwatsa a media.

Kishin fu'ad ke taso mata sosai saboda ganin tarin comment din yammata a kansa. Shi kadai amma ya fita daban a cikinsu,komai nasa daban yake,wani irin kwarjini me hade da nutsuwa da suka qarawa fuskarsa kyau da kuma kamala.

_"Lallai baaba ma da babansa fa.....duk kyan azurfa bata kai ya gold ba.....the jadda.....guy dinnan daban yake fa=?%?d'?
=?%?"_ comment din wata daya gilma kenan daya sanya zuciyar sabreen quntata,ta kuma ture screen din daga fuskarta tana jan wani qaramin tsaki,can qasan ranta kuma tana mita.

"Bansan me yake damun 'yammatan yanzu ba,kamar mayunwata suke akan maza.....idan suka saka namiji a gaba baji ba gani?,ba kunya ba aji ba kamun kai?" Daga huda har amna sun fahimci me takewa qunquni,sai suka qunshe dariyarsu saboda zuwa yanzun suma suna jin tasu soyayyar da angwayensu har cikin jininsu.

Kayanta take hadawa dama,saboda tanason wucewa gida ne kafin su qaraso,tanaso ta kimtsa ta tarbeshi da kyau,idan yaso gobe sai ta dawo gidan annin. Kiran wayarsa ya sanya ta ajiye duk abinda takeyi,ta kuma daga kiran tana samun wajen zama.

"A ina kake?" Tambayar data fara masa kenan wadda ta bashi mamaki.

"Na dawo guest house masauki.......me ya faru?" Wata sassanyan ajiyar zuciya ta saki,tana jin dadi daya dawo din,at least ya tsira daga kallace mata shi da wadancan mayunwatan 'yammatan sukeyi.

"People are commenting about you everywhere
You're all over social media muffin" Ta fada da wata irin narkakkiyar shagwaba.

"What?" Ya fadi dariya nason qwace masa.

"Like nine angon?" Ya sake tambayarta.

"Am serous muffin" Ta sake fadi tana narke masa.

"Am all yours......am yours forever my World" Ya fadi da wani irin calmness daya bawa zuciyarta nutsuwa. Ajiyar zuciya ta sauke sannan ta soma gaidashi.

"Ya taron?"

"Alhmdlh.....but babu dadi coz bakya kusa dani".

"Nan da awanni kadan zamu kasance tare in sha Allah" Ta fada tana bashi confidence.

"In sha Allah" Shima ya maimaita. Lafiyan yaranshi shine next abinda ya qara tambaya,tayi murmushi tana dora hannunta saman mararta data fara tasawa tana bashi amsa.

"They're fine.....suna gaida abbunsu.....sunyi missing nasa"

"Me too my world.....akwai kyakkyawar gaisuwa tsakaninmu idan na dawo.....so get ready,be at home as soon as possible"

"Yanzun nake shiri in sha Allah"

"But.....karkice zaki fita da mota daya....ki jira su abdulgafar zasu kaiki har gida.....and nace su qara yawan security na gidan". Ya fada da serious murya.

"I hope komai lafiya ko?" Kai ya jinjina,kawai yana jin wani abu daban a jikinsa.

"Lafiya.....in sha Allah" Ya fada yana son tabbatarwa da kansa haka.

Cikin nuna tsananin kewa da qaunar juna sukayi sallama shida ita,kai tsaye kuma ya kira abdulgafar.

"Zamu qaraso gurin qarfe biyar......get ready please,a qara yawan security a airport da gida na harda gidan anni......har gidan farouq.....if possible inaso kowa cikin ku ya zama ankare da kowanne parts".

"As you wish sir" Ya fada cikin girmamawa.

"Ku rakata gida safely abdulgafar......bazan iya jurewa ba if something happen".

"Bazai faru ba sir in sha Allah"

"Good abdulgafar" Ya fada yana yanke kiran.

Iska me zafi ya furzar daga bakinsa yana dan wani gajeram tunani da shi kansa baisan na meye ba,sake daukan wayarsa yayi ya tura rubutaccen saqo ga duk wani guard da suke tare dashi a halin yanzu haka a maiduguri,sannan ya sauka yana laluben wayar farouq don jin yadda zasu shirya tahowa kano kada lokacin tashinsu ya fita.


& Daga samanta tana iya hangen yadda duk wani shige da fice yake gudana cikin gidan hamza kibiya. Wani ajiyayyen qullutun baqinciki ne yake tsaye a wuyanta,shi bai fita ba shi bai sauka ba. Idan akace mata a baya nasararta zatazo da irin wannan salon tsaf zata qaryata......a irin wannan yanayin zata iya cewa bikin d'anta akeyi.......amma koshi yaron nata bata samu martabar ganinsa ba bare ta shiga lamarin bikin,balle kuma ta samu girma da daraja irin na kowacce uwa.

Agogo ta kalla,tana jin ta matsu ta kuma qagu komai ya faru,tana jin a ranta afkuwar komai din shine zai bawa abinda ya tsaya mata a wuyan damar fadawa.

Knocking akayi sannan aka turo qofar dakin. Bata damu ta waiwaya kota tambayi waye ba har zuwa sanda ta fara magana.

"Maamah ga abincinki fa,tun na safe bakici ba.....na rana ma haka,ga na dare a hanya,kuma likita yace ki dinga kula da abinci ko don yanayin ciwon...."

"Ciwon ubanki?.....nace ciwon ubanki?". Ta fadi tana katse laila da dukka tashin hankalinta ya tattaru ga ganin alamun maamah din tana cikin damuwa,tashin hankalin da takeji tana jin yafi wanda maamah dimma ke ciki.

"Maamah kiyi a hankali ki daina fushinnan ko don lafiyark......".

"Waini sa'arki ce?,to kiji na gaya miki na rantse da Allah kika qara Dangantani da wani cutar hawan jini saikin gwammace uwarki hajja bata haifoki na......idanma qullawa kukayi don ku cuceni ku kasheni saboda ba idon 'ya'yana ko to?,to kunyi qarya kun kwana da yunwa,ni mariya warki ce daidai qugun kowa.....ni mariya kuma ni kad'aice gayya......fita kiban guri" Ta dakawa laila tsawa tsawar da har saidata zabura.

"Allah ya baki haquri" Ta fada ta juya tana fita a dakin kaman zata kifa.

Fitar laila sai ya zama kamar ta fita da iskar da take shaqa ne,take taji iska tana mata kadan,wuyanta ya soma riqewa iskar bata samun daman isa ga hunhunta. A daddafe ta samu waje ta zauna tana qara gudun fanka da Ac din dakin,wani irin haki yana sarqeta. Likitan ya gaya mata,kada ta yarda ta fadi muddin irin hakan ya sameta tana a tsaye,idan ba haka ba komai zai iya faruwa.

Ta kusa mintuna talatin a haka kafin taji a hankali numfashinta yana daidaita har ya koma normal. Wayarta ta jawo,ta kira number wayar da take sanya ran shigowar kiranta tun dazu.

"Baki da damuwa.....muna ankare da kowa da kuma komai.....ki jira jin sakamako daga yanzu zuwa gobe da safe"..

"Godiya nake" Ta fadi tana ajiye wayar tana kuma sake jin relief sosai a ranta.

Cikin wani irin mugun matakan tsaro jirginsu ya sauka,yayin da baqaqen motocin dake dauke da tambarin JADDA kimanin ashirin sukayi convoy cikin wani irin tsari me daukan hankali da kuma matakan tsaro sosai bisa umarnin fu'ad.

Lafiya lau suka qaraso unguwar,suka kuma jera kansu zuwa kyakkyawa kuma makadediyar harabar mansion House din alhj hamza kibiya.

Duk wani dake da jibi da ahalin alhj hamza kibiyan yayi tattaki ya fito daga cikin gidan,yayi tsaye a farfajiyar saboda girmamawa ga fannah,wadda aka fito da ita nannade cikin wata lafiyayyar Cotton lafaya butter colour da ratsin maroon.

Yana daga cikin motar amma yana iya ganin komai,yabi kowa da ido da yadda abun ke kasancewa,sai yaji wani abu yana taso masa,don haka ya maida idanunsa ya lumshe.

Lallai babu wani babban arziqi a duniya irin uwa ta gari......babu wani babban jin dadin rayuwa irin samun uwa ta gari.......alhmdlh yana godiya ga Allah a bisa dukkan ni'imomin da yayi masa,kuma ya karba cewa tasa qaddarar tana kan MAHAIFIYARSA tasa jarrabawar tana kan UWA da Allah ya bashi.

Amna dake nade cikin tata lafayar sai wani irin farinciki taji yana lullubeta,tana jin kamar suna dab da gina wani babban ahali ne,yau BB farouq dinta.....ya saddik,ya musaddiq da hammanta dukkaninsu yana da matar aure,wadannan matan kuma kowacce ana sanya ran zata basu baby,babies din da zasu taru su zame musu wata tawaga kuma family na musamman.

Kasa jira tayi a qaraso da fannah,saita taka da dan hanzarinta tana cimmata ta riqe hannunta,abinda yasa matar dake riqe da fannah din sakin hannunta taja baya,wannan ya bawa amna daman magana da ita qasa qasa.

"Welcome to alhj hamza family,welcome to jadda family adda fannah......bansan ya kuke cewa adda da kanuri ba.....anyway muna miki maraba".

"Na gode" Siririyar muryar fannah ta fita wanda ta tabbatar ita daya ta jita.

Cikin girma da martaba dangin anni dana abba suka amshi fannah aka qarasa ciki da ita,bayan anyi addu'a an kuma bawa su anni amanarta,sai annin ta sanya aka ware daki daban aka bawa fannah din ta huta suci abinci sannan sai a wuce da ita gidanta,hakanan danginta suma aka basu wani dakin daban.

Sai data tabbatar babu kowa a dakin sannan ta yaye lafayar dake kanta. Amna da huda ke dakin,hudar da sam ta kasa sakewa,ta hana kowa ma ya ganta throughout saboda surukuta da takeyi da dangin anni.

Musayar murmushi sukayi,amna ta nuna huda.

"Wannan itace huda.....qanwar adda sabreen,matar ya saddiq" Lokaci daya huda ta yiwa fannah,ta miqa mata hannu sukayi musabaha. Ita da amna sai take jinsu karon farko kaman qannenta,don ta tabbatar ta girme musu,saidai ba wani da yawa bane.

Qaramar walima akayi cikin gidan,baqi sukaci suka qoshi suka huta,sannan anni ta bawa fannah kyauta irinta surukuwa kaman yadda ta yiwa sabreen.


*_ME FARUWA!_*


Tun bakwai da rabi aka soma shirye shiryen qarasawa da fannah gidanta. Musaddiq da saddiq ne akan komai na game da shirya motocin da za'a dauketa a qarasa da ita ainihin gidanta dake maqociyar unguwarsu.

Tunda aka fara jera motocin daga harabar gidan zuwa qofar gidan amna ta kasa zaune ta kasa tsaye. Tana bala'in son zuwa gidan ya farouq,wannan yana daya daga cikin mafarkanta tun kafin tasan rayuwa zata juya lokutan aurensu guri guda,tun kafin ta taba tunanin zata kasance qarqashin igiyar auren yaa musaddiq a wannan lokacin.

Yadda kowa ya shirya haka ta shirya,tanason ta tambayi ya musaddiq ko shi ya dauki mota subi ayarin kai amare,a qalla tana tunanin bazai hanata ba,tunda zai wahala idan ta shiga nata gidan ya barta fita da wurwuri,don musaddiq din wani irin tsaro ne dashi tun wancan lokacin ballantana yanzu data zama mallakinsa.

Zaune tayi tana gwada wayarsa,sai data kirashi a qalla sau hudu sannan ya daga.

"Ya akayi baby doll?" Cikin shagwabar nan tata ta narkar da kai.

"Besty.......gidan amarya please,don Allah muje" Idanunsa ya waro waje kaman tana gabansa.

"What?.....aah karmu fara haka dake babe.....zakije amma bayan munyi wasu watanni" . Kukan shagwaba ta sakar masa wadda ta qarasa susutashi,da qyar da ban baki ta shawo kansa.

"Amma kinsan anni zatayi fada ko?".

"Karka gaya mata please,nayi alqawari muna zuwa zamu dawo". Shuru ya danyi,bayan wasu sakanni yace.

"Ban miki alqawari ba gaskiya babe... Kema amaryarce kaman kowa,kodon kinga ban tada rigima a kaiki yau ba?"

"Am sorry besty....don Allah"

"Nace banyi alqawari ba,but ki jirani idan hali ya yiwu zan miki magana saiki fito" A haka suka rabu da musaddiq,duk sai taji ranta ya jagule,tunda taji ya fadi hakan probability na rashin zuwanta yafi na zuwan nata yawa,saita buga tagumi tana zaman jiran tsammani,har sanda aka shigo aka fita da fannah alamun tafiya zasuyi.


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login