Showing 192001 words to 195000 words out of 265571 words

Chapter 65 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28911

bane ita dai sama sama ta dinga jin yakaka dagachan kuma barci ya sake Daukanta la"sar nayi yakaka tatasheta tace ta tashi tayi salla ta Daina kuma barcin la"asar.
Fadi take"Ke bake kadai ba..Ki rika barci har yamma tayi in kina son Lafiyanki da abunda ke Cikin ki sai kin kiyaye wasu abubuwan ku yaran yanzu komai Cikin gata kuke yi mu alokacin da in kina da Ciki ko barcin sai kin Ragesa har na Dare bama na yammah ba..!
Amina dai batace komai ba ta Fada Tiolet ta Dauro alwala tazo tayi sallar tayi addu"a domin ta daina Sakaci da addu",an kamar baya da kuruciya yake Dauke mata hankali.
Tana Idarwa ta Dauko Sauran wainar Fulawanta ta Sake ci tana ci tana jan yaji Yakaka na kallinta tana Girgiza kai fadi take"Ki Sautata ma kanki Cin yaji nan wajen haihuwa nake jiyemiki basir ya taso miki..!
Amina tace"Au daman yana Tasowa ne..!?
Yakaka tace"Zaki sani ne in kika shiga Dakim Haihuwa..!
Amina Dariya kawai tayi sai ga Ya Aisha ta shigo tana Fadin"Amina wayar ta Cika na kunna miki..Rike ta Hannunki na Fadama ya Danmallam Zai kiraki yace..!
Ta Fada tana mika mata wayar ta karba tana Tura baki ya Aisha ta Dunguremata kai Tana Fadin"Kinsan Allah ki fita Daga idonaa Amina na Rufe..!
Zamu zo mu Tsara abubuwan da Zaki rika koya fanni girki da gayu dasauran abubuwa sannan har karatu Zamu rika yi,ga yakaka nan na san ban da matsala zata koya miki Dubarun Zaman duniya..!
Yakaka tace"Ai ita Duniya basai an koya maka Dubarunta ba..Ita ke koya maka yin Hankali da ita..barni da ita ai muna Tare har Madina in tayi ba Daidai ba tasha rankwashi..!

Amina tace"Tab wazai bisa madinan..?
Ya Aisha tace"Yakaka kina jinta ko..!?
Tace"Yi tafiyarki barni da yar nema..!
Bata lambar mijin nata ta Kirasa da kanta..!
Ya Aisha tace"Munyi mgana yanzu yace zai kirata..!
Yakaka ta amsa da Toh fita Aisha tayi ta barta da yakaka sai Fada take mata ta shiga bata labarin irin yadda tayi gwagwamarya agidan kakan su Usman Cikin mata Biyu har sai mijinsu ya rasu ana ta Kishi da ita Amina dai tayi bakam tana jinta kafin tace"Yakaka in ka hadu da masu asiri fa suna zuwa gidan Boka..?
Yakaka tace"To Sai me..,?
Ai akwai su duniya ta lalace sai ka koma gefe ka rike Allah ka sa aranka Bawa bai isa yayi maka abunda Allah bai maka ba..yar nan rike gaskiya ki rike Allah ko min Dadewa gaskiyanki Zata bayyana sannan Allah baya barin Azzalumi da sannnu hakki zai bayyana .!
Kai ta jinjina domin ta gamsu da mganar Yakaka suna Cikin hirar ne Taji karar wayar dake gefenta da Farko ta Firgita sai da Yakaka tace mata wayar tace sannan hankalinta ya kwanta Mikewa yakaka tayi da Go ranta ta fice tana Fadin"Mgana mai Dadi kuma ban da Tura masa wannan bakin..Ki ce sabuwar amaryansa tana gaishesa .!
Ta fice ta bar Amina da waya a Hannunta sai da ta Katse sai kuma ya Sake kira tabi jerin lambobin da kallo bata Nigeria bane,Daukan wayar tayi Domin sak irin ta yaya ce tasan yanayinta tana Daga Kiran taji Sanyayyar Muryansa yana mata sallama sai taji kamar an kwara mata Ruwan sanyi ko"ina na jikinta yayi Sanyi har Bakinta ma yayi nauyi ta kasa amsa mai sai da ya maimaita sannan ta iya amsa murya shake Cikin Haibansa yace"Amina ya jikin ki..?
Tura baki tayi kamar yana ganinta kafin tace"Ni ai lafiyata kalau..!
Gemunsa ya sosa kujeran Office dinsa tana Dan juyawa dashi,yace"To ko ya nauyin jiki zan ce..?
Amina sai taji kunya ta kasa mgana cikin wani yanayi yace"Nayi ta Kiranki ban samu ba tunda Hajiya tace min ta baki wayar..!
Uhm kawai tace ya Cigaba da Fadin"Amina kinga lamarin Ubangiji ko..?
Wannan rabon Dake Tsakanin mu shine silar Faruwar duk abunda ya Faru..!
Amina tayi shuru batayi mgana ba shims shurun yayi kafin yace"Ba inda ke miki ciwo ko..?
Amima sai taji wani Rauni ya shigeta kafin tace"Eh..!
Cikin Rudewa yace"Eh kuma..?
To ina ke miki ciwo..?
Amina kai Tsaye tace"Menene mgani in an yi ma mutun sihiri sannan ta wata hanya Zai gane an yi masa..?
Umar yaji mamakin mganarta Cikin mamakin yace"Amina waye akayi ma Sihiri..?
Cikin wani yanayi Amina tace"Ni ce..!
Baki ya Bude kamar tana ganinsa Cikin mamaki yace"Ke kuma..?
Ta ce"Eh..!
Sai kuma kawai ta Fashemai da kuka Har da Sheshsheka Saboda Dacin abun na taso mata lokaci Daya Rauninta na bayanna.
Danmallan jikinsa yayi sanyi Cikin wani yanayi yake fadin"Kinga Amina..bar kuka nan yimin bayani yadda zan gane..!
Ina ko jinsa batayi sai faman kuka take yi Dagacin kukan datake yi Daga karkashin Zuciyarta ne kansa ya Dafe Cikin wani yanayi duk da yasan yarinyar akwai kukan banza har da na siyarwa sai dai jin kalamanta da wannan kukan datake yi tabbatar wani ya faru wanda kedamunta acikinta kuma ta kasa fadamawa kowa..!
Cikin sigar lallashi yake fadin"kiyi hakuri ki daina kuka sanar dani abunda ke faruwa..!
Sai taji muryansa kamar wani waraka ne ga matsalanta yasa tace mai cikin kuka"ban taba Fada ma kowa ba sai kai..Wlh duk abunda Zan fada maka ba karya bane ya Dannallam..!
Da Sauri yace"Eh naji bazan Fada ma kowa ba taimakeni kibar wannan kukan saboda yanayin Dakike Ciki..!
Amina ta share Hawaye tana jan majina tace"Yaya..Yaya. !
Ta fada sai kuma ta kara sakamai kuka Umar ya shiga wani yanayin Tashin hankali da jin kukanta Cikin mamaki yace"Yaya. ?
Amina tace"Eh yaya ba mutuwa tayi ba Kasheta MAMANMU tayi..!
Ta fada tana matse bakinta kada kukanta ya kara fitowa yana Zaune ne sai da ya mike Cikin wani yanayi a Muryansa yace"Yaya ba mutuwa tayi ba kuma..?
Mamanmu ta kasheta..?
Amina ta amsa mai da Eh Cikin kuka Umar ya katseta Cikin Muryansa da kaifi yace"Ki bar wannan kukan yimin bayani sosai yadda Zan gane..!
Amina sai kawai taji ta yarda Data Fadama Danmallam abunda taji ko zai Daina Damunta aranta ko Zata Samu Saukin abunda take ji..
Cikin kuka ta fara Fadamai komai Tun farkon wayar da taji Anty Amarya nayi a ranar da Hajiya tace zata tare da kuma Ranar da Ta kama mamanmu tana mgana da duka mganganunta,Sai dai ta Boye sunan Hajiya Uwa tunda bata san meye Tsakaninsu ba..
Amina ta sharbe hawaye tana Fadin"Da kunbina naji suna waya ya Danmallan..Da kunnina naji mamanmu na Fadin malaminta ta saka ya kashe mana uwa Saboda ta Samu Aba yadda take so Sannan da kunnena naji tana Fadamin Ba ni taso na ZAMA haka ba ya Jafar taso ya lalace da kunnina naji Tana Fadin Bazan haihu Dakai ba Sai Sakina sannan sukace har Abada sai dai aurena Dakai ya kare a gantali..Zuciyata tana min Zafi tun Ranar da naji haka..nayi kukan rashin Uwa Ya Danmallam bansan Dadinta ba Duka Mamanmu ta nesanta dashi ya Zanyi..? Abun na Damuna Zuciyata zafi take min kamar Zan mutu. !
Ta karishe fada Cikin kuka Danmallam Zufa kawai yake yi kansa na juyawa Mamaki da Dimuwa da al"ajabi sun kamasa ya kame awaje daya salati kawai yake maimaitawa acikin Ransa kafin ya samu yar natsuwa Cikin Wani irin Sauti yace"AMINA..!Kin tabbatar da mganar da kika Fadamin..?
Amina ta kara fashewa da kuka Tana Fadin"Wlh in nayi maka karya Allah ya..!
Da Sauri ya Katseta da Fadin"Amina ba kyau irin wannan rantsuwan ba kyau..!
Sai yaji yama kasa mgana Saboda mamakin abunda yaji,Amina kuka ta Cigaba da yi kamar ranta zai Fita yana jinta ya kasa mgana sai chan yace"Kin Sanar da Hajiya ne..?
Saboda yana tunanin kodai Hajiya ta sani ne Data Dauki wannan matakin sai Amina tace bata Fadama kowa ba...kansa ya Daure Tunaninsa ba Lokaci Daya bane yana Bukatar natsuwa Cikin lallashi yace"Ki daina kuka..Sannan ki cire damuwa aranki..Zan yi Bincike a barayina in dai mganar ki gaskiya ne akwai yuyuwar kowa yaji labarin nan,Alkawari Zaki min zaki Daina Tunani da Damuwa bakin gayamin ba .?
Da yardan Allah komai zai zama Daidai kada ki damu..!
Amina ta koma sheshshekan kuka tana Fadin"Haka mamanmu ZAta kashe mana uwa a banza kenan ya Danmallam..?
Kai ya girgiza kafin yace"Ai hakkin Rai ma bazai barta ba Amina..In ma da Gaske ne Allah bazai barta ba sai ya Wulakantata aduniya..Sannan ai Allah ya nuna musu basu isa ba..Suna nasu ne Allah shi kuma yayi nashi..Amina Kina da juna Biyu wannan kadai ya isa kisan Allah ne Kadai mai yi alokacin da yaso a kuma Sanda yaso..!
Amina taji jikinta yayi sanyi ammh bata bar kuka ba shi kuma ya tattaro Jarumtarsa yana ta bata baki da lallashinta Shima kenan datake da shekaru ya shiga wannan Halin balle ita mai karancin shekaru kamar Amina..?
Dakyar ya samu Amina ta bar kuka shi Tunaninsa ma kada Damuwar ta Haifar da Matsala ga abunda ke Cikinta sai da ya tabbatar da ya lallasheta tare da alkawarin komai zai zama Daidai ya karishe da Fadin"Zan zo Gida watan gobe..In nazo sai mu Sake zama muyi mganar musan yadda zamu bullo ma lamarin ni dai ki daina Damuwa Sannan kada ki Fadamawa kowa..!
Amina ta gyada kai kafin tace"Zaka zo nan ne..?
Wajena..?
Yace"Eh zan zo na ganki naga yadda Kika koma in kuma ga yadda Cikina ya zauna ajikinki !
Sai kunya ta kama Amina ta kasa mgana shi ma bai wani Damu ba,baya Cikin natsuwarsa Daganan ya mata sallama ya katse kiran.
Zagayen office dinsa ya farayi kansa ya Dafe ya shiga Tunanin mganganun Amina bai san mamanmu a boye ba sai dan Zahirinta Daya sani kadan ana Fadin Kirkinta,ko abakin yaya yasha jin haka Sannan shi bai da wani Sakewa da ita iyakarsa su gaisa sannan ita kanta Anty Amarya gaisuwa ce Tsakaninsu har gwara itama sukan yi Doguwar mgana Sanadin Sakina Sai dai kuma ya fara jiyo kamshin gaskiya kan mganar Amina Duba da Yaya ance Lafiyalau ta kwanta sai gawa duk da ita Mutuwa ko da Ciwo ko ba Ciwo sai an tafi..!
Ammh Amina yarinya ce ba yadda Zata Zauna ta Tsara mgana haka in ba ji tayi ba Sannan ya tuna yadda Sakina tada hankalinta kan Auran sa da Amina da kuma Matsalan data Faru tsakaninsa da Sarood Aliyu ya fara Hangomai Lamarin a matsayin Shihiri ammh bai yarda ba sai da Mallam ya sanar dashi Cikin Hikima har ga Allah bai zargi Sakina ba ammh kuma yanzu Dayaji wannan mganar sai ya shiga kokonta ya tuna Bakin kishi Sakina da Burinta ita ta Samu Ciki ta Haihu har wani Lokacin ya Dinga mata Fadan ta roki mafi alheri..
Bawai ya yarda da mganar Amina Duka bane sai dai kuma ya shiga Rudi da kokwanto agidansu ake wannan Tsantsan jahilcin da mugunta har da kashe rai..!
Indai ko gaskiya ne Anty Amarya da mamanmu Allah bazai barsu ba sannan sai ya nuna musu basu isa su raba auran da Allah ya kulla da kansa ba.
Cikin tashin Hankali ya kira jafar a waya yana Tambayansa Amina na karya?.. tunda sun fisa sanin yarintar ta shi ba mazauni banw baisan komai kan Rayuwarsu ba.
Ya jafar ya fara fada yana Fadin"Hala iskancinta ta maka..? Ai Amina sai Allah..Wlh ya Danmallan ka daina Sake mata ne. !
Cikin haushinsa yace"Tambayata zaka bani amsa ko zaka Tsaya kana gayamin abunda zan yi da matata ne..?
Saj jafar ya rike baki yana yar Dariya kafin yace"Amina bata da Halin karya..Bata da kumbiya kumbiya ita Free take abunta bata da Tsoro sannan tana da kafiya da Taurin kai yadda kasan zuciyan kafuran farko bantaba ganin wanda duka baya Sata tayi Laushi ba sai Amina..Ko zaka kasheta sai tayi mgana sannan abunda yake gaskiya take fada
Bansanta da karya ba gaskiya..Sai dai Rashin kunya da tsiwa da Tonen fada da Yawon tsiya..!
Danmallam ya jinjina kai alamun gamsuwa kafin ya Datse kiransa ya jafar afili yace"Ko son Amina ya Danmallam ya fara ne..?
Dariya yayi kafin yace"Tab..bai Fada hannu na gari ba..Amina ai jidali ce..!
Danmallam kuwa suna gama mgana ya saki Huci Amina tana da gaskiya wani abu na Faruwa sannan ya Fara ZArgin Hajiya tasan wani abu shiyasa ta hana Amina ta zauna a gumel sannan kuma ta hana kowa yasan da Cikin jikinta tabbas ya hasaso wani abu..
Sai dai koma menene ya kamata yaje Negaria yaga Amina su yi mgana sosai sannan yaga ta ina zai Bullo ma al"amarin da ke faruwa agidansu karkashin Tarbiyan mallam..?
Lalle ana Zaton wuta a makera sai aka sameta a masaka..Zuciyarsa ne taji ta Bude da duka mganar Amina da Tsausayinta da bai taba jiba ba..Dole ya tafi gida cikin watanan mai Shiga abubuwa Dadama suna Bukatar yaje ya gabatar dasu tukunnah..!








*Janafty*

*TFZB2018*

*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*

Tun daga ranar Danmallam bai taba kwana batare daya Kira Amina ya lallasheta ba ganin da gaske fa abun na cinta aranta Fatansa Allah yasa kada Damuwar ta haifarma da abunda ke cikin wata matsala sannan bayaso ta fadama kowa abunda ta Fadamai mganar tana Bukatar Bincike da Lura sannan ba kowa bane zai iya Daukan mgar har ya Fahimceta sannan yayi tunanin mafita Shiyasa yake kokarin kiran Aminar yana amfani da Hikimarsa wajen kara Lallashinta da bata Baki.
Wani Lokacin yafi Kiranta in yaje Wajen aiki ko in ya bar gida Zashi masallacin Madina ammh in yana Gida baya Kiranta Daga ita har Sakinar saboda Gudun matsala Ga Sarood kamar ta goyasa haka take ji Dashi bazai so yayi abunda zai ci mata Fuska ba shiyasa yake kiyaye wasu abubuwan sannan nauyi ne akansa ya kwatanta adalci Tsakanin mtansa.
Abunda Amina ta Fadamai na nan aransa kamar ya Tuntubi Hajiya da mganar sai kuma ya fasa yana Tunanin ta ina Zai fara duk da fa yana da Zargin Hajiya tasan wani abu Shiyasa ta Boye Amina da Cikin Dake jikinta,Mallam ma kamar Zai mai mgana sai kuma yaga ai bai da wata Sheda itama Aminar ji tayi bata Nadi murya ba Tunkarar wani da wannan mganar ma a yanzu bai taso ba,Sannan abu ne na Kashe rai duk da daman kowa yasan Mutuwa ta Allah ce sai dai mutum ya Zama Sanadinta.
Bangaran Sakina kuma ai ya Dade da Fahimtar mganar Amina Hakane kodaga yadda bata taba mai mganar Amina ba Ranar Dayake so? ji ta? Bakinta suna waya sai Rigima take mai kan yaushe zai zo ya Dauketa..?
Ita ta gaji da Zama agarin nan baya nan sannan ta yi bari tana son maida Cikinta,Mirmishi kawai yayi kenan mganar Amina ta fito su Burinsu kawai Sakina ta Samu Ciki ta Haihu..?
Saboda ya jarabata yasa yace mata Bata taba Tambaynsa ina Amina ba..?
Sai Sakina tayi Tsaki kafin tace"To ni ina Ruwana..Tunda ta bar min gidan mijina ban damu ba..Ba"an ce hajiya takai ta wani waje ba..?
Yana jinta ammh Daganan bai kara mata mganar Amina ba Itama Sakinan bata Damu ba,ita kamar ma Dadi Take ji tunda ta bar mata gidanta ai taje koma ina ne bata Damu ba Allah ya raka taki gona..!
Allah duk ya shafe musu Tunanin Mezai sa rana Tsaka a Dauke Amina Daga Gumel..?
Duk basu yi wannan Tunanin ba Idonsu ya Rufe da nasu Cikar Burin dukkansu.

******

Usman mijin Aisha ya Dawo washegari suka kai Amina asibiti shi da Aisha speacialist? Hop suka kaita Inda Aisha ke zuwa in Bukatar Hakan tataso,anyi mata Scan cikin Amina Har ya shiga wata na Biyar sannan jininta yana sama kadan Saboda Tana saka Damuwa sannan kuma Sugar masu Ciki na son kamata ammh ita da Abunda ke Cikinta suna Cikin koshin Lafiyan an bata mganin karin jini su Vitamin c da sauransu sai kuma? na cin abinci tunda Aisha Tayi Korafin batacin abinci Likitan yace Normal ne indai tana cin abunda Cikin yake so ba wata Damuwa...!
Ya sanar dasu zata fara zuwa awo Duk bayan Sati Hudu sannan in yayi? shiga wata shidda za"a sake mata wani Scan din
Basu Dade a asibitin ba suka Dawo Gida suka ijiye Amina suka kara Fita kasuwa suka shiga Aisha ta Zabo ma Amina Dogayen Riguna guda Biyar da Wanduna plazo sai ruguna masu yalwar wadanda zasu mata Saboda ta kara kiba kaya wanda tazo dasu sun mata kadan sannan nata bazasu wadaceta ba.
Data kawo ma Amina taji Dadi sosai kamar ta goya ya Aisha tana Daga rigunan adakin Yakaka take fadin"Yakaka kalli Rigar nan bata miki kyau ba .?
Tana zaune saman Cafet tana Gogan goranta tace"Sosai ma ai sai ma kin sakata Ajikin ki takwarata ai mu duk kayan da muka saka sai ya karbemu..!
Ya Aisha na Dariya ta Fice tana Fadin"Ki fito kiyi ma Darling godiya yana Falo..!
Amina in Aisha ta Kira mijinta Da Darling mamaki take bata,agida shuru shuru kamar bazata aikata ba kamar ma batasan komai ba.
Kwashe kayan tayi ta maida a leda ta Saka Hijabinta ta fita falo ta Durkusa tama Usman godiya ya amsa mata yana Fadin"Bakomai Matar yayanmu..Kin dai ji abunda Likita yace ko..?
Ta gyada mai kai kanta na kasa tana jin kunya ya cigaba da Fadin"To sai ki yaye in kina Bukatar wani abu ga Sweety nan ga kuma Yakaka Dukkansu They are Their for u..!
Kanta na kasa ta amsamai Lokaci Daya damai godiya kafin tatashi ta koma Dakin yakaka tana Santin kayanta ta gwada wannan ta gwada wannan tana nuna ma yakaka ita kuma tana yabonta Amina ta gwada wata Riga Mai yalwa ta juya ta Sake juyawa kafin tace"Sai yanzu najini Daidai...Ammh wacce ya Aisha ta bani jan nan tamin kadan fa yakaka..!
Yakaka tace"To Daman ai irin wannan ne Daidai dake..Daga gani ba wani Girman Ciki Zaki yi duk a kiba Zai tsaya .!
Amina ta bata rai kafin tace"Wai sai nama kara Kiba yanxu..?
Yakaka na cin soyayyan gyadan da su Aisha suka siyomata a kasuwa tace"Af ai sai kin ninka kibanki na yanzu..
Ai sai Amina ta Zauna akasa ta Fashe da kuka Yakaka ta saki baki tana kallonta Kafin ta tabe baki tana Fadin"Yarinyar nan kin samu waje..Ki bari Balaraban Madina yazo sai ki mai wannan shagwabar..!
Amina Ta tura baki Batayi mgana ba Yakaka tayi Dariya kafin tace"Tsoro kike ji kada su kwace shi..?
Amina tace"Tab..Allah ya Tsareni ni bana tsoron su har ita gajeran ma..!
Yakaka tayi Dariya kafin tace"yauwa haka nake son naji Tsoro ai ba namu bane..kada ki Damu kina Haihuwa Zaki Dawo silandiyan dinki..!
Amina ta washe baki Tana Fadin"Da Gaske kike yakaka..?
Yakaka tace"sosai ma ai mu ko da kiban mu muka je mune agaba bazamu taba komawa baya ba. !
Amina ta amsa da wlh kuwa Daganan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login