Showing 51001 words to 54000 words out of 265571 words

Chapter 18 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28929

nufosu gadangadan tana Fadin"Kaga min yan iskan yara marasa Tarbiya..!
Kafin kace me sun Zura a Sittin Amina ce kan gaba sai hanyar waje suka Nufa suna Dariya Ta riga ta saki jikinta Tana kuma Gudu tana waigen su Hanne Dake bayanta sai ji tayi Ta buge Mutum agabanta Da kuma karar Faduwar wani abu wanda ya bada Sauti Tus...chas..!
Baya tayi da Sauri bayanta ya Bugu da Goshin Hanne Dake bayanta Sauran Kadan su Fadi Hamida ta Rikesu tana Fadin"Zaku fadi fa..!
Sai alokacin Hamida ta ga wanda Amina taci karo dashi ta kuma Lura da yadda Haraban Gidan ya Cika da maza bayansu ya Jafar har da wasu bakin Fuska ma.
Salati ta saka ranta Jikinta ba inda bai Rawa hanne kuwa datagama Fahimta baya ta koma tana Kifta ido kamar wacce tayi karya
Amina kuwa Tsoro ne ya kamata sanda ta Dago ido ta ga Ya D'anmallan agabanta Fuskar nan tasa ba Annuri ko Kadan Cikin Shigarsa wacce ta kara Fitomai da kyansa da Zatinsa Lokaci Daya da kwarjinsa.
Shikadai ne bata iya Hada ido dashi bazata iya jure kallonsa ba Tunda suka Hada ido taji gabadaya bakinta ya Mutu gabbanta sun saki ta yi Saurin Sadda kanta kasa tana Bin waayarsa Tadata watse akasa kenan lokacin data ci karo dashi Tayi sanadiyar Faduwar wayar.
Kamar wacce aka kai kasa haka ta durkushe ta fara Tattara wayar tana Fadin"Bansani bane..Kayi hakuri..!
Su Hanne suka saki baki suna kallonta Hankulan mutanen Dake wajen ya Dawo kansu har su ya Shamsu sun matso da ya Nazeem kallonta yake tana Tatarra wayar tayi Daidai yace"Amina ce ko..?
Wlh Yaya kaci Ubanta yarinyar nan sam bata da Hankali..!
Bata kara mgana ba sai da ta Tattaro wayar ta Mike bata yarda ta Kallesa ba ta mika mai wayar kanta na kasa.
D'anmallam Cikin Takaici yake kallonta ya kasa karban Wayar wai meyasa yarinyar nan bata da natsuwa ne..?ji yadda ta kwaso gudu kamar wata ballagaza kamar wata Namiji..?
Ganin yaki karba yasa Abokinsa Aliyu Dake Gefensa ya saka Hannu ya karbi Watsatsiyar Wayar yana Fadin"Ba kyau gudu acikin gida..!
Yafada yana kallon Amina acikin Ransa yana Tunamin ko kanwar Danmallan ne to bai santa ba.
Sai da yayi mgana ne Amina ta Dago suka Hada ido da Aliyu sai alokacin tasan ba Ya Da'nmallam ya karbi Wayar tasa ba.
Gabadaya taji ta muzanta ne ganin da Maza awajen yasa ta Ja kafafunta zata wuce su hanne kuwa suna gefe sun Rakube kamar wasu marayu.
Ba zato kawai taji wani Dogon Hannu mai Laushi ya Riko Duka Kafadunta da karfi ya Dawo da ita gabansa Cikin Mutuwar jiki ta Dago manyan Idanuwanta ta Sauke a nasa da suka Fara Sauya Launi saboda bacin rai.
Ya Jafar suna chan nesa suna Hira da wasu abokansu su ya Nazeem ne ke kusa ya Nazir kuma yana chan gefe saman manyan Darduman da suka shimfida a Haraban gidan yana kallon meke Faruwa ammh bai maida Hankali ba Chart suke da Hidaya matarsa Tana Fadamai Hayaniya ya Isheta sai yake tambayanta tana ina..?tace tana Bedroom din Hajiya inda ta Sauka shi bai ma tsaya lura da abunda ke Faruwa ba.
Kamar mayen karfe haka suka Tsaya suna kallon Juna shi yana mata kallon Haushi da Takaichi ne ita kuma ta kasa Sauke idanuwanta ji take kowani gabobinta suna yin Sanyi kamar yana Hukuntasu duk Rashin kunyarta yau sai da aka ga Tsoro a cikin Idonta Lokaci Daya kuma Jikinta ya fara rawa.
Ya Shamsu ne ke fadin"Yaya ka bari ni na Chasa su basu jin mgana Daman Abida ta kawo min karan su jiya Wajen Walima suna ta Satan Takeway kamar baza"a abasu ba kuma Shugabar su Amina ce gatanan batajin mgana ta Raina kowa..!
Awannan karon a Saman Labbansa ya Furta"Sata again..?
Meke damun yarinyar nan ne..?tana so ta zama Wata gangarriya..!
Sai alokacin ta iya Sadda kanta tana jin kamar kafafunta bazasu iya Daukanta ba.
Cikin Muryansa mai Sanyi Da Zaki yace'"Meyasa kowani abu sai ace ke..?kece Satan nama..?abinci..?rashin kunya Kazanta sannan Main din shine Rashin Natsuwa..?ke kadai ce agidan..?
Ina ce su Hannatu age Mate dinki ne..?
Why..?
Ya fada yana Jijjiga Kafadanta kafin ya Saketa da karfi yana Fadin"Abunda ke Raba Mace da Namiji shine Natsuwa da kamewa..Duk macen da bata da Natsuwa sannan kazama ce ita..Sunanta ba Mace. sunanta ballagaza..!
Yafada yana jin Bacin Ransa na Sauka da Hannu ya nuna su Hanne yana Fadin"Daga ina kuke..?ina zaku cikin maza awaje..?
Hanne kamar tayi kuka tace"Ba..ba ko"ina..!
Hannu ya daga ya nuna su dashi yana Fadin"Duk yaran Dake cikin gidan nan ko yara kanana iyayensu basu bar su sun zo suna guje guje ba sai ku..?Ku yara ne..?wato duk iskancin ku da ake Fada akanku gaskiya ne ko..?
Hanne ta kwaso Rantsuwa tana Fadib"Wlh Yaya..!
Shutt up..!
Ya katseta da Karfi Cikin Bacin rai yace"In kun raina su Jafar ni sai na Ladabbar daku kafin na koma ku bar ganin bana Duka inna na Fara Dukan yarinya sai na Fasa mata jiki..Comom Ku wuce ko ku koma cikin gida Wlh ko da Wasa na ga Fuskar Daya Daga Cikin ku bama awaje ba anan Haraban sai na Karya mata kafa Daya..!
Ku wuce ku bama Mutane Waje..Wawayai kawai kun girma bakusan kun girma ba..!
Ai kafin ya Rufe baki su Hanne sun juya Sumai sumai sun wuce Amina ce kanta na kassa da idon kowa ke kanta ta kasa gaba ballatana baya Sau Biyu kenan ya Taba Tozartata na Farko Ba Mutane ya Abida ce kadai sai su Hanne yau kuma bayan su Ya Nazeem har da Bakib ido..
ya sake kiranta Barauniya,Sannan yasake ce mata kazama kuma yau harda ballagaza Gabadaya sai taji Ruwan Hawaye sun cika idonta aranta Fadi take"Ni ba barauniya bace..kuma ni ba ballagaza bace..!
Ammh ta kasa Furta haka afili Tama kasa wani motsi.
Aliyu ne ya Dafasa yana Fadin"Cool down Shehi..Bana som Fushin nan naka mara kyau..!
Ya Nazeem ne ganin Amina taki tafiya yace"Au ke bazaki wuce bane..?
Ya uzairu yace"Duka fa take so ya Nazeem ba"a shiga Jikinta bane..!
Mamakin Tsayuwarta yake Cikin Daga Harshensa yace"Bazaki wuce ba..?
Yafada kuma yana Daidaita Fushinsa Da Sauri Aliyu yace"Amina wuce ki koma Cikin gida kin ji ko..?
Ya fadi sunanta kamar yadda yaji an Fada Bata Dago ba kamar wacce muryansa ta bata gwarin gwiwa maimakon ta Juya sai ta fara Tafiya kawai da Sauri ya Shamsu yace"Ke ina zaki..?
Daman wanda zata Huce akansa take nema wanda yayi mata yafi karfin ta Ja dashi yasa jin muryan Shamsu ta waigo cikin Fada tace"To gida zani..!
Tafada Lokaci Daya tana Sakarmai Idanuwanta tana kuma Murgudamai baki harda Harara sai kuma Hawaye dukkansu sun gani Shamsu ya Zaburo yana Fadin"Ke ni kike juyama baki..?zan karyaki in na rike ki..!
Amina ta Tsaya kyam tana Fadin"gani..Kada kabarni da rai ya shamsu don Allah..!
Tafada tana kallonsa da Jajayen Idanuwanta..
D'anmallam yakalleta ta fa Daina bashi mamaki Aliyu yace"Kai shamsu kyaleta..baka ga yanayinta ba inajin ba ita kadai bace..!
Ya Nazeem yayi Dariya bai ce komai ba acikin Salo Salon iskancin Amina wannene basu gani ba
Ya shamsu yace"Wlh lafiyarta Kalau..Duk Salon rashin kunyarta ne Daman bata tsoron kowa ta bari nazo ta gani..!
Ya fada zai nufeta yaji D'anmallam ya Dakamai Tsawa yana Fadin"Shamsu kyaleta...
Ke bar nan wurin..!
Ba musu ta juya bayan ta kara juyama Shamsu baki tana kunkuni ta wuce tana Sharan kwallah D'anmallam ya Saki Siririn Tsaki yana Fadin"Kazama kaawai..!
Ya Uzairu yace"Yaya da ka bari Shamsu yaci Ubanta..Ko"ina ta Addabi mutane chan ma bata bari Baba Sa"idu ya Huta koda yaushe Fitinarta..!
Hannu ya Dagamai yana Fadin"Nace ku bar mganar ko..?
Dole suka koma suka zazzauna shi kuma sai Sakin Huci yake Kafadarsa Aliyu ya Dafa yana Fadin"Allah huci Zuciyar Shehi..Ungo wayarka kila sai ta Hau kan Teburim mai gyara..!
Karba yayi Lokaci Daya yana ganin yadda Sreen din wayar ya tashi aiki.
Karamin Tsaki yaja kafin yace"Yarinyar nan bata jin mgana..kamar ballagaza bata da natsuwa ji asaran da ta jamim
Wayar nan fa sai dai na Sauyata ta gama aiki..!
Aliyu yace"Is ok..Kayi Hakuri muna da kudin Siyan wata kannen namu ne sai Hakuri..naji Uzairu na Fadin Baba Sa"idu Hala Diyarsa ce..?
D'anmaallam ya gyada kai bayason mgana ba Domin Kada mallam yayi Fada da Tuni yana gida ya kwanta ya Huta.
Aliyu yace"haba na kamar su da Yaya..Hala Diyarta ne..?
Nan ma kai ya gyadamai Aliyu ya Kalli Umar yana shafa gemunsa yace"Irin su ne Sweet Sisty Shehi..Anya bazan kama Daya Cikin kannen nan namu ba..?tunda kai ka yi auranka da balarabiya..!
Danmallam ya kallesa a adage kafin yace"Wadanan yaran zaka kwasa..?
Aliyu yace"ofcourse sun fi Dadin harka ne..!
Danmallan yayi Tsaki kafin yace"Wlh baka da Hankali..kai yanzu Gemi gemai dakai AA kace wadanan yaran kake so ka aura..?Ya"yan Cikinka..?
Aliyu yace"Bangane ya"yan Cikina ba..?nifa ba Tsoho bane mallam Shekara Talatin da taran ma ban cika ba..Sai watan jibi..!
Wani Tsakin ya kara ja kafin yace"Me yayi Saura a arba"in AA..?Wlh da auran Fari mukayi dukkanmu da muna da kamarsu ko basu kai su ba suna Tsaransu..!
Aiyu na Dariya yace"Kai nifa ba Tsoho bane..Ko yanzu naso zan auri yar 12 ma ballatana yaran nan sun Haura 15..!
Dan mallam ya Dafe kansa kafin yace"Plz ka kyaleni da wannan Shirmen naka am not in d Mood..!
Aliyu na Dariya yace"Kai Shehi..Kaifa nasan sai ka cike kofa Danmallan fa kake..!sunnar nan sai ka ciketa..Ina baka Shawara in zaka kara ka karo irin yan yaran nan sun fi Dadin Sha"ani nidai kar ka manta ina kamun Daya Daga Cikinsu duk wanda ka bani am Greetfull..!
Danmallam ya fara ma Aliyu kallon ya Tabu ganin haka yasa ya Buga Kafadarsa yana Fadin"Am Serouis fa Shehi..!
Danmallam ya Kauda Fuska yana Fadin"Plx ka cireni cikin Shirmen naka..Kuma wlh in kace zaka auri irin yaran nan sunanka Sorry ka kai Jidali Gidanka da kanka am Telling u..!
Aliyu yace"Eh bakomai..Tanque for ur Advice..!
Ko kara kallonsa bai yi ba shi kuma Aliyu na Dariya yace"Tunda ka gaji dani..Bari na kira Aliya nace ta fito ita da yaran mu kama Hanya..!
Kamar bai son mgana yace"Ka bari yaran chan su tafi mana..!
Aliyu yace"Wasu yaran..?
Yamutsa Fuska yayi kafin yace"Amaran mana..!
Aliyu yayi Dariya yana Fadin"Shehi Umar..Mijin Sakina ango Saratu..!
Hararansa yayi kafin yace"Sarood na ce maka..!
Aliyu yace"oh..Sarood kasan bakin ya saba da Hausa ba irin ku da bakin ya Juye da Laranci ba..Angon Balarabiya..!
Yake fada yana Dariya Danmallam Mirmishi kawai yayi kafin yace"kana da matsala AA..!

Sa da aka fara Haraman fita da Amare su Hanne suka Tabbatar da Amiba bata gidan sun Duba ko"ina basu ganta ba.
Zafira tace"To ina taje..?
Hamida tace"Gida ta koma fa..!
Zafira tace"Muje to..!
Hanne ta harareta kafin tace"Jeki a karya miki kafa..
Zafira ta kama bakinta kafin tace"Au na manta ne kai ban kara zuwa Bikin Gidan nan Wlh..mu achan gusai in ana Biki ba inda bama zuwa bamai Takura mana..!
Hamida da Hanne suka ce Hamm atare sun kasa mgana.
Suna gani aka fita da Amaran suna kuka ammh ba Halin su bi Tawagan masu Rakiya.
Falon Baba Maallam aka shiga Dasu Hajiya Babba,Sai Hajiya uwa sai Yaya kadai suka shiga dasu.
Baba Maallam da Aba sai su ya Danmaallam da Su ya jafar ya Nazeem ya Nasir ya Nazir dukkansu dai mazan suna ciki hatta su ya shamsu Sauran matan kuma suna Waje suna Jiransu Ciki harda Sakina da su Sarood da Aliya sakina taso ta bi Sadiya zuwa Dutse Umar ya hanata yace ta bari Daga baya.
Nasiha ne maallam yayi musu,Kadan Ba da yawa ba Domin yace duk abunda zai Fada musu an sanar dasu sai Aba shima yayi nashi sai Ya Danmaallam sannan ya Nazir sai su ya Jafar hatta su shamsu sun musu sallama.
Daganan Baba Mallam ya ba kowacce Qur"ani Izu Sittin da azkar da Casbaha yace in suka rike kyautarsa sun gama Lafiya..
Daganan ya mike suka fito shi da Aba da Hannayensu suka saka kowacce a Motar da za"a kaita gidan Mijinta suna kuka suna Daga ma iyayensu Hannu.
Su ya jaleela da su ya Nazifa da su ya Fatima duk suna Kofar gida bakin Motocin suna sallama dasu sauran matan suna daga cikin gida.
Daya Bayan Daya Motocin Amaran suka tashi sai fatan Allah yakai Lafiya sannan mata suka koma cikin gida.
Alokacin ne Danmallam suka shiga cikin gida shida Aliyu suka gaisa dasu Hajiya sannan yace Aliya ta fito su tafi sai da taje ta ma Hajiya sallama ta bata kayan Cincin na biki tana ta Godiya.
Kafin La"asar suka wuce Bayan sun Rabu kan suma suna nan zuwa.
Sallar la"asar kadai yayi a anguwan ya Shiga Mota ya koma gidansa ya kwanta Saboda Hayaniya.
Zuwa Dare gabadaya Amaren Dake nesa sun isa Mazajensu sun kira Baba Maallam suka shaidamai sai Hamdala gidan kuma sai aka Fara Hada hadan kayan Tafiya zuwa gobe hatta su Ya Jaleela ma Baba Mallan yace kada wacce ta kai mai jibi agida ya Jadwa ne kadai zai Dagama Kafa sai visan su ya fito.
Ya Akila da ya Fatima gobe zasu bi mazajensu su koma su jidda ne jibi zasu koma ammh gobe Dutse zata sauka bayan tagama ganin Dakin kanwarta ta wuce kano..!
Su hanne sai Dare suka ga Amina adakin Mamanmu taci kukanta ta Share hawayenta duk yadda suka so su Zolayata yau Amina bakinta ya Mutu kazil batace ba haka suka kwana gari na wayewa sun sani suka Fara shirin tafiya Hadda harta su ya Abida kuwa.
Kafin su tafi sukayi sallama da Zafira aranar zasu tafi Allah Sarki Sabo kamar kada su rabu,ko kafin su Dawo makaranta da yammah yan gusai sun koma,gida ba kowa sai goggo Husai da Ya Jadwa da Ya Jaleela da gobe jirgi zatabi zuwa Lagos ya Jawahir ta bi yan Gusai sun koma.
Ya Zahra ma jirgin yammah tabi ita da Mijinta Daman yazo Daurin auran sai ya Zulfa da gobe zasu koma ita dasu Ya Uzairu su ya Nazir da Matarsa tun safe suka hau jirgi suka koma Lagos.
Chan gidan Baba mallam ma kowace Danginta sun tafi yan maiduguri kadai suka Rage sai gobe zasu wuce Ya Jidda ta Sakina da Sarood sun tafi Dutse tun Safe,Danmallam yaso ya hanasu Tafiya Hajiya tace ya barsu su tafi sai gobe zasu dawo.
Ta bangaran kowacce Danginta sun Tafi Sai daidai su Baba Lami nata Faman gyaran gidan.
Koda sukaje Hadda Amina bata manta ba sai da Taja Mariya da fada aka Fitar dasu Waje Mariya ta rika yima Amina Allah ya isa.
Ta kalleta tana Dariya kafin tace"Allah ya isa taki ce awajen Amina kin ga kaina tafi Dubu..
Take fada tana ma Mariya gwalo sai Da aka tashi Hadda aka Sallamesu da aka shiga islamiya ba haka ta Dinga Tsungulinta sai da aka kara Kadata waje.









*Janafty*

*TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janaftyd'?*



*
Kimanin Sati Biyu kenan da Watsewar Bikin su ya Zulaihat baki na nesa da na kusa duk sun koma Gidajensu Goggo Husai ce mutanen Jordan da ya Jadwa basu Tafi da wuri ba saboda Mtsalan Visa sai cikin Satin nan suka samu tafiya.
Amaran suna gidajensu cikin Koshin Lafiya sai Fatan Allah ya Zaunar dasu Lafiya Bakin Madina ne kadai ya Rage basu koma ba suma suna ta Shirin Tafiya cikin karshen watan da muke ciki Zasu fara sabuwar shekarar Musulunci achan Madina din.

Yau ta kama Laraba ce Tun Safe Amina ke kwance kanta na ciwo Daga Dakinsu sai ta koma Dakin Mamanmu saboda Hamida ta isheta ta Mitar ta tashi ta gyara Kayanta data Zube kan gado wajen nemam Hula ta saka ma kanta ita kuma ta mata banza Tun bayan kallon Hamidan da tayi tana Fadin"Don Allah Hamida ki gyaramin kin ga fa ban da Lafiya..!
Hararanta Hamida tayi Kafin tace"Kin ma isa..?Wlh bazan gyara ba Daga neman Hula sai ki baro da Duka kayanki a kasa ai da gangan kikayi Tunda kinsan kina da mai gyara miki yau kam bazan yi ba ki tashi ki gyara da kanki ko kuma ki bar Kayan naki su Rube anan wajen..!
Amina kallon Hamida ta Rikayi acikin Ranta Tana Tunanin Hamidan ta Rage Mutumci yanzu ganin dagasken bazata gyara ba kuma tana ta Damunta yasa ta mike ta Bar mata Dakin Tana Fadin"Kici kanki ke Kadai..!
Allah yasa ya Zeenatu bata nan Tana makaranta Sai su agida tunda basu fara zuwa makaranta ba tukunnah.
Dakin Mamanmu ta shige ta Kwanta Chan saman gadonta Batama san tana ciki ba sai Daga baya ta shigo ta ganta Tashinta tayi tace ta tashi taci wani abu tasha Ko panadol sai da mamanmu tayi da gaske sannan Amina ta tashi tasha Tea ta Hada da Panadol ta koma ta kwanta Sai barci kuma barcin mai Nauyi ne ya Dauketa Ta Dadebatayi irinsa ba Tunda ba barcin Rana Amina keyi wani Lokaci ba.
Ba ita ta farka ba sai Wajen uku Saura na Rana taji kan nata ya Sauka sai kuma Kasala ya kamata ta kasa tashi ta koma ta kwanta Sama sama tana jin kamar tashin mganar mutane Daga Falon Mamanmu sai dai bazata iya tantance ko su waye ba Ita duk a zatonta su ya Zeenatu ne da Hamida yasa ta gyara Kwanciyarta sai Bayan La"asar taji mamanmu na Kiran sunanta Idanuwanta Cikin yanayin Barci da Nauyi ta Bude manyan Idanuwanta ta Sauke kan Mamanmu wacce ke Tsaye kanta tana Fadin"Amina ki tashi hakanan kiyi sallah kici abinci in kan bai Daina ba In Aba din ku ya shigo na Fadamai ko Asibiti sai akai ki..!
Amina na shirin komawa barcin Mamanmu tace"Tashi mana Amina...Kada ki koma barcin nan .!
Dole yasa ta mike tana Mika Lokaci Daya tana Fadin"Wash...!
Mamanmu na Shirin Fita Daga Dakin tace"Ki rika Salati mana Amina.!
Daga haka ta fice Daga Dakin Dakyar Amina ta zuro da Kafarta Ta Sauka Daga kan gadon tana gyara Zaman Doguwar rigar Dake jikinta na Wata jar Atamfa Sai ta Dauki Hulanta ta Rufe kanta sannan ta fito Daga Cikin Uwar Dakin kanta tsaye ta fito Falon Sai dai Fuskokin data gani ne yasa ta Dan Tsaya tana binsu da kallo kamar yadda suma suke kallonta.
SArood ne ta washe mata Fararan Hakoranta daya sa itama ta Sakar mata Dariya.
Sakina kuma Kanta na kasa tana Danna wayarta Sai da taji mamanmu na Fadin"Kin taso..?ki farayin Sallah sai kici abincin ina Fatan kan ya Sauka..?
Da kai ta mata mgama ganin yadda Sakina ta Dago tana mata kallon Sama da kasa,Mamanmu ta cigaba da Fadin"Matan D'ammallam ne suka zo mana Sallama jibi zasu koma tun Dazu suka zo Lokacin kina ciki kwance..!
Amina ko Tsayama bin mganar mamanmu batayi ba har takai Kofar Dakin Sanda Taji Sakina na Fadin"Yarinyar nan bata da kunya
Bata iya gaisuwa bane..?yar wajenki Hamida ta fita hankali da natsuwa..!
Sanda Amina takai Tsakar gidan Sai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login