Showing 39001 words to 42000 words out of 265571 words

Chapter 14 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28920

bisa gadonta ita da Hamida alokacin Ya Zulaihat bata Dakin ya Zeena na makaranta.
Hanne tace"kunsan wani abu..?
Hamida ce ta girgiza kai Amina kuwa Yamutsa Fuska tayi kawai duk da Hannen na kusa da ita ne.
Hanne tace"Ashe balarabiyar nan mai kyau dinan da ya D'anmallan yazo da ita matarsa ce..!?
Amina ta Zaro ido kafin ta mike tana Fadin"ki bari don Allah Hanne..?
Hamida tace"Nima naji Mamanmu da yaya suna mgana da safe..Wai Aba ya Fada musu jiya da Daddare..!
Hanne tace"Kwarai muma jiya Mallam ya taramu har da ita ya fada mana aka gabatar da ita acikin mu Ashe Diyar dai abokin Baba mallam ne na Madina ya aura ma Ya D'anmallan diyar tasa achan Madinan.!
Amina tace"Ya su Sa"adatu sukayi..?Ina Anty Sakinar..!
Hanne tace"Abun mamaki basu nuna komai ba Anty Amarya tafi kowa ma karban Abun tatashi ta Rumgume Anty Sarood din agaban kowa tana mata maraba..!
Amina tace"Jar uba..Wlh na karya ne..Wannan matar din..?
Hanne tace"Bakisan wani abu bama..Ta kwace ta Daga Shashenmu tace ma Hajiya ita ke Saukan Anty Sakina to yanzu bata Sauya ba ita zata Sauki Anty Sarood jiya ai shashenta ta kwana..Sai da Safen nan suka wuce gidansu kuma Anty Amaryan ta rakasu Mallan yace taje..!
Amina sam Labarin bai kwanta mata Baki ta Tabe kafin tace"Uhmm!
Daganan bata kara mgana ba aranta bata yarda don Allah tayi ba Matar da ko su Mamanmu suna Fadin Rashin Kirkinta sun ce ko Aba bata cika mgana Dashi ba tana jin Haushinsa Sabida Hajiya da Baba Malam.

Tundaga Ranar Amina bata kara yarda ta koma gidansu Hanne ba Duk kuwa da Tasan ya Danmallan yana gidansa ammh ai kusan nan anguwan yake zama Saboda bada sallah haka kurum taji batason su kara Haduwa Ya riga ya gama da ita tunda ya ce mata kazama kuma mara natsuwa bawai ta tsaneshi bane sai dai Acikin Ranta bai burgeta ba,duk da baya Duka ammh kuma yana mganar da zai saka ka kwana kana kuka aran Amina tasa masu sanyin Halin nan ba masu Kirki bane to Danmalam yana Daga cikinsu.

******

Shiryen shiryen Biki ya cigaba da Gudana ta kowani bangare kamar yadda Al"adar gidan mallam take ana Saura kwana Goma sha Hudu Biki Aka je akayi jerin Dakunan Amarya Tunda kayan suna isowa kowacce inda zata Zauna aka Sauke nata,Ikram aka fara ma nata Jerin nan Kusa da gidan Sarki Inda Dan Sarki Mahaifin Sultan din ya gina mai wani Dankarern gida su Mamansu suke je jeren su da su Hajiya,Sai Ya Zulaihat da ita agarim jigawa aka mata nata jeren agidan mijin nata Daya gina duk da kano zasu koma da zama inda yake aiki itama su yaya suka je dasu Hajiya uwa.
Sai Ya Sadiya itama Garin Dutse aka mata Jerin duk da itama bayan Bikin America zata bi mijin nata.
Ya Aisha sune yan kaduna Anty Amarya ce kan gaba ita da Hajiya Nasara da Mamanmu suke je suka mata Jerenta suka Dawo..
Daganan shiri ya cigaba da kamkama ta kowani bangare..
Tun ana Saura Sati Daya Biki baki suka Fara zuwa goggo Husai ita da Jadwa suka ssauka Daga Jordan gidan Dan"uwanta ta sauka Baba Sa"idu.
Asatin Shiri Daya akeyi na Walimar su ya Zulahait da za"a hada da Saukasu a Haraban makarantar Islamiyarmu za"ayi Taron,Gida ko"ina ya cika ba matsaka Tsinke duk da Baba Mallam baya son taro ammh ai bai isa ya Hana Dangi zuwa ba,Mutanen gusai ma sun iso,sannan ga su Ya Nazifa tazo jidda ma tazo ya Akila ma haka ya Fatima tazo gidan Baba Sa"idu ma ya cika su Jaleela yan lagos sun sauka jamila ce bata zo ba uwar mijinta ba Lafiya sai Jawahir itama ta iso.
Ana jibi Daurin aure Hidaya matar ya Nazir ta iso Daga Lagos ashashen Hajiya uwa take Sauka Daman in tazo,Ya Nazir sai jibi zai iso tace.
Amaran kuma Kaf dinsu suna Gidan su Ya Jafar chan Hajiya ta roki Baba Mallam ya bari suka tafi Danginta yan Maiduguru sun zo suna chan suna gyaran Amaran sannan Bakin bazanga ma mata sun zo mazan sai Ranar Daurin aure.
Kowa yazo yaga Balarabiya sai yace Daga ina sai ace Amaryan D'anmallan ne Abunda ke bama kowa mamaki yadda Sakina tajata ajiki Ko'ina suna Tare kamar kawaye,Sarood bata da Zabin kanta sai abunda Sakina tace kamar itace jagoranta.
Da su ake ta Hidima gidansu suke kwana ammh kullum suna nan anguwan Danmallam shi kanshi yayi mamakin yadda Sakima ta Saki Lokaci Daya sai da yafi kowa Murna da hakan ganin yadda ta karbi Sarod Hannu Bibbiyu Hajiya bata ce komai ba Domim ita a kan Hurumim D'anmallam Mallam yafi ta karfi ta wannan bangaran.
Amina Bakinciki take in za"ayi taro Saboda yadda kowa ke mai dasu jakai yayi ta sakasu aiki.
Kusan ita da Hamida da Hanne gidansu suke kwana Saboda su ya Zeenatu suma chan suka tare da Amaran yau aka kawo musu Sabbin kayansu da Hijabai Dukansu iri Daya na Amaran ne kadai ya bambamta sai na iyayensu mata.
Yau kwata kwata basu zauna ba sai saasu aiki akeyi,aikin ma na Wahalan Cirema yara pampers ko Ronensu su kuma suna ta aikin yi Cake da Donut da meatpie,suna ta sakawa cikin Takeway wanda za"a raba gobe wajen Walima ga Drinks nan da Ruwa cikin Falon Aba na Hidima da Rabo banda wanda ke chan Gidan Baba Mallam rabawa akayi nan ana Snaks gidan Baba Mallan suna gyaran kayan Miya na abincin da zasu yi su ya Jaleela kuma ana fama da suyan kaji da Nama.
Sakina dai bamai ganinta tana Shashen Anty Amarya ita da Sarood ko aiki batayi ba kuma wanda ya Damu duk da itama chan gidansu akwai Biki Tunda yayanta da suke Uba Daya Sadiyan zata aura.








*Janafty*
*TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janaftyd'?*

*Sadaukarwa ga Halima yusuf gwarzo (Besty) Alherin Allah ya kai miki har inda kike*

_Ya Allah ina rokon ka da ka Saukar da Farinciki,salama da kwanciyar hankali Da Aminci, zaman lafiya Da kaunar juna,sadaukarwa da yarda da,kima da mutumtawa, martabawa agidan auranki *AISHA ALTO* (Sisina) Allah yasa,kin shiga a sa"a Allah yasa gidan zamanki ne na har Abadan Da"iman Ameen_


*
Amina ta gaji da sakasu Reno ya"yan da ake yi ko kuma dawainiyar Cire pampers duk wanda Yarta ko D'anta yayi kuka su ake kwalama Kira su zo suyi Dawaniya Hamida da Hanne basu nuna gajiyawarsu ba sai Amina Domin ta tsani in ana sha"ani a Rika nuna su yara ne basu isa komai.
Dalilin haka yasa taja su hanne suka koma Chan koridon gidan wajen Dakunan da su ya Jafar sukayi zama Tun suna matasa sai ya zamana nan Aba ke sauke yan"uwansa maza in sun zo Daga gusai ko wasu baki dai Dakunan duka akwai Cafet da katifu aciki Wannan karon ma nan yan gusai suka sauka matan mazan sai Ranar Daurin aure zasu taho.
Cikin guda Daya su Amina ke kwana Tunda Dakinsu su ya Jaleela sun zo sun koresu chan gidan baba Mallam ma ko"ina ya cika Tunda kowani Shashe cike da yake da baki Daga Duka bangaran matan kowacce Danginta sunzo Shashen Hajiya ba matsaka Tsinke cike Taf da Danginta na Maiduguri.
Nan Amina ta jasu suna Fira Yawancin Firan Labarin Littafan Hausa ne da Amina ta smu yar"uwan yi suna ta Hiran Zafira D'iya take wajen Aba tunda Babbar diyar goggonsa ce Sa"aninsu Amina ce koma nace kawarsu ce suna Dasawa da ita Saboda indai Mamata mamanta zata zo da ita take zuwa itama ta fara karance karancen Littafansa Hausa shine suka Hade da Amina suna ta Labarinsu Hanne da Hamida Tagumi kawai sukayi suna kallonsu suna mamakinsu.
Amina ce ta kalli Zafira tana Fadin"Kin karanta garin kallon Ruwa...?Labarin Faruq da khaleesat..?

Hannu Zafira ta bata suka Tafa Lokaci Daya tana Fadin"Kai kai..Na karanta wannan Littafin yayi Amina..Salon soyayyar Faruq dabam ce..!
Tare suka saka Dariya Hamida ta tabe baki tana Fadin"Ke Zafira a ina kike samun Littafan nan kina karantawa..?ammh Mamata bata sani ba ko..?
Zafira tace"Anty Aina take dasu..In ta ijiye sai na sata na karanta kuma ina aron wasu a makarantar mu..!
Amina ce tace"Hamida munafuncinki ya baci..To bata Sani ba ko zaki je ki Fadamata ne..?
Hamida tace"Ina Ruwana..?ammh aikwai ranar da Dubu zata cika..Nama fi Tsausayamiki yadda su ya Jafar zasu Bandashenki Domin sai kin Daku Abunda ko Lokacin su ya Jadwa basu yi wannan karance karancen ba Sai ke..!
Amina ta daka wani Tsaki kafin ta Tabe baki tace"In sun kamani kada su bar ni da Rai kin ji Hamida..? Ni fa bana son munafunci malama in kina son Fada musu ai ba sai kin zo kina wani Yadamin mgana ba ke bazan Fasa Karatun ba yanzu na Fara in ma baki je kin Fada ba sunanki ba Hamida .!
Tafada tana kumfar baki ganin Abun na neman zama fada Hamida na Fadin"Da ina son na Fada da Tuni an wuce wajen kema kin sani..! Kawai gaskiya nake Fada miki..!
Amina tace"Munafunci ba..Kin Saba..Hamida ki kyeleni ko?ance ba"a son gaskiyan ko Dole ne..?
Ni bana son sa"ido kowa yaji da kansa mana .!
Hamida zatayi mgana Hanne ta Tareta da Fadin"Kyaleta Hamida..!
Hamida itama ta fara harzuka cikin Daga Murya ta fara fadin"Saboda me .?Saboda ita tafi kowa sai ta rika yadda taga dama ana kyaleta..?ai ba wani abu nace ba Fadan taso kanta nayi mata ina amfanin karatun Littafan da takeyi..!alhalin bata maida hankali a duka karatunta da zai amfaneta watarana..Ammh da anyi mgana sai ace a kyaleta to bazan yi Shuru ba nima yau ina daidai da Jidalinta Wlh..!
Ta karishe Fada tana Hararan Aminar Dake kallonta kamar taga Kashi.
Kafin ta yi Dariyan gefen baki tace"ban fi kowa ba Hamida..Ammh ni Dake ba Daya bane .ke sunanki Hamida ni kuma Amina nake..Ance ba"ason gaskiyan ko ana Dole ne..?ke wai ina ma Ruwanki da Rayuwata ne. ? anki a Tsaya ayi karatun sai me..?har kina Fadin zaki iya da Jidalina na Rantse da Allah baki da wannan Juriyan da zaki iya dani in kuma zaki iya Bismillah..!
Ta Fada Lokaci Daya tana Chakumo Wuyan Hijabin Hamida suka Mike Atare Hamida ta Zuciya zata rikota Hanne da Zafira suka Tareta suna Fadin"Amina saketa..!
Amina na Hararanta tace"Ku gayamaya ta daina Shiga harkata..ana Dole ne nace ta kyaleni ko..?
Hanne tace"taji..Saketa..dafa mutane acikin gida in akaji fa kina ta Daga Murya.
Amina ta Saki Hamida tana Fadin"Aji mana..Sai mene..?
Daga bayansu sukaji ance"Meza"aji din..?
Gabadayansu suka juya suna kallon mai mgana Anty Shamsiya ce matar ya Jafar Tsaye daga Bakin koridon Daga alamu bayi zata shiga Domin ga Buta nan a Hannunta da Katon cikinta agaba tayi wata katuwa ba kyan gani.
Amina Tayi kamar bata ganta ba ta Juyar Dakai Hanne ce tayi saurin cewa"Bafa komai Anty Shamsiya..!
Tana kara nazarinsu tace"Fadan da kuka saba kuke yi ko..?
Da sauri Zafira tace"Wlh ba Fada bane..!
Kai Tsaye tace"To tunda ba Fada bane ku zo ga aiki..Daman tun dazu Jaleela ke nemanku zaku Daukar mata Walid ya hanata aiki Zahra ma sai Cigiyarki take ashe ku gaku anan wajen..!
Amina Sai hararanta take ta kasan ido ita ko Fadi take"oya ku zo ku wuce..Zahra ai ga su Hannatun nan fa...?ana ta nemansu..!
Ta juyatana fada daga Cikin Gida su Hamida sun tafi Amina na wajen taki Tafiya Shamsiya ta kalleta tana Fadin"Ke da kike Tsaye fa?
Amina ta Tura baki cikin kunkuni tace"Kiji da kanki dai da wani katon bakin ki..!
Tana kallonta yasa tace"Badai zagina kike yi ba ko Amina..?
Da Sauri Amina tace"ni..?cewa fa nayi gani nan zuwa..!
Kwafa tayi kafin ta juya tana Fadin"Kada ma kizo..Jaleela gafa Aminar nan taki zuwa kinsan ta batasan aiki..!
Amina ta Mele baki tana Fadin"Ai ni ba Jaka bace..!
Su hamida sun shiga cikin gida yasa ta bisu jin Ya Jaleela sai kwala mata kira take yi tana shiga taga an saka su Hanne Wanke wanke mai uban yawa Daga nan ta Tsaya afili ta Furta"Jaruba..Kamar wasu jakai..!
Bata gama Rufe baki ba aka Rankwasheta asaman kanta Dafe kan tayi tana kallon Ya Jaleela Dake Tsaye kanta Da yaronta Walid a hannunta.
Mika mata shi tayi tana Fadin"Ke da ba Jakar ba..Karbesa ki cire mai pampers ki wanke mai ina ga ya batashi ne kije Dakin mamanmu wajen kayana ki Bude karamin akwati zaki ga kaya da pampers ki Sakamai ki goyasa sai rigima yake min..!
Amina bakinta kamar zai Fado Saboda Takaichi hakanan ta mika hannu ta karbesa yadda take yi ne yasa Jaleelan kallonta tana Fadin"Kada ki kadamin da yaro..Nasan Zafinsa ko bazaki yi bane..?
Amina Dakyar tace"ni fa ban ce bazan yi ba..!
Jaleela tace"Au naga kina neman min kuka ne..?daman baki iya komai ba Mamanmu ta gama bataki..!
Ya Jawahir Dake kusa dasu tana Bare leda tace"Kamar kin sani Allah yasa ta iya ma saka pampers din..?Dama Hamida kika saka ko hannatu.Amina kiyuwarta da son jikinta bai barta ta iya komai ba..!
Jaleela ta kara Dungurinta tana Fadin"Sai kazanta..da Rashin kunya zaki wuce kiyi abunda na sakaki ko sai na mareki..!?
Acikin kunkuninta tace"Ni ba kazama bace.Haka kurum ko da haihuwa ni nayi ta wahala da yara..!
Suna ganin tana mgana Jaleela tace"Me kike cewa ne..!?
Wucewa tayi tana Fadin"Ni ban yi mgana ba..!
Hanne da Hamida suna Duke suna Dariya kwafa tayi ta wuce wajen Bayin waje ta dukar da yaron da bai wuce shekara Daya da rabi ba ta Zare mai ido ganin zai fara kuka tace"Kai kama bakinka..bar ganin idon uwarka Wlh kana min kuka sai na Dirkeka..!
Tafada tana Zaremai ido kamar yasani sai yayi Shuru kwafa tayi tana Fadin"Shegen yaro mai kama da Ubansa..!
Tana Ciremai pampers din tana Ta Mai masifa ubansa ya sha Zagi harda uwar ma,Amina Fadi take""Kun iya haihuwa..ammh bakusan yadda zaku reni ya"yanku ba Amina ai ba Jaka bace..!
Inda Allah ya taimaka Fitsari kadai yayi aciki a Bola ta watsashi Tana Fadin"Allah yaso ka..Da kayi kashi Wlh bazan wanke maka ba..Sai da na Sake nadeka dashi..!
Ko Tsarki batamai ba Ta Daukeshi Fuu Sai Dakin mamanmu Dayake suna ta aiki ba wanda ya Lura da ita Tana shiga ta Dungurar dashi a kasan Cafet ba kowa afalon Yasa ta Zare mai ido tana Fadin"Kai zauna anan..In ka sake ka tashi sai nayi wuji wuji Dakai..!
Gwanin Tsausayi haka ya koma ya Zauna yana so yayi kuka Lekowa tayi taga hankalin kowa baya kanta ta bar Walid chan ta sababo wajensu Hamida Daidai kunnenta tace"Ku taso mu gudu..!
Hamida ta kalleta dasu Hanne da Sauri tace"Wannan uban wanke wanke yaushe zaku gama..?ai biki suka zo su yi aikinsu ne nidai kunga tafiyata in kuna son kuyi ta aiki ku zauna..!
Tafada tana wucewa ba wanda ya Lura dasu domin yammah ta Farayi suna ta aikinsu.
Zafira ce ta fara tashi tana Sake Hijabinta Data Daure Lokaci Daya tana Fadin"Amina jirani muje..!
Daman ita ke wankewa Hanne da Hamida na Daurayewa ganin sun wuce yasa Hanne ta kalli Hamida tana Fadin'"Mu bisu Hamida in muka Tsaya Laifin duka zai shafemu..!
Ba musu suka Tsame hannunsu Daman da Hijabansu ajikinsu,Su Amina sun riga sun fita daga Tsakar gidan su Hanne Jawahir ta Hanga da Sauri ta fara kiransu"Kai ina zaku kuma..?kun gama aikin ne..?
Ai ina kafa mai naci ban baki ba su Amina Dake jiransu ganin suda gudu yasa suma suka Ruga Jaawahir ta saka Salati tana Fadin"Yaran nan basu da mutumci sunbar aikin sun gudu..!
Zahra ce ta jita tace"Amina ce zata ce su gudu..ammh Hamida da Hanne basu da kiyuya.!
Jawahir tace"Amina na Dakin Mamanmu tare da Walid..!
Bata rufe baki ba Mamanmu ta Fito da Walid a hannunta tana Fadin"Jaleela garin yaya ki bar walid a daki shi kadai sai faman yanka ihu yake..?
Zahra suka kalli juna da Jawahir kafin Tace"Daman na Fadamiki..!
Jaleela nachan suna aiki Saka Abu a Takeaway aka mika mata Walid ta karba Tana Fadin"Sai naci uban Amina Wlh..!
Zahra tace"Inda kika ganta ba..ai sai ma kin ganta sannan kici uban nata..!
Gabadaya Dariya aka saka ana Fadin Halin Amina sai Allah ya Shirya.

Su basu tsaya ba sai da suka fita Daga gidan sannan suka Tsaya suna Haki Hanne tace"Ya Jawahir ta kamamu tana ta kiranmu muka gudu..!
Amina tayi Dariya tace"da kun tsaya..!
Tafada daidai Lokacin da sukaji Hayaniya suna juyawa suka ga ashe Karatun Baba Mallan ne aka tashi Maza sun fara fitowa daga masallaci.
Hamida ta zaro ido tana Fadin"Mu shige gidan Baba malman gasu ya Jafar nan sun fito masallaci kunsan in ya gammu a waje sai yayi mana mgana..!
Amina tace"mu tafi gidan su ya jafar inda su ya zulaiha suke muga abunda suke achan..!
Dukkamsu sukayi Shiru suna kallon Amina kafin tace"Dilla mu bi ta nan baya bamai ganinmu..!.
Jin haka yasa suka yarda nan da nan suka Zagaya suka bi ta baya suka fara Tafiya akuyan Daure ta samu Sake sun san gidan Dayake ba wani Nisa Sosai a kasa sukaje sai gasu abakin get din gidan Amina ta fara buga get din gam gam..gam gam.kamar zata Fasa kofar
Daga chan sukaji Muryan Abida tana Fadin"Waye haka..?ana zuwa kada ya balla get din..!
Ido suka gwalo sun san Halinta kafin suyi mgana ta Bude get din Tana kallonsu tasha kunshi ja hannu da Kafa Hararansu ta farayi Daya bayan Daya kafin tace"Daman Araina sai da naji kune..To kuma uban me kuka zo yi..?ko nan da sa"anninku ne..?
Amina tayi Saurin cewa"Mufa mun zo muga amare ne..!
Abida ta ballaa mata Harara kafin tace"ku musu mene..?kaji min yara da iyayi to bAzaku shiga ba ku juya ku koma..nasan ba wanda yasan kun fito Daga gida..!
Hanne tace"Muna ganinsu zamu tafi ko Amina..?
Da Sauri Amina tace"Eh Wlh..muma kinga basai amana irin kunshinki ba..ko Hamida..!
Gabadayan su suka amsa Domin su ba wanda yabi ta kansu ma mganar kunshi gwara Hanne da Hamida suna ma kansu Amina kuwa sai dai in Mamanmu ce ta kamata ta kunsa mata.
Abida ta Daure Fuska Kafin tace"To wlh bazaki shiga ba irin lalle na ko..?ni sa"arku ce..?kuna yara da ku sai son shiga cikin manya dillah ku wuce ku bama mutane waje..!
Amina ta tura baki kafin tace"To mu leka..!?
Abida tace"To leka..!.
Da Sauri Amina ta Zura kai ta wajen Hannun Abida Data Bake get din zata Leka taji ta Daketa abaya Dayasa ta Dawo da kanta da Sauri Abida tace"Matsa ku bani waje..Marasa kunya kawai ba sa"anku anan..!
Tana gama Fadin haka ta fara kokarin maida get din Amina ta kalleta tana sosa inda ta Daketa da karfi tace"Dadin abun ai ke ba Amaryan bace Ehe..!
Tana gama Fadin haka ta Zura da gudu su Hanne suka mara mata baya Abida ta saki baki tana kallonsu afili ta Furta"Yaran nan sun bala"in Raina ni..!
Kan bala"i zamu hadu ne duk sai kun ci ubanku..!
Tafada kafin

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login