Showing 150001 words to 153000 words out of 265571 words

Chapter 51 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28939

mafita bace in mukace haka bazata saba da gidan auranta ba gwara ta zauna watan watarana zata saba..!
Da haka mallam ya yarda da Hujjanta yace su Hamidan su tafi da kanta ta Kira uzairu yazo ya kaisu da Daya daga Cikin motocin gidan Daman tun jiya daya Dawo key din motar ke hannunsa.
Har suka tafi Hajiya bata Daina mamakin Balaraba ita sai kawai taji abun yayi mata wani iri.
Sai da ta koma shashen nata ta ga Sinasir din datace su hanne su dibar ma Amina saboda sauri sun manta dashi kawai ta girgiza tana mirmishi suna ta zumudi dole su manta.

Ita kuwa mamanmu Rana Tsaka kawai hanne tazo tace Hajiya tace ta bada Sako zasu wajen Amina..
Ita har ga Allah mantawa ma take da wata Amina kudi kuma tabi ta kansu? Shiyasa ta Dauko wannan Turaran Tsinke wanda mamata ma ta bata shi ya Dade bata taba amfani dashi ba tamikama hanne domin bata taba Zaton Sa"idu yayi zencen ya bata kudi da Hajiya ba. ganin suna ta Murna yasa batace komai ba gwara Hamidan taje ta gano wani irin Halin da Amina ke Ciki don ta tabbata Sakina bazata mata wasa ba ita fa a gayyas gida yanzu ya Rage daga ita sai mijinta Jawaad yanzu in Aba ya Dawo yadaina zuwa saboda samunsa tayi tajamai kunni yaro kuma da Tsoro ko Aba ya Dawo ko ya kirasa daya zo sai yace yana da Homework sai ya tafi hakan yafi ma Mamammu Duniyarta take so taci ita kadai bata san Takura.









*Janafty*

*TFZB2008*


*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488*

Amina tana rakube a falo tsoro duk ya cikata tunda Danmallam ya fita take duban idon su hanne ammh har Dare ya fara shiga ana gabda kiran sallar mangariba bata gansu ba Tsoronta Allah kada Dare yayi basu zo ba bazata iya kwana ita kadai ba Tana jin tsoro.
Tana zaune kan kujera a rakube saman kujera tana fiki fiki da ido,kamar mara gaskiya ko kwakwaran motsi bata yarda tayi ba, saboda tsoro,Saboda yanayin Datake ciki yasa ko karan Bude get bata ji ba sai ihun kiran sunanta da Hanne da Hamida suke mata kamar daga sama haka taji tana kyalla ido kawai taga Hanne da Hamida da kaya niki niki a Hannunsu,bata san sadda ta Diro daga kan kujera ba duk da yanayin Datake ciki bai sa ta tsaya ba Cikin Farin ciki da murnan da Rabonta da tayi har ta manta ta fada Jikin Hanne Tana Fadin"Oyoyo..oyoyo..!
Haka take fada sai hawaye sharr kafin ta Saki hanne ta Rumgume Hamida tana Fadin"Nayi kewarku..Nayi kewarku ba adadi Hanne da Hamida..!
Ta fada tana sharan kwallah suma sai da kwallar ta kawo musu suka kara Rumgumeta suna fadin muma mun yi matukar kewarki Amina.
Hannunsu taja tana fadin su kariso mana Bakinta yaki Rufuwa Saboda Murna basu Tsaya a falo ba sai Dakin Data kan gadon suka yada Zango Hanne da Hamida suna ta bin Gidan da Dakin da kallo.
Amina Murna yasa ta rasa me zata basu kallonsu tayi tana fadin"Kuna jin yunwa.?
Ga Abincin chan da ya danmallan ya siyomin kafin ya tafi zaku ci na Dauko muku..?
Binta kawai suke da kallo har ta Fice sai gata ta Dawo da shi a Hannunta Hade da maltina,tana shigowa Hamida tace"Mufa mun koshi Sai dai anjima..!
Amina ta Dago tana fadin"Hanne kema bazaki ci ba..?
Hanne tace"Mun ci abinci agida..Sannan ni ba abincin siya zan ci ba girkin Ama?????
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
rya Amina zan ci..!
Hararanta Amina tayi kafin tace"ai sai ki ci abinci bayan matar gidan ta Kulle Kitchen dinta ta tafi bansan inda taje ba..!
Hamida ta zaro ido kafin tace"Bangane ba..?
Hanne ta karbe da cewa"Naji Hajiya na Fada ammh inaga ya Danmallam ya mata mgana ga keys din gidan gabadaya na wajen Hajiya tace nazo miki dashi..!
Amina ta tabe baki batayi mgana ba, Hamida da Hanne sai binta suke da kallon kurillah Amina sai ta Tsargu ta balla musu harara kafin tace"Wai kallon fa na miye..?
Hamida ta kalli Hanne suka Tsintsire da Dariya Amina sai ta sha kuni Tana Fadin"Bana son munafunci hanne da Hamida..!
Hamida tace"Ba wani gulma munga kinga sauya ne Amina kin rame sannan kinyi wani sanyi kamar bake ba..Eye Amarya Amaryan Ya danmallam to ya amarcin ne da Dadi ko ba Dadi..?
Amina sai Hararanta take yi kafin tace"Sai dai ango..Sannan ba Amarci ba amaro..!
Gabadayansu suka saka Dariya Farimciki ya cika Amina bakinta yaki Rufuwa Hanne ce tabi Dakin da kallo kafin tace"Dakin waye wannan hala..?
Amina tace"Na Sarood ne..!
Hamida tace"To ba kayanta a Dakin ne..?
Amina tace"Dillah kun isheni ko bari ma na Tambayi mutanen gida baku yi ba..Hamida shegen son jin kwakwaf to da kayanta zaki ganni aciki ne..?
Hamida na Dariya tace"Allah ya baki Hakuri Daga tambaya..!
Amina ta mata banza ta zauna kusa da Hanne tana Fadin"Hanne ya su Hajiya da Baba mallam..ke kuma Hamida yasu Mamanmu da Aba ina Jawaad su ya Zeenatu sun san an kawo ni nan..?
Ta fada a marairaice kamar zatayi kuka Hanne ta tura mata Ledan Hannunta tana fadin"Kowa lafiya..Ga Sakon hajiya tace mu kawo miki Sannan tana gaisheki sosai..!
Hamida ma tace"Mamanmu ma na gaisheki Aba da Jawaad duk suna lafiya sannan kowa yaji kina gidan ya Danmallam sunce duk a gaisheki..!
Sai Amina ta jawo leda ta fara fito da kaya bakinta yaki Rufuwa Fadi take yi Duk ni kadai wannan..?
Tana Daga kaya da Hijaban tana fadin"Wannan nasan aikin baba mallam ne..!
Ta daga su yaji da kayan da Hajiya ta Hadamata tace"Wannan kuma na Hajiya ne..!
Hanne tace"Kamar kin sani ta kasa sukuni komai sai tace na Amina ne..!
Amina sai hawayen Farinciki Fadi take nagode nagode sosai Kafin ta kalli Hamida tana fadin"Hamida ina abun Dadin da mamanmu ta bada ki kawo min bana son wasa fitomin dashu kafin raina ya bci..!
Tafada tana mikamata Hannu Har da shan kuni.
Hamida sai taji wani iri ta kasa mgana Domin ita dai mamanmu bata bata komai ta kawoma Aminar ba Hanne ce ta ceceta ta Dauko mata Turaran? wutan da mamanmu ta bata ta Saka ma Amina a Hannu tana fadin"Ga shi in ji mamanmu..!
Amina ta karba tana jin Dadi tace"Kai nagode sosai nayi kewarta sosai Allah Sarki mamanmu..!
Haka take ta fada suna Binta da kallo Sai da tagama gani duka sannan zata kwashi kayan ta maida a ledan Hamida ta hanata ta karba tana fadin"Bari na jera miki Cikin Kwabarki..!
Amima tace"Wayyo Anty Hamida i miss u..!
Ta fada tana Rumgumeta Hamida ta kwace jikinta tana fadin"Ni sakeni..Dole kiyi missing dina anan bamai miki nasani..!
Amina tace"Wlh kuwa kamar kinsani..Ya Danmallam ne in yayi mun masifarsa nake dan ninkewa shi baya son ganin Datti..
Hanne tace"Tab baki san kyamkyamin ya danmallam bane baya shiri da kazami sam Amina sai a Rage son jiki..!
Amina ta Harari Hanne kafin tace"In an ki fa..!?
Hanne ta mike tana Dariya tace"Sai a Daku..Don Wlh keda megidan ne ba ruwana.!
Jin haka yasa Amina tayi shuru su kuma suna mata Dariya Hamida ta Bude Wardrope din taganshi Tsab Cikin mamaki ta juyo tana kallon Amina kafin tace"Amina kece yau da gyaran kayanki..Lalle aure dabam ne..!
Amina ta tabe baki kafin tace"Bani na gyara ba shi ya gyara ni fa tunda nazo gidan nan ban saki jikina ba sai yau dana ganku..!

Atare Hamida Da Hanne suka Hada baki wajen fadin"Shiwa..?
Amina ta kallesu kafun ta ce"Bansani ba..!
Lokaci Daya tana juya musu ido Dariya suka kwashemata da shi Hamida tace"Soyayya ruwan zuma ka sha ka bama masoyi..!
Amina taki cewa komai ta kyalesu suna ta mata iskanci Hanne ta taya Hamida suka gyara ma Amina kayanta suka jera nasu suma da suka zo dashi suka tsinke da labarin makarantar su da Amina sai dai ta tambayi wance da wance sai jin Dadi take yi Amina ta Dauka Aminene ta tafi kenan sai ta gane cewa har yanzu Aminene na nan Rayuwa ce ta sakata tayi sanyi nan da nan kewar makaranta ya kamata Cikin Jin Dadi tace"Ai ranar monday nima zan koma in ji ya Danmallam..!
Hanne tace"Naji yana fadama Hajiya.!
Hamida tace'Yauwa gwara ki Dawo Wlh daga Unity har islamiya ba Dadi baki Amina..!.
Amina tace"Nima bakusan yadda nake kuka in na tunaku bane kamar in yi Tsalle in gani agida..!
Hamida tace"Wlh muma Hajiya take Lallabamu da mallam in sukaga muna kuka ko mun Damu Saboda baki nan..!
Hira ce kawai ta Tsinke kamar bakin su bazai gaji ba Daga Dakin Amina Kitchen sukaje suka Bude Hanne ta Sassaka ma Amina su Samosa da danbun namanta a Fridge kar ya lalace suka kuma jera maltinan aciki Duk da akwai lemuka kala kala aciki Sannan suka Diba samosan Hamida ta soya musu.
Sai alokacin sukaje sukayi sallar mangariba Amina kamar an bata Kujeran Hajji Saboda murna yau gata ga Hanne ga hamida
Bayan sun idar da salla su ka koma Falo sukaci Takeway din nan suka hada da samosa suka kuma sha Tea suka Dora da maltina ransu Fes gashi akwai Wuta basu Dauke ba Amina bata manta da shan mganinta ba bayan sun yi sallar isha"i ta Dauko Zata sha su Hamida suka tambayeta tace tayi Zazzabi ne basu matsa mata ba Tunda daman sunga ta rame kadan sai suka yar da da mganarta..
Afalo suka baje suna Hira Hanne ta kuna kallo gabadaya Tasoshin na wa"azi ne dana addini Ta kashe ta Dawo ta zauna tana fadin"Na manta gidan ustazai ne nan ba"a kallo..!
Hamida ta yi Dariya kafin tace"Ko agidanku ai ba kallon kike ba..!
Amina tace"Gulma da iyayin Hanne mana..ku wai ina Sa"adatu ne..?
Hanne tace"Tana nan mun manta da mun mata mgana mun zo da ita..!
Amina ta Harari Hanne kafin tace"Wlh da kuwa daga ke har ita ba matsiyaciyar da zata shigomin gida..!
Hanne ta Bude baki ita da Hamida kafin su kalli juna su hada baki suna Fadin"Uhm masu gida da miji..ammh nan ana kuka ana ba"a so..!
Ashe dai ana son ya Danmallam din..!.Hanne ta karishe Fada tana Dariya Amina ta karkace baki tace"Allah ya isa Tsakanina daku..Kuma Wlh wuta..!
Suka karisa mata da bal bal..!
Suna Dariya ta tashi tana jefansu da filon Kujera tana fadin"Munafukai kawai..!
Sai da suka gaji suka koma suka zauna Hamida tace"Wato Hanne Halin mutum zanen dutse Amina ko ta Sauya akwai wasu hallayanta da Har Abada bazata sauya su ba..!
Hanne tace"Kamar Taurin kai da Tsiwa da Fada..!
Amina ta kallesu ta harare su batayi mgana ita kanta ta zata ta koma Ruwan sanyi ammh Sanadin zuwansu yasa ta Fahimci Aminene bata Mutu ba Doguwar suma tayi ta Fara Farfadowa yanzu.
Sai kusan goma na Dare suka je suka kwanta achan dim ma wata Hirar suka Dasa tuna irin abubuwan da sukayi suke yi suna Dariya Amina in ta Fara Dariyan mugunta har da Hawaye yau gata ga Hanne da Hamida suna kwance waje Daya Amina ce a Tsakiya Hamida tace"Wai har yanzu baki daina shegen tsoron nan ba..Ke in ba kin kwakwume mutum ba bakya iya barci..?
Hanne tace"Ga ya danmallam sai ta Rika kwantamai abaya in suna barci..!
Amima ta balla musu harara kafin ta juya ta yi Daidai hannunta kan Cikin Hanne kafanta kan kafafun Hamida suna Tureta tana kara Dorawa Dole suka gaji suka kyaleta Daga haka sukayi addu"an barci suka kwanta.
Dayake sun riga sun saba da tashin asuba kiran sallar farko suka tashi suka yi alwala sukayi Raka"atul Fijir sukayi sallah sannan suka koma barci su Hanne an samu waje sai goma na Safe suka tashi suka shiga Kitchen sune har store sai da suka Bude babu abunda babu na kayan abinci kamar ma ba"a Dade da Zuba su.
dankalin Turawa Amina tace su soya da kwai haka kuwa akayi Hamida ta Fere Dankalin ita da Amina Hanne ce mai soya kwai wajen Rabin Kires suka soya yazo yayi musu yawa ga Tea nan suka Ragesa cikin su ya cika Hanne tace"Ko zamu kaima megadi ne..?
Hamida tace"Ke ina ruwanki ga matar gida batace ba..!
Amina data gama shan mganinta ta koma ta kwanta saman Cafet Cikinta ya Cika tace"Uban matar gidan ce Ina ga da wannan gajerar matar yayan Hanne kike mgana itace mai gidan..!
Dariya sukayi kafin Hanne tace"Kema me gidan ce wlh..Gashi Dalilin ki har mun Dankwali arziki ko ba Haka ba Hamida..!
Ta Daga mata kai suna Dariya har da ta tafawa Amina tayi karamin Tsaki kafin tace"Yan iska kawai..!
Sukace sun ji ba bakomai karshenta saman Dining suka maida suka rufe amjima zai musu amfani.
Amina Daganan barci ya kwasheta su koma sai suka tashi Hamida ta gyara Dakin da suka kwana da Kitchen Hanne ta gyara Falo suka goge shi Tas sun nemi burner nasa Turaran wuta basu gani ba sai suka kunna na Tsinke Gidan ya Dau kamshi Sai da suka gama Amina tatashi ganin aikin da sukayi ne yasa tayi mika tana Fadin"Dadina da Kawayena akwai aiki kamar Dawakai..!
Baki suka saki suna kallonta Hamida tce"Zaki ga Dawakai nan da jibi in muka tafi in kika fara yi da kanki..!
Amina tamarairaice kafin tace"wai ku nan da gaske tafiyar zaku yi..?
Hanne tace"Wlh Hajiya tace Ranar Lahadi idi zai zo ya Daukemu..!
Amina tace"Tare dani kenan domin kafar ku kafata..!
Suka Sheke da Dariya kafin Hanne tace"Wa ?ai kin zo kenan yarinya har Abada..!
Hararansu tayi ta tashi ta shige Dakin nan ta gansa tas har da Tiolet Hamida ta wanke shi Tas kwanciya tayi kan gado tana kara jin Dadin ganin su Hanne Tare da ita.
Su kuma basu kwanta ba Wanka sukayi Hanne ta farayi sannan Hamida da suka ma Amina mgana bayan sun Daketa tatashi Tana masifa Hanne tace"Ki tashi kiyi wanka malama sai ki kwanta..!
Amina ta koma ta kwanta tana fadin"Jiya nayi wanka..Wlh ni yau bazan yi ba haba kamar wata
kwado..!
Basu yi mamaki ba Saboda susan Amina bata shiri da wanka Hamida tace"Amina da fa da yanzu ba Daya bane..Ke yanzu matar aure fa kazanta bana ki bane..!
Ko kallonsu batayi ba Hanne tace"Ita ta sani..kishiyoyi dai har Biyu gareki kuma Duka yan gayu ne sannan ya Danmallam bai shiri da kazanta..!
Hamida tace"Kuma bazamu ji Dadi ya raina mana ita ba ko kishiyoyinta su ran mata ba..!
Amina ta Dago kanta kafin tace"Da ku da Kishiyoyin duk naci ubanku na Zauna Lafiya..!
Hamida ta kalli Hanne suka Hada ido suna kunshe Dariyansu tana ganinsu tayi banza dasu daman Hanne da Hamida akwai gulma sun kware wajen munafunci.
Haka Amina ta wuni batayi wanka ba sun gaji da mata mgana sun kyaleta da Rana basu yi girki ba sauran kwan daya rage suka ci suka kuma kara soya samosa suka ci suka hada da maltina da Daddare kuma suka Tarun ma Dambun mana suka ci suka kwanta Washegari Hamida da Hanne Dakyar suka ga Safe suka kwana Murdawan Ciki da Zawo Amina Daman akwai Lafiyan ciki bakomai ke bata mata Ciki ba.
Haka ta Dinga musu Dariya Hamida tace"Hanne Amina wlh muguwace tasan cikinta ita lafiyansa kalau ba sai tace kada mu ci da yawa ba..!
Hanne daman nada ulcer tana Mai da Numfashi tace"Ni sam na manta inda Ulcer ma..!
Amina me zatayi ban Dariya Cikin Dariya tace"Hajiya ni tace ku kawo ma abu ammh Saboda maita ku sai an ci komai daku kadan kuka gani..ma..!
Haka ta wuni yi musu Dariya Ranar ban da Tea basu iya cin komai ba sai da Daddare da suka ji sauki Zawon ya Tsaya da ciwon ciki sannan suka Dafa Doya sukayi miyar kwai suka ci suka kwanta.
Washegari ma barcin su suka sha sai sha Biyu suka tashi suka karya da Sauran Doyan jiya suka gyara gidan Amina na zaune tana kallonsu An samu Amina tayi wanka jiya ammh yau kam tace bazatayi ba ta gaji sudai sukayi suka Sauya kaya Daganan aka Fara Tunanin me za"a Dafa.
Amina tace Hamida tayi musu wainar Fulawar datake yi agida mai Dadi Tunda ga Yajin da Hajiya ta kawo mata .
Nan da nan suka yarda da mganar Amina suka Dunguma zuwa kitchen suna neman Faluwa sun sha mamaki Fulawa buhu Guda ko kwata ba"a taba ba Nan suka Diba suka kwaba suka saka kwai ma"ishi suka yanka albasa Hanne tayi Gireting din kayan miya da suka gani Cikin Freezer harda nama wanda Amina tace soya shi za su yi Hanne tace sai dai Ferfesu basu da lafiyan ciki..Amina na Dariya tace"A soya yafi Dadi..!
Hanne tace"Muguwa muguntarki ta kare miki Amina..!
Sai Dariya Amina ke kyatatawa har tana Hawaye.

********

Mamanmu na kitchen tana soya kifin da Aba yaba Jafar ya kawo Dazu wayarta Dake tsakar gida kan Tabarma ta Dau kara alamun kira Gidan ba kowa sai ita kadai Hamida suna gidan Amima jawaad kuma sun tafi Hadda.
Burin Mamanmu ya cika ita kadai ke juyi a gidan Sa"idu sai abunda tace akeyi sai kuma an nemi Shawaranta.
Fitowa tayi da Sauri bayan ta juya kifin Dake kan gas kada kafin ta Dawo ya Kone.
Tana Daukan wayanta taga Madina ke kiranta sai da gabanta ya fadi Bata rai tayi afili ta Furta"Har Abada madina baza ta barni na Huta ba
Haba wannan kawwazzaba dame tayi kama mtswww..!
Ta ja wani Dogon Tsaki kafin ta Daidaita kanta ta Daga kiran tana Fadin"Buhun Sikari baki Farin banza ba..!
Dagachan bangaran Anty Amarya ta Katseta da Fadin"Ba bu abunda zaki Fadamin Ya sanyayamin rai Dayyaba..Ki ma yimin shuru kawai..!
Mamanmu ta marairaice kafin tace"Me kuma ya faru..?
Allah yasa ba kwabarmu ce zatayi Ruwa ba..!
Anty amarya tace"Kwabata dai Zatayi Ruwa Dayyaba...aike kin samu abunda kike so shiyasa kika maidani Wata Shashasha ko nema na baki yi Dayyaba Tunda na gama Taimaka miki kin samu Sa"idu a Hannunki ni kuma kin kasa taimakamin nawa Burin ya cika ko..?
Ni ban raba Maallam da Sa'idu ba sannan ta bangaran Sakina har yau ba wani mgana mai Dadi..!

Mamanmu ta Harari wayar kafin tace cikin karyewan murya"Haba Madina meyasa kin cika gaggwa ne..?
Kin Tsaya na gayamiki irin kokarin da ni ke nan ina yi miki akan abubuwa su Daidaita kuma da kike Fadin na Samu Sa"idu ai ban ga samunsa ba Domin har yanzu akwai rina akaga Hajiya da mallam sun sha gabana..mganar Sakina kuma ai mun gama mgana kince zaki sa ka mallam yasa turama danmallam son ko ya tafi sai ya Dawo ya Dauketa sannan mu na Fatan Zata samu ciki kuma zai zauna Zata Haifesa da yardan Allah mganar Shegiyar yarinyar nan kuma Amina sai dai su mallam su gaji su Raba bazai Taba wani amfani ba..!

Sai alokacin Anty Amarya taji ta dan Sauka Cikin Saukan Numfashi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login