Showing 93001 words to 96000 words out of 265571 words

Chapter 32 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28947

ya Kirata ya Fadamata,Ita ta shaidama Jadwa wanda akace sai da ta suma Mijinta na chan na nema musu Visar tahowa sai Mutanen gusai da Aba ya Kirasu ya shaida musu..!
Jaleela kuma ya kira mijinta ya Fadamai shi ya Fadamata sai kuka Domin mutuwar farar Daya tafi shiga Jiki sosai ance sun samu Jirgi sun taho Ita da megidanta da ya"yanta da Ya Nazir da matarsa tafiyar su daya..!
Sai ya Jamila Dake gombe ita din ma Mijinta aka kira aka Fadawa yace suna Tafe suma,Jawahir kuma da yan Gusai zata taho Allahu akbar rai bakon Duniya..!
Zulfa ma an gayamata tana Hanyan Tahowa ita da Nazeem Uzairu na Exam,sai Zahra Dake parthercourt Itama Tafiyar Jirgi tace zatayi sauran Iyalan Baba Mallam na kusa duk sun ce suna Hanyar Tahowa..tunda Rasuwar ta Safe ce..!
Dan mallam Dake chan Madina abakin Ya Nasir yaji Rasuwar Yaya Mutuwar data sanyayamai jiki matuka yana cikin makaranta sanda yaji Rasuwar ko kafin ya koma gida Sakina taji Labari itama cikin Tashin hankali ya fita nema musu Visar tafiya shi da Sakina Sarood nan zai barta Saboda kada Zirga zirgan tayi yawa..!
Ko kafin karfe Dayan an gama Hada yaya,Hajiya Babba da Wata Tsohuwa daga Gusai da suka iso suka hadu suka mata wanka suka shirya har alokacin Amina bata bar dakin ba kuma ko Hawaye Daya batayi ba..!
Kofar gida kuma ya cika Damkam da Jama"a tunda har agidan Radio an Sanar da Rasuwar zuwa Lokacin yan gusai sun iso sannan Ya Fati dake Dutse ta iso ita da Ya akila da Jidda ko"ina ya cika ba matsaka tsinke domin Yaya ta jama"a ce uwa uba kuma Aba dasu ya Jafar da abokan aikinsu sun cika wajen Allah sarki Aliyu abokin Danmallan yazo Jana"iza Tunda Umar ya fadamai yace sai yazo ya samu Janaza..!
Gida bai kara Daukan Kuka ba sai da aka zo fita da gawa bayan an kira duka Ya"yan Aba domin su mata addu"a wadanda suka iso kenan Ya Jawahir da ya Jafar sune manya sai su Amina da su hamida addu"a suka mata da Fatan dacewa Har Hamida da Hanne sun duka gaban gawanta sun mata addu"a Amina kuma sai da Hajiya ta Dukar da ita gaban gawan tana Fadin"Mamah yi ma mahaifiyarki addu"a..!
Sai ta zama out of Control yan"uwanta nata basu damu da Rashin kukanta ba susan bata Damu da yayan ba sai dai abunda basu sani ba awannan gabar Amina ta fisu bukatar uwa a raye domin ita ke cikin Tsaka mai wuyar da Uwace kadai zata Tsaya akanta da addu"a ammh kuma addu"a uwa ga ya"yanta har gaban Abada bata yankewa..!
Tana gaban gawan Kanta sara mata yake yi gabadaya yan Dakin sun koma masu fararan kaya haka take ganinsu kuka take so tayi ammh ta kasa kawai sai ta Sulale ta Rumgume gawan Yaya tana Fadin"Ki yafemin Ki yafemin..MAMA..!

Haka take ta fada cikin ihu Saboda tana so tayi kuka ta kasa sai Tsausayinta ya kamasu Da jawaad suke Tsausayamawa ammh Halin da suka ga Amina sai Rauni ya Tarun musu mamanmu na wajen tana ta kuka Hajiya Babba ke fadan ba kyau wannan kukan da suke mata..!
Ya Jafar ne ya jawo Amina Jikinsa ya Rumgume su ya Nasir suka kama gawa zasu fice tana ganin haka ta fara Fizge fizge tana Fadin"Ku bar min gawanta..Don Allah ku bar min ita..!
MAAMA...!

MAAAAMMAA..!!!!

Hake take fada cikin karyen Sautin da duka kowa yasan ba Sautin Amina bane Ana fita da gawan ta fara Bige Bigen da sai da tafi karfin Jafar su Hajiya suka taso suka sakamata karfi. Da Karfi take fadin"Ku dawomin da ita..Mamatace..!
Haj Nasara na sharan Hawaye tace"Allah sarki..akace Uwa uwace Ko da akan Bola take kwana..!ba wanda yayi Tunanin Amina zata damu don Yaya ta bar gidan Duniya..!
Ana gama Fita da gawan sai ta Daina ihu da Fizga ta koma kuma ta Sume musu kamar yadda aka kwashi mamanmu da ya Jawahir suma sun Zube kai anga Tashin hankali gida ya Rude da koke ba wanda akayi mamakinsa sai Aba ya nuna Jarumta ko Daya ba wanda yaga kukansa Dashi aka sallaci gawan Yaya aka kuma kaita makabarta yana rike da Hannun Jawaad da yaci kuka ya koshi..Aba bai yi kuka ba sai da Mallam yace ya matso shi da Ya Jafar da Ya Nasir da yan"uwanta suka sakata Cikin Kabarinta su ka kuma Debo kasa suka Rufe dashi sai alokacin yaji kuka ya taho masa Baba Mallam na bashi baki kan kabarinta ya Duka har su ya jafar suka gama mata addu"a bai tashi ba Fadi kaawai yake,"Tun zamana da ita bata taba Sabanin da gangan ba..Allah ya jikanki Hadiza har abada bazan samu makwafinki ba..!
Dakyar Baba Mallam ya rikosa suka bar makabarta suka Dawo nan Haraban gidan Mallam aka Saka Dardumai da Tabarmu ana karban gaisuwan m?????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????? aza, mata kuma suna cikin gidan Aba ko"ina Kaje sai yabon yaya ake yi ba wamda zai Bude baki bai Fadi Alherinta ba an samu su Amina sun Farfado sai dai ita Tunda ta Farfado bata kara mgana ba kuma bata kuka tana kusa da Hajiya kogaisuwa akazo sai dai tabi mutane da kallo..!
Sai Dare gidan ya kara Rudewa isowar sauran baki su ya Zahra da ya Zulfa da su ya Jaleela da yaya Jameela sai ya Nazir da Matarsa su ya Aisha duk sunzo karon farko zuwansu gida ba cikin Dadin rai ba,ya Sadiya ce bata zo ba suna Ameriaca inda Mijinta ke aiki tadai kira tayi gaisuwa..!
Ita Mutuwa daman ai bata da Sabo..ko abinci ba wanda ya Nema duk da ana ta kawowa Sadaqa,haka wadanda Mutuwar ta shafa sukayi kwanan zaune suna kuka da addu"an Allah ya jikan Yaya su ya jafar kuma suna waje suna karban gaisuwa sai dai in Mazan sun nemi shigowa sai suyi musu Jagora..!
Ko su saka su shamsu su shiga dasu hatta yan makarantar Islamiyansu da Hadda sun zo gaisuwa su da Malamanau da Dalibansu Sai alokacin akaji Amina tayi mgana data amsa gaisuwan mariya yar ajinsu Sa"adatu duk suna nan gidan suna tare dasu Hanne duk wani mai imani in yaga Amina sai ya tsausaya mata ta Fyade ta rame bata ci bata sha sai an matsa mata..!
Ranar da akayi sadakar uku Goggo Husai ta iso da ita da Jadwa sai mutuwar ta Dawo sabo aka fara koke koken Zuwa yammah sai ga Yaya Danmallam da Sakina sun iso suma..!



*AKWAI SOFTY COPY DA HARDCOPY NA LITTAFIN GIDANMU MAI BUKATA SAI YAMIN MGANA SANNAN LITTAFIN ZAMAN GIDANMU MAI CIKE DA KUNCI SHIMA ZA"A SAMESA A SOFTY COPY DA HARDCOPY KAN FARASHI MAI SAUKI A TUNTUBE NI TA WANNAN LAMBAR DOMIN KARIN BAYANI 09069067488*






*Janafty*

*TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janaftyd'?*


*
Aranar dai Danmallam bai shigo cikin gida ba yana kofar gida wajensu Aba da Baba Mallam,Sakinar dai ta shigo nan cikin gida ana ta yi musu barka da sauka Daki daki ta shiga tayi gaisuwan kafin ta koma Dakin su Amina inda su Ya Jidda ke zaune..!

Sai washegari da Misalin karfe shaDaya na safe suka shigo shi da ya jafar da ya Nasir da abokinsa Aliyu..!
Dakin yaya suka fara shiga tunda nan su Hajiya Babba ke zaune ita da Haj.Nasara da goggo jumai sai jama"ar gusai,sai Amina da Tun da akayi Rasuwar tana Dakin Bata yarda ta kwana ako"ina ba Sai gefen hajiya wacce ke Tsausayinta tana kula da ita Su Hamida da Hanne da zafira da suka zo Dakinsu suke kwana su da su ya Abida sai dai wasu na Ragewa in Dare yayi su koma gidan Baba Mallan su kwana ammh hajiya Babba da Haj.uwani nan suke kwana Anty Amarya ce da Hj.Nasara ke komawa gida su da ya"yansu su kwana..!
Sanda suka shigo Amina na Tsakanin Hajiya Babba da Mamata mahaifiyar Zafira sanye da Hijabin nan nata na Makaranta Tun da akayi rasuwar ko wanka batayi ba ballatana tayi Tunanin Sauya kaya gabadaya ta sauya kamar ba Amina ba mgana ba Tsiwa ba Hayaniya ashe ashe akwai Watarana da Bakin Amina zai mutu..?
Daga Ciki suka shiga suka Durkusa suna gaida iyayan nasu Danmallam ya Dago kansa yana kallon Hajiya cikin Tausasawar Sautinsa yace"Hajiya ya karin hakuri kuma..?Allah ya jikan yaya Allah yasa ta huta..!
Hajiya ta amsa da"Ameen ya Allah Hakurin duka namu ne Danmallan Fata kun zo lafiya..?Naga sakina ban ga Saratu ba..?
Kansa na kasa yace"Tafiyar ba Shiri Shyasa ban taho da ita ba..Ammh tace ayi muku gaisuwa Haka ma Abu kattab yace yana muku gaisuwa shi da Mami Sara..!
Hajiya tace"Mungode kwarai Allah ya bar zumunci..!Aliyu ma ya gaisheta ta amsa tana tambayan iyalansa yace suna Lafiya sai godiya Hajiya take yi tana Fadama Danmallam da Aliyu akayi Janaza in ji mallam..!
Nan ya juya suka gaisa da Haj.Nasara da goggo Husai da mamata da sauran yan gusai ana ta Nunasa ana kuskus din fadin shine babban yaron Mallam dake madina..!
Amina na jinsu tun sanda suka shigo Gabanta yake faduwa bata son ma ta Dago kanta ta ganshi Domin zuciyarta har alokacin ta kasa karban gaskiyan ta Auri wanda bai dace da Rayuwarta ba,Shiyasa tun sadda suka shigo kanta na kasa bata yarda ta Dago kanta ba ballatana ta ganshi..!
Sai dai duk Gudun hakan da tayi bata Tsira ba,Saboda Ya Jawahir ta shigo da kulan abinci tana Fadin"Hajiya ga Alale an kawo daga gidan Mallam Sidi..iyalan nasa sun fara shiga Dakin mamanmu ne..!
Hajiya tace"Angode Allah ya bada Lada..!
Sai kuma ta kalli Amina Dake gefen hajiya Lokaci daya tana fadin"Amina ko zaki Daure kici abinci ne ga Alale an kawo nasan kina so..?
Tafada Cikin Tsausayinta da ganin yadda Mutuwar ta daketa Fiye da Tunanisu kiran sunanta da Hajiya Tayi shi ya jawo hankalin Danmallan gareta Wanda kansa ke kasa har Lokacin Duke kan kafafunsa Daga chan gefe shi da Abokinsa Aliyu,Su ya Jafar sun fita tsakar gidan suna mgana da Ya Jadwa ne..!
Daidai Lokacin itama Amina ta Dago Manyan idanuwanta da suka zama sune kadai afuskan nata ayanzu karaf kuwa suka Hada ido Hudu atare gabansu ya fadi ras..!
Ambaton sunanta yasa abunda ya faru kwanaki hudu kafin wannan Rasuwar ya fadomai Alokacin abun na ransa yana Damunsa sai dai wannan Rasuwar ne ta shafemai wannan Tunanin,Kamar yadda yake kallonta haka itama take kallonsa Cikin wani yanayin da bai gane ba Shidai kallonta yake yi yana auna Mallam bai kamata ya aura masa wannan yar Cikinsa ba,Ba shi ya Dace ba ga Nazeem ko Nasir sune zasu yi Daidai da yarinyar bashi ba da bai hango da inda suka yi dacen da Mallam zai zabosa ya aura masa ita ba Bayan haka baya shiri da mara kunya ko Fitsarrre sannan yasan yarinyar nan Gangararriya ce gata kazama ga Rashin Natsuwa ga yarinta ayadda yake jin kansa Sakina da Sarood ma Nauyi suke mai ballatana an aura masa wannan yarinyar kamar an gayattomai Jidali ne da Rashin Sukuni acikin Rayuwarsa..!

Ita kuwa ba kare masa kallo take yi ba Zuciyarta ta Kuntake waje Dayan data kasa gane komai ita dai tasan Sanye yake da Farin Boyel Riga da wando da Hula zanna Bukar,sannan ya kara Fari Gemunsa kuma kamar ya kara Tsawo sai dai kallo Daya zakayi mai ka san Jin Dadi da Hutu sun zauna mai Saboda yanayin Fatarsa da yanayin Murjewan jikinsa zaka Fahimci Hutu da jin Dadin Rayuwa sun samu kyakyawan zama awajensa..!
Tana kallonsa ne tana jin kamar ta yanka Ihu acikin ranta ta kasa dora Mizanin komai domin tana ji kamar bata da Hankali Domin yin wani nazari kan Rayuwarta sai Hankalinta ya Dawo Jikinta kamar yadda ta kafe shi da ido shima a fakaicen yake kallonta sai dai abunda bai sani ba azahiri ne take kallonsa abidini kuma ta shiga wani yanayi ne yanayin da bawan da Allah ya Jarabta yake ciki..!
Haj.Uwa ce ta sako baki tana Fadin"Ai da ruwan zafi ta fara sha Hajiya sai hanjinta su sake..!
Wannan mganar ta Haj.Uwa shi yasa Danmllam Saurin Dauke kallonsa Daga gareta itama sai alokacin ta maida idanuwanta kasa tana Faman kokuwa da Numfashimta..!
Hajiya tace"Eh kuma na sha"afa Domin tun Rasuwar nan banga Amina taci abinci ba sai ruwa..Sai Hakuri Allah daya fimu sonta ya Dauketa Mamah addu"an ku kadai take Bukata yanzu..!
Mamata na gefe tace"Wlh sai hakuri ni Aminar ce ta bani mamaki..Yadda Mutuwar yaya ta Daketa na Dauka Ko zai Daki kowa banda ita Tunda Balaraba ta Kore mata Kishir ruwan uwa. !
Haj.Uwa ce tace"Uhm bari mamata..Kinsan Girman Daraja da Kaunar dake tsakanin uwa da abunda ta Haifa..?Mutum bai isa ya Fada ko ya kwantata ba..Allah Kadai yasan iyakarta..!
Sai Dakin ya dau mgana kowa na Fadin albarkacin bakinsu yawanci mgana suke kan yaran bazasu maraici ba ga Balaraba wacce take Tsaye kan yaran Tun yaya nada rai bata san wahalan ya"ya ba komai Mamanmu ce..!

Danmallam ganin mganar ta koma wani bangare yasa suka yi ma su Hajiya Sallama suka fice Amina ta Bisu da kallo gani tayi ma kamar ya kara Tsawo da zai fita sai da yadan Rankwafa duk Tsawon kofar yaya..!
Dakin Mamanmu suka shiga inda take karban gaisuwa ita da Anty Amarya da Haj.Nasara sai sauran yan"uwanta ,Sai su Sakina Dake dakinta ita da Jidda da Su Zulfa,nan suka yi musu gaisuwa yaran kuma na Rawan jiki gaishesu basu jima ba suka fito suka shiga Dakin yaran Lokacin Jawahir da Jadwa sun shigo Dakin Suka gaishesu suka amsa kafin suyi musu gaisuwa basu jima ba suka Fice Daga gidan zuwa kofar gida inda ake zaman gaisuwa..!

Sai da suka zauna chan Nesa da Tabarman su Baba mallam inda manyan Mutane ke zaune abokan aikin Aba da kuma Amintattun malamai abokan Da"awan Baba mallam,Sannan Danmallam ya kalli Aliyu yana Fadin"A cikin dakin da yaya da muka shiga kaga wata yarinya da Hajiya ta Kira da Amina..?
Bai bama mganar Muhimmanci ba yace"Eh wacce ake cewa bata ci abinci ba Tun bayan rasuwar..?
Da kai ya amsa masa kafin ya Cije baki yace"Wai ita Mallam ya aura min kwana Hudu da suka gabata..!
Sai Aliyu yaji kamar bai ji da kyau ba ya kallesa yana Fadin"Bangane ba..?
Dammallam yayi mirmishin Takaici kafin yace"Am serious abunda kaji gaskiya ne Aliyu..!
Aliyu ya Dafa kafadan Danmallam yana fadin"Kai..Abu haka kwatsam Shehi.Oh wlh yarinyar Sweet Sisty ce Abokina kace kaima kabi shawarata kafara yin gaba kafin ni..!
Kalamam Aliyu sun kara batamai rai Cikin Takaicinsa yace"Kai yanzu in nace maka da son raina na auri yarinyar chan sai ka yarda..?
Tsiyana Dakai wauta..Wlh tallahi bazan iya da mata uku ba Aliyu.bama haka ba yarinyar tamin kankanta sa"ar autan Hajiya ce fa Hanne tare suke fa ina zan kai yar cikina Aliyu..?bana son jidali Allah ma ya taimakeni Sakina ta kwantar da Hankalinta Sarrod kuma bata da Hayaniya ammh ina Tabbatar maka auran yarinyar nan sai ya Rusani Aliyu kasanni bana son Hayaniya da Damuwa ya kake gani na Hada yarinyar nan da sauran matana..?
Ba ka hangomin tashin hankali azama na dasu..!?

Ya karishe fada cikin Rauni Aliyu ya jinjina kai yana fadin"Eh kaima kayi mgana..To ya abubuwan suka faru..Ai nasani Mallam baya aurar dasu sai sun yi candy..!
Danmallam yace"Abubuwan da suka faru suna da yawa...Aliyu Abu Daya na sani Mallam ne ya Kirani ya Tambayeni yardata ba kuma neman izini ba Aliyu tayaya zan watsama Mallam kasa a ido..?
Bazan iya ba..Yana da Kima da Darajan da ko Wuta yace na Fada zan fada Uwa uba kuma Diyar Baba Sa"idu ce har Abada jininsa nada Daraja awajena sannan Diyar yaya ce Allah ya jikanta ko kasa sun shafe idonta bazan ki karban Abunda ta haifa ba Aliyu Yaya Mutum ce Hajiya ta Fadamin bayan ita data Haifeni yaya tayi wahala dani Wahalan da ko ya"yan data Haifa bata musu ba kana ganin in naki karban abunda suka Haifa Allah zai yafemin Aliyu..?
Yafada yana saka yakininsa da Kallonsa kan Aliyu da yayi Kasake yana kallon Umar din..!
Bai basa zarafin mgana ba yacigaba da Fadin"Sai dai abu daya na sani..Meyasa Mallam ya Zabeni..?
Bayan ni akwai Nazir,Ga Nasir ga Nazeem ayadda nake gani akwai kwaruwa yarinyace karama da batasan komai ba sai Shirme an cutar dani An cutar da ita Dukkanmu Rayuwar batayi mana Daidai ba Aliyu..!
Awannan gabar ji yake kamar ya saka kuka sai dai ina Jarumtarsa bazata barsa ba..!
Aliyu ne ke Bubbuga Kafadansa yana Fadin"Easy mana Shehi..Biyayya kayi kuma insha Allahu bazaka tabe ba..Komai da kaga ya faru tsarin Allah ne..Sannan da kake fadin gasu Nasir ai mallam din ya san dasu ko..?kuma ya Zabeka na Tabbata kamar yadda ya Zabeka cikin ya"yansa yana da kyakyawan yakinin bazaka basa kunya ba..Sannan kai din kafi su chanchanta kabar mganar yarinya ce Annabi ma ya auri Nana Aisha As tana da Shekara Tara ne kaga kuwa sunna ce sannan yarinyar nan ba karama bace yadda kake tsammani zata kai 16 to 17 fa Shehi ai kuwa batayi kankanta ba wadanda ma basu kaita ba anayi musu aure kuma su zauna Lafiya kuma mganar yar cikin ka yaushe ta zama yar cikinka..?Just 39yrs fa gareka Shehi ta ina zaka iya Haifanta banda Tsabar son girma da Sharri irin naka..!
Sai da ya Murmusa jin kalaman Aliyu kafin yace"Ammh dai kasan da auran wuri nayi..Da yanzu ko ban haifi kamar ta ba na kusa..!?
Aliyu na Dariya yace"Uhmm.Naji Ka dai kafin naji watarana yar cikin naka ta baka Wahala..!
Ya karishe fada yana kallon sa kasa kasa karamin Tsaki yaja kafin yace"kasha kwaya ne..?ko ka fara Hauka inaga..Ni fa duk ba wannan ba Ina cikin Tashin hamkali ko su Sakina ban yi mgana dasu ba fa..!
Aliyu yace"Tab..Ai sai kayi hakuri..Domin tama ji ta gama Tunda dai kuka zo nan..!
Dammallam ya Sauke Numfashi bai yi mgana ba Diramar da zasu kwasa Kadai yake hangowa in Sakina taji Labari ganin haka yasa Aliyu yake ta Kwantar mai da Hankali tare da bashi Shawarwarin da zasu mai amfani kuma ya natsu yana jinsu aransa yana godema Allah Daya Hadasa da aboki nagari kamar Aliyu.


Hakika an ga jama"a Domin kungoyin Matam malamai duk sun zo gaisuwa,Kowacce cikin masu auran nan Dangin mazajensu sun zo gaisuwa,Mutane ne suke ta Zuwa har abun yaso bama Mutane mamaki,sai dai kuma ba abun mamaki bane sanin Wacece Yaya shaidar duniya itace ta Lahira Tabbas yaya ta dace
Kowa sai mamakin Aba akeyi ganinsa Cikin natsuwarsa ba wanda yayi Tunanin Mutuwar bazata Gigitasa ba..Sai dai ina wadanda suke son ganin gazawar tasa basu gani ba Tabbas Mutuwar ta tabasa sai dai ya Riga ya yarda da Allah ke kashewa kuma ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login