Showing 198001 words to 201000 words out of 265571 words

Chapter 67 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28908

Fadin"Mallan nace tunda Nazeem ya gama karatun nan ya Dawo gida kafin aiki ya samu kasan kasar tamu yadda takkoma sai Kana da wani asama..Sai naga Tunda shima bangaran Kasuwanci ya karanta mai zai hana ya fara Bin Sa"idu gidan gona yana ganin waau abubuwan yana taimakai ko wajen Rubuce rubuce ne tunda naga Jafar ke taimakamai shima kuma kaga ga aikinsa..!
Har ta Sare da ba nasara taji mallam yace"Hakane..Zan m Sa"aidun mgana sai ya fara Binsa yana da kyau hakan Zai taimakamai..!
Haj.Uwani taji kamar ta goya Mallam Dole ta karama Mama kudi haka ta shiga yi ma mallam godiya sai da ya ji mamakinta.
Abunda bata sani ba wani abun yana Tarda Sa"a ne mallam yayi la"akari da nazeem ya Dawo gida Zaman banza zai yi kafin ya samu aiki daman kuma yana da wannan Tunanin shiyasa bai mata gaddama ba.
Da Safe da Aba yazo su gaisa ya Sanar dashi yaji Dadi Sosai,suna ma Cikin Tattaunar ne sai ga Nazeem ya shigo gaida mallam nan ya sanar dashi bai iya cewa komai bs tunda Haj.Uwani tace in yayi gaddama sai ta sabamai.
Shi dai zai bi umarninta dana mallam ne ammh yana samun aiki bazai Zauna ba.
Aranar suka fara tafiya gidan gona shi kanshi a wuni Daya kawai da yayi aikin Lissafi kadai ya yi sai da ya Jinjina Dukiyar baba mallam Aba na Fadamai a duk sati ana Fita da kwai Fin na miliyan Daya sai da ya Rike baki ya dai san gidan gonar babbane ammuh bai Taba maidakai akai ba.
Da Daddare suka Dawo Haj.Uwani daya Shigo Falonta Tana jansa da Hira anan nema ya gayamata tana jin Uban kudi ta zare ido tana Fadin"kaji ko..?
To ban da na gonakinsa kila in kaji abunda yake samu a shekara sai kanka ya Kasa Dauka..!
Sai jin Dadi take yi tana Mirmishi shi dai wannan baya gabansa dukiyar Mallam bazata Burgesa ba Tunda ba nasa bace.
Kwana Hudu da Fara zuwan Nazeem gidan gona da Sakar masa ragamar Wasu abubuwan da Aba yayi Mamammu taji labari shima suna Tare ne taji yana waya da Nazeem da ya gama ta tambayeshi yake fadamata Tare suke kasuwancim mallam yanzu yana taimakamai sosai da Umarnin mallam din.
Mamanmu jiki na rawa ta koma Daki ta kwalama Anty Amarya Kira ta Sanar da ita abunda Aba ya Fadamata.
Anty Amarya ta lailayo ashar ta maka kafin tace"Ammh Uwani dai an yi bakar Tsinanniya..Allah dai ya Tsine mata albarka..
Mamanmu ta amsa da Ameen madina da gaske take yi fa..!
Anty Amarya tace"Ai na rigata..Nasha gabanta wlh..!







*Janafty*
*TFZB2019*

*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*


Mamanmu tace"To yanzu menene mafita..?
So nake ki nuna ma Hajiya Uwani ita din banza da wofi..bata isa ba kuma bata kai ba wlh..
Anty Amarya tayi kwafa kafin tace"Ki kyaleni da ita Dayyaba..Ni yanzu abu Daya ke gabana Umar yazo ya tafi da Sakina Madina,kuma Hakan na gabda Faruwa saboda Cikin sati nan mai shiga yana tafe sakinar ma ke fadamin jirgin yawo zai fara yo gaba da kayansu..Kinga suna komawa shikenan hankalina ya kwanta Sai na Fuskanceta na nuna mata bata isa ba Daga ita har Sa"idun sai sun Dawo karkashin cewata ai Fara Bin sa gidan gona ba shi ne Mallam ya sakar mai komai ba Tukunnah dai Dayyaba akwai sauran rina akaba..!

Mamanmu gabadaya yanayinta ya Sauya jin kalaman madina har suka gama wayar sama sama take amsata tana faman mata gatsine,Har dai ita mamanmu tagaji ta katse kiran lokaci daya tana bin wayar da Harara tana fadin"Haka kurum na kiraki da kudina da wayata ki Zauna kina neman gayamin mgana ina Dalili..!
Dukiyar ai bataki bace Ko shi mallam din Daya tara bai Damu da ita ba sai ku kuna ta neman halaka kanku Saboda ita har kina Fadin har sa"idun sai ya Dawo karkashin cewarki..?
Haka kurum ba kara sai ki maidamin Miji kamar kwallo ki dinga garasa yadda kika ga Dama to wlh madina Baki isa ba kan Sa"idu zan iya yin komai Ciki har da Raba Hanya Dake sai kowa yayi ta kansa kan mene ina Dalili wannan Bakinciki ina jin Dadi na Samu yadda nake so aikuwa Allah ne ya Hada mallam da Sa"idu ban ga mai rabasu ba haka kurum Madina ke wata mganar banza..!
Surutun ma tana yi ne bata san tanayi ba Aba ne ya fito zai shiga bayi yaji tashin mganarta har ya shiga ya fita tana mganganunta shiyasa ya Leka Dakin nata yana Fadin"Balaraba ke da waye kike ta fada haka..?
Tun dazu nake jin tashin mganarki nama Zata ko da hamida kike ne sai na Leka Dakinsu naga sun kwanta ita da Jawaad.
Sai alokacin mamanmu ta Dawo Cikin Hayyacinta ta fara inda inda tana Fadin"Ni da masu yarenan ne yan iskan sai su kira ka suna maka gwaranci ko kai basa kiranka..?.
Ya saki labulen yana Fadin"To da kin ji sune ai sai ki kashe wayar ki ni ai bani da Lokacin Sauraran irin su. !
Da haka ya koma Dakinsa Mamanmu ta Sauke ajiyar zuciya ta biyosa tana Fadin"Shikenan kuwa haka zan dinga yi musu sai mu rabu lafiya. !
Aranta sai taji salama da Aba bai Tsinkayi wasu daga cikin magnganunta ba.
Ai data shiga goma ba uku ba.

Acikin Satin kamar yadda Danmallam ya Tsara jirgi ya fara yo gaba da kayansu saboda yayi ma iyayansa da matansa siyayya musamman ma Amina Komai ya gani sai yace zai ma masu Ciki kyau harda kayan jarirai masu kyau duk ya siya ammh bai bari Sarood ta gani ba sannan yazo da Ruwan Zam zam mai yawa saboda mallam yamai mgana yana so da Dabinio sai sauran abunda ba"a rasa ba kuma bai sanar da kowa shi da Sarood zai taho ba sai dai agansu kawai.
Kwana Biyu Tsakani kayan suka iso Jafar da Nasir suka je Filin jirgin Kano suka karbo kayan Direct Gidan mallan akayo da kayan Dakin Hajiya Daman kowa yasan in irin wannan ya faru kayan da komai Shashen Hajiya ake ijiyesu kafin ya Danmallam din ya sauka.
Sakina ana chan ana shiri miji zai Dawo tayi gyaran kai tayi kunshi Sannan tayi gyaran jiki da na chan Shawaran Aliya ne ita ta Hadata da mai kayan matan ta siya awajenta.
Miji kawai take jira ta riga ta gama Shiryawanta.

Ko Amina in sukayi mgana in ta tambayeshi yaushe zai dawo sai yace ya kusa bai saka mata rana ba,yaki gayamata ranar da zai dawo so yake ya bata mamaki sai dai ta ga ya Kirata da Layinsa na Nageria.
Haka kuwa akayi Ranar laraba suka sauka da karfe sha biyun Dare,kwana Biyar da sau kan kayansu suka iso a kano jirgi ya saukesu saboda Dare ne yasa bai kira kowa ba suka samu Tashar Mota shi da Sarood sai jakar kayansu suka nufo gumel sai wajen Biyu da wani abu na Dare suka iso gidansa ya wuce kai Tsaye sai dai Sakina taga Bakin Dare sai murnanta ta koma Ciki ganin Sarood sai da ta nuna afuskantar duk yadda taso ta boye hakan Sarood ko Cikin Murna taje ta Rumgume Sakina Tana Murnan ganinta....
Sakina tayi yake kawai tana Tunanin yadda Umar ya maidata banza ai bai gayamata kafarsa kafar matarsa ba Tana jin dadi ta gagari Amina Zama agumel shine zai jajibomata wannan Sakaryan.
Dakin da aka bama Amina ta Zauna Sarood ta shiga sai dai yanayin Dakin da sauran kayan Amina Data gani yasa tasan an zauna adakin Saboda Gajiyan Hanya da kuma Dare yasa sai da Safe ta ma Sakina Zencen tunda suna Dawowa Umar Dakinsa ya nufa yayi wanka ya kwanta Sai barci sai da Safen suna kari Sarood ke tambayan sakina kayan waye tagani adakin ta..?
Sakina Cikin kissa ta ke sanar da ita kayan Amaryan sa ne Amina nan ta Zauna Sarood ta kallesa sai dai batace komai ba ammh ranta ya baci meyasa Sai Dakinta baga Dakinsa ba..?
Sannan wato ita aka raina meyasa bai ce ta Zauna Dakin Sakina ba..?
Kwafa tayi har suka gama karyawa batace komai ba Sakina sai jin Dadi take yi ranta Fes domin da asuba sai da ta ribaci Umar yayi wani abu da ita kuma taga Chanji Sosai yadda ya rikice mata sannan karin jin Dadinta yadda ta zuga Sarood Cikin Ruwan Sanyi batare data gane ba Tunda ita Sakaryace shi kuma Danmallan kunu yasha baisan wata mgana yasan Nufin Sakina tunda ba yau ta saba raina ma Sarood din hankali ba.
Ganin yadda ya Hade rai ne yasa Sarood din bata yi mganar ba Sai dai Daga yanayin ta sha ka matuka da Kishi Sosai.
Suna gama karyawan suka shirya suka suka nufo Gidan Mallam Jafar ya Kira yazo da mota ya Daukesu daman Tun shekaranjiya an san sun iso
Gida ya Rude da Murnan dawowarsa Gabadayansu har da Matan nasa duka Shashen Hajiya suka fara Sauka Har Sakinar domin ba hanyar da zata fara wucewa Shashen Anty Amarya ganin yadda ya Tsare gida..
Gabadaya matan mallam har da Anty Amarya nan shashen Hajiyar sukazo musu maraba su Hajiya Uwani kada aji labari sai barin jiki take yi Danmallan kallon Anty Amarya kawai yake yi yana Tuna labarin da Amina ta sanar dashi bai san Dalili ba sai yaji bai yarda da ita ba Tun balle ma ganin yadda take ta Kiftama Sakina Ido tana so su kebe suyi mgana ganin wannan balarabiyar da bata san da Zencen zuwa da ita ba, yana ganin su yayi kamar bai gani ba.
Nan ya barsu ya tafi falon mallam shi da Nazeem suka hadu da Aba suka gaisa basu Dade ba suka tafi gidan gona ya Dade shashen mallam suna kara Tataunawa .
Fitarsa ne ya bama Sakina Daman sulalewa ta koma Shashen Anty Amarya suka kebe Anty Amarya Cikin Bacin rai tace"Sai naga kuma wannan Sakaryan. ?
Sakina ta tabe baki kafin tace"Nima yadda kika ganta haka na ganta..Ashe da ita zai taho..!
Anty Amarya tace"To me kika fahimta da Zamansu tana nan a Hotonka ko kin Fahimci sauyi. !?
Sakina tace"Anya..?nidai ban Fahimci komai ba..!
Anty Amarya tace"To ki saka musu ido duk nasan aikin mallam na Dadewa yana Tasiri..!
Da toh sakina ta amsa mata suka Ciga da Kulle kullen su tana bata Labarin Tambayar da Sarood tayi na wacce ta Zauna Adakinta da abunda Sakinar tace mata Anty Amarya na Dariya tace"Gwara da kika fadamata haka..Sakaryan sai ta bisa da tsiya..Ai Amina ba zaman gidanki ba ma Mijin da garin gumel gabadaya ne ya gagareta. waya gayamata Barno gabas take..!
Sakina Tayi dariya kafin tace"Wlh kamar fa anyi ruwa an Dauke ko mganar fa bayayi..!.
Anty Amarya tace"Ai bazai yi ba..Wayama sani ko auran ya Dade da Mutuwa fasawa ne ba"ayi ba kada aji kunya su Hajiya an yi Zani an yi Riga. !
Sakina tace"Zai iya yuyu wlh Anty..!
Allah ma yasa hakan ne..!.
Ta amsa mata da Ameen suna Dariya Ranar dai suna gidan har Dare wannan karon Sarood Shashen Hajiya ta Zauna tare da su Hanne tunda suna gida basu da Jarabawa wannan karon Sakina taji Haushin zuwa da ita da akayi yasa bata jata ajiki kamar baya ba
Sai Dare suka koma gida,Washegari shi kadai yazo su suna gida Shashen Hajiya ya yada Zango aka Bude kaya ya bama Hajiya Tsarabanta na Turaren da Hijabin larabawa na mata sai Dogayen riguna guda Biyu masu kyau da Tsada da takalmi haka ma Anty Amarya da Haj.Nasara da Haj.Uwa dogayen riguna da Turare,Wannan karon har Hanne da Hamida yama Tsaraba domin bazai manta da kaunar da Amina ke musu ba, waya goma sai ta ambace su shiyasa daya siyo mata suma ya siyo musu Ya kuma nuna mata tsaraban Amina da Siyayyan kayan Jariran Da yayi,Hajiya Taji dadi sosai ta dinga yabawa sai dai Bata ga Tsaraban Mamanmu ba Tunda Har Aba ya yoma Tsaraba Sai alokacin ya tuna ma da ita Har ga Allah bai yi niyyar bata bane kawai Saboda tundaga Labarin da Amina ta basa yaji matar bata kwanta masa ba sai bai nuna ma Hajiya ba yace ya manta ne sai Hajiya tace bari ta bata Cikin nata.
Sai ta hada mata da Ruwan Zam zam da Dabino.
Hajiya ta aika ma su Haj.Nasara da Tsaraban Danmallan suna ta godiya haka su Hanne suka yi ta Tsallen murna,Ganin har dasu a Tsaraban Hamida da Hannen ma suka kai ma Mamanmu nata ta karba tana ta godiya da Santi tana auna kanta in tayi ma Aba kwaliya da ita..
Mallam dai Turarensa ne na Arab sai Zam zam da Dabino.
Tsaraban sakina gida yakai mata nata Sai jin Dadi take yi ganin har da takalma ga kayan masu kyau da Tsada
Na Amina kuma wajen Hajiya ya barsu su hanne kuwa tunda suka ga basu ga Amina ba kwana uku da Dawowar ya Danmallam ba labarin Dawowar Amina sai suka cire rai da Mganar Hajiya da kullum take sanar dasu Amina zata dawo nan kusa sai suka Sare..
Gashi har sun yi nisa a jarabarwarsu suna gabda gamawa gabadaya sai basa jin Dadin zama,ba Amina suma sun yi ahuru kamar basu agidan da ko da Amina ke nan wlh sai su shiga gidan mallam sau goma gidan Aba ma haka Rashin jinsu kawai yasa Dole ma asan dasu ammh yanzu sai a kwana awuni ba ba"aji ko motsinsu ba.
Islamiya da Boko ma an gaji da Cigiyar Amina Daga baya ma su Hanne cewa kawai sukayi an cireta Daga mkaranta bata agarin harta mariya abokiyar fadanta da malaman makarantarsu Mallam Datti da kansa ya Kira mallam ya tambayesa Amina Mallam yace mai Amina bata gari ne shiyasa..!

Kwana hudu da dawowarsa Ranar yazo Gidan da Safe Ya shiga shashen Hajiya suka gaisa da sauran matan Sannan ya koma wajen mallam to basu Dade da Mallam ba aka kirasa agidan mai anguwa Idi ya tafi kaisa Aba kuma baya nan sai ya tafi Dakin Nazeem ya dan kwanta ya Huta Sarood Tun abunda Sakina ta Fadamata take shamai kamshi sai bai Biye mata ba Sakina kuma kamar rana Daya zai mata Ciki takuranta ne ya Ishesa,yake barin mata gidan ita da Sarood din su ci kansu.
Amina kuma tun washegarin ranar daya sauka daya Kirata bayan ya saka Layinsa na nan ya fadamata ya Dawo suka gaisa har take fadamai sun je asibiti ta fara awo sannan an mata Scan,basu wani jima suna mgana ba yace zai sake kiranta,kuma bai Samu Lokaci ba,Basu zauna sun yi mgana da Hajiya bane yana so yaje ya ganta kafin ya koma tunda ba wani Dadewa zai yi ba Sati Biyu ne zasu yi,zasu koma.

Yana kwance har ya fara barci yaji sallama kamar daga sama yana Bude idanuwansa ya ci karo da Hanne da Hamida suna rabe raben shigowa Hanne na Tura hamida itama tana Turata mikewa Zaune yayi Daga kan gadon yana fadin"Ku shigo mana..!
Jin haka yasa suka shigo Dakin kansu na kasa kamar wasu marayu duk suna Sanye da manya Hijabi har kasa mamakin ganinsu yayi gabansa suka Duka kamar masu neman gafara gaishesa sukayi ya amsa yana Dan Nazarinsa dazu a falon Hajiya yaga Hanne sun gaisa hamidan ne dai bai gani ba. !
Hamida kuma hanne ce taje ta jawota kan suzo su tambayi Ya Danmallam Tunda Hajiya taki fadamusu inda Amina take kila shi zai fadamusu shine suka zo a bakin Hajiya sukaji yana Dakin ya Nazeem Shine suka zo sun kuma kasa mgana saboda ba Sakewa Tsakaninsu sannan yana musu kwarjini.
Shine yaga suna Sunkuye sunkuye kai da taba juna yayi mirmishi kafin yace"Lafiya..?
Baku je makaranta bane yau..?

Hanne tace"ai jarabawa muke yi yau bamu dashi sai monday..!

Ya gyada kai sai yanzu ya tuna da Tsarin Tun farko,tunda Hajiya ta sanar dashi yadai manta ne,Cikin Sanyinsa yace"Kuyi mgana ina Fatan dai lafiya ko..?
Hamida ta sanda kanta kasa tana Fadin"Dama..Dama..Muna so mu tambayeka ne ya Danmaallan..!
Zama ya gyara yana Fadin"Allah yasa na sani..!
Hanne ta zungura ita kuma sai ta kara kasa da Murya tana Fadin"Dama kan mganar Amina ne yaya..
Kai Tsaye yace"Amina..?
Me ya faru da Aminar.?
Hanne tace"Bakomai tunda Hajiya ta tafi da ita har yanzu bata Dawo ba..Muna ta tambayanta ina take taki gayamana gashi har mun fara jarabawa ba Amina muna kewarta ne Hajiya sai tayi ta ce mana zata Dawo Zata Dawo ammh shuru..Shine mukace bari muzo mu tambayeka muji ko kasan inda take..?
Wlh kuma bamajin Dadin Zama ba Amina..!
Hanne ta karbe da cewa"Kawayen mu sai tambayan mu ita suke yi..Kowa sai yace ina Amina.?
Mu kan mu muna son sanin inda take..!

Sai da suka gama Mgana yana kallonsu kafin ya saki Mirmishi ya tuna sanda ya kira Amina yace ya Dawo abunda ta fara tambayansa yaga Hamida da Hanne..?
Don Allah ya gaishesu yace tana missing dinsu.ai shi shaida ne Saboda Rabin wayarsu mganar Hanne da Hamida ne ya Dade yana jinjina wannan kaunar Dake Tsakaninsu Amina tana matukar ji da Hanne da Hamida in tana Hiransu haka Zakaji Farinciki da Murna acikin muryanta Shi bai wani zauna dasu ba ammh yasan dai tare suke su uku ammh baisan Rayuwarsu ba gaskiya.

Gyaran Murya yayi kafin yace"Kada ku Damu Amina na Cikin koshin Lafiya..Itama tace na gaisheku sosai tana kewarku..!
Suka kallesa kafin su koma su kalli juna sai Hawaye duk ya Cicciko Idanuwansu Hanne tace"Muma muna kewarta don Allah tana ina..?
Kuma yaushe zata Dawo..?
Kai Tsaye yace"kuyi hakuri bazan iya Fada muku inda take ba..Ammh tana Cikin Koshin lafiya..Sannan zata Dawi kowani Lokaci itama bata manta daku ba koda yaushe Cikin Zencen ku take yi..!
Kawai sai suka fara mai sharan kwallah ya kallesu baki bude bai yi mamaki ba in ya Tuna yadda suka rika uban kuka Ranar da zai tafi da Amina gidansa.
Gyara zama yayi kallesu yana Fadin"ku share hawayenku..Ku Zauna Dakyau yau labarin Amina zaku bani Tundaga Farko har karshe..!
Yau ina so naji nima..!
Hama kurum yake son jin Labarin Amina,batare da yasan Dalili ba.
Jin haka yasa suka gyara zama suka Fara bashi Labarin Amina da yarintarsu Hanne tayi in ta gaji Hamida ta karbe in suka fadamai wani abu baya sanin ma yana Dariya jin jina Jidalin Amina kawai yake yi aransa ashe haka tayi nisa bai sani ba ?
Kirarinta ke basa Dariya in ya Tuna wai Aminene ikon Allah badai ta Mutum ba sai ta Allah lalle yarinyar nan sai Allah taci kuma kirarinta..
Hanne ta Karbe da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login