Showing 75001 words to 78000 words out of 265571 words

Chapter 26 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28935

Dawowa..!
Kai suka gyada gabadayansu Baba mallam ya cigaba da musu nasiha yana Nuna musu illah yanke hukunci Cikin fushi da aibata ya"ya da kalamai marasa Dadi sunan nan sai gasu Hajiya sun Dawo falon Aba suka shigo Gabadayansu Hamida ta Tsaya Daga wajen Daman tunda suka tafi ta ke kuka Tasani Amina tana da Jidali sai dai bata taba Tsammanin Jidalin Amina yakai har ya huce yadda take tsammani ba
Amina da plasta a goshinta bakinta kuma wankeshi akayi ya Kumbura mamanmu kuma mgani aka bata baba Mallam ya kalli Amina Dake Nanike da Mamamanmu kafin yace"Hajiya ki tafi da Amina ta zauna awajenki har ta samu sauki..Ke kuma Balaraba kiyi hakuri kin ji..
Sa"idu ya maidake Dakimki Don Alllah ina so har Abada bayan mu anan kada wani yaji wannam mganar..!
Mamanmu tace"Insha Allahu mallam..Bakomai..!
Baba Mallam yaji Dadi yana ta saka albarka kafin ya Mike shi da Hajiya wacce ta Riko Amina da hannunta ke cikin na Mamanmu kanta ta Dafa tana Fadin"Kada ki damu
Har Abada ina nan a matsayin Mamanki Diyata.!
Gobe zan shigo na Dubaki zan zo miki da kayanki..!
Kai ta daga mata Zuciyarta ta Sauka Tunda Aba ya janye sakin da yayi mata radadin Dake ranta ya Sauka haka suka fito har kofar gida suka rakasu dukkansu Hamida ta rike ma Amina hannu sai haawaye Amina ta Rike Hamida tana Fadin"kuyi hakuri Hamida ku yafemin..!
Hamida ta saka mgana har Hajiya taja Amina suka tafi wannan wani irin almari ne..?
Bata fatan kara ganin mai kama da wannan Ranar.
Achan gidan Baba Mallam kuwa Su Hanne duk sun yi barci Dakinta Hajiya takai Amina ta saka mata Ruwa mai zafi tace ta shiga tayi wanka ta gasa jikinta ita kuma ta Fice Shashen Mallam shi yake karanta mata abunda ya faru bataji Dadi ba ammh Tunda Mallam yace zai yi mgana da Amina shikenan komai zai Daidaita.
Bata jima ba ta Dawo shashenta,Saboda Hajiya nasara tazo wajen Mallam koda ta koma Amina tayi barci Dayake an mata allura a asibitin Tsausayinta Hajiya taji wata Kaddaran bamu ke Dorama kanmu ba Allah ne..!
Hajiya shimfida tayi akasa ta kwamta ta bar Amina akan gadon sai Washegari ne su Hanne su ka ganta Shima Hajiya ce tace su shiga su Duba Amina bata da lafiya kafin su tafi makaranta Allah yasa ma suna Revesition ne su Amina su kuma su ya Abida suna Mock ne.
Da suka Tambayi me ya sameta sai Hajiya tace Zamewa tayi a bandaki Hanne tafi shiga Damuwa da Halin da Amina ke ciki,Sannan kuma Amina ta Riketa tana Fadin"Keda Hamida nayi muku laifi ku yafemin Hanne..!
Bata iya gane komai ba,Sai da Suka je makaramta suka hadu da Hamida ta Fadamata komai Hanne ta shiga Tashun hankali Fadi take" kin ji ko.Hamida..?
Amina ta Debo jidalin Dayafi karfinta..!
Hamida tace"So nake ta kara jin Sauki..Sai mu turketa ta Fadamama yaushe ta fara aikata abu batare data sanar damu ba..!
Hanne tace"Tabbas..!
Da haka suka bar mganar sun fada a makaranta Amina bazata samu zuwa ba bata da lafiya bayan sun dawo ne suka shiga Har hamida gidan Baba mallam ta Duba Amina har da su Sa"adatu da yake an Fada Aminar bata da lafiya da ya Shamsu yaga bai ganta ba Hamida ta Fada acikin mota sanda Idi ya Daukesu
Taji sauki sai dai Kumburin bakin kadan shima ya Sauka goshin ma yayi Sauki Mamanmu ma ta warware ta shigo har Fatan wake da Hanta tayo ma Amina Hajiya na mata tsiyan cewa ko ta mata kara ta bar mata Amina sai ta Biyota Mamanmu na Dariya tace"To karan me Hajiya..?
Zan iya kara akomai banda Abunda ya shafi Amina..!
Nan suka yi ta raha da Hajiya Amina taji Dadin ganin mamanmu ta Rumgumeta tana fadin"Mamanmu ki yafemin..!
Mamanmu ta shafa kanta tana Fadin"Kada ki damu..har Abada matsayinki bai Sauya ba Diyata..Allah yayi miki albarka..!
Su hanne suna son mgana da Amina basu samu zama ba itama tana so ta yi mgana dasu tana so ta fada musu komai Saboda taji sauki aramta tana cikin wani hali Bata barci Aminu na cikin ranta tana so tasan Halin Dayake ciki gashu bata san ta wacce hanya zata sani ba Duk abubuwan da suka Faru basu saka ya fita ranta ba yana nan a makale ta damu dashi ta Damu tasan wani Hali yake ciki.
Tunda ga Ranar bata kara ganin Aba ba ballatana Yaya ammh har ya Zeenatu tazo sun gaisa su ya Zulaihat ma duk Mamanmu ta fada musu sun kira sun gaisheta kuma ba wanda yasan me yafaru sai dai ace abandaki ta Zame har su Anty Amarya sun shigo sun Dubata duk da tana ta Bin Diddigi Dalilin ganin Amina agidan.
Sai da Amina ta kwana Hudu awajen Hajiya sannan suka samu kebewa da Amina suka tambayeta ta fada musu komai Hanne da Hamida suka Saki baki suna kallonta Amina ta cigaba da Fadin"Wlh bansan yaushe ne ba..Ban kuma sam Lokacin da soyayyar Amin ta shiga raina ba..Ammh wlh ina son shi ko da wannan abun ya faru ban ji ya Ragu araina ba ina nan kawai ammh ina cikin tashin hankali da Damuwa na san yana chan cikin Tashin hankali..!
Hamida tace"Kina nufin wannan dai gayen da muka taba gani..?
Amina ta daga kai Hanne tace"Amina kuskuranki ne..Meyasa baki barsa yaje wajen mallam ba..?
Amina ta Dafe kanta tana Fadin"Bansani ba Hanne..Bansan haka zai iya faruwa ba..Gani nake kamar komai bazai yi daidai ba in yazo..Kuma wlh yanzu Ina son Aminu bazan iya Rabuwa dashi ba kuban shawara..!
Hamida da hanne suka kasa mgana Hamida ce tace"Bamu ta cewa Amina..Mgana tana wajen Aba da Baba Mallan sai dai in zaki bi Shawaranmy kada ki nuna abunda ke Ranki..Ki bari har muga komai ya Daidaita..!
Hanne tace"Nima abunda zan ce kenan..Gwara ki tsaya kiji abunda zasu ce..ammh koni kaina zan so ki Boye abunda ke ranki..Ina ji ajikina Ki rabu da wannan Mutumin Amina Shine Alherinki..!
Amina kallonsu kawai take yi batace komai ba Rabuwa da Aminu ba abu bane mai Sauki,Abu ne da bazai taba yuyuwa ba Domin don basu san me take ji bane..!
Shuru tayi musu kamar ta bar mganar sai dai ta kasa sukuni Baba mallam bai ce mata komai ba kuma yana zuwa Dubata,ammh bai ce mata komai ba,ga Damuwar halin da Amin yake ciki tasani kila ita tafishi kwanciyar hankali tasan yadda yake sonta Allah kadai yasan wani Hali yake ciki

Kwana Biyar da Faruwar abun ta kasa Daurewa ta samu Hamida da Hanne ta Rokesu su samo mata waya ta Kira Aminu ko hamkalinta ya kwanta Hamida ta kalli Amina tana Fadin"Amina kada ki kara jawo wani Jidalin don Allah..!
Hanne tace"In dai zata kirasa ta Fadamai ya rabu da ita zan Dauko miki wayar hajiya..Ammh da sharadin wannan shine na karshe..!
Da sauri Amina tace"Naji Hanne..Naji..!
So take kawai tayi mgana dashi Hamida kamar zatayi mgana sai kuma ta fasa,Hanne taje ta Dauko Wayar Hajiya Amina ta shige Tiolet din Dakinsu Hanne su kuma suna Waje suna Tsaro kada wani ya shigo su Lalace.
Jikin Amina na rawa ta saka Lambar Aminu ta Kira tana Di..Di..Di..kamar Zuciyarta zata Fito gabda zata Tsinke Taji an Daga Cikin Sanyinsa akoda yaushe yayi sallama Amina Kafafunta sun fara rawa kawai sai ta sakamai kuka yana jin haka zumbur ya mike Daga kan gadon Hotel din daya kama yana Fadin"MEENATA..aminatu..Alhamdulillah..Amina na shiga wani Hali..Tun washegarin abunda ya faru ina garinku Amina kullum ina anguwanku ina ganin yan"uwanki ina so nayi musu mgana na rasa yadda zan yi..Meena kina ina ne..?
Meena ina so na ganki ki taimakamin in banganki ba wlh zan lalalace Meenataaaa..!






*Janafty*

*TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janaftyd'?*

*Sadaukarwa ga Halima yusuf gwarzo besty*

_Jinjina ta musamman gareka NAZIFI YARIMA..Nagode da karamcinka gareni na yaba matuka Allahu ya bar zumunci Ameen_



*
Jin ta kasa mgana sai kuka take yi yasa ya kara marairaicewa yana Fadin"Meenata kina ji kuwa...?
Ki yi hakuri ki daina kuka ki bari nazo Domin nasan ta yadda zamu Bullo ma al"amarin Kinji ko..?
Gabadaya yadda yake mgana ya gama kashe ma Amina jiki Tsausayinsa ya kara kamata tasan yadda yake sonta tasan Halinsa bazai taba kwanciyar Hankali ba sai ya ganta sai dai bata da wannan Damar ayanzu komai ya gama Lalacewa.
Tana jinsa cikin Damuwa ya kara Fadin"In zo Amina..?Don Allah kada kice A"a..Ina son ganinki..!
Hawayenta ta share cikin muryan kuka akaron Farko tace"Bazai yuyu ba..Kayi hakuri Amin komai ya kare..!
Ta karishe fada cikin kuka Tsabar yadda kalamanta suka gigita yasa ya koma ya zauna gefen gadon Daya tashi Cikin wani yanayi yace"Bangane ba Meeenata..?
Me kuma ya kare tsakanina Dake..!
Amina na Danne bakinta da kuka tace"Komai daka Sani ya kare..Soyayya ta dakai ta zama Tarihi kayi hakuri ba Laifina bane..!
Sai kuma ta kara Fashewa da kuka kukan da Aminu yake jinsa kamar acikin Ransa.
Cikin Fitan Hayyaci yace"A"a Amina kada kimin haka..Kada ki ce zaki Rabu dani alokacin da nafi kowa Bukatarki kinsan bani da kowa sai ke sai Nenne wlh in na rasaki Meenata zan Lalace ki bari nazo na ganki..Ki bari na bayyana kaina Amina Ina sonki Rashinki babban Gibi ne ga Rayuwata Amina ki taimakeni..!
Yana mgana hawaye na Bulbulo masa kamar famfo batasan sadda ta saki kukanta da karfi ba,Lokaci Daya ta abude Kofar Tiolet din ta Fito tana Gunjin kuka,bata kashe wayar ba ta mikama Hanne da Hamida da suka yo kanta ganin tana kuka kan gadon su Hanne ta Fada ta na Sakin kukanta Wlh itama tana son Aminu kuma Rabuwa dashi babban Ciwo ne agareta ammh ya zatayi..?
Aba zai kasheta in ya kara jin Labari makancin wannan,Zai iya mata baki Watarana shiyasa take tsoro sai dai tana Tsausayin Aminu tasan yadda yake sonta da gaske ne zai lalace akanta in ta rabu dashi.
Hamida ce ta isa gareta tana Fadin"Menene Amina..?Don AllAh ki Daina kuka hakanan..?
Hanne ce ta Lura wayar na tafiya yasa ta saka wayar a speaker daidai Sanda Aminu ke fadin"Meenata kina jina..?
Don Allah kimin rai ki taimakeni na ganki..Wlh kwanana Hudu agarin nan Saboda ke in ban ganki bazan taba Samun natsuwa ba..!
Ayadda yake mgana kowa yaji sa sai ya basa Tsausayi Amina kara Fashewa da kuka tayi zuciyarta na suya ashe ashe akwai irin wannan Ranar da Farinciki zai koma bakinciki bata Tsammanci Ranar nan kusa ba bata zata zata zo yanzu ba..!
Hamida da Hanne jikinsu ya gama yin Sanyi Hanne ce tayi gyaran Murya kafin tace"Ba ita bace..sunana Hannatu ni yar uwartace..!
Da Sauri Aminu yace"Hannen Amina..Hannen Hamida ai na ganeki..Amina tana bani Labarinku..Don Allah Hannatu ki taimakamin naga Amina don Darajan ma"aiki Salallahu alaihi wasallam..!
Suka karisa gabadayansu Cikin tsausayinsa Hanne tace"Akwai matsala ne..abubuwa Dadama sun Faru wadanda bazasu fadu ba..Ina Kara Jadaddamaka Haduwarka da Amina bazai yuyu ba kayi hakuri..!
Tana shirin yanke kiran ne yayi saurin Fadin"Koda na minti biyar ne..?
Koda na ganta nayi mata sallama ne Hanne..?Amina itace ni Hannatu..Wlh in bata zan Lalace Hannatu..Nenne zata rasani zata rasani..!
Dagajin yadda yake mgana kuka yake gabadaya sai hanne ta kasa mgana Cikin Tsausayi take kallon Hamida wacce ta Zabga Tagumi Ta rasa mafita sai Amina Dake kallonta idanuwanta Jajir tana kuka Dagachan taji magiyarsa Cikin Raunin Murya"Ki taimakeni Hannatu..Nayi miki alkwarin wannan shine na karshe..Don Allah ina son ganin Amina..Don Allah..!
Hanne ta saki ajiyar rai kafin tace"Shikenan..Kazo da Daddare bayan Sallar isha'i..'
Cikin Rauni yace"Meyasa ba yanzu ba Hannatu..!?
Hanne tace"Ba dama ne..Kabari dai Daddare shima sai mun san yadda zamu iya ku hadun..!
Suna jin Saukan Numfashinsa kafin yace"Nagode kwarai..Nagode Hannatu..Bazan taba mantawa da karamcinki ba..!
Da haka Hanne ta Datse kiran Hamida tayi saurin cewa"Hanne kikasan me kika aikata kuwa..?
Hanne tace"Ya zan yi Hamida..?Tsausayi ya bani..!
Hamida tace"To yanzu ta yaya zasu hadu batare da wani ya sani ba..?
Nidai ina Tsoro fa..Yadda abubuwan suka Lalace In muka kara wani laifin ba Amina ba har mu bazamu taba Fita ba Hanne..!
Hanne shuru tayi batayi mgama ba sai chan tace"Zamu samu mafita Hamida..Kada ki damu..!
Amina dai kukanta kawai take yi Cikinsu an rasa mai Lallashinta gabadaya Tsausayinta ya gama kamasu suna Tunanin har yaushe ne Amina ta bari ta fara soyayya har tayi wannan Zurfin basu sani ba..!
Sai da suka gaji da jin kukan nata suka Fara bata hakuri kana ta Hakura ta Daina kuka sai dai idanuwanta sun kumbura ido ya sauya Launi saboda kuka har zuwa yammah sun gagara samun mafita Hamida ta kalli Hanne tana Fadin"Ki basa hakuri kawai Hanne..banga mafita ba..Waje fa kinsan su Baba mallam suna nan ta ina zasu hadu batare da wani ya gansu ba..!
Hanne dai batayi mgana ba tana ta Tunanin mafita ba har akayi sallar Isha"i basu samu mafita ba Ya Abida ce ta shigo ta gansu zugun zugum Dariya tayi tana Fadin"Ku kuma Lafiyarku kukayi zugum kamar masu zamam makoki..?Ko Aminar ce taki Warwarewa har yanzu ku cigaba da Iskancin naku..?
Cikinsu ba wacce tayi mgana itama bata Damu ba baki tatabe tana Fadin"Bakin Amina ya Mutu..Na Hamida da Hanne daman bai kai nata Tsini ba suma sun mutu..Allah Sarki..!
Ta karishe Fada Tana Dariya wannan karon Mirmishi kadai Hamida tayi mata Ta fice daman wani Littafin koyon Turanci ta Dauka cikin Jakar makarantar ta fice.
Hamida Bini bini ta kalli Hanne tana Fadin"Kin samo mafitan ne..?
Sai hanne ta Girgizakai Cikin Damuwa Hamida kan ce"Jikina na Sanyi..Ina ji kamar wani abu zai faru Hanne..!
Itama Hanne haka take ji ammh Tsausayin Amina take ji da Aminu Shiyasa ta kasa cewa A"a tunda Farko Tunanin wani abu tayi taja hannun Hamida suka fita Leke suka fara yi Domin ganin wadanda ke waje Allah ya taimaka ba kowa masallaci ma an Rufe ba Motar ya Jafar bata Ya Nasir kenan sun tafi gida Saannan Allah ya taimake su Aba ya Dawo da wuri ga Motarsa nan sannan sunji mganarsa afalon Baba Mallam da Hajiya Babba..!
Hanne ta kalli Hamida tana Fadin"Na samu mafita..In..!

"Su waye anan..?

Gabansu ya fadi da sukaji Muryan ya Shamsu Cikin Daburcewa suka juyo Hamida ce tayi mgana"Bakomai ya shamsu cikin gida zamu shiga..!
Yana Tsaye Daga kofar Dakinsu yace"Cikin gidam ina..?

Da sauri Hanne tace"Zan rakata gida ne ya shamsu..!
Kamar zai yi mgana sai kuma suka ga juya ya koma Daki ya Dauko Buta Makewayin Dake bayansu ya wuc???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?e bai karama kallonsu ba ganin haka yasa suka Sauke Numfashi Hanne taja Hannun Hamida suka Fice daga gidan zuwa gidansu wayar Hajiya tun mangariba ta Dauketa tana Hannun Hannatu.
Gidan su hamida suka je suka zauna Har Aba ya dawo sannan Hanne tatashi tace zata tafi Hamida ta rakata mamanmu har tana Fadin"Hanne baki kwanciyar anan..!?
Da sauri Hamida tace"Mamanmu Amina zata bari ita kadai in ta kwana anan..!
Mamanmu tace"Kuma fa hakane..To maza ki rakata Hamida ki Dawo Dare yayi..!
Da haka suka samu suka Fice Aba na Shashensa Yaya ta kaimai abinci suka Fice akofar gida suka Tsaya Hanne ta Leka Wani lungin jikin gidansu Amina Dake da Duhu kadan Tunda Kofar gidansu dana Baba Mallam gauraye yake da Hasken Gen da aka kunna Hamida ta nuna ma wajen tana Fadin"ZAn kirasa yazo ta nan su hadu..Ni zan Tsaya anan ki shiga ki Fito da Amina yau Hajiya Shashen baba mallam zata kwana zamu Tsaya Daga chan muna gadinsu kada wani yazo..!
Hamida ta kalleta cikin Tsoro kafin tace"Kina ganin ba Matsala..?
Hanne ta Sauke Numfashu tace"Insha Allahu..Ki fadama Amina kada ta bata Lokaci..!
Kai hamida ta gyada ita ta Fara wucewa zuwa gidansu Hanne ita kuma ta koma kofar gidansu Amina ta Danna ma Aminu kira Daman ta adana Lambar da sunan Amina.
Tana shiga kamar yana jira ya Daga Kiran kafin tayi mgana yace"Ina Hangenku tun dazu hannatu..Amasallacin gidanku nayi sallar mangariba ma..!
Hanne ta zaro ido ta fara waige waige Daga chan gaba ta hango hasken Mota motan a kashe sai kuma aka Bude Mota aka fito Cikin son Tabbatarwa Hanne tace"Kai ne Daga nesa..Ka fito a mota..!?
Cikin wani sanyi yace"Eh nine..!
Da Sauri Hanne tace"To ka kariso da Sauri..Yanzu Hamida zata zo da Amina..!
Daga haka ta datse kiran ta shigo gidansu Amina jikinta na rawa kada wani ya fito ya ganta Aminu da Sassarfa ya kariso duk ya rame kamar wanda yayi jinya yana Sanye da Riga da wando bakake ya saka wata Rigar Sanyi mai Hula ya Rufe kansa yana zuwa Hanne ta Leko sai da Tabbatar ba kowa sannan ta fito tana Fadin"Don Allah minti goma..Akwai Hatsari Aba na cikin gida hakama Baba Mallam sauran yayyinmu ma suna cikin gida kada ka bata Lokaci har komai ya Lalace don Allah..!
Hulan kansa ya cire fuskarsa ta bayyana Cikin Muryansa kamar ta waya yace"Insha Allahu Nagode Hannatu..!
Zatayi mgana kenan sai ga su Hamida sun fito Amina na bayanta da Hijabi tana Tafe kamar wata mara Laka ajikinta Allah ya taimake su ya Abida na Kitchen Hajiya kuma na shashen Baba Mallam suka samu suka Lallabo suka fito Allah yasa ba wanda ya gansu..!

Tundaga nesa yake kallon Amina Hankalinsa ya tashi da suka kariso yaga saman kanta da Ciwo an cire Plastan tuni,Da hanzari ya karisa gabanta yana Fadin"Meenata me ya sameki ne..?
Yadda yake kallonta haka take kallonsa Hawaye sun tarun mata ganin yadda ya rame hamida da Hanne sai suka koma gefe suna kallon Ikon Allah ganin yadda Amina ta Fashe da kuka Aminu ya Rude ya rasa ya zai yi Cikin wani yanayi yake fadin"kiyi wa Allah Amina kibar kuka ki Fadamin me yake faruwane..!
Hanne ce taga Tsayuwar bata da Amfani kada wani yazo ya gansu yasa tace"Amina ku shiga nan.Kinsan dai Halin da ake ciki ko..?
Tafada tana nuna mata lungun bayan gidansu da kai Amina ta amsa mata Kafin ta wuce tayi gaba shi kuma yabi bayanta su kuma sai suka koma Cikin Haraban gidansu Amina suka Labe Jikin Get gabansu na Fadi Fat Fat suna Tunanin anya basu yi ganganci ba..?
Amina kuwa suna shiga dan lungu ta Fashe da kuka ta Duke Aminu yabita shima ya Durkusa Kamar yayi kuka yana Fadin"in kika cigaba da wannan kuka Amina zan iya shiga wani Hali..Kiyiwa Allah ki Fadamin abunda ya Faru..!
Yadda yake mganar ne yasa Tsausayinsa ya kamata yasa ta Dago Cikin kuka ta fara Fadamai abunda ya Faru Tundaga farko sai dai ta boyemai Sakin da Aba yayi ma mamanmu akanta Ba saboda komai ba akwai Kunya ta ce an saki Mamanmu Saboda ita ta karishe Da Fadin"Soyayyarmu zata zama Tarihi ne Amin..Rabuwar mu shine Alheri Wannan abun da ya faru kadan ne akan wanda zai kara faruwa..Ni kaina nasan ba Domin baba Mallam na sona ba da yanzu wani Labari akeyi..Wlh bawacce tataba aikata abunda

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login