Showing 195001 words to 198000 words out of 265571 words

Chapter 66 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28955

ta warware suka Cigaba hirarsu Daman kukan Aminar na Tabara ne da jidalinta.

Hajiya suna waya da Amina ta wayar Amina Tunda Aisha ta Tura mata lambar Aminar koda yaushe sukayi mgana sai Amina tace ina su hanne abasu su gaisa sai Hajiya tace ba yanzu ba ko Aba bata yarda ta Kira ba sai Mallam kawai ta Turo mata Lambarsa ta Kirasa suka gaaisa ya Dinga mata nasiha da Saka albarka yaji Dadin jin tana Lafiya kalau..
Amina tana jin kewar su Hanne sosai Kamar yadda suma suke kewarta Tunda suka ga sun fara Jarabawar Fita Amina bata Dawo ba suka Sare Hanne tace da sun san ba tare da Amina zasu zana Jarabawar Fita da Mallam ya bar su sun gama SS3 Kamar kowa sai dai ina bakin alkalami ai ya Riga ya bushe.
Duk damuwarsu basu kai Sa"adatu ba wanda hakan da mallam yayi yanuna cewa bazasu Dade agida ba suma zai aurar dasu Shine tashin hankalinta su kuma su Hanne Amina ce Damuwarsu Saboda rayuwar ba Dadi ba ta abaya ashe ba Rashi sukayi ba Tunda Amina na kusa dasu yanzu kuma da basu da tabbas din ina take sai Damuwar tafi ta baya,Sun gaji da Tambayar Hajiya sun kare har Mallam sun tambaya yace su tambayi Hajiya Hamida data tambayi Aba shima yace Hajiya bata Fadamai ba.
Ganin Hamida ta Damu ne yasa Mamanmu ta Kikkira su Jaleela ta tambayesu ko wajen su Hajiya ta kawo Amina ammh har Jordan ta Kira amsar Daya ne A"a sai ta fara Dawowa Hankalinta ta fara Tunanin ina Hajiya takai Amina..?
Har su Zulaihat ta Kira suma suka ce mata bata wajensu kuma kowacce ta Kira sai ta nemi karin bayanin ina Aminar ba"a ganta bane..?
Sai Mamanmu tace wayasani Hajiya dai tace Zata kaita Gidanjenku gashi Wajen Wata Daya da wani abu ba Labari sannan Hajiyar taki Fadan inda take in sukaji basa Damuwa cewa suke ai Hajiya bazata kai Amina inda Za"a Cutar da ita kada ma mamanmu ta Damu Hajiya Zata Dawo da Amina kamar yadda ta tafi da ita.
Mamanmu ta fara Tunanin kodai da wani abu ne..?
Sai kuma ta Tuna ance Dubaran Zaman aure za"a koyamata tuna haka yasa ta watsar da mganar Amina aranta tana ma Hajiya Dariya Tana Wahalar da kanta ne saboda auran Amina da Danmallan ai haka zai kare agantale.
Da sukayi waya da Anty Amarya ma sai da ta mata batun Anty Amarya ta Saki Tsaki Tana Fadin"Nace miki ki daina mana wannan mganar mun gama da wannan shafin..Ba inda Zata kaita Daya wuce maiduguri garinsu tana da inda yafi chan ne..?
Mamanmu tayi Dariya kafin tace"Ai Tunanina bai kawo nan ba..To Allah ya raka Taki gona ya mganar Sakinan..?
Madina ina son kema naga Burinki ya Cika kamar yadda nawa Burin ya Cika .!
Anty Amarya tace"kada ki Damu Saura kadan..Cikin watan nan Danmallan zai zo ya tafi da Sakina kinga in ya tafi da ita shikenan sai naji da Hajiya uwani kuma..!
Mamanmu tace"Ai Hajiya Uwani matsiyaciyace..!
Anty Amarya tace"Babba ma kuwa sai kin ga yadda take shigema Hajiya..Kamar ta Allah..!
Abunda basu sani ba ai Daman in Dubunka Zata cika rasa Dubara kake yi Hajiya gefe ta koma tayi bakam tana karban kowa yadda yazo mata Sannan tana Daina yarda da kowa ta gama Sarewa da lamarin duniya sannan Haj.uwani bata san wani abu ba ita adole tana shigema hajiya tasan wasu sirrukan ai ta Dade da Cin Taliyar karshe tunda Hajiya ta ganota ta DAina bata labarin abunda ya Shafeta da ya"yanta..
Har Falonta tazo tana bin bakin jin ina Amina take taki Fadamata Saboda Sai Daga baya tasan ma Aminar bata bata nan shima abakin Haj Nasara taji Data Tambayi mallam yace hakane ita mamakinta Daya meyasa Hajiya ta Kauda Amina Daga gabanta..?
Ko madinar Aka Turata sai dai tana Tunanin ba Haka bane Tunda taji ana mganar Dawowar Danmallan din Cikin wannan watan..
Sai Hajiya ta bangarar da Tunanin Haj.Uwani da cewa Amina ba Nisa tayi ba Jarabawa take yi a inda take in ta gama Zata Dawo to ganin suma su Hanne sun fara sai ta yarda da mganar Hajiya aranta tace ita wannan auran ai su Amarya da Balaraba sun gama gantallar dashi.
Dayake itama ba Aminar ne agabanta ba Sai ta Watsar da mganar ta Ita yanzu babu abunda ke gabanta sai Shirye shiryen dawowar Nazeem gabadaya Cikin Sati mai Shiga yace mata Zai dawo gabadaya in ya Dawo kuma aikin da zata karisa ai kadan ne har ta Fara hango kanta ta Cika Burinta mganar Anty Amarya kuma bata gabanta tasan ko giyan wake tasha bazata fasa mganar nan har wani yaji ba..Kuma tasan Mama ta sha gaban Bokansu har Mganin Data Karbo ma Sakina sai da mama ta labartamata Dariya kawai tayi in su suna zaune ita ai ta Dade da kwana atsaye kan Cikar Burinta ko kofa bata taba badawa ba ballatana a samu matsala..!
Ashe ashe bata sani ba shi Allah ba"a masa Dubara sannan a lokacin Daka ke Tunanin ka Rufe kofar gefenka ta kofar da bakayi Tunani ba sai Allah ya Wangale taa asirinka ya gama Tonuwa a idon Jama"a.

*******

Kamar yadda Aisha tayi ma Hajiya alkwarin ta kuma ta gayama Amina bata? sauya Shawara ba Haka take tasa keyar Amina Kitchen in suna Girki da Saude ta rika gani tana koya mata Saukakkun girke girke,Tun Amina na Tura baki tana kunkunin tana barcinta ya Aisha na takura mata har tazo ta saki ta Fara maida hankali To Saboda ko ta koma Daki Yakaka ke Fatattako ta dole ta Dage tana maida Hankali ballema ya Aisha data koyi Fada tunda tayi aure.
Haka Zata Zaunar da Amina tana koyamata yar shagwaban nan da yadda zata rika ma ya Danmallam mgana da karaiyaya Amina sai ta Dinga Dariya aranta tana Fadin a ina ya Aisha ta san wasu abubuwan agidan kamar in ka samata Hannu abaki bazata Cija ba Kamar ya Aishan tasan abunda take Tunani ta Dunkure mata kai tana fadin"Ban son iskanci ana koya miki yadda zaki zama Tauraruwa wajen ya Danmallan kina Iskanci ko..?
Nasan kina mamakin ina duk nasan wadanan abubuwan ko..?
To ai gidan aure makaranta ne Amina sannan tunda ya siyamin babbar waya nake dan shige shige ina koyan wasu abubuwa sannan Addini ma ai ya koyamana yadda zamu yi mu"amala da kowa har da gidan auranmu..!
Amina ta jinjina kai Domin tana ganin? yadda ya Aisha ke yi in ya Usman yana gari kwalliya da salon mgana da kwarkwasa duk tana gani kuma tana Dauka Domin a Zahirin gaskiya itama tana so ta zama mace sannan tunda ga inda kaddara ta kaita ai sai ta Dage Uwa uba kuma taci Uban Sakina ta nuna mata nasu ba irin nata bane Sannan bazatace ta fara son ya Danmallam ba ammh sun fara Shakuwa da juna tunda koyaushe suna Tare a waya kullum Cikin Tambayar baki da wani Damuwa ko.?
Yau da gobe bata bar komai ba sannan ita ai Zuciya tana son mai kyautata mata Amina tana da Budaddiyar zuciya ne shiyasa nan da nan mutum ke Shiga ranta abunda bata sani ba shi ya Danmallam ai jinin jikinta ne shi da take Dauke da Kwansa acikin jikinta,Sannan kuma ba kamar Soyayyarsu da Aminu bane,da ba Sakewa Cikin Tsoro da Fargaba tayi ta wannan kuwa a sake take sannan in suna waya sai tarika jin wannan fa ai mijinta ne wani abu ke shiga ranta batare data sani ba.
Sannan abunda ya Faru Tsakaninsu ya Haifar da wani bond mai karfi wanda Bawa bai isa ya hasaso farkonsa ba ballatana karshensa ba abu Daya ta saani tana jinsa aranta sannan tana Kishi da Sakina daman chan tana jin haushinta balle yanzu da suka Hada miji ko sunanta taji sai ranta ya baci bata ma Damu da balarabiyar nan yadda ta Damu da Sakina ba.
Ko kwana Daya yayi bai kirata ba ta Dinga fushi kenan tana Tura baki in ya Kira taki Dauka Sai Yakaka ta mata Fada da cewa"Tsiya na Dake Sarkaci Takwara..Haka ake karban miji a Hannun kishiya..?
Amina na hura Hanci tace"To bashi bane Jiya fa bai kirani ba..!
Yakaka ta aika mata da Dakuwa tana Fadin"Kin ga naki nan..?
Don bai Kiraki ba sai me..?
Ai kinsan yana da uzuri ko..?
Kada ki Dauka sai ki barma ita balarabiyar ki koma baya ke ko yan Dubaran nan na yaran Zamani da suka iya su Tadama Mazajensu hankalinsu in suna nesa saboda su zo wajensu da wuri baki iya ba,Sai Sakarci da Kunkuni kadai kika iya..!
In yakaka ta fara fadanta bar mata Dakin Amina ke yi abunta ranar kuwa sai taja mai aji Zata Daga kiransa in kuma ta Dauka yana mgana ta basar dashi yasan Laifinsa sai yayi mirmishi yace"Amina kiyi hakuri..!
Sai ya fara fadamata Uzirinsa sannan Zata Hakuri koda yaushe Cikin Tambayanta lafiyanta yake yi tana Bashi amsa ba wata matsala bawani Hira suke ba na ma"aurata ba sai dai suna Hirar abunda ya shafi mganar da Amina ta Fadamai koda yaushe sai tace mai yaushe zai taho Ranar dai yace mata"Cikin karshen watanan..Sannan yana so yazo da Sarood su yi Sati Biyu sai su koma Tare da Sakina..!
Ai Har suka gama wayar Amina bata kara Dariya ba wani Tukikin Takaici take ji wato zai zo da wannan balarabiyar sannan ya koma da Sakina ita ko Oho..?
Sai kuka da Ya Aisha tazo ta ganta Tana kuka Har Hankalinta ya tashi ta Zata ko jikin ta ne take jin wani abu..?
Sai Amina na kukan ba Hawaye tsabar Takaici tace"ba ba..ya Danmallan bane yace wai zai zo da balarabiyar matarsa ba..Sannan in sun tashi tafiya su koma da wannan gajerar matar tasa..!
Galala Aisha ta Saki baki tana kallon mgana kafin ta Tsintsire da Dariya Amina ganin haka yasa ta kara bare Baki ya Aisha ta buge bakin tana Fadin"Kefa ko ya'ya Dubu Zaki haifa na tabbata wannan iskancin naki bazai barki ba..Miye na bare min baki kmar na yankaki Salon yakaka Dake Daki Taji tace nayi miki wani abu..!
Amina ta hura Hanci kafin tace"To bake bace ina gayamiki mgana kina min Dariya ba .!
Ya Aisha ta matso ta kama Hannunta tana Fadin"to na bari kanwata gayamin yaki keso ayi..?
Amina tace"To ni kada ya tafi da Sakinar nan gaskiya..ni fa kadai zai bari anan kuma sai ya Dade kafin ya Dawo. !
Ya Aisha tace"Yanzu waya isa ya hansa tafiya da matarsa Amina..? Ai bamu isa ba matarsace kuma kinga Daman achan take sannan duk keki keda matsala ina nan ina Koya miki irin? kissar da zai saka Miji yazo gareka bai sani ba kin ki Dauka nace miki watarana ki sakamai kuka kice cikin ana Miki motsi ke zaki mutu ki Tadamai hankali yayi lallashi ki kinyi Shuru Da gudu zai taho ma Lokacin Tafiyarsa bai yi ba ammh sai ki kalleni kina Dariya..,!
Amina tace"To ai kunya nake ji..Kuma kuma..!
Ya Aisha tace"Kuma me..?
Amina tace"to ai naga shi babba ne. !
Dariya ya Aisha tayi kafin tace"to ai ke kin ji Dadi ma baki san sirrin auran irin su ya Danmallan ba..?
Gaki da kuruciyarki Amina da Shagwaba da Yarintarki zaki sacemai Zuciya shi kuma ya lalace akanki Wlh irin ku an fi sonku kiyi ta Jidalinki yana lallabaki shiyasa na Fada miki shima wannan Jidalin naki aikwai Inda ZAI miki amfani balle nasan shima ya Danmallam din ai yana son soyayya..!
Amina tayi Dariya "To kuwa matarsa bata iya ba..bandai sani ba ko wannan Sarood din..!
Ya Aisha tace"Ke ya akayi kikasan bata iya ba..?
Amina tace'Tab ai na Zauna da su..!
Aisha tace"ai bata iya komai ba sai Fadin rai ita kuma wannan Sarood din naga kamar ta Biye mata sun maida ta wata wawiya ma..!
Amina tace"ai kamar ma wa??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????wiyar ce..!
Dunkure mata kai ya Aisha tayi tana Dariya tana Fadin"Tunda ke kin iya sai ki Dage ki rikitamana yayanmu.!
Amina taji kunya ta kasa mgana.
Tundaga ranar ta Bude kunne tana kwasan Abubuwa awajen ya Aisha Da gaske take yi duk sai ta nuna ma su Sakina basu iya komai ba Aminene ai Ta musu Zarra.
Bangaran karatu kam sai da ya Aisha tasha mamakin Amina ba inda baza"a bude mata a Qur"ani ta karanta ba Hadisi kuwa tunda ga na farko har na bakwai suna kanta sannan ta haddace Arba"una Hadith sira ma haka Tajwid wasu Littafan Ya Aisha mamakin Amina ya isheta sai da ta Furta mata tace"Yanzu daman Amina kin iya wannan duk abubuwan kike iskanci a makarantar islamiya da Haddda..?
Amina Dariya kawai tayi tana Fadin"ai ya Aisha ba kowani Hali muke sani na mutanen da muke Tare dasu ba..Muna sanin wanda suka bayyana mana ne..!
Ya Aisha ta jinjina kai tace ba Shakka ko bangaran Boko sai da ta Kusa raina kanta sun yi kunsan mintinaa Talatin suna hira da Usman Cikin Harshen Turanci Amina bata kage ba sannan ba Turancin yan koyo ba Turancin ya Zauna abakinta sosai har Usman sai da yayi mamaki yace mata"Amina fa tana da kwakwalwa..In ta samu cigaba da makaranta sosai zata Zama wani abu watarana. !
Ya Aisha ta jinjina kai tana Fadin"Agida ko sai kace bata gane komai..Bama Damuwa tayi da karatun bafa..!
Dariya yayi yace"ai irin su sun fi raina ma mutane hankali da basa ganewa nan kuwa sun fi kowa Dauke komai Lokaci Daya..Muma lokacin muna Secodary sch muna da wani Dan ajin mu haka mai suna yahaya kamar wawa fa ana karatu yana wasa wlh a Exam shine Overoll..!
Ya Aisha tace"irin Aminace..A aji Dakikiya a Result sai kaga ta Doke kowa ko su hanne Dake maida hankali Tana gabansu..!
Usman yace"Da yawam irin masu baiwar nan basa samun masu Courage dinsu ne in ana kushe su ana cewa basa yi sai su boye baiwarsu sun fi bayyanasa wajen wanda ya yarda suna da ita kanta baiwar..!
Ya Aisha ta jinjina kai domin tagamsu da hakan yanzu sannan baba mallam koda yaushe Cikin Fada yake Uwata yar baiwace nan gaba sai mun baku mamaki aiko gashi ta bata yau wlh Bata Taba jin Amina tayi Turanci ba Duk azatonta batajin komai sai Tsinta tsinta.
Daman haka Lamarin Allah yake Tsammanin Abunda baka Tsammani ba..!

*******

Bayan kwana Shida..!

Nazeem ya Diro gumel Ranar wata Laraba da yammah tun Safe Haj.Uwani ta kasa zama ayi chan ayi nan tasa su Baba lami sun shiryamai kayattacen abincin daya fi so Priderice da soyayyan kaza an yi pepe dinta da kunin aya,Tasa su Akilu sun Share masa Dakinsa an gyara an goge an Baza Turaran wuta Duk ta kasa Zaune sai da ya Shigo gidan Abunda yafara bata mata rai duk yadda Taci Burin Dawowarsa sai da ya Fara Shiga Shashen Hajiya suka gaisa ya Dade ma suna Hira sannan ya kariso wajenta ammh Dayake yar Duniya ce sai bata nuna mai ba ta karbesa Cikin maraba da lalenta kamar ko yaushe.
Ya Duka yana gaisheta ta amsa Cikin Sakewa tana Fadin"An gama karatu gabadaya Nazeem an dawo gida..?
Daman ance kowa ya bar gida..Gida ya barsa..!
Yana Dariya kansa a kasa yace"Hakane Mommy..Mun dawo sai Fatan mu samu aiki atayamu da addu"a..!
Tana Dariya cin nasara tace"ai kama samu aiki ka gama Nazeem..kai fai tashi ka karisa Dakinka kayi wanka ga abincinka nan tafe. !
Ya mike yana mata godiya har ya fara Tafiya tana Binsa da kallon alfahari ganin ya kara girma sam bai yi kama da ita ba yafi kama da Mallam ne kuma suna bala"in kama da Danmallan.
Juyowa yayi yana Fadin"Mommy ina Umai..?
Ya jikinta..?haj.uwani tace"Taji Sauki har ta koma ma islamiya da Hadda.
Kai ya jinjina ya fice yana fadin Allah ya bata lafiya..
Yana fita itama ta fita Kitchen din Tsakar gida tace su kaimai abincinsa da komai da komai tana Tsaye sai da Taga an Dauka an kai ta koma Shashenta ta Kira Batula ta Fadamata Dawowar Nazeem.
Batula tace"Dakyau..To gobe zan yi Sammakon zuwa Minna in samu mama na mata bayani yadda ake Ciki Zaki ji..!
Haj Uwani tace"Nagode batula..Kada kiyi sanya..Kinsan wani Lokacin jinkiri ma yana batamana aiki. !
Da sauri Batula tace"Haba a baya ma ban yi sanya ba..Ballatana da yanzu da muke gabda Cikar Burinmu..?
Kedai sai kin jini..
Daga haka suka sauke wayar Haj.Uwani Bakinta har kunne sauran matan ma su Anty Amarya sai Da Daddare suka san Nazeem ya Dawo da suka gansa Falon Mallan har suka gaisa
Mallam yaji Dadin Dawowarsa Saboda Nazeem akwai natsuwa ga Hnkali yana ta mai fatan alheri da fatan samun aiki mai kyau.
Ranar Hajiya Uwani bata Samu kebewa da Danta ba washegari ma Tare da yan"uwansa Nasir da Jafar suka shigo mata ranta ya sosu sai bata nuna ba ta barsa sai da ya kwana Biyu da ya shigo gaisheta da Safe tana Dakinta taji suna gaisawa da Umaima da Jikin nata yayi sauki yanzu har tana Fitowa falo ta Zauna.
Daman jiransa take yi yana shigowa bayan sun gaisa ta sako mai mganar Dake ranta Cikin Dakiyarta tace"Tunda ka Dawo gida..sai ka fara bin Baban ku sa"idu gidan gona kana Duba wasu abubuwan tunda kaima Harkan kasuwancin nan ka karanta..Wani abun gwara ku masu Dukiyar kuna kusa zaku fi ku kula dasahi Dakyau akan bare..!

Ya Dade yana mamakin kalamanta kafin yace"Mommy ai baba Sa"idu kuwa ba bare bane kema kinsani..Kada ma ki Fada baba yajiki bazaki ji Dadi ba sannan shekaru aruru yana kula da kasuwancin Baba ko Da rana Daya bamu taba jin kansu ba..Sannan infact ma ni bana Sha"awar aiki a karkashin Mahaifina gwara na samu aiki na tara gumina..Na ma yi interview da wani kamfanin Sarrafa fata dake Lagos sun ce xasu neme ni Albashi 100k sukace zasu rika Biyana Duk wata..!
Kafin ya gama mgana ya sha Harara nan ta Rufesa da Fada tana Fadin"Inda Uzairu ya fika kenan shi Burinsa ya gama karatu yazo ya taimaka ma mahaifinku kai kuma Shashaha kana wani mganar kamfani Dubu Darin banza..?
Kasan iya adadin Dukiyar mallam ne..?
To ahir dinka..ba inda zaka yi aiki sai karkashin mallam kuna chan sake da Baki wasu dagachan nesa suna amfana da abunda yake watarana mallakin ku ne.
Gargadi na shine in mallam yamaka mgana ka amsa mai wlh ka kunyatani sai na sabamaka..!
Har ya fice yana mamakin me yasamu mommy ne take irin wannan mganganu ?
Washegari Batula ta kirata tace Mama tace yau da Daddare ta tunkari mallam da mganar bazai mata gaddama ba.
Cikin jin Dadi da Nasarar ta Ta tunkari mallam adaran Daman ita keda Turaka yana cin abinci ta lamkwashe kafa agabansa tana

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login