Showing 216001 words to 219000 words out of 265571 words

Chapter 73 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28927

sani shiyasa bata yarda da kowa ba yanzu Daga ita sai mallam suke sirrinsu ko matan sun Lura da hakan sai dai daman ba wanda yasan Tsakanin Hajiya da mallam tare aka gansu irin su Hajiya Uwani da Anty Amarya sai Bakinciki Daga nesa..!
Hajiya ta zama kadagaren bakin Tulu basu da yadda suka iya da ita. !








*Janafty*

*TFZB2023*

*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*

*Gumel..*

Yau ta kama laraba ne da wuri suka dawo daga islamiya saboda anyi rasuwa ne Baban wata yar ajinsu Samira yahaya ne ya rasu sai aka zabesu su goma sha biyar maza biyar mata goma sukaje gidansu samira gaisuwa,bayan sun dawo mallam Ahmad yace kowa ya wuce gida sai Ranar asabar.
Dayake sun cigaba da zuwa islamiya da Haddarsu kamar yadda suka saba suna dawowa ba su wuce gidan Baba mallam ba sai suka yada Zangonsu gidansu Baba Sa"idu Sa"adatu daman bata je islamiyar ba wai batajin Dadin haka sukaji Sabeeha na fadama kawarta mariyan ajinsu.
Mamanmu na cikin Daki ta baje a Tsakar falonta ta baje wasu Sabbin kaya sababbin Dinkunanta ne da tayi Domin da gaske take yi sai ta shiga ta Fita ta kece raini a wannan Bikin.
Tana cikin Duba Dinkunan taji Sallamarasu kafin ta kauda kayan sun Daga Labule sun shigo Da fara"arta ta Tabersu tana fadin"A"a Amare ne da kansu Ashe daga ina haka..?
hanne gefen Mamanmu ta Zauna yayinda da Hamida ta zauna kan hannun Kujera tana Fadin"Daga makaranta .!
Mamanmu tace"To naga kun tashi da wuri Lafiya..?
Hanne tace"Rasuwa akayi mukaje gaisuwa daganan mallam Ahmad yace kowa ya tafi gida sau ranar asabar..!
Mamanmu tace"Oh..Allah ya jikan musulmi..!
Suka amsa da Ameen kayan take Dagawa Bakinta Har kunne tana Fadin"Kayan da zan ci fitar Bikin ku ne fa..Kun gansu nan ba"a Dade da aikomin dasu daga wajen Dinkin ba..
Less din take Dagawa har Hanne ta amsa tana fadin yayi kyau Hamida kuma kayan take kallo da mamaki ita dai bata saba gani ba ko ana Biki mallam ke ma kowa kaya daga manya har su yara sannan kwananan mamanmu Facaka kawai take da kudi yawancin Suturunta duk ta sauya su Taoffinta kuma ta aika dashi Gusai Tana ta sota mata mgana kuma ta kasa bata san ta ina zata fara ba Sannan ko Jiya taje kasuwa ta nuna mata Dinbin kayan data siya mata na Kitchen da sunan ita ta siya mata alhalin Hajiya ke siyan komai bama haka ina Mamanmu ta samu uban kudi haka datake ta kashewa..?
Abunda bata sani ba Aba yake bata ko Da bai yi niyya ba da tace ya bata bazai iya mata gaddama ba ko nawa tace ya bata haka zai dauka ya bata.
Hanne ce kadai ta Daga kayan ta gani ta yaba Hamida kuma daga inda take tace sun yi kyau basu wani jima ba suka tashi suka koma Dakin su Hamidar Hanne kan gadon Amina ta kwanta daman ko gidan ta kwana nan take kwanciyarta Hamida kuma tana Tsaye tana ninke Hijabin jikinta Data Cire ta ga Hanne tayi tagumi tana Tunani.
Sai da ta maida Hijabinta Cikin Dirowarta sannan ta isa kusa da Hanne ta Dafata da Sauri Hanne ta Dago tana kallonta cikin wani yanayi Hamida ta sauke Nunfashi kafin tace"Haba hanne wai wannan mganar har yanzu bata daina damunki ba .!?
Hanne sai kwalkwal kamar zatayi kuka Cikin wani yanayi tace"Hamida ya Zanyi..?
Da wani ido zan kalli Amina in ta Dawo taji yadda abubuwa suka koma..!
Hamida tace"Na fada miki ki daina Sako mganar Amina a wannan mganar..Amina fa yanzu ba kamar da bane..Matar aure ce kinga kuwa Igiyar aure ai ya kore komai Hanne..Ayadda nasan Amina Zata fi son kwanciyar hankalinki fiye da nata Hanne ni shaida ce irin kaunar dake Tsakaninmu..!
Hanne ta Saka tafukan hannayenta ta rufe fuskarta na wani Lokaci Hamida ta rike hannayen nata tana fadin"Dom Allah ki daina damuwa..Matar mutun fa kabarinsa Wani ai baya auran matar wani..haka ita ma matar wani bata auran mijin wata..Ga misali da Amina waya taba Zaton zata auri ya Danmaallam..?
Ammah dayake matar sa ce tun daga Launil Mahafuz ba gashi ya faru ba..Ki kwantar da Hankalin ki hanne Hajiya da mallam bazasu taba Zaba mana Abunda zai cutu garemu ba..!
Hanne ta cire hannayenta a kan Fuskarta lokaci Daya tana kakalo Mirmishi Hamida ta saka hannu ta Share mata hawayen tana Fadin"Bana son na ganki cikin Damuwa duk nima sai naji na shiga damuwa..!
Hanne tayi yar dariya kafin tace"Nagode Hamida..Na rasa Amina ammh baki barni nayi kewarta sosai ba..!
Hamida tace"dukanmu muka rasata Hanne..Kuma junanmu ne bamu bari kewarta ta mana illah ba..Sai dai Amina wata aba ce awajen mu da mantawa da ita abu ne mai Wahala..!
Hanne tace"Ni damuwata har da yarda za"ayi auran mu hamida ba Amina..!
Hamida tayi shuru kafin tace"Nima abun na raina..ko xamu je mu roki Hajiya ne don Allah Amina tazo mana Walima ko bayan Bikin namu ai sai ta koma inda basu san mu sani din..!
Hanne tace"Kin kawo shawara mu yi sallar mangariba sai mu shiga. !
Haka kuwa akayi suna Idar da Sallah suka ma mamanmu sallama wacce ta idar da sallah ta amsa musu da sai da Safe saboda tasan har Hamida ba lalle ta Dawo ba Jawad ma ya shigo ya Cire Kayan makaranta ya saka na gida ya fitaa masallaci domin wannan tarbiyan ta salla Cikin jam"i ko yaro karami ne yasan da ita agidan mallam yunusa Bazanga.
Sanda suka shiga shashen Hajiya sun sameta tana addu"a ne bayan ta idar da sallah sai da suka jira ta shafa Daman tun da ta ga shigowarsu sun wani uban buga Layi agabanta aranta ya bata mganar Amina ne domin shi kadai ke sakasu kaga sun zama kalar Tsausayi..
Tana rike da Cashabanta ta kallesu tana Fadin"Lafiya na ganku haka..?
Ko duk Tunanin barin gidan ne ya"yan Hajiya..!
Kansu na kasa suka gaisheta ta amasa Cikin Fara'arta tana fadin"Amaran namu duk sun rame sai dan wuya..!
Mirmishi kadai sukayi kansu na kasa kafin tace"Nasan da mgana a bakin ku ko..?
Hanne ta Dago tana fadin"Hajiya mganar Amina ce..haka za"ayi Bikin mu Amina bata zo ba Hajiya..!
Hajiya sai da tayi dariya Har Hakoranta suka bayyana Cikin Girgirza kai tace"Daman ai nasan Tatsuniyar gizo ai bata wuce ta Koki..Daman ai labarin kenan Amina..Amina ita ma tana chan duk mganarta da Zencenta Hanne da Hamida..Wannan kaunar junan naku Allah ya barta har ya"yan ku da jikokin ku su hadu a aljannah Firdausi..!
Suna Mirmishi suka amsa mata da Ameen kai ta gyada tana Fadin"Amina ce dai damuwar ko..?
Atare suka Daga mata kai Tana jan Casbahanta tace"To ku sha kuriminka..Amina na nan tafe da yardan Allah da ita za"ayi sha"anin auran ku..!
Ido suka zaro a tare suka ce"Da gaske kike yi hajiya..!
Cikin Yar dariya tace"Insha Allahu..Itama tana chan tana shiri..Bikin Hanne da Hamida bazai wuceta ba insha Allahu..!
Saboda murna sai da Hamida da Hanne suka rumgume juna kafin su saki juna suna ma Hajiya godiya ta amsa musu cikin sakin fuskar tana ce musu sai su sudaina ramewa Amina Zata Dawo haka suka fice suna Murna ammh bayan Hajiya ta gargade su kada su fadama kowa sukace ba wanda zasu fadamawa.
Ita kanta Hajiya bata isa ta hana Amina zuwa Gumel ba wannan karon Duk taso sai Amina ta Haihu ta Dawo da ita ammh Mallam ya nuna mata kada su kwari Amina da yawa bata da Zence sai na Hanne da Hamida in har sukayi aure bata zo ba abun zai mata Ciwo suma haka sannan Mijinta ma yabada goyon bayan su taho tare da Aisha shiyasa ta amince bayan tayi wani Tunani sai taga haka din shine Daidai.
Hanne da Hamida jin Labarin zuwan Amina wajen Hajiya Bakin da bazai musu karya ba yasa suka saki jikinsu Damuwasu ta ragu,Shiryen shiryen Biki kuma babu abunda aka fasa su dai basa wani shiru tunda basu da kawaye daman Amina ta fisu gayyar kawaye sai Sa"adatu su bama su fadin zasu yi aure da Bakinsu koma tambayansu akayi shuru suke yi abunsu.saboda lamarin yazo musu ne alokacin da basu taba zato ba ballatana Tsammani ba..
Daman ai haka rayuwa ta gada..Sau Tari abubuwa da dama suna Faruwa damu ne bamu tsammaci Faruwarsu ba..Haka lamarin Ubangiji yake.

******

*ABUJA..*

Ya Aisha na cikin bedroom dinta tana gyara kayanta da aka karbo wajen mai wanki da guga nata dana Amina sai na yakaka tun jiya aka kawo bata samu Zama ta saka nata cikin Wardrope ba tana ta shirin tafiyarsu Gumel ita da Amina gashi Hajiya tace tare da kayan Lefen Amina da kuma kayan Haihuwarta zasu taho sannan itama Daga barayinta akwai abubuwan data siya mata sannan Darling ma ya bata kudi yace ta siya ma Aminar wani abu tunda in ta tafi ba Lalle bane ta Sake dawowa ba..jiya ma kasuwa taje bata samun zama Sosai shiyasa.
Tana Tsaye ne tana Shirya kayan nata acikin Wadrope din Amina tayi sallama ta shigo Dakin ta juyowa tana kallonta Lokaci Daya tana amsa mata sallamarta.
Kallon Amina take yi tana dan Mirmishi tana kara jinjina ma Ubangiji Amina da Ciki Haihuwa ko yau ko gobe domin cikinta ya shiga watan Haihuwansa ko scan dinta na Biya ya nuna EDD Dinta karshen watab nan ne sannan ai Tsarinsa befare ne ko after.
Ta kara Kumbura kafafunta da fuskarta sun kumbura sai da tana da Tsawo shi ya taimaketa ammh Cikin yayi girma sosai sannan sai yayi kasa soaai alamun ya kusa fitowa duniya.
Har ta kariso Aisha na kallonta ta samu gefen gado ta zauna Dakyar Aisha ma mata sannu Sanye take da doguwar riga baka cikin Tsaraban ya Danmallam ne ta madina Daya aikomata daahi Amina na son Rigar bata san Dalili ba.
Sai da ta zauna ta gama hakinta ya Aisha na mata sannu sannan tace"Ya Aisha yaushe zamu je gyaran kai ne..?
Ya Aisha ta na yar dariya tace"Oh yau watarana Aminene na tambayan yaushe za"a je gyaran kai..?
An girma an zama manyan mata an Daina kazanta raahin wanka da yin wata uku da kitso ba gyara kenan..!
Amina tayi dariya da Idanuwanta da suka Shige Ciki tace"Ko abaya ma ba Laifina bane har da Sakaci da kuma rashin kula ya Aisha..!
Cikin dan mamaki tace"Bangane ha..?
Amina tayi wani mirmishi takaici kafin tace"Bazaki gane ba..Ammh ki yarda da mganata ai hamida da Hanne tare muka taso ai ba haka suke ba ko..!?
Ko haka suke..?
Ya Aisha ta girgiza kai tana Fadin"Sukan tun abaya suna da kokarin gyara kam..!
Amina tace"ki barsa a yadda na Fadamiki..!
Ita dai ya Aisha bata damu da mganar Amina ba yasa tace"Kada ki damu ki bari sai gobe in muka dawo daga asibiti sai mu biya mu yi gyaran kan ko..?
Ni kitso zan yi kefa..?.ko kuma ki bari in kin yin Haihu Lafiya sai kiyi na suna..!
Amina ta kauda kai tana Fadin"Sai na tambayi ya Danmallam in yace yana son Kitso sai nayi..!
Ya Aisha ta rike Baki tana Dariya kafin tace"Ina yakaka tazo taji..Eyye masu miji manya..!
Amina tayi mirmishi batace komai ba ya Aisha tace"To har yanzu bai tashi Daga ya Danmallam din bane..?
Amina ta hura hancinta Daya kara Girma kafin tace"To ai nima bai sauyamin suna ba da Aminata yake kirana..!

Ya Aisha tace"To ai ke zaki sashi ya Sauya miki ina ruwanki da sai kin jirasa..Shi da yake da mata Biyu kowacce da sunan data ke kiransa kema sai ki samu naki tunda dai shi balarabe ne ki rika cemai HAbibi..!
Amina ta kalleta a karkace kafin tace"Allah ya tsareni..Habibi fa..Sunan da wannan gajerar matar tasa fa take kiran sa dashi kenan..!
Sai nima na Dauka..!.?
Ai na tasani kwaikwayo sai ta Rainani ma ya Aisha in taji ina kiransa da haka..!
Ya Aisha na Dariya tace"Oh ai bansani bane da gaskiyanki tobari mu sami wani suna ki rika kiransa da Norul kalbi mana..!
Amina ta yamutsa fuska kafin tace"Bai yi ba chanza wani..!
Ya Aisha tace"To Hubby..!
Amina tayi shuru kafin tace"Hubby..?
To har gwara ma wanman..!
Ya Aisha tayi dariya kafin tace"Yayanmu ya shiga uku..ya fada komar Aminenen hajiya da mallam..!
Amina na Dariya tace"Ko zaku Cirosa ne..?
Ya Aisha tace"Ina fa ai muna jin Dadi..Acigaba da kula mana dashi Allah ya kara kauna da soyayyah..!
Amina tace"Shi yace miki yana sona..?
Ya Aisha tace"Basai ya fada..Kowa ya ganki ai yasan kun fadama juna..!
Amina ta Hura hanci kafin tace"Ku ke gani ba..Ammh ai matansa yafi so akaina..!
Ya Aisha Dariya kadai take ma Amina Cikin zolayarta take kara gayamata Wasu sirrukan zama da miji,Amina ta Bude kunne tana Saurara bata da kalmar da zata gode ma Ya Aisha da yakaka zaman ta dasu alheri ga Rayuwarta har Abada bazata manta da gudumuwarsu ba.
Ta Dade a Dakin ya Aisha Sai azahar ta fito ta koma Dakinsu ita da Yakaka tana Shigowa yakaka na goge goranta ta kalleta tana Fadin"Ki rika dan yawatawa Takwarata sai kafafuwan naki su saki sannan ita mai juna Biyu ba"a son ta rika kumewa waje Daya .!
Amina tace"To yakaka ai baki rakani ba yau..!
Yakaka ta mike tana fadin"To Dauko mayafinki mu taka zuwa Haraban gidan..Ai bana ki takama Takwarata ba..!
Duk da dai kishiyatace ke domin kinsan dani komawa madina ba tashi..!
Amina na Dariya tace"Sai kun dawo..Ai ina nan zaki dawo ki sameni in wadanan guzumayen matan nasa suka koroki..!
Yakaka tace"Su har sun isa..?
Ai mu in muka shiga mun shiga kenan Asiri ko tsafi bai isa ya Girgizamu ba..Allah muka rike shiyasa gamu nan a Tsaye ga Kafafunmu..Kainuwa dashen Allah..!
Amina sai dariya take yi ta saka mayafinta tana fadin"Kwarai yakaka mu ikon Allah ne da na mutum ne da Tuni sun Shafe babinmu..!
Yakaka tace"Af keda kika san komai..!
Da haka suka fito daga Dakin Yakaka ce ta leka ta fadama Aisha sun fita takawa ita da Amina ta musu fatan Dawowa lafiya haka suke yi tunda Cikin Aminar ya tsufa.
Yakaka kitchen ta shiga suka gaisa da Saude ta Daukan musu ruwa suka fice Tunda in Amina najin tafiyar har karshen Layi Yakaka take janta iyaka in sun gaji su zauna Amina ta sha ruwa ta huta.
Sai da suka kai karshen Layin Maitama sannan suka juyo suka Dawo suna tafe a hankali suna Hira sama sama har suka dawo kuma Amina hakan ba karamin taimaka mata yake yi ba sai da suka dawo sukayi sallah Sannan suka zauna suka ci abinci Amina tuwo taci miyar kuka wacce Tun jiya Saude ta mata shi.bayan tashi ta koshi sai kuma ta kwanta ta Huta Daganan sai barci karar wayarta me ya Tada ita Daga barcin daman bata wani barci mai Nisa Tunda Cikinta ya tsufa..yakaka Dake Dakin ta miko mata wayar tana Daga kwancen tace"Gashi nan tun dazu ake ta kira..Ina jin mijinki ne to ban da ma shi ba wazai kira..?
Amina ta amshi wayar yakaka sai ta fita kamar yadda ta Saba ta bata wuri.
Sai da ya kara kira ta Dauka Cikin Shakewar murya suka gaisa jin yanayininta yasa yace"Meke faruwa ne..?
Kai Tsaye tace"Me ka gani..?
Dagachan bangaran yace"nayi ta kira baki Dauka ba..Sannan yanzu kuma kin Dauka naji muryanki ta Chuse fata dai ba jikin bane..?
Amina ta muskuta ta mike Zaune tana Fadin"Lafiya lau na dan kwanta ne shiyasa ban ji kiran wayar ba..!
Kai ya gyada kafin yace wani abu kawai yaji tace"HUBBY..!
Tsayawa yayi yana Tunanin ko dai bada shi take ba sai da yaji ta kara maimaitawa"Hubby..nayi kewarka sosai yaushe zaka taho..?
Danmallan Dake Cikin Office dinsa bai san sanda yayi baya da kansa kan kujeran Dayake zaune har da sabule Hula yana Shafa gashin kansa..
Cikin wani yanayin Farincikin Dayake Ciki yace"Yau nine Hubby Amina..?
Yaushe na tashi Daga ya danmallam din..?
Bakinta ta Tura kafin tace"To ko baka son sunan ne..?
Da sauri yace"Wa ne ni..?
Sosai sunan yayimin dadi..Sannan nima ai ina kewarki sosai..Zan dawo Cikin Satin Bikin insha Allahu kada ki Damu nima ina son nazo na ganki ke da Abunda ke Cikinki..!
Amina ta murmusa kafin tace"Ammh ai nima baka sauyamin suna ba..!
Dariya ta basa yasa ya Murmusa yana Fadin"Waya fada miki..?
Amina tace"Ai ban taba ji bane..Da fa Amina kake kirana..!
Kai Tsaye yace"Uhm kece dai baki Taba jiba..Ni nasan sunan da na saka miki Acikin raina sannan dashi nayi Saving din lambarki a wayata. !
Amina tace"Don allah ka fadamin..!
Make kafada yayi kamar tana gabansa yace"Naki bazan fada ba. !
Amina ta fara Shagwaba tana Fadin"Don allah fa nace..!
Kuma ai ni na fadamaka sunan da na saka maka..!
Jin zata faramai kukanta na Fama yasa ya Dakatar da ita yana Fadin"Tsaya Tsaya.kafin ki faramin wannan kukan naki da bayajin Lallashi..Ai ke NOOR ce..Haske ce ke Amina acikin Rayuwata Tun da kika shigo Rayuwata nake ganin haske kan komai nawa sannan nake ganin Daraja kima da martabawa wajen Iyayena sannan suke kara sakamin albarka da godiya gareni..Daga nan na Fahimci ke haske ne ga Rayuwata..!
Amina sai ta fara Hura Hanci tana jin Dadi sai wani Blushing take yi Cikin Fara"a tace"Da gaske ni Haske ne awajenka..?
Yana shafa kirjinsa yace"Ki bari nazo ,zan kara tabbatar miki Noor..!
Amina ta washe baki ta kasa mgana Dadi take ji akan ranta Cikin wani yanayi yace"Ya Bby na..?
Yau yayi motsi kuwa..?
Amina tace"Dazu muna dan takawa ni da yakaka sai naushi na ake yi aciki..!
Tafada Cikin yar shagwaba har da Jan hanci Danmallam yayi dariya Amina na jinsa sai ta sakamai kuka tana Fadin"Dole kamin Dariya tunda kamin Ciki ka tafi ka barni da wahala kana chan kai da matanka kana jin Dadin ka shine har kana min Dariya..!
Ya rude Hankalinsa ya tashi ya fara Lallashinta yana fadin"Wani jin Dadi baki kusa dani..?kinsan Allah ni fa kina Haihuwa zan taho Dake nan bazan jura zama baki kusa dani ke da abunda zaki haifa ba. na riga na samar Miki Shaidar zama a kusa dani..!
Amina jin haka yasa tace"Da gaake..?
Yace"Sosai ni dai kimin alfarman ko Hajiya tace bata yarda ba kice ke Zaki bi mijinki abunki..!
Amina ta fara Dariya tana Fadin"Wlh ba ruwana..!.
Wai shi zai mata wayau yana Fadin"Au baki son ki koma garin da Monzon Allah sallahu alaihi wasallam ya Zauna..?
Baki son zuwa makka ne kiyi Hajji..!
Amina tace"Ina so naje..In na ganni a gaban ka"aba Hubby kasan me zan fara roka..?
Yace"A"a Noor..!
Amina tacigaba da Fadin"Zan duka in Dafa ka"aba in rokar ma yaya Afuwa da salama sannan na roki Allah ya Hadamu a darussalam..!
Kai Tsaye yace"Allah ya Amsa ina jinki sai me zaki roka..?
Amina tace"Zan rokar ma Hajiya da maallam gamawa da duniya lafiya..Sai kuma Aba shima zan rikor

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login