Showing 231001 words to 234000 words out of 265571 words

Chapter 78 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28950

ya girgiza kai Cikin Wani yanayi yana Fadin"Innalillahi wa"inna ilaihirraju"un..!
Kafin ya karisa ya samu Daya Daga Cikin kujerun falon Hajiya ya Zauna Rawaninsa duk ya jike da zufa Aba kuma yana Durkushe inda ya Sulale kansa na kasa ba wanda yasan Halin Dayake ciki su Nasir da su Nazir kuma duk kasa suka sulale suka zauna jin wannan labarin mai kama da al"amara.
Su ya Jadwa da su Jaleela suma kafafunsu ne ya kasa Daukansu suka zube nan saman cafet suna Faman kuka kada su Zulfa su ji Labari gabadaya kowa da abunda yake sakawa acikin ransa Amina kuma na Rumgume jikin Danmallam Tana kuka yana faman share mata Hawaye yana Shafa bayanta Jafar kuma kansa ya Dukar kasa Hannunsa Daya Dafe da kan nasa ya kasa yarda da abunda yake ji kuma yake gani
Gabadaya kowa acikin Falon ka kallah sai ka Hango tashin Hankali da al"ajabin wannan abunda dake Faruwa.
Mamanmu ta Dago Jajayen idanuwanta ta Sauke kan Anty Amarya da jikinta ya fara rawa sai alokacin ta Fahimci Komai fa ya kare sai dai babu wani tsumi ballatana Dubara.
Cikin Muryan kuka da Nadama Mamanmu ta Cigaba da Fadin"Ban taba Sanin bayan ni agidan Baba mallam akwai mai irin Halina ba Sai daga baya..Har ga Allah da Farko bansan Haka marliya take ba sai da watarana na jita tana waya da malamin Dake mana aiki kan Hajiya da mallam alokacin nasan itama irina ce..muna neman abu Daya agida Daya sannan alokaci Daya..!
Ban nuna mata na jita ba Sai daga baya,Na koma na nuna mata fuskata na bayyana mata Duka Burina da Fatan zata bani Hadin kai mu cure waje Daya wajen Cikan nmu burin..!
Tafada tana kallon Anty Amarya da kallo ya koma kanta komawa tayi ta Zauna Dabas saman Cafet sai kuka Cikin wani yanayi ta cigaba da fadin"Alokacin da Balaraba ta zo min da wannan bayanin na tsorata Saboda ko ni ban taba Tunanin haka take ba..Ammh data zauna ta warwaremin komai sai na Fahimci Rauninta nima ina Cikin irin haka..Sannan in muka Hada Hannu zamu cika namu Burin atare..!

Mallam Dake zaune yana jin abun al"ajabi ya Bude Bakinsa Cikin wani yanayi yace"Ke menene naki Burin..?
Burin daya sa kika fifita Duniyarki Fiye da Lahirarki marliya. ?

Anty Amarya bata iya kallon mallam ba Saboda yadda taji muryansa ba wannan amon ballatana karkashi Abunda ke Faruwa ya Dakushe komai Tana sharan Hawaye ta Cigaba da Fadin"Ni burina shine na Zama Tauraruwa a wajenka..Na zama ni ce agabanka kafin kowa..Sannan Burina na zama na Dara duka matanka a wajenka..Sai dai ina burina bazai taba Cika ba indai Hajiya na Duniyarka na yi barnar kudi akan ka mallam da Hajiya Saboda kawai na Zama Tauraruwa a wajenka sai dai hakan bai Samu ba kowani aiki baya Tasiri akan ku saboda kun rike Allah sannan ko acikin Wani Hali baku daina ambatonsa ba. !
Sannan tun zuwana gidan nan na Fahimci Hajiya ta yi mana Fintikau,Komai naka itace,Daga ita Sai SA"IDU sune kadai suke gabanka da su kake shawara sannan uwa uba Sa"idu ne ke jan Ragamar Duka Dukiyarka nayi iya Bakin kokarina na Raba hakan sai dai ban cimma gashi ba..Sai na S??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????auya shawara da taku..Na Fahimci in ni bazan zama Tauraruwa ba ta Sanadin Sakina zan iya Cika Burina Har fiye da yadda nake Tunani..!

Tunda ta ambaci Sakina Danmallam ya zura mata ido yana kallonta sakina kuma jin an zo wannan gabar kawai sai ta kara Volume din kukanta ta soka kanta Tsakanin Cinyoyinta tana gunjin kuka ko Aliya Dake gefenta bata da karfim gwiwan lallashinta.
Anty Amarya na jan Hanci da majina ta Cigaba da Fadin"Har ga Allah Lokacin da na Dauko Sakina ta zauna awajena da zuciya Daya ne sai daga baya..Data fara girma na Fahimci Tana matukar Kaunar Umar in ta gansa ta Dinga mai rawan jiki kenan shi kuma alokacin bata gabansa ita da su Jidda da su Nazifa duk Daya ya Daukesu..Ban tabbatar ba sai da na Samu Sakina mukayi mgana ta Nuna min in ba Umar ba bazata iya auran kowa ba Daga Lokacin na hango Cin ma nasarata ta bangaran Sakina..!
Ni na shiga na fita na Karkato da Hankalin Danmallan akan sakina..Duk da alokacin akwai ya"yan malamai manya wadanda suka fita komai da suka so su hada zuru"a da Maallam kwatsam yace Sakina yake so..Nasam ko Hajiya alokacin tayi mamaki Sanin ba wata alamar Soyayya a Tsakaninsu sai dai sanin ita bamai yawan maida kai kan sha"anin Umar bane yasa bata nuna komai ba ko a Fuskarta ba..!
Hajiya ta jinjina kai tabbas ai Biri yaso yayi kama da mutum Rana Tsaka Danmallam yace Sakina yake so ashe Ba yin kansa bane lalle Allah shine Sarki.
Anty Amarya tacigaba da Fadin"Mallam kuma bai nuna komai ba sai ma farinciki zai yi tuwona maina..Tunda yarcda ya rikeni Sakina Tsakani ga Allah haka yake rike da ya"yansa Daya Haifa,ammh duk ban gani ba Zuciyata ta kekashe da cikar Burina..!
Ban yi salama ba sai da aure ya Kullu Tsakanin Umar da Sakina sannan naji Hankalina ya kwanta sannan na sanya aka doramai shakkar Sakina da Duk abunda zatamai bazai taba gani ba ballatana ya Dauki mataki akanta Shiyasa sai tayi ta yin abubuwa bai Taba Daga ,kai ya Dubeta ba Sannan wannan aikin mai girma ne Tunda shima yana da Tsari ajikinsa Dakyar aka samu nasara akansa..!
A wannan gabar ne muka Hada hannu da Balaraba wacce ainihin sunanta ne Dayyaba..Ni kuma marliya nake ammh ana Kirana da Madina sai muka juya sunayemmu Domin kada Bacin rana a fahimci in da muka Dosa..!
Ni na kai Balaraba wajen malamin Dake min aiki anan Dutse Bukatarta ta Farko shine ayima Jafar mugun asirin da zai Fandare ya zama gagararree ya bi Duniya ya lalace kada yaji mganar yaya ballatana ta Sa"idu ya Zama YA FITA ZAKKA Acikin Dangi wanda Daga karshe Sa"idu zai gaji ya tsine mai kada dai ya amfana da Haihuwarsa har Abada..!
Sai akaji goggo Husai ta saka Salati Tana kuka tana Fadin"Innalillahi..Ammh wlh Balaraba kin cika bakar muguwa azzaluma..!
Sai kawai ta koma ta zauna tana Fadin"Allah yayi gaskiya..Zai Tsare bawansa a duk inda yake..!
Jafar kuwa ko Dagowa bai yi ta kasan Inda yake zaune Hawaye ne ke Digar masa Danmallan kuma Hannayensa Jimke Cikin na Amina tun labarin Anty Amarya na Sanadin Auransu da Sakina yake ta Hailala acikin ransa..!
Mamanmu kuka take yi kamar ranta zai fita ita da Anty Amarya da suka san yau komai yazo karshe..!
Ba wanda yace musu kala su kansu ya"yansu zuwa Lokacin sun Fahimci komai ban da tashin kukan au bakajin komai afalon..!
Mamanmu na Toshe kukanta ta Cigaba da fadin"Sai dai an samu matsala..Aikin sai ya kuskure maimakon Jafar sai ya Sauka kan AMINA tun Yaya nada Tsohon Cikinta alokacin..!.
Sai kallo ya koma kan Amina wacce ta kifa fuskarta kan hannun ya Danmaallan tana ta kuka,mamanmu na kallon Amina ta gyada kai tana fadin"Tabbas abun bai sauka kan kowa ba sai kan Amina..Mallam din da kansa ya fadamana haka ni da Madina da muka koma da Korafin aiki bai ci ba..Ya sanar damu aiki yaci Sai dai ba akan Jafar ba,akan Abunda ke Cikin Yaya..!
Alokacin gani muke kamar wasa sai da Yaya ta Haifi Amina sannan muka gasgasta kowa yasan tun Haihuwan Amina ta fita zakka cikin ya"yan gidan da kowa ma,sai kuma nayi amfani da kissa na,na rika jan Amina ajiki ina nuna nafi kowa sonta tunda kowa baya kaunarta Saboda Rashin kunyarta da Kuma Yadda ta addabi kowa ban so Amina ta tsaya haka ba naso ne ta Lalace tabi Duniya ta Zama Karuwa sai dai ina burina bai Cika ba Allah ya Tsare Amina duk Rashin kunyarta bata mu"amala da maza ba Sannan Tarbiyan gidan su data gidam Baba Mallam ta Zauna mata Daram Sannan Allah ya Tsareta da Fadawa wannan Halakar..!
Duk soyayyar da nike nuna ma Amina na karya ne bayan Sihirin Dake tare da ita nima na bada tawa gudummuwar wajen kara Lalata Rayuwarta,Ban taba mata Fadan tayi ba Daidai ba,Duk da alokacin in na Fadamata zataji Domin na Fahimci Duk Duniywa bayan ni da su Hajiya Amina bata yarda da kowa ba sannan tana kaunata Fiye da yaya data kawota Duniya da hakan nayi amfani na Gurbata rayuwar Amina ban taba bari ta ma kanta wani abu ba bana so watarana hakam ya amfaneta sai na Zabi na Sangartata kada ta iya komai ta tashi ahaka ta kuma rayu ahakan na Tabbata watan watarana sai haksn ya Zama illah agareta.
Saboda irin Kaunar da nike nuna mata ba wanda ya taba Fahimta ta Komai sai dai in saka Hamida Amina kuma na Dauketa wata Shashasha ce da bazata iya moran rayuwarta ba Sannan na kara nesantata da Mahaifiyarta yar da har Yaya ta koma ga Allah Amina ko da na Minti Daya bata taba rabarta ba. !
Amina ta Dago jajayen idanuwanta tana kallon Mamanmu kallon Tsana da wani Bakimciki haka Hamida itama da su Zulfa suke kallonta Cikin kyama da wani Takaici Aba dai bai Dago kansa ba har alokacin..!
Mamanmu bata Damu da kallon da suke Binta dashi ba ta cigaba da Fadin"Duk abunda kuka ga Amina nayi ba yin kanta bane..Tana da Sihiri ajikinta sannan da Shafar aljanu su suke sakata ya wan tsorata da kuma Mugayen mafarkai sannan duk abunda ya Faru da Amina kan Aminu na sani ammh ban taba Hanata ba..Ban kuma nuna mata na sani ba da Gangan nake ijiye wayata in da Zata gani saboda ta Dauka alokacin Naso ne Aminu ya lalata Amina Ya yi mata Cikin da zai yi Sanadiyar tsarwata zuciyar Sa"idu da yaya Tunda na Fahimci har ahakan Kaunar da suke ma Amina na Dabam ce ta fita zakka ko acikin ya"yansu ita din mafi
soyuwarsu ce..!
Wannan Karon har Hajiya sai da ta Saki Salati Amina taji kamar dan Ciikinta ya juya ta fara Kokarin tashi Daga jikin Dannallam kawai sai ya kamata ya Rumgumetw zuciyarsa na Bugawa Fat Fat ammh bai Daina kiran sunan Allah ba kada ya rasa natsuwarsa Amina ta nitse Cikin kirjinsa ta wani Fashe da wani marayan kuka Mamammu ta Cutar da ita Cutarwa da bazata taba iya yafe mata ba..!
Mamanmu kanta na kasa tacigaba da Fadin"Sai dai Burina bai cika ba..Allah ya tsare Amina Daga tarkona..Acikin wannan tsukin mallam ya Shammacemu ya Daura mata aure da Danmallam auran daya sa na Harzuka Madina ta harzuka itama,Auran da shine Silar Sanadin mutuwar YaYA..!

"KARYA KIKE YI..Hadiza bata mutu ba..Ke kika KASHETA Balarabaa..!

kawai sai jin kakkusan muryan Aba sukaji ta karade Falom Cikin wani amo mai karfi da ba"a taba jinsa yayi irinsa ba..!
Sai kallo ya koma kansa ayadda Idanuwansa suka kada suka yi Jajir kamar gauta sai ya baka Tsoro ya mike jikinsa na karkarwa yana nuna Mamanmu da yatsa yana Fadin"ke kika kasheta..Kika rabata da Duniya Batare da ta miki komai ba. ?
Meyasa kikayi haka..?
Meyasa kika kashe ran da bata taba Sauya matsayin ki aranta ba .?
Balaraba Bazaki taba gamawa da duniya Lafiya ba..!
Kawai sai kuka jikinsa ya fara rawa yana neman Faduwa Jafar ya mike da gudu shi da Nasir suka taroshi ya Fada Jikinsu yana kuka jikinsa na rawa yana karkarwa yake fadin"Ita ta rabani da Hadiza..Ya Allah ka wulakantata..!.
Sai kuka gabadaya sai kowa yaji ya kara Raunana.
Jadwa da Jaleela suka ruga wajen Abba suka rikesa suna kuka sai ga Jamila itama da Jawahir,har da Jawaad na wurin yana kuka duk da ba Duka yake Fahimta ba ya Fahimci kan Rasuwar Yaya ce.
Ganin haka yasa Amina ta kalli ya Dannallan cikin rauninta tace"Ina so naje wajen Aba!.
Bai musa ba ya Saketa Lokaci Daya ya mike ya taimaka mata ta mike ya karisa da ita gaban yan"uwanta dukkansu suka Dago suna kallonta Aba yana Kuka Kukansa na Fitowa yace"Ki yafemin Amina..ki yafemin..!
Kawai sai Amina ta zube kan kafafun Aba ta wani saki kuka,kukan da kowa yaji sai da jikinsa ya kara yin sanyi Su Jamila suka Fada kan Aba suma suna kuka mai tsuma zuciya Danmallam na gefe yana jin kukan Amina har Cikin Ransa da Ruhinsa ammh ba yarda ya iya Bai isa ya hanata kuka ba..!
Su Zulfa suna ganin su ya Jawaheer wajen Aba ammh kunya da Bakimciki sun saka sun kasa karisawa garesa suna Zaune sai sharban kuka suke kada Hamida ma taji Labari..
Anty Amarya ta runtse ido sai ga Hawaye lokaci Daya Tana Fadin"Tun Lokacin da naji labarin wannan auran Hankalina ya tashi..Saboda bai kamata wata tazo ta sha gaban Sakina ba..Duk da duk kokarina Burina bai Cika ba,Sakina ta samu Ciki sau hudu tana barinsa..Auran Amina ya razanani ni da Sakina razanan da bamu yi shi Lokacin auransa da Sarood ba Saboda ita na saka mallam ya maidata Hoto..An yi ma Umar Sihirin da bazai iya Zama namiji awajenta ba..Awajen Sakina ne kadai zai amsa sunansa Namiji..!
Danmallam ya kalleta Tsam kafin ya juya ya kalli Mallam shima shi yake kallo.
Danmallam kansa ya maida kasa bayan sun Hada ido da Aliyu da mamakin abunda ke faruwa yasa ko motsi ya kasa Anty Amarya ta Cigaba da Fadin"Yadda Mallam ya shammacemu ne yafi batamin rai..Sannan ina Tunanin da Sanin Sa"idu komai ya faru..shiyasa na yi alkawarin shima sai ya Kurbi kwatancin bakimcikin daya kunsamin na Kira Dayyaba muka yi mgana..Nace mata ya kamata Yaya TA,MUTU..ita kuma tace Tabbas ya Dace ta Mutum..Ko domin ta Rama Bakin cikin da Sa"idu ya Dade yana kunsamata aranar na Kira mallam na Fadamai komai,Adaran kuma ya Turo ma yaya Hayakin Daya Turketa ya Sarke mata Numfashi...Numfashin Da yayi Sanadiyar mutuwarta..!
Anty Amarya ta karishe Fada Cikin gunjin kuka ita da Mamanmu gabadaya Falon aka Dauki Salati sai kuka Mamata na Sharan hawaye tana Fadin"Wannan wani irin mugunta ne..?
Gaskiya Balaraaba bazaki gama da Duniya Lafiya ba sai kin lalace..!
Hajiya kanta sai da ta Durkusa kan gwiwiyonta cikin rauni tace"Wani irin Rudin Duniya yake diban ku da har kukayi Tunanin Kashe ran da bata muku komai ba..?
Kai Haabunallahi wa"inamal wakeel..!
Hajiya take fada sai ga Hawaye ganin yadda Hajiya ke kuka ga Aba nayi da su Amina sai kusan kowa ma ya fashe da kukan banda Mallam da Mazan dake da sauran kwarin zuciya.
Ammh yau kam Jafar shima kukan yake rerawa Hawaye wani na korar wani.
Anty Amarya bata yi shuru ba ta cigaba da fadin"Mun so auran Amina da Umar ya kare a lalace ne Ganin An Dibi Lokaci basu tare ba sai muka Saki jiki..Sai kuma kwatsam Hajiya ta taso da mganar tarewar Amina Data rugazamin Shirina ni da Dayyaba ba yadda bamu yi ba kada hakan ta Faru ammh ina Bakin Alkalami ya riga ya Bushe Allah ya Rubuta kaddara zama Tsakanin Amina da Umar..Bayan ta tare na saka mallam ya kara mata rashin kunya da Fitsara saboda Umar ya gaji ya sakota sai kuma yazo ya bar garin ta kare abunta kan Sakina..Alokacin hankalina ya karkata kan yadda Umar zai zo ya tafi da ita Madina har kiranye na saka an yi mai ammh ba Nasara hankalina ya kara tashi Lokacin da Sakina ta samu Ciki ta karayin barinsa alokacin ne na gane bayan ni acikin matan mallam ma akwai wata mai Buri irin nawa..Saboda mallaminmu ya tabbatar min da ita ke lalata duk cikin da Sakina take samu..!.
Anty Amarya kawai ake kallo wacce ta Runtse ido ta cigaba da Fadin"Dana Fahimci ko wacece naso nayi fito na fito da ita Sai dai ina sai ta nuna min In an shirye nake ita atafe ta kwana..Daga karshe sai ta nemi ta lalatamin Duka Shirina ta lankwasa komai ya koma kaina..awannan gabar na rasa madafa.sai da naga Umar ya Danu sannan su Hajiya ma haka sai Hankalina ya kwanta..Ban taba kawo ma kaina wani abu zai ya faruwa ba nan gaba ko da Hajiya ta Dauke Amina nayi Tunanin maiduguri ta kaita sannan Daga baya sai mukayi Tunanin ba auran ne sannan Balaraba kuma hankalinta ya karkata kan Sa"idu da ya koma sai abunda tace mai ni kuma ma samu Natsuwa tunda Umar yazo ya tafi da Sakina sannan Sarood bamu da damuwa akanta Sakina tajata ajiki da farko da sai da ta riga ta mata illah taja baya da ita..Sannan Mallam ya tabbatarmin dacewa sai dai ta gaji da zama dashi araba auran sannan ita kanta Aminar banmu taba Zaton wani abu zai shiga Tsakaninta da Umar har ta samu Ciki ba Shiyasa muka bar wannan Gibin bamu Cike ba..Na rantse har ga Allah Sakina bata da Laifi nice idona ya rufe da Cikar burina ammh ita bata san komai ba,sai soyayyar Mijinta da kaunarsa komai ta aikata ni ce Sila..Ni ce silar duk abunda ya faru..Don Allah ku yafemim..!
Sai kuka har da Shasaheka Falon yayi shuru sai tashin koke koke Mallam kansa na kasa yana ta Salati kansa ya Daure acikin gidansa acikin zuru"arsa Shirka ya samu wajen zama bai taba Sani ba..?
Bai sani ba sai da Hajiya da Danmallan suka zo suka same shi da mganganu wadanda ya kasa gasgasta su ya rude ya shiga Dimuwa Sannan alokacin ya kasa gasgasta mganarsu ammh yaji Daga Bakin da bazai mai karya ba Hajiya da Umaru...sannan Amina bazata taba fadin Wani abu kan Balaraba ba indai ba Gaskiya bane..ita kanta Hajiya ta shiga Rudani sanda Danmallan yake sanar da ita abunda Amina ta Fadamai sai dai bata ji ita kadai ba,ta tarasa suka isa gaban mallam ya sanar dasu abunda Amina ta Fadamai alokacin zuciyar Mallam ta raunana matuka tundaga wannan Lokacin baya barci Damuwa da bakincikin irin wannan abunda yake faruwa acikin iyalansa bai kara barinsa ya runtsa Dakyau sannan tun alokacin jikinsa yayi sanyi da bai Taba yi ba.
Danmallam ma ya girgiza da jin wannan al"amarin ballatana mallam..?
Hajiya kuwa duk ta san wani abu sai da labarin Balaraba ya girgizata.
Dukkansu shuru sukayi da mganar Suna jiran wannan ranar da dukkan sirrin Boye zai fito Fili.!
Baba Mallam ya Dago kansa Rawaninsa ya jike da Zufa duk da Sanyin A.C dake cikin Falon Cikin son ya kara Tattabarwa yace"Wacece ita wacce take Lalata Cikin da Sakina ta samu..?
Muna so mu santa sannan mu ganta..Allah ne ya nufemu da Sanin Ainihin Fuskokin wadanda muke Zaune dasu..!
Yafada cikin raunin murya raunin da ko Hajiya bata sam mallam dashi ba.
Anty Amarya zatayi mgana kenan sukaji muryan Hajiya Uwani Daga Bakin kofar Falon na Fadin.

"Gani nan..!

Sai kowa ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login