Showing 90001 words to 93000 words out of 265571 words

Chapter 31 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28961

ya"ya na ne kadai Mallam zai kallah yaji Dadi ba..Tunda Mama ta fadamana Mallam yana matukaar son ganin kwam Umar aduniya na Mike Tsaye,Duk Shigen Shigen Marliya sai da nasha gabanta Bata sani ba ko gobe Sakina ta samu Ciki sai ya Lalace Mama ta tabbatarmin Umar haka zai zo ya koma bazai taba ganin kwamsa aduniya ba..!
Batula tayi dariya kafin tace"Wai itama balarabiyar madina din kin gama mata aikin..?
Haj.Uwani tace"Tun yaushe..Tare suka sha mganin Mama cikin Ruwan Tea din da suka tako har Fadona na Hada musu sun koma ba Dadewa..Sakinar tayi bari har Umarun yaxo karban mata mgani da Marliya ta karbi mata na Hausa..Araina nace kyayi ki gama..Wannan gidan na Uwani ne da ya"yaanta..!
Atare suka saka Dariya kafin Batula tace"To wani mataki zamu Dora sabuwar zuwan namu..?
Haj uwani tace"Tsarin da na Dora na gabanta zan dorata..Duk da nasan ma Umar b abunda zai ci da wannan mara kunyar yarinyar sai dai kinsan Namiji baka rainasa..Awajena bata da wani amfani kamar yadda na Maida yaron nan NASIR mara amfani a wajen Mallam in ba ya gansa bama mantawa yake yi dashi..!
Wata Dariya suka saka har da Tafawa kafin Batula tace"Don Mallam din da Giwar suna Tsaye ne..Ai da tuni burin mu ya cika..!
Haj.uwani tace"Abu daya na kasa..Kai Maallam kasa shi da Hajiya..Mama tace har Abada bazan ci galaba akansu ba sai dai kan yaran
Basa wasa da ibada sannan azkar kamar ya zama jikinsu in ba ikon Allah ba Sihiri bazai taba kamasu ba..!
Batula tace"Shiyasa nace ki bar asaran kudinki..Mu koma inda Mama tace sai muga riba..!
Haj.Uwani ta saki kayayyatacen Mirmishi kafin ta koma ta kishingida kan kujera Lokaci daya tana Fadin"Aikuwa naga Riba Batula...!

Ashe ashe basu sani ba..Suna Tufka ne..Daga gefe wata Boyayiyar Fuskar tana Faman warwara..!







*Janafty*
*TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janaftyd'?*



*
Rai bakon Duniya..!
Misalin karfe 7:00am..!

Gabadaya gidan Baba Sa"idu haka suka tashi zuciya ba sukuni,Wasu sun samu barci da yar natsuwa ammh akwai wadanda basu runtsa ba ciki har da Amina domin yadda taga Rana haka taga Dare ita ba kuka take ba Domin zuciyarta ta kekashe bata ma jin yin kukan abu daya ta sani bata son tuna inda kaddaranta ta jata ta kaita domin in tana tuna yau ita ta haramta ga Aminu sai taji gabadaya Duniyar na juya mata,Abu daya yake mata nauyi acikin kirjinta Aminu shi take so ta san wani hali yake ciki ammh babu dama sannan sai Aba da Yaya wanda bata taba tsammamin Fushinsu zai dameta ba abu daya ke damunta Shedar iskanci da suka Zargeta dashi sauran bata damu ba Domin ta aikata ammh abu daya ke sata bakinciki yadda aka kasa Fahimtar abubuwan da suka faru kan yadda suke..!
Tun bayan data idar da sallar asuba bata jirga daga inda take zaune ba ta kalli gabas da katon hijabin haddarsu bangon Dakinsu ta kurama ido ita ba kuka take ba ammh kana ganinta kasan bata cikin natsuwarta cikin kwanakin nan gabadaya Amina ta Zafge sai idanuwa fuskarta tayi wani iri tayi zuru zuru Hamida da Hanne ne ke tare da ita acikin Dakin Domin Ya zeenatu ta fita Kitchen ita bata koma barci ba.
Hanne ce ta gaji da ganin Amina ahaka yasa tatashi tsam ta koma kusa da ita tadafata tana fadin"Amina don Allah kiyi hakuri..Ki yi hakuri..Haka Allah ya kaddara miki!
Kamar bazata tankata ba tama yi Tunanin bata jinta yasa ta kara Girgiza kafadanta tana Fadin"Ameena kina jina kuwa..?
Sai alokacin Amina tayi motsi da bakinta Cikin wani irin Sautin da Hamida da Hanne zasu iya Rantsewa da Allah basu taba jin Amina cikin wannan Sautin ba..!
Asaman lebenta mganar ta fito cikin karyewan zuciya da Rayuwa tace"Ina jinki Hanne..Tun jiya keda Hamida kuke maimaita kalmar nayi hakuri..Tawa kaddaran kenan baku Tunanin na Haddace wannan..?
Tafada Lokaci Daya tana sakarma Hanne manyan Idanuwanta cikin wanu yanayi na neman ma tallafi Dayasa Hanne saurin kauda kanta Tana fadin"Na sani..Ammh ki sani mai hakuri shi ke da riba watarana..Ko Hamida..!?
Hamida da duk jikinta ba Dadi tace"Sosai ma Hanne..!
Tana jinsu gani take su din suna cikin Farinciki tunda rayuwarsu bata yi musu juyin waina kamar yadda tayi mata ba..!
Kara murmusawa tayi wanda kana ganinsa zakasan ba Annuri ko jin Dadi acikinsa tace"Hakane..Nagode bazaku je hadda bane..?
Ta fada tana son kauda mganar domin tasan bazasu taba gane wani Hali take ciki ba..!
Hanne ce tace"Bazamu ji dadin zuwa baki ba Amina ki saki jikinki..Sati mai zuwa sai mu koma tare..!
Amina taji kamar tayi kuka alokacin Dama dama ace baya zata dawo Da tafi kowa jin dadi bata samu zarafin mgana ba Hamida tace"Ni kaina bazan ji dadin zuwa ko"ina ba baki ba Amina..Tare muka tashi muke komai tare..Wh damuwarki tamu ce Amina don Allah kiyi hakuri..!
Tana Fada sai kuka hakama Hanne sai ta rumgume Amina tana kuka hamida ma tazo suka hadu suka Rumgumeta suna Fadin"Amina wlh mu zamu shaidarki..mun sani Fahimtar hakane basu yi ba..!
Amina cikin wani irin kuncin zuciya tace"Wlh ban taba iskanci ba..Bantaba kadaicewa da Wani Namiji ba da sunam alfasha ba..Abunda ya faru ranar Tsausayi ne..Wannan itace kaddaran daman datake jiran bawa koda yaushe..?
Itace kaddarata sannan kuma natabbata na Fita zakkan da ake yawan Fadi akaina Tunda gsshi ni Tawa Rayuwar ta kare ba yadda ta kowa take karewa ba..Hanne da Hamida kun ji dadinku bakinciki bai gauraye jin dadinku ba..Wlh ayadda nake ji dama ace Ban hadu da Aminu ba dama komai kamar mafarki ne..!
Take fada sai kuma ta fashe da kukan da ba Hawaye daga gani abun yana Fitowa ne daga kasan ranta ne
Haka suka hadu suna ta kuka kamar wasu yara bame lallashinsu cikin wannan yanayin sukaji muryan Ya Zeenatu tana Fadin"Jawaad wai lafiyan ka kuwa..?
Me yayan zatayi maka Dakake ta mata wannan uban kiran..!
Muryan Jawaad sukaji a Tsakar gida yana Fadin"Ya zeenatu tun dazu nake tashinta taki tashi..!
Tana daga kofar kitchen ta Hararesa yana Sanye da zani da alamu wanka yayi Cikin dan fada tace"Bazaka je ka shirya ba sai Idi ya tafi ya barka ko..?
Cikin Tura baki yace"To ai ban ga Jallabiyata ba shine nake ta tashin Mama ta Daukomin taki tashi..!
Domin kaf gidan nam Jawaad kadai ke kiran Yaya Mama shi har alokacin sunan Yaya bai kama bakinsa ba..!.
Ya zeenatu da mamaki ya kamata tasan yaya bata barcin safe In ta idar da Sallar asuba sai gari ya waye tana Lazimi koda bata ga fitowarta ba Tasan tana da Bayi adaki kila ciki tayi Hidimarta ammh cikin son kwantar da Hankalin Jawaad yasa tace"Kila barci ne ya Dauketa bayan tayi sallah jeka ka Duba cikin Dirowa kila ka gani kayi sauri fa..!
Har ya juya sai ya juyo yana Fadin"Batayi sallah ba fa ya Zeenatu..!
Dam gabanta ya fadi cikin Fitan hayyaci tace"Bangane ba..!?
Cikin yarintarsa yace"kuma fa bata motsi..!
Karaf Sai a kunnen Mamanmu Dake zaman jiran wannan sakon ya isketa Mikewa tayi bakinta kamar ya Tsage Cikin Yar dariya tace"Komai ya kamallah..!
Daga haka ta gyara yanayinta Lokaci Daya tana fitowa alamun barci a idonta tace"Zeenatu me ya faru nake jin hayaniya..!
Zeenatu da Hankalinta ke tashe tace"Mamanmu jawaad fadi yake yaya bata motsi fa..?
Ido ta zaro tana fadin"Bata motsi kamar yaya..?
Tafada cikin bayanna Firginta Wanda ya fito dasu Hamida Daga daki har da Amina Da suke jin meke faruwa gabanta ke fadi jikinta ke rawa tana Fatan ba wani abu bane zai kara kutse Cikin Rayuwarta ba..!
Ya zeenatu ce kan gaba wajen shiga Dakin Yaya har bedroom dinta jawaad suka kara samu akanta yana jijjigata yana faman fadin"Mama ki tashina ina jallabiyata..?
Yake fada ammh ko gizau dukkansu kamar an dasasu sun kasa karisawa gareta tana kwance sambal Cikin Hijabinta,fuskarta tar ta kara wani Haske sai dai abu daya ya Sandarar dasu shine ganin Idanuwanta suna kallon Saman Dakin ammh kuma bata Motsi gabadayansu kamar an Sassake jikinsu haka suka kasa karisawa..!
Jawaad daya gansu ya sauko yana jan Hannun Mamanmu yana fadin"Mamanmu taho ki gani..!
Haka yake fada kamar rakumi da akala haka ya jata har gaban gadon yaya inda take kwamce daidai Lokacin da sukaji sallaman Ya Jafar Ya zeenatu kamar walkiya ta fice da Sauri kamar ta kifa a tsakar gida taga ya Jafar Bayansa Aba ne,Kaya ne ahannun Ya Jafar da bargo da Filo sai Kwandon abinci,Bata Tsaya ko Gaida Aba ba tace"Aba ya jafar kuzo ku gani Yaya bata NUMFASHI..!
Dukkansu haka mganar ta shigesu Aba kuwa dakyar ya iya Tsayuwa da Kafarsa Meke faruwa ne..?,Tabbas wanu abu ya faru ko kuma zai faru Domin Tun jiya yake fama da Faduwar gaba da yanayi mara Dadi sai ya Danganta haka da Kila abunda ya faru ne na Amina ammh kalaman Zeenatu sun saka gabbansa kara Saki Cikin wani yanayi.
Ya jafar ne ya tsaya yana fadin"Bangane bata Numfashi ba..?
Aba bai Tsaya sauraransu ba ya taka ya shiga Dakin yaya jafar na ganin haka ya watsar da kayan Hannunsa yabi bayansa Zeenatu sai ta kasa Binsu kafafunta sun kasa Daukanta koda batasan Mutuwa ba Ta tabbata yaya MUTUWA tayi..!
Ba wanda yasan da shigowar su Aba sai dai ganinsu kawai akayi Kamar Daga sama Hamida da Hanne da Amina sun rirrike hannun juna cikin wani yanayi Mamanmu tana ganin Aba sai ta fara sauya yanayinta Taga yadda take kallon yaya tana Sakin Mirmishin jin dadin.
Kan jikinta ta fada lokaci Daya tana Fashewa da kuka sai kuma ta Mike ta Nufi Aba tana nunamai yaya Lokaci Daya tana fadin"Sa"idu duba ka gani..Kamar yaya ta MUTU fa bata motsi..!
Kalmar ta Mutu shi ya shiga kunnen Amina da wani yanayin da har Abada bazata manta dashi ba..!
Aba kuma sai ya Ture Mamanmu ya karisa gaban Yaya ya jafar na bayansa Cikin wani yanayi Kallonta yake yi yana kokuwa da Numfashinsa Allahu akbar ashe ashe mganar da sukayi jiya itace ta bankwanansu Allah ya jikanki Hadiza ya fada acikin ransa kafin ya Dago hannunta da yayi sanyi karau har ya fara sandarewa na dan Lokaci kafin ya saketa Mamanmu ta Dora hannu aka tana fadin"Ta Mutu ko..?mun shiga uku mun Lalace wayyo ni Balaraba..!
Kan Yaya tayo da Sauri Aba ya Riketa yana fadin"Natsu mana Balaraba..Wa ya ce miki ta mutu..?
Cikin dan Daburcewa tace"Bata Mutu ba..?
Kallonta yake da dukkan zuciyarsa yana Faman karanto duk addu"an da tazo bakinsa shima natsuwarsa ke neman kwacemai yasa ya Saketa yana Fadin"Jafar je kazo da Mallam..!
Da haka ya koma jikin Wardrope din Dakin ya jingina kansa yana jin kamar zai fadi Jawaad da ya fara kuka ya isa garesa ya Rumgumesa yana Fadin"Aba kace mama tatashi..!
Sai Sa"idu yaji kamar ya Sulale kasa Ya sume saboda yanayin Dayake ciki rumgume Jawwad yayi kawai yana fadin"Kayi hakuri jawaad..!
Haka kawai yake fadi zuwa Lokacin Kukan Mamanmu ya cika Dakin su hamida ma sun fara ita da Hanne banda Amina da ta kasa Fassara yanayinta ji take kamar ta Bude ido Taga komai ya koma mafarki ne..!
Sai dai ina abunda take gani gaskiya ne domin ba Dadewa sai ga Ya Jafar da Baba Mallam sun sake shigowa Cikin Tsashin hankali Aba na ganinsa yace"Dubata Mallam ta rasu ko..?
Baba Mallam bai Sauraresa ba sai da ya isa kusa da yaya ya kalleta na wani Lokaci ko bakasan mutuwa ba in ka kalli yaya zakasan ta amsa kiran Mahallicinta Cikin Fargaba yake da Tashin hankali Tun zuwan jafar dama ga Damuwar abunda ya faru gabadaya shi kanshi Baba Mallan fata yake yaya bata rasu ba baisan da wani ido zai kalli Sa"idu ya Fadamai Hadiza ta rasu ba..!
Hannunta ya rike na wani Lokaci kafin ya saka kunnensa Saitin zuciyarta na wani Lokaci cikin Sanyin Jiki ya Dago yana kallonta kafin ya Juya yana kallon Aba da kaifaffun idamuwansa da na ya jafar suke kallonsa da su Hamida Mamanmu kuma Sai kuka take rusawa..!
Aba ya kalli Baba Mallam yana Fadin"Ta rasu ko..?Don Allah in ta rasu ka fadamin..Na yarda da Allah ke kashewa kuma shi ke rayawa..!
Baba mallam yayi mamakin Kalaman Aba aransa yaji salama Cikin Dattakomsa yace"Kayi hakuri Sa"idu..Allah yayi ma Hadiza RASUWA..!
yafada Lokaci Daya yana Dafa kafadarsa alamun Lallashi abun mamaki bai ce komai ba illah matsawa da yayi ya shafe idonta sannan ya Dagata ya cire mata Hijabin jikinta ya Lullube kanta dashi Lokaci Daya yana Fadin"Allah ya jikan ki Hadiza..Allah ya kyautata zuwanki...Allah ya Sadaki da Mala"ikun Rahma hakika ke yar aljannah ce Laifin da kika aikatamin da ganga da wanda kika sani da wanda baki sani na yafe miki Duniya da Lahira Allah ya yafe miki kema yasa ki kwanta Cikin kabarinki Cikin Salama ke da kika tafi baki Gaggawa ba..Muma da muke duniyan Jiranta muke Allah yayi miki Rahama Hadiza..!

Sai alokacin Muryansa ta fara rawa yasa ya Dakata Baba Mallam da ya Jafar dake kuka Suka amsa da Ameen Mamanmu ce ta fasa wani ihu ta Fadi kasa sumammiya shi ya shigo da ya Zeenatu Dake kuka itama ganin Yaya Lullube yasa itama ta fasa kuka tabi ayarin su Hamida Dake durkushe gaban Mamanmu suna kuka ya jafar ne yayi jarumtar fita ya Debo ruwa suka shafa mata sai gata ta farfado tana kuka tana mganganun Rudewa da yadda Mutuwar ta Daketa matuka..!
Baba Mallam ne yace"Balaraba ba kuka Hadiza ke bukata ba sai addu"a ayi hakuri..kinji ko Allah ya jikanta..!
Mamanmu fadi take"Yaya ta rasu..?Innalillahi..Wayyo Allah na..!
Haka take fada tana kuka jikin ya Zeenatu dake ta kuka itama su sun samu Damar kuka ita Amina ta nan Tsaye kukan ma yaki zuwa mata maimaitawa kawai take yi wai yaya ta rasu..?ina wannan ai ba gaskiya ne yayan da jiyanan lafiyanta kalau..!
Baba Mallan ne ya Dago Aba Dake duke gaban Yaya yana kokarin Daidaita Numfashinsa cikin lallashi yace"Sa"idu tashi.kayi hakuri ka nuna Jarumta..In ka rushe suma iyalanka zasu rushe..!
Ba Musu ya Mike yana Rike Jawaad da Zuwa Lokacin ya Fahimci abunda ya Faru shekarunsa goma sha Daya yasan Mutuwa rumgumesa yayi yana kallon Baba Mallam Lokaci daya yace"Asanar ma da Mutane Baba..Jafaru kuma sai yazo da mai awon Likkafani domin ashiryata mu sallaceta zuwa gidanta na gaskiya..!
Baba Mallam ya jinjina kai kafin yace"Shine abunda zamu mata mu nuna mata soyayyarmu.muje waje..Bazaku iya zama da gawa,kuna wannan koken koken ba..Bari naje na Turo Hajiya..!
Ya jafar gaban yaya ya karasa ya Bude Fuskarta kafin yace"Allah yayi miki Rahma yaya..
Kuka ke neman kwacemai yasa ya fice da Sauri Su ya zeebatu suka kama Mamanmu dake kuka Sai alokacin Baba Mallam ya Lura da Amina cikin wani yanayi yace"Mamana sai hakuri kin ji..?Hadiza addu"an ku take Bukata kawai..!
Abun mamaki kallonsa tayi da idanuwanta cikin wani yanayi tace"DA gaske yaya ta rasu..!
Kai ya gyada mata kafin ya samu Zarafin mgana tace"Ba sai ka kira Hajiya ba..Ni zam zauma da ita har ku dawo..!
Gabadayansu suka kalleta Har Aba da su Mamanmu Cikin Sautin Amon muryan data Sadaukar dakomai tace"Eh zan zauna da ita..Don Allah kada ku hanani..Ku barni na zauna da ita na wani Lokaci na karshe a Rayuwata..!
Sai kuma taji kamar Rauni zai bayyanan mata sai ta Dake domin ji tayi kamar zuciyarta ta kara Bushewa ba wanda bai ji Tsausayinta ba Baba Mallan ya dafa kanta yana Fadin"Shikenan Mamana ki zauna da ita banda kuka kiyi ta mata addu"a..!
Da kai ta amsa mai kafin ta Nufi gaban Yaya ta tsaya sai kuma ta Sulale ta Zauna da katon Hijabinta Cikin wani irin Sauti tace"Nan zan zauna..har Ku dawo baba Mallam..Ko bata ji Dumina ba..Zan tuna watarana na zauna da ita alokacin da Numfashinta ya bar jikinta..!

Ba wanda ya tankata har suka fice Baba Mallam da Aba suka fita daga gidan su Zeenatu kuma tsakar gida suka koma suna ta kuka kafin kace me Mutuwar yaya ta Zaga ko"ina duk wanda ya kamata yaji wannan Mutuwar data girgiza mutane da Dama kowa akace yaya ta rasu sai yace Daman tayi ciwo ne..?Mutuwa ko babu ciwo ana tafiya..!
Hajiya babba Mutuwar Yaya ta Daketa Matuka duka matan Baba Mallam suna gidan Baba sa"idu tare da Mamanmu da Yaran,Amina taki Fitowa Daga Dakin yaya tana zaune gaban gawan ba kuka take ba sai dai da ka ganta bata cikin natsuwarta Fata take taga komai ya koma ba yadda take gani ba Hajiya tayi tayi Amina tatashi ta koma Falo in da su Mamanmu ke zaune dasu Anty Amarya su hanne suna Dakin mamanmu sanye da Hijabai su da matan su ya jafar sun saka hijabai suna ta karatun Qur"ani suna Hawaye tunda Hajiya ta hana su kuka..!
Ammh Amina taki tashi fadi take"Hajiya ki kyaleni..Wlh Lokacin Yaya na Raye ban taba zama da ita ko na minti biyar ba..?Bazaki barni na zauna da gawanta ba ko naji Dadi..!
Daganan Hajiya tasan Amina ba kalau take ba,Sai ta kyaleta sai itane tazo suka zauna anan tare tana mamakin ko Kwallah Daya Amina batayi ba..!
Tana fatan kada abunda suka faru da su saka zuciyarta ta Harbu da wani matsala..
Alokacin bataasan me Amina ke Tunani ba..Mganar Aminu ta Tuna da taba cemai ta fison Mamanmu akan yaya alokacin Dariya yayi yana mata kallon yarinta kafin yace"Meenata ke yarinya ce har yanzu shiyasa baki san girman uwa ba..Ammh Har Abada Uwa uwace bamai kwace wannan Matsayin Allah ne ya basu..Bazaki Fahimce matsayin Uwa ba sai Ranar da kika rasata ina mai Tabbatar miki ko muna tare ko bana Tare sai kin fi kowa kukan rasa yaya..Ga Mamanmu din da kike fada ammh Bazata iya kare miki wannan Jinin ba Amina..Bazata iya shafe miki makwafin UWA BA har Abada..!

Sai ayanzu mganarsa take Dawo mata Domin abaya in ya fada bata Damuwa da mganarsa ashe ashe ranar ma tanan nan kusa abu Daya ke damunta Yaya ta bar duniya tana Fushi da ita da ZArginta sannan Tunda ta haifeta bata taba Hutawa da Jidalinta ba Abun yana Sakata jin kamar ta Mutu in ta Tuna bata taba zaman minti Biyar da yaya ba da sunan Hira ba..Anya bata zama asararriya ba kuwa..?Kaiconta ita Amina in akwai wacce Mutuwar Yaya zata kasassara to itace domin su ya Jafar har ta bar Duniya bata taba Daga baki akansu ba sai ita kadai da ta fita Zakka cikin ya"yanta..!
Karfe Daya na rana aka saka za"ayi Jana"izarta zuwa Lokacin harta kannen iyayenta da suka rage na nan Gumel din sun zo sai wata goggonta goggo Jumai Sun zo suna gidan Sai su ya Zulaihat da suna Jigawa Labarin Rasuwar ya isketa sai ya Ikram da ke kusa duk suna nan gidan suna ta kuka Goggo Husai Mallam da kansa

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login