Showing 261001 words to 264000 words out of 265571 words

Chapter 88 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28952

suka samu natsuwa sannan sukayi wanka tare bayan sun fito taje ta Hada masa Tea ta kawo mass Yakaka da yaran Tuni har sun yi barci.
Sai janta da Hira yake yi taki Sakarmai Fuska sai dai eh ko A"a shima yasan ai yaga karshensa ina shi ina kara ma Amina Laifi..?
Irin wannan Hukunci haka..?
Duk Fushinta kafin wayewar gari ta Sauka sannan ya Lallabeta suka koma Ruwa wajen Danko yake mai Amina tasha gyaran da yasa Danmallam ya kara raina kansa da duk abunda yake Takama dashi.
Amina sai yanga take mai sai da Safe ne ya Dauki su Aba bayan Yakaka ta musu wanka Allah yasa bata da Paper ranar ammh taso tana dashi tayi Tafiyarta ya karata shi kadai
Tunda ya Dawo bai fita ba ko Sallah acikin gida yake yi wayarsa ma kasheta yayi saboda yasan Halin Amina da zafin kishi yanzu ya samu ta Dan Sauko ai sai su Sakina su Ballomai ruwa ya shiga uku..!
Yakaka sai ta koma zaman Daki Ta bar ma"auratan su ci Lokacin su Taji Dadi Data ga sun sasanta kansu.
Allah ya taimaki Danmallam kwana Hudun da yayi Amina bata da Jarabawa da su yayi amfani ya Gurji Amarcin sa sannan ya samu ya Nuna ma Amina matsayinta duk da ta gamsu bata wani Sakin mai sosai shifa Jidalin Amina shi zai bada Labari Domin shi yaga komai ganin Idonsa..!
Ranar kwana Biyar tana da Jarabawan Safe sai da taje tayi ta Dawo bai Fita ba har tace mai ko gidan mallam bazai leka ba saboda ya wanke maata zuciya yasa yace Zuwan nata ne baki ta tabe bata nuna mai tawani ji Dadi ba aranta kuma ai tasan ko yanzu kasuwa tatashi Dan koli yaci Riba..!
Sati Dayan da Danmallam yayi komai ya Daidaita Tsakaninsa da Amina Saboda kada ya kara ballo ma kansa ruwa yasa yace in ta gama jarabawar ta shirya tafiyan ta gaya masa sai yasa Jafar ya nema mata Visa sannan ya Sanar da ita ya Sama mata Takardan zama achan na Dindin bata wani Nuna murnanta ba sukayi sallama Ta Abuja ma wannan karon ya kara tashi Sai washegari ya isa jidda Daganan mota ta kaisa garin Madina Ya kirata ya samu ta Daga wayan Daman kafin ya Tafi sai da ya roketa alfarma shi yanzu Lallaba Amina yake tasha shi ya warke..!
Yar ya tafi su mallam basu san yazo ba bai gayamusu ba sannan kuma itama Aminar bata gayamusu ba tayi gum da Bakinta itama Yakaka bata Fadama kowa ba..!
Danmallam Daya koma sai ya Fara Cukun Cukun sama ma Amina gida sun yi shawara da Aliyu akwai kudi a Hannunsa zai siya mata gidanta ne ya Fasa,karban na cikin makaranta Yasan ko giwan wake yasha bazai Hada Amina zama dasu Sakina ba..!
Tafi su kishi da Jidali zaman ma bazai yi Dadi ba,Sannan Aliyu ya bashi goyon bayan ya samata gidanta ita kadai Saboda tana da yara sannan kuma hakan ne ma ya Dace zai fi Samin kwanciyar Hankali da hakan suka Tsaida mgana da Taimakon Abu Kattab ya samu karamin gida nan cikin gari kusa da Masallacin madina..!
Bedroom biyu sai Falo sai Kitchen da karamin haraba kafin dai abubuwa su Daidaita,sannan yasa aka gyara gidan ya Zuba abubuwan amfani na Daidai misali Duk da ya Takura bai da kudi sai da Aliyu ya turomai wasu suna waya da Amina ta fadamai sun kusa gama Jarabawa.
Ya kira jafar suka yi mgana kan zai nema ma Amina Visa ammh sai ta amince sannan Jafar mamaki ya kamasa su ya Danmallan an shiga Hannun Amina sai Allah..!
Ko su Hajiya bai Fadama Amina yake jira ba sun zata fushin da yayi bai Sauko bane suka zubamai do suga iya gudun ruwansu..!
Amina sun gama jarabawarsu Cikin Sa"a sai Fatan Nasara asatim Matar Aliyu ta haihu Aliya jin haka yasa Danmallam yace ta shirya taje suna ta kwana Daya batamai musu ba ana Gobe suna Idi yakai su ita da Yakaka da yaran Aliya nata ina ta saka dasu sai Faman nuna ta take yi a matsayin Amarya abokin mijinta Amina dai Sama Sama domin ita bata da yarda ne kan wasu abubuwan sannan bazaka nuna mata ki da Farko ba Sannan ka Dawo ka nuna mata so ba, Daga baya baya ba..!
Kuma Aliya sukan yi mgana da Sakina ammh ba kamar baya ba Sai dai Sama sama kawai kowacce tasan matsayin yar"uwanta sakina kuma sai dai a gaisa da Labarin Duniya Tariga ta gama Shiga Taitayinta..!
Kwana Daya sukayi suka Dawo Gumel ammh sai da Amina taje ta kara Duba Anty Amarya abun sai addu"a Yanzu takai sai ana kulleta adaki Itama Daga Bakin window ta Lekata Sai da ta mata kwallah Mamanmu ma suna waya da su ya Zeenatu an sallameta tana gida sun ce dai da Sauki ammh ba Baki har yanzu ganin ma dai sai ahankali ita kanta Hajiyar uwar ma Duk ba wani Cigaba sauki sai na Allah itama har yau an kasa gane Cutar Dake Damunta..!
Amina batayi gaban kanta ba sai da ta Samu Hajiya ta Fada mata yadda sukayi da danmallam da yazo sai dai Ta Boye Rigimansu Hajiya tayi ta Dariya aranta Ta kuma godema Amina sannan ta godema Allah ko banza yarta nada Daraja Hajiya tace zasu Tattauna da mallam tana mai mganar yace ta shirya tabi mijinta Hajiya tace to..Anty Hadiza tama mgana aka Hada mata kayan gyaran jiki Sannan da Dake Dakem kayan kamshi da sauransu na Tafiya.
Sannan Hajiya ta kira Danmallam taji Tsarin Tafiyar na Amina da inda Zata zauna ya fadamata ya siya mata gida Hajiya taji Dadi tana ta sakamai albarka..Sannan ta mai mganar Yakaka yace sai in Amina ta Fara Tahowa sai yaga yarda za'ayi shima yasan zaman Yakaka da Amina taimako ne sosai
Danmallam bai saka a fara neman mata Visa ba sai da Amina ta Kirasa da kanta tace ta amince zata taho sannan ya yarda Jafar yazo ya amshi pasport dinta sannan yace ta Hada kayanta saboda jirgin yawo zai yi gaba Dashi..!
Jin haka yasa Hajiya ta siya mata Kamshin Girki kala kala da su garin kuni aka shanya mata wake surfaffen da Danyen shinkafa kaya da marasa Nauyi da su fulawa da Sauransu,Sai kayan sawanta dana yara duk da ba Duka ta Diba ba..!
Ansamar mata Visa zata su tashi nan da kwana goma ta Abuja,sai Amina ta Cigaba da shirinta ta kira duka yan"uwa awaya tayi musu sallama su Hanne suna ta Fadin zasuyi kewa da kuma Fatan in suka Haihu Allah yasa tazo tace tasan da wuya. !
Ana jibi zasu tashi Suka kulle gidan suka je gidan Baba mallam tayi sallama da Aba da Anty Hadiza anan ma gidan ta kwama itama Yakaka ta musu sallama Domin abuja gidan Ya Aisha zata koma kayan su Tuni suna Madina har Danmallan ya karba. !
Washegari Idi yakaisu Abuja gidan ya Aisha suka kwana washegari karfe Uku na Rana su ya Aisha da mijinta da Yakaka suka Raka Amina Filin jirgi tana Sabe da ya"yanta daya a gabanta ta Sakashi Cikin Abun goyo Daya kuma yana Kafadanta suma yaran sun yi Bul Bul Dasu suna Daga mata Hannu Amina sai da tayi kuka Lokacin da Jirginsu ya Daga Tana Salati Allah yasa akwai wata Farar mata agefenta ita taimaka mata ta saka mata Belt sannan ta rike mata Aba Dake hannunta..
Amina jikinta sai rawa take yi yau gata ajirgi duk bata cikin natsuwarta addu"a kan har ta shiga bayi sai da tayi matar dake gefenta nata mata Dariya saboda ganin yadda take yi sai da Tambayeta ammh bata taba shiga Jirgi ba tace eh tayi Dariya tace kodaga gani to maatar ne ma yasa ta Saki jikinta ba kamar Farko ba suna ta Fira nan tasan sunan matar Surayyah a Nageria take itama aiki yakai mijinta madina suka koma yanzu ma tazo ganin gida ne su yan Abuja ne suna ta Hira da Amina duk da ta Girmeta itama ta Fadamata wajen Mijinta zataje sai santin su Aba take tana jin Dadin ta samu yar"uwa a Nageria..!
Sai Dare suka sauka a jidda Danmallam Daman tun tasowarta ya Sani yana Jidda shi da Sarood da Sakina suna jiran Saukan Amina Saboda ya gayamusu sai ko ga Amina ita da Surayyah wacce ke rike da Aba ita kuma mallam na Hannunta .!
Sakina baki ta saki tana kallon yadda Amina ta koma Cikin Abaya baka tayi Rolling jan gyale Takalmin kafarta ja ne da Jakarta ga yaranta sai dai kace Masha Allah Danmallam ya nufeta
Ya karbi Jakarta lokaci da mallam yana mata maraba har da Rumgomta sannan suka gaisa da Surayyah Amina ta Fadamai irin taimakonta da tayi a jirgi ya mata godiya itama Mijinta yazo Daukanta har suka gaisa da Ya Danmallam sai ma suka ga sun san juna suna Haduwa wajen karatu a masallacin cikin madina suka gaisa cikin girmamawa basu rabu ba sai da Surayya ta karbi Lambar wayar Amina da alkwarin zata zo har gida sannan ta shiga mota suka wuce ita mijinta, Amima kuma ta saki Fuska suka gaisa da su Sarood har da rumguma Sakina kuwa Amina sama sama ta amsa mata ko Hannun Datake bata,ta kauda kanta bata karbi Musabahanta ba,Motar Haya suka shiga zuwa Madina Danmallam na rike da Aba Sarood ta kankame Mallam itama cikinta har yayi girma Sakina na gefe kamar maraniya mamaki ya kamata jin yadda Amina da Sarood ke Hira Cikin Larbaci..!
Gidan su Sakina suka fara zuwa Sai da Amina tayi sallah taci abinci sannan suka Dumguma zuwa gidanta ta iske komai an gyara har kayanta da suka Rigata isowa Data tambayi Danmallam yace mata Sakina ce Sarood suka zo suka gyara bata kara mgana ba nan suka barsu ya rakasu suka Hau mota suka koma gidansu Yau dai ga Amina amadina Duk Gajiyan da ta kwaso na Tafiya Sai Da Danmallan ya Famshe sai washegari ya barta ta Fara barcin gajiya sannan shi ya Kira chan Nageria ya Fada musu saukanta .!
Saboda ita bai riga ya siya mata Layin nan ba,Amina kamar bugagiya wajen Sati tana Hutawa sannan ta Fara Fita ita da Danmallam gidansu Abu Kattab suka fara zuwa ta wuni mami Sara nada Kirki sannan Amina taga inda Sarood ta Dauko rashin Hayaniya har suka bar gidan Su Aba na hannunta tana wahala dasu Daga Ranar Amina bata zauna ba suna Fita Cikin gari yana nuna mata wurare Amina tayi kuka data ganta a msallacin ma"aiki Bata taba Zaton haka ba,Sannan sun raba kwana yana kwana Biyu gidansu Sakina ita yana mata kwana Daya Sai dai tana Wahalan Renk ita kadai ta Saba yakaka ta Saba mata duk sai ta Sangarce.
Ammh yanzu Reno kadai ya isheta sai in yana nan yake tayata Reno Sai Daga baya ne ya siya mata layin chan ta saka suna mgana da yan'uwanta Amina daman kusanta da son yawo ballatana an samu garin Madina tuni tasan ko"ina Ballatana ma da Surraya ta Kirata tazo gidanta ta wuni itama Ranar Danmallam ya kaita ta wuni Amina ta sami Sake tunda Danmallam bai mata shamaki da Fita ba Saboda wani Lokacin baya kusa ko yana cikin makaranta waya kawai Amina take mai tace zataje masallaci Kusan koda yaushe nan take sallar mangariba da Isha"i kafin kace me Fatar ta Goge ta zama kamar bakar Balarabiya atamfa sai tana Gida in zata fita kuma Jallabiya ce Ita da kyawawan yaranta gwanin ban sha"aawa..!
Watan Amina Daya da zuwa Madina Sarood ta Haifi Yar mace kyakyawa a gida ta Haihu sai daga baya sukaje asibiti aka Dubata Yarinya kamar tace sak kamar yar larabawa,Amina tana zuwa kullum saboda suna dan dasawa da Sarood Tsakaninta da Sakina kuma sama sama ne ko" ya"yanta sai a bayan idonta take Dauka In Amina na wajen bata bari Har Danmallam yaso yayi mgana Sanin Jidalin Amina yasa bai mata mgana ba..!

Ba suna akayi ba an dai yi taro na Murna Har Surayya sai da tazo wacce suka kulle da Amina suka zama kawaye Ballatana da Surayyah ke kaunar Amina Saboda Allah sannan tana son Haihuwa shekara tara da auransu bata taba ko batan wata ba..!
Agida Nageria an ta kira ana ma ya Danmallam barka da arziki sannan yarinya taci sunan Hajiya wato Zainab suna kiranta Banu princesss..!
Sai da aka tura musu Vidoes da Hotunan Bby kamar yar Labarawa to ai uwarta balarabiya ce..!


***********

*BAYAN SHEKARU BIYU..*

Bayan shekaru biyu da komawar Amina Madina da zama abubuwan alheri sun faru sosai ciki har da karin Haihuwan da Amina da tayi ta Haifi mai sunan Yaya Hadiza suna kiranta Iman,Sannan Amina ta koma jami"ar Madina tana karatun a bangaran Islamis studies,Sannan Yakaka tana wajen Amina Danmallam ya cika alkawari yayi ma yakaka takardan zama agarin na har abada tazo tana zaune a gidan Amina suna tare.
Sannan Sarood ta kara Haihuwan Namiji yaci sunan Kattab suna kiransa da Kattab dinsa..!
Sannan Danmallam ya cikama Amina Burinta taje Saudiya ta Sauke Farali Taga ka"aba tayi addu"a sosai addu"o"in da tayi Fatan ta roka ma kanta da iyayenta da mijinta sannan bangaran su Hamida duk sun haihu ita da Hanne wacce ke da wani Cikin ya Aisha ma ta Haihu su ya Zulaihat ma Duk sun Tara zura"a..!
Sannan an samu rashi Mamanmu ta amsa kiran Allah Rasuwarta ya girgirza Amina sai da tayi kuka basu je ba ammh ta Kira yan"uwanta ta Musu gaisuwa Hajiya uwa na nan kwance Jinya taki karewa sannan Anty Amarya kam ta Haukace abun dai ba Dadin ji sai ka tsausaya ma ya"yansu saboda Halin da iyayensu ke Ciki bayan tahowarta sun je gida Sau Daya dukkansu shima rasuwar Umaima ce ta kai su Umaima Allah yayi mata rasuwa wahala ta kare ance Mutuwarta ce ta kara girgiza Hajiya uwani Jikinta sai ya rikice..!
Sannan bayan Dawowarsu Hajiya da Mallam da Aba da Anty Hadiza da ya Jafar da ya Nasir da Aliyu suka zo Madina Aikin Hajji basu sauka agidan Danmallam ba suka kama Hotel kar su kara musu nauyi sai dai sun je sun ga inda suke Dukkansu har gidan su Sakinar sannan suna Haduwa a masallaci gabadayansu sannan a wannan shekaran ma suma sun isa makka sun kara Sauke Farali.
Basu Dawo ta Madina ba Daga makka jidda suka koma suka hau Jirgi suka koma Nageria cikin jin Dadin yadda suka ga Danmallam shi da iyalansa cikin Shiga mai kyau da muhalli.
Su Aba kuma suna Tafiya ba inda basa zuwa sun yi wayau suna da Shekara Biyu Cikin na uku ga Imam har tana Rarrafawa..,!

********

*MURFI..*


Yau tun safe Amina ta kasa sukuni ita ke da Miji yau,Sai shiga take tana fita,Tana Sanye da riga da wando na pakistan, Amina da ta zama babbar mace yanzu yar kimanin shekaru Ashirin da Daya a duniya.
Iman tana rarrafe nan tsakar Falon Yakaka na zaune gefenta Mallam ke hawa bayanta yana Sauka Aba kuma na rike wuyanta Yakaka na fadin"Sai kun karisa ni kenan..!
Take fada tana Dariya Iman ta Rarrafo Tana turesu Yakaka tace"Yauwa uwar Hakuri Korar min su..!
Amina na jinsu hankalinta baya kansu Alkubus take yi ma Danmallan yau da Miyar agusu saboda da sukaje Gida tazo dashi,kuma ya Kirata yace yana so tayi mai shi haduwarta da Surayyah yasa ta kara kwarancewa wajen girke girke da Sannin siirukan Zama da miji Har gobe tana godema Allah tana godema Hajiya domin sune Sillar Inganta rayuwarta ita da mallam.!
Hankalinta bai kwanta ba sai da gama komai ta gyara gidan yana tashin kamshin Turarukan wuta masu kamshi Sannan yakaka tama yaran wanka suka Fito Tsab suna tashin kamshi suma Sannan banda Yakaka bamai ma yaran Hausa Babansu Larabci yake musu ita kuma Amina Tana musu labarci da Turanci Kuma yaran sun iya domin sun fi iya yaran fiye da Hausa sannan suna zuwa wata Tahfiz su Aba tun Safe sai yammah shiyasa harshensu ya tashi da Labarcin sosai.
Yakaka ce ma ke fadan meyasa basa musu hausa suna Hausawa suna wani iyayi ita dai Amina sai dai tayi Dariya bata mgana.
Iman ce suke bala"in kama da Banu din Sarood itama kamar Sarood din ta Haifeta ga gashi gata kamar yar larabawan wasu ma Dauka suke Sarood din ta Haifesu Amina ta yarda da komai banda Sakin Ragamar mijinta da ya"yanta wajen kishiya abunda ya Faru agidansu ya zame mata izinina..!
Bata dai mufin kowa da Sharri..Ammh Sama sama ne gwarama Sarood har lambar wayar juna suna da ita banda Sakina da Amina bata ma son tana Daukan mata yara Ita kuma ga son yara wlh kamar kayi mata kuka akwai ranar dasu Amina sukaje chan gidan Iman ta rarrafa wajenta ta Dauketa Amina ta karbe yarta abun yayi ma Sakina zafi tayi ta kuka har sai da yakaka ta mata Fada Sannan ta Sanar ma da Danmallam ya mata Fada ai Amina data Fara Fushinta sai da Danmallan ya raina kansa ya koma yana Lallashinta abunda ya Faru ya sa ma Amina rashin yarda kuma shi bazai iya Cire mata wannan abun acikin ranta ba sai dai ya tayata da addu"a..!

Yau bata shiga mkaranta ba sai gobe take da karatu kuma tasan sai bayan Isha"i zai shigo gidan shiyasa kafin Lokaci ta shirya Cikin Riga da wandonta,Masu roba sun kama jikinta Sosai ta taje gashinta ta Daureshi Tana gayu dashi yaran sunci abinci da yakaka Iman kuma ta bata Nono har tayi barci tana Dakin yakaka su Aba nata Damunta da Hayaniyarsu sai ga ya Danmallam ya Shigo Gidan Amina taje ta Tarosa kamar yadda ta Saba ya rumgumeta yana Kiran sunanta.
Noor nayi kewarki..!
Itama tace nayi kewarka Hubby..!
Danmallam daya kara zama babban mutum kimanin shekarunsa na Haihuwa Arba"in da biyar kenan ya kara haske sannan Hutu da jin Dadi da yanayin zaman garin madina yasa ya koma kamar balarabe sannan uwa uba kulawar matansa garesa musamman Amina sun taimaka wajen bayyanar da kwanciyar hankali ajikinsa da zuciyarsa.
Jansa Amina tayi zuwa Ciki bayan ta taimakamai yayi wanka suka fito Falo sannan yaran sukaji muryansa suka Fito suma na mai oyoyo.
Ya rumgume su yana Murnan ganinsu Yakaka ta fito suka gaisa sannan ta Janye yaran suka koma ciki Sai Amina ta Fara Cinyar da Mijinta kamar yadda ta Saba yana ci yana kallonta aransa yana saka mata albarka.
Suna gamawa ta kwashe komai takai Kitchen sannan suka Tallafi juna zuwa Cikin Bedroom dinsu

Suka Zube kan

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login