Showing 66001 words to 69000 words out of 265571 words

Chapter 23 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28902

kunni Lokaci Daya taji yana Fadin"Gata nan Nenne..Don Allah ki Roketa..ta ce tana sona..kada ki rasa Aminunki Nenne..!
Dagachan Bangaran Nenne tace"Bata wayar Aminu..Ni don ka kimin ne..da na Share kafata nazo har gabanta na Duka mata..!
A speaker ya saka wayar Cikin ido yake kallon Amina kafin yace"Nenne ta ce..Itace Duniyata..Takasa gane kaina na bata labarinki ammh nace kina Wahalar dani..!
Nenne tana jinki ki roketa don Allah ta Saurareni..!
Amina bata gama mamaki ba sai da taji muryan matar tana Fadin"Amina..Kina jina..Amina don Allah ki Saurari Aminu wlh yana sonki..Da gaske yake Aminu bai taba zuwa ya Duka yana min magiya kan mace ba sai akanki Amina ba don ni ba..Don Allah ki tsaya ki Saurareshi Yana sonki so na Tsakani ga Allah..!
Amina taji gwiwanta ya saki karamar kwalkwlwarta ta kasa Fassara mata komai
Sai da taji Nenne tace"Ko na Duka kan gwiyoyina ne Amina..?
Ina son ganin Aminu cikin Farimciki maraya ne bashi da kowa Amina don Allah ki tallafamai..!
Amina taji kwalla sun cika mata ido Tana ji Nenne na fadin"Kina jina Amina..Amina..!
Dakyar tace"Naji zan saurareshi
Saboda ke
Saboda ke..!
Da sauri Nenne tace"Nagode Amina..Allah yayi miki albarka Nagode..!
Take ta fada kamar zatayi kuka yanke Kiran yayi yama kallon Amina Cikin Galabaitar da yayi kwana Biyu da bai ganta ba yasha zata nemesa bata nemesa ba shi kuma ya kasa jurewa ya Fadama Nenne komai tayi???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? tayi ya bari ta gayama Alhaji Babba sai atura manya Tunda gidan malamai ne yaki barinta yace sai ya samu Soyayyar Amina bai sani ba wannan kuskuran wannan Soyayar itace zata yi katanga Tsakaninsa da Amina har Abada Zanen kaddara ya riga ya zana bawa bai isa ya kauce masa ba.

Yaga tana Shirin juyawa ne batace mai komai ba yasa da Sauri yace"Kin ce mata zaki Saurareni fa Amina..!
Tsoro take ji wannan Tsoron ya shigeta Daga Fara Haduwa dashi.
Tasani wannan abun bai Dace ba ammh bazata iya Ture alfarman matar nan taji nauyinta.
Yasa ta waiga taga ba kowa sai yara Dake wucewa Daman anguwan bata da yawan Zirga zirgan jama"a
Wani Lungu tagani kamar hanya yasa ta Nufi chan tana Fadin"banda karfin Gwiwan Tsayuwa Dakai a hanya .Ina jin Tsoro ka Shigo nan..!
Bai musa mata ba ya bita Daga Farkon lungun suka Tsaya kanta na kasa tace"Meyasa sai ni.?
Agidanmu bawanda na Taba ganin yayi wata soyayya kowa da Lokacinta yayi Baba Mallam zai turo mata mijinta haka akeyi tun kafin a haifemu har kuma yau da muke bata sauya ba..Ka tafi kabarni ban dace Dakai ba ni ba wacce Kake nema bane..!
Bai barta ta Dire ba ya karbe da Fadin"Sai afara ta kanmu Amina..Ina sonki..Kuma soyayyarki bazata taba barina na kyaleki ba ki yarda dani..Ki soni na Rantse iki komai zai zama Daidai da kaina zan samu Malan namai bayani bazai hanani ke ba Amina..!
Kamar yana da wani abu a mganarsa yana mgana tana jin gaskiya a mganarsa ganin ta tsaya tana kallonsa yasa ya fara bata Labarinsa Tundaga Farko har karshe sai taji Tsausayinsa maraya ne cikin Sanyin jiki tace"Allah ya jikansu da Rahma..!
Ya amsa mata da Ameen yana Fadim"Kin ji kadan Daga Labarina Amina..?
Ke nasan komai akanki bana bukatar ji..Kice kina sona ko Hankalina zai kwanta..!
Ido ta zaro kafin tace"Komai fa kace..?
Kai ya gyada kafin yace"Eh..Harda Bakin Tsiwanki nasani..!
Sai ta rufe baki da Hijabinta tana kallonsa Yar dariya yayi lokacin Daya Hangi ledan hannunta yace"Wannan ledan fa..?
Ina zaki..?na tsaya yau ne kawai ba Domin nasan zan ganki ba yau jumma"a ba makaranta sai dai jikina ke bani zaki fito..!
Zuwa yanzu ta fara rage tsoronta Cikin Sanyinta tace"Sako ne Mamanmu ta aikeni na kaima Hajiya..!
Kai ya gyada kafin yace"Zan so na ga mamanmu nima..Yaushe zan je na gaisheta ko kuma yaushe zan gabatar da kaina wajen Mallam..?
Zai karbeni kuwa..?
Wlh ba waka bace kadai Sana"ata ina saida Motoci da kayan Gyaransu sannan ina da shagon gwalagwalai anan kano..Nayi alkwarin zan rike ki Amana..!
Amina ta katseshi da sauri ganin kamar baya cikin natsuwarsa yasa tace"Ba yanzu ba..Kada kaje ba yanzu ba..!
Kai Tsaye yace mata"Saboda mene..?
Bazata iya kallonsa ba yasa kanta na kasa tace"Yanzu ba Lokacin Daya Dace bane..!
Shuru yayi mata akwai tsoro atare da ita yasa ya dan Sausauta mata kansa ya Shafa yana Fadin"Lokacin yayi Amina..Ko ba yanzu zamu yi auran ba ina son na Rika ganinki duk sanda naso..!
Ido ta waro kafin tace"A"a bazai yuyu ba..!
Shima kai tsayen yace"Zai yuyu Amina..tunda kin hanani bayyana kaina ki samamin mafita..Zan susuce akanki baki ga alama ba..!
Amina tayi shuru ta kasa mgana ganin yadda ya marairaice yana kallonta ta kasa mai gaddama yasa tace"Sai dai mu rika haduwa anan lungu ko wanchan layin da muka Fara Haduwa..In wani ya ganni dakai agidanmu kasheni za"ayi..
Idanuwanta yake sha"awa in tana Taoro yasa yayi dariya kafin yace"To ta ina zaki san nazo..?
Amina tayi shuru tana Tunani kafin tace"Sai ka rika zuwa bayan kwana Biyu..!
Da gaske take yi ayadda ta Fada yarintarta ya gani yasa ya yi Dariya yana shafa sumar kansa yace"Amina ina aiki fa..?garin nan bansan kowa ba sai ke bazaki Tsausayamin Zirga zirga ba..In Nenne taji zatayi Fada dani nima zata kusa kasheni in taji ina yawo Tsakanin Titin Kano zuwa Gumel..!
Sai da ya fada Taga wautarta Ido ta Juya ta rasa me zatacemai bata so ta Fadi wani abu yaji ba Dadi Tsausayi yake bata ashe maraya ne.
Ganin tayi shuru yasa yace"Ina katin da na baki kwanaki..?
Kai tsaye tace"Yana gida cikin Dirowata..!
Kai ya gyada kafin yace"kina Daukan wayan Mamanmu ko..?
Kai ta gyada kafin tace"Tab...Ni kadai ke Dauka...Bata mgana in ko su Hamida ne sai ta Rankwashi mutum..!
Ta karishe Fada tana Dariya shima Dariyan yake yi kafin yace"Daga gani mamanmu din nan na sonki..Ko kice Auta..?
Amina tace"A"a ina da kani Jawaad..Mamanmu ta Dabam ce..Kamar yadda kace Girman Nenne a wajenka haka Mamanmu duk da ba ita ta Haifeni ba nafi sonta akan Yaya..!
Ido ya zaro yana kallonta kafin yace"Ba ita ce mamanki ba..?
Tana Dariya tace"Kaima kaji mamaki ko..?
Haka kowa ke fadi in aka shigo gidanmu Yaya kamar ba ita ta Haifemu dukkanmu mamanmu ce komai namu..!
Gyara Tsayuwa yayi yana Fadin"Bani kadan Daga Labarin Mamanmu Amina..Naji ina sonta kamar Nenne ta..!
Amina saboda Shaukin Labarin Mamanmu yasa Ta manta da Tsoronta da aiken da akayi mata ta shiga basa Labarin mamanmu da yaya da Aba da ya Jafar da su hamida ta karishe da Fadin"Ko sau goma akace in yi zabi Mamanmu zan zaba akan Yaya..Kwata kwata bata sona kullum bata Fadin Alherina..Mamanmu ko laifi nayi tasan shi bata Fadinshi sai ta Boye Laifina ko ya"yanta bata hada kansu Dani ni ta Dabam ce awajenta..

Kallonta yake sai yanzu yake ganin yarintatarta Uwa uwace kuma ai ta wuce wasa duk da alabarin ya Fahimci mamanmu macece ta kwarai ammh bai kai Amina ta Girmamata Fiye da Mahaifiyarta ba,sai dai ba yanzu zai nuna mata haka ba Lokaci bai yi ba sai nan gaba bai sani ba nan gaba na Tare da wani boyayyan Kaddara, kaddaran da bazata bashi Dama ya Nuna ma Amina Muhimmancin uwa ba.
Ganin Lokaci ya tafi yasa ya kalli Amina yana Fadin"Shida ta kusa..!
Lokaci Daya yana Kallon agogon Fatan Dake hannunsa Ido Amina ta Zaro kafin tace"Na dade..kada Mamanmu tajini shuru..!
Kai ya gyada kafin yace"Hakane ki tafi..Ki Ari wayar mamanmu kimin Flashing zan kira in naga Nombar zamu rika mgana Amina ai zaki min wannan alfarman ko..?
Gabanta na Faduwa tace"In aka ganni zan shiga uku wlh..!
Yana Dariyan mganarta yace"Zaki boye ai ba wamda zai gani ko..?
Saboda ni da Rokon Nenne..!
Ya fada yana marairaice mata jin haka yasa ta Daga kai da sauri yayi dan Ihu kafin yace"Nagode..Zan jiraki kinji..!
Da kai ta Dagamai kafin ta fara tafiya sai kuma ta juyo tana kallonsa hannu ya Dagamata kafin ta dagamai sai da tace"Yanzu Yolan zaka tafi..!?
Kai ya girgiza mata kafin yace"A"a kano zan koma Amina daman nan din A hotel nake kwana yau nazo saboda na ganki muna da Shooting gobe in Oscar bai ganni ba ai na Shiga uku Amina..Nura ma in ya fara kirana sai ya Kasheni da raina..!

Yadda ya fadi karshen mganar ne yasa ta yin Dariya tana wucewa da Sauri Lokaci Daya taji yana Fadin"Wlh Ina sonki Amina..Ni na sani ina sonki..!

Har takai gidansu Hanne Mirmishi bai bar Fuskarta ba kamar almara wani Farimciki take ji yana shiganta Tunasa take da Duka kalamansa sai taji kamar tana yawo a gajimare.
Sauri sauri tayi dataje gidansu Hanne Ko zama batayi ba Duk da Hanne tayi ta janta da Hira don ta zauna ta kosa ta ganta agida ta Nemi katin nan kada ace ya bace data Shiga uku.
Ko Rakiyar Hanne bata jira ba Data Shiga Daki ta Dauko Hijabi Tana jin Ya Abida na Fadin"Amina yau Ba"a son zama kuma..Sai faman sauri take..!
Hajiya ma sai da tayi mgana ita dai Amina gaba tayi koda Hanne ta fito ta wuce abunta Baki Hanne ta tabe kafin tace"Amina tsiyanta nada yawa..!
Amina bata ji kwanciyar Hankali ba sai da ta Binciko Katin nan Cikin Dirowarta bayan ta gama yin Dai'dai da kayanta.
Mamakinta ya ishi Hamida batayi dai mgana ba Ya Zeenatu ne tace"Wlh Amina ki kwashe mana kayan nan..Nasan Halinki sai kice kansu zaki kwana..!
Amina batabi ta kanta ba Sai da taga Katin nan sannan ajiyar rai ya kwace mata da sai da suka kalleta Dukkansu Hamida tace"Me kike nema ne wai..?
Amina tace"To kuma ina Ruwanki Uwar saka ido..!
Hamida ta tabe baki tana Fadin"Ki gyara kayanki kuma da kanki Wlh..!
Jin haka yasa Amina ta marairaice Tana Fadin"Kayya Hamida..Yi hakuri badake nake ba..Anty Hamida yar aljannah..Allah yasa ki auri Shugaban kasa muje Villah mu Bude Hanci wai waya ga Amina Aminene a Villa Jar Uba akwai Daga kai..!
Yadda ta karkacen ne yasa Dole har ya Zeenatu sai da Dara tana Fadin"Ke ai Tun get din farko Sojojin Villa zasu Wurgoki waje..!
Amina tace"Tab kaji ya Zeenan nan..Mune fa kalan masu kudi kalan yan gayu..!
Take Fada tana wani Fari Zeenatu na Dariya tace"Aifa kalan masu kudi a bushe kirji gandas Amina kamar kin shafi kasan kabari Ko Hanne fa ta Fara Nanna banda ke suna chan makale a kirji kamar na maza..!
Amina ta Chuno baki itama abun na Damunta kafin tace"Wlh nima abun ya isheni kaf yan ajinmu baki ga nasu ba Tumbul tumbul..Ni don Allah ko Hamida zata san min nata ne..?
Kalli nata kamar Lemu sun yi Bulbul dasu..!
Salati Zeenatu ta saka Hamida kuwa har da cin Tuntube wajen Fita ya Zeenatu tabi bayanta tana Fadin"Mamanmu ki fito..kiji Abunda Diyarki ke fadi..!
Da gangan ta koresu suna fita ta Dauko Katin tana kallo acikin Haban Sikat din ta Boye shi ta fara maida kayan tana kwalama Hamida kira.

"Hamida.Haba mana Hamidas..Zan yi miki zaman Daki na sati Daya zan tayaki gyaran gado..Yaya Hamida..Anty Hamidassassas..!
Take fada Hamida na jinta tayi mata banza Daga Tsakar gidan tace"Bafa zan tayaki ba ki gyara da kanki..!
Kamar Amina tayi kuka tace"Shikenan Baza"a ma ace Antyn ba Hamidan ba..Hamidu din..!
Ba Hamida ba Hatta Yaya Dake Dakinta tana jinsu sai da ta Dara Mamanmu na cikin Bedroom dinta ko ta jisu ma bata fito ba Jawaad ne ke wasa ya kyakyalce da Dariya yana Fadin"Ita kuma Aminuu ba..!
Zeenatu da Hamida suka saki Dariyan Amina na ciki na jinsu taji sunan Daya ambata yasa ta Daga Murya tana Fadin"Jawaad ina wasa dakai ko..?
Wlh in na kamaka sai na yi kasa kasa Dakai..!
Tagumi tayi tana maimaita sunan Aninu acikin ranta Tsikar jikinta sai da ya tashi wani yanayi ta shiga da batasan Dalili ba.
Sai ta gama gyara kayanta Tsab har Hamida data shigo sai da tace"Yau wata rana Amina anyi abun kai..!
Tana Hararanta tace"Yau jumma"a munafus aga ban gyara ba..!
Dariya take mata Lokacin data fita alwalar mangariba ta shiga Dakin Mamanmu tana Tiolet din Cikin Dakinta yasa ta Dauki wayarta ta Sake a Sikat sai dakoma Daki tayi sallar mangariba Lokacin Yaya da Mamanmu da su Hamidi sun fito baranda kamar yadda suka saba suna Hira ta Lallaba ta shige Dakin mamanmu har cikin Makewayi ta kuma Sakama Kofar key.
Kan abun bahaya ta zauna ta fito da waya da katin Duk yadda Tsoro ya Cikata kalaman Aminu na yana jiranta Cike da yakini yasa ta kwashe Daya Cikin Lambobin ta Doka mai Kira.
Sai da ta shiga har taji an Dauka sannan wata zuciya tace"Amina me kika aikata..?
Da sauri ta kashe sai dai ta makara Tunda yace ta kirasa yaji ajikinsa zata kira din yana ganin bakuwar Lamba yasan itace.
Karar wayar yayi daidai da Daukewar Nunfashi Amina kafin gabanta ya koma ya Fadi Dam..!
Ta rude yasa batasan ta Danna Dauka ba sai da taji muryansa yana Fadin"Hello Amina..
Nasan kece..Daman ina da yakinin zaki kirani..!
Fitar muryansa kamar wani Sinadiri ne ajikin Amina hakanan taji kamar komai yana kwance mata wannan Tsoron kuma yana Fita Daga cikin kanta.
Bata sani ba wannan wayar itace mafarin Kaddaranta Itace mafarin FITA ZAKKAN da tayi acikin Yan"uwanta da Danginta..!


Yanzu muka shiga labarin da sauran mgana agaba..!




*Janafty*

*TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janaftyd'?*




*
In wata Kaddara zata sameka Sanadin wani abu to baka da tsumi ballatana Dubara sannan Tsoro bashi da muhalli a wannan bangaran to kamar hakane ya faru da Amina inda ta san Sanadin Aminu zanen kaddaranta zai bayyana da tasani zatayi zatace Daman Tun farko komai bai faru ba.
Amina bata taba tsintar kanta ahalin data tsinci kanta ba Yarinya ce mai son yabamata a nuna mata so da Muhimmanci zuciyarta karamace ba bu kowa acikinta shiyasa cikin Sauki Aminu ya samu Dama mai yawa akan Amina.
Tun fara wayarsu ta farko abun bai Tsaya ba sai ya cigaba duk sanda Amina ta samu dama zata Dauke wayar mamanmu ta shige Tiolet dinta ko na Tsakar gida,flashing take mai yana gani kome yake yi zai ijiyeshi ya Kirata su sha Hira cikin abunda bai gaza sati Biyu ba, suka yi wani irin Shakuwa ta ban mamaki ko shakka babu Aminu ya samu Matsugunni azuciyan Amina tana sonshi tana kuma Tsausayamai saboda Maraya ne.
Komai take aboye take yinshi bata taba yarda a Fahimci Halin data ke ciki Daman chan bata da tsoro sai da soyayyar Aminu yasa AMina ta koyi Munafunci da nuku nuku ko bata fito Fili ta Fada ba,kowa yasan tana cikin Walwala da Farimciki ba wanda yayi Tunanin wani abu daman ita Amina akullum cikin Jidali take da Tsiwa sai Chanzawar bai wani damu kowa ba Hatta dasu Hanne da suke tare da juna koda yaushe.
Kafin lokaci yaja Amina ta gama sanin komai na Aminu duk halin Dayake ciki in sukayi waya sai ya Fadamata Amina ta zama kamar wata bangonsa yana Tunanin ranar Daya rasata baisan ina Rayuwa zata kaisa ba komai nata yana Burgesa komai tayi a wajensa mai kyau ne.
Abokan aikinsa ba wanda baisan sunanta abaki ba Musamman ma Oscar,da Nura koda yaushe suna waya sai yace"Minata kinga Oscar ko..?
Yau bai barni na Huta ba. !
Minata kinga Nura ko..?
Yana sani yawan mgana...!
Komai nsshi itace"Minata kinji me Nenne tace..?
Wai bazata yarda na Daukeki zuwa kano ba Tare zaku zauna ayola kin yarda..?Ira iran irin wadanan zantukan Amina ta gama Haddacesu acikin kanta indai akan Aminu ne.
Taki bari su kara haduwa wannan Tsoron bai saketa tana aikata abunda ko su ya Jadwa zamansu ba wacce tayi Tsaurin idonta sai dai ina Zuciyarta bazata iya bata ma Aminu ba Daya matsa ta amincemai yazo ya ganta Ranar Jumma"a da basu da Ismilya Daman sun yi mgana jiya da Daddare zasu hadu in da suka Hadu Na Karshe Alayin Gaban gidansu bayan La"asar.
Haka kuwa akayi Tana idar da Sallar La"asar tace ma Mamanmu zata shiga wajen hanne ba wanda ya tankata sanin basu da Shamaki da gidan Baba Mallam
Mazan duk suna masallaci suna Karatu ta sabe ta tafi koda taje har ya iso yana Jiranta,Ranar sun sha Hira Amina ta kara sanin Aminu sosai ta kuma gama yarda ma kanta itama In bashi bazata iya auran kowa ba Ko alokacin yayi yayi ta bari ya Turo a tambayan mai Izini Amina ta nuna ba yanzu ba tana tsoro ko Ss2 Bata kai ba ta Tura Saurayi gida ai su ya Jafar sai su kusa kasheta da ranta Tana Tunanin da Sauran Lokaci bata sani ba Daga ita har Aminun wannan Tunanin nasu shine ya bada kofar shigowar wannan kaddaransu kaddaran da zata Haramta musu juna har Abada kila da bai bi mganarta ba da Kaddaran tajasu zuwa gurbi ko matsayin da suke Fata
Abu kamar wasa karamar mgana ta zama Baba Soyayya mai karfi ce Tsakamin Amina da Aminu agida ba wanda ya sani duk bayan sati uku yake zuwa ya ganta ta fita da Niyar zuwa gidansu Hanne sai su hadu alayin gaban gidansu wani Lokacin Nikab take sakawa saboda kaucema Idon Mutane wani irin so Aminu yake mata so mai zafin da komai zai iya yi kan Amina Yaso ta bashi dama ya Hidintamata ammh kuma taki yarda bata yi Tsaurin idon da zata karbi wani abu Daga wajensa ba Ranar da Dubunta ta Cika sai ta Mutu ta Dawo Saboda duka tasani akwai wannan Ranar watarana zata zo sai dai bata san yaushe ne ba ammh Tabbas akwai Ranar kin Dillanci.
Zuwa Lokacin ba wanda Aminu bai sani ba agidansu Amina da gidan Baba Mallam ba,su ya Jafar kuwa har ya Haddace Labarinsu da su Sa"adatu da basa ga maciji Hanne da Hamida kuwa Koda yaushe suna waya rabi Duk Labarinsu ne Ya riga ya sani Hamida da Hanne sune gaban goshin Amina sannan kaunar Dake tsakaninta da Mamanmu kaunace da Allah ne kadai yasan Girmanta.
Nenne kuwa koda yaushe suna mgana da Amina in yazo ko kuma in yaje Yola Nenne tana ganin abun kamar wasa sai kuma karamar mgana ta zama Ita dai jikinta bai bata ba tana ganin wannan hanyar da Aminu ya Biyo anya mai bullewa ce kuwa..?
Tana Tsorom watan Watarana komai yazo ya Rikice tasha cemai"Aminu Anya bazaka Daina Biyema yarinyar nan ba..!?
Kafita Hankali fa kai babba ne kana ganin wannan Soyayyar taku ta Boye ba wanda ya sani agidansu watarana in aka sani bazata Haifar maka da matsala ba..!
In ta fadi haka Dariya kadai yake mata yace"Haba Nenne..Bafa komai mai Wahalar Meena ce..In tana sona ko Duniya zata hade bamai rabani da ita so kada ki damu babu abunda zai faru..!
Kallonsa take yi bata cewa komai ba ganin idonsa ya Rufe ammh ajikinta Tana jin kamar zuwa gaba wannan zai zame ma Aminu kabule babba ma kuwa da bazai

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login