Showing 147001 words to 150000 words out of 265571 words

Chapter 50 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28909

yaci gandan ya sha mgani nan kasa ya shimfida bargo ya kwanta Alokacin har Amina tayi barci batama sani ba shi ya cire mata Hijabin Jikinta data kwanta dashi Saboda tasha iska ko motsi batayi ba bayan ma mgani ya Lura tana da nauyin barci.
Shima yana kwanciya bai Dade ba sai barci saboda na muran yana saka barci karfe hudu na asuba ya tashi yayi wanka ya fice zuwa masallaci sai 6 ya dawo ganin Amina bata da Niyar tashi ya tasheta yace tayi sallar kamar mashayiya haka tatashi tana Idar da Sallar ta koma ta kwanta tana samun Hutu sosai.
Shi kuma yana falo yana kallon labarai wayarsa tun jiya ta cika ammh Hakanan yaki kunnata baya so ma wani yasan yana nan Tafiyarsa shekaranjiya bata samu ba sai yau,Sai wajen 8am na safe ya leka Amina tana ta barci bai tasheta ba ya shiga Tiolet kayan data tara a Kwandon wanki ya kwashe harda zanin gado yaso ma ya Kira mai musu wanki ne sai kuma ya fasa,Gwara ya wanke su da kansa yasan in ya tafi bai wanke ba akwai matsala Amina bata san ciwon kanta ba Tukunnah ko kuma yace ba"a koyamata ba Daga yanayin yadda bata iya komai sai tace Mamanmu ko Hamida ke mata Daga gani su suka batata ammh ace kamar ta ace batasan gyara ba sai kazanta.
Ta harabn gidan akwai wata Kofa inda suke da famfo da tankinsu na ruwa nan ne sukayi wanki ko shanya in wani abu ya faru na gaggawa,nan ya kwashe kayan ya fita dasu Allah yasa Megadi na Dakinsa bai gansa ba ba Omo kwata kwata agidan sai da ya Fita ya siyo ya Zage ya wanke zanin gadon nan tas da kayan Amina pants dinta kuma Data wanke basu fita ba ya Zubar a Bola domin bazai iya wanke mata ba, ba domin yana kyamarta ba yana da kyamkyami sosai ne sosai bazai iya wankewa ba,Ammah ai karshen kyamkyami kuma ai ya kare tsakaninsa da Amina tunda mai afkuwa ta riga ta afku

Abun da ya kusa bashi Dariya Har da Vests cikin kayanta shi yaushe Rabon da ya ga ana sa Vest aransa yace shi ne madadin Bra dinta shi kadai yana wankin yana Dariya har alokacin in ya Tuna Haduwarsa da Amina sai yaji wani iri acikin Ransa yanayi ne da bazai iya Fasaara shi ba ammh yaji matukar mamakin yanayin daya shiga Lokacin kasancewa da ita ko shi yasa Aliyu ke son auran irin su masu kananun shekaru..? Yadan gano sirrin kadan duk da Abun bai wani Samesa Yadda yake so har yaji ya ishesa ba an Dai Taba kawai an bari shima Tabawan kamar kudirin Allah ne.
Tas ya wanke su ya Daureye ya shanya su saman igiya sannan ya koma Cikin gida ya Zage ya gyara falon ya Share saboda duk yayi kura saboda isar da akayi shekaran jiya..
Dakin da Amina take ciki ya koma har Lokacin tana barci Zagewa yayi ya shiga Tiolet ya wanke shi Tas ya zo kuma ya gyara Dakin ya share duk ya Gaji bayansa har ciwo yake yi bai zauna ba wanka ya shiga yayi ya fito ya Saka Jallabiya baka ya Dauki walet dinsa ya fita yaje ya siyo musu abinci da katan din Faro sai na maltina Saboda Amina da kuma Tafiyarsa.
Sanda ya dawo ta tashi Daga barcin Kuma tayi wanka batare da yace mata ba Sai dai kayan jiya ta maida sai yace ta Cire ta sauya wasu ita daman tayi wankan ne saboda ta Lura yadda yake son wanka kamar kwado koma batayi ba sai yace tayi shiyasa tayi ammh yaushe zata jure wannan aikin kamar wata yar ruwa..!
Atamfa ta saka Riga da Sikat sai Alokacin yake ganin Rashin girman Jikinta tsawo dai gareta ba Kiba,Ammh a shekarunta in da tana da manyan gabbai da Tuni tayi Jiki Tunda Hamida da Hanne sun fita Girma yan kirjinta yake kallo kamar yayi Dariya abun chan manne Lalle kwaila ce Tabbas kwailace ya aura kuma kwailan nan ne ta Daukesa Tsab Allah mai iko domin ya yarda da akace abun ba daga shekaru ne ko Girma ba..!
Chiips ne ya siyo mata shi kuma Ruwan zafi yace su bashi achan yazo dashi ya sha Tea da buredi ita kuma ta Dora da maltina tayi gatsa ta sha mgani da ruwa yace taje ta kwanta Haka ta mike tana Tafiya sannu sannu ya Bita da kallo Hankalinsa ya kwanta ganin har tafiyarta ta Fara Daidaita ya Fara Tunanin in ya tafi yau Amina bazata iya zama agidan nan ita kadai ba ita kuma wanchan baisan yaushe zata Dawo ba..!
Shi kan shi akwai gajiya ajikinsa yasa ya kwanta saman kujera sai barci sai gabda azahar ya farka Sauri Sauri yayi alwala ya tafi msallaci bai Tsaya ba Illah abinci da siyo ma Amina da kayan su Fruit ayaba kankana lemo da Sauransu koda ya dawo ta tashi tayi sallah tana kwance ammh ba barci take yi ba.
Inda yayi wanki ya koma ya kwashe kayan Tunda sun bushe ya kawo su Falo ya zauna ya ninke mata sannan ya Shigar mata dashi har Cikin Wardrope ya saka mata yana Fadin"Mai wanki duk bayan sati daya yake zuwa karba..Ki rika Hada kayanki wadanda suka kamata banda Undies nasan ba hankali kika cika ba sai ki Hadamai da Vest dinki..!
Kunya ta kama Amina taji kamar ta Nitse shikenan ita kuma ya gama ganin komai nata Zanin gadon ya Ciro ya kalleta yana Fadin"Tashi na Shimfida..Kije falo na siyo miki abinci da Fruit..!
Kamar zata fita sai kuma ta fasa ta kallesa yana kakkabe gadon zai shimfida Zanin gadon tace muryanta kasa kasa"Kawo na shimfida..!
Ko kallanta bai yi yace"Ki wuce nace..!.
Da sauri ta wuce har tana Hardewa sai da taji wani iri a kasanta duk da ya fara warkewa sosai ta ke tsarki da Ruwan zafi tana gani a littafan Hausa in haka tafaru kuma tana so ta warke shiyasa batayi wasa ba sannan kuma Ai da sukaje asibiti Dr haka ya fadarmuau hakan.
Tana fita ta jawo ledojin priderice sai kayan Marmari? Ayaba kadai taci sai kankana cikinta ya cika sosai mganinta na Dakin ita kuma tana jin kunyar komawa ba Dadewa sai gashi ya fito da mganin ya zauna gabanta yana Fadin"Matso na nuna miki yadda zaki sha kowanne..!
Ba musu ta matso ya nuna mata Duka kuma ya tabbatar da ta gane ya bata ganin bataci abinci ba ya Tambayeta tace sai an juma ta koshi.
Da kanta ta maballi mganin tasha ta koma gefe ta Rakube kanta na kasa shima bai bi ta kanta ba ya sha Kankana kadai ya mike ya bar mata falon ta Bisa da kallo aranta tace ashe yana da Mutumci wani lokacin..!
Wanka ya shiga Sauri Sauri yake yi Saboda yana so ya isa kano da wuri kuma Motar haya zai bi jirgin su karfe Takwas na Dare zai tashi zuwa jidda.
Sannan kuma wa zai kira yanzu yace mai bai tafi ba..?Kowa na da uzurinsa sannan kuma basusan an samu wannan Tsaikon ba,Duk da yasan sun neme sa a layinsa na Saudiya zasu ji a kashe layinsa na nan kuma bai kunna wayar ba yasan zasu yi Tunanin gajiyar tafiyace yasa bai Dora Layin ba yana da Tabbacin harda mallam ya Kirasa yaji ya ya sauka bai samesa ba..har ya shirya cikin Pakistan riga da wando masu ruwan madara yana
Tunanin mafitar yadda zai yi da Amina baza ta iya zama ita kadai ba sannan Hajiya bazata taba yarda ya maidata agida ba.
Tunanin kiran Hajiya yayi yace ko su Hanne ta saka idi ya kawo su yasan Aminar zata ji dadi da wannan Tunanin ya fito Cikin Shirin Tafiya Rataye da Jakarsa Amina ya iske tana Barci a zaune ya Dade yana kallonta karamar Fuskarta har ta Fada sai yaji Tsausayinta gashi zai tafi ya barta ba wani babba kusa da ita Allah yasa ma taji Sauki sosai.
Fuskar yaya yake gani a Fuskarta sai yau ya kara kare ma Amina kallo yaga ba inda ta bar yaya a kama,Baisan sadda ya Furta"Allah ya jikan ki yaya.!
Afili yana kara kallon Amina lokaci Daya yana kara ganin yarinta muraratun a kanta ganin har Biyu ta gota yasa ya karisa gabanta ya Durkusa yana Buga jikin kujeran Data jingina tana barci lokaci Daya da Kiran sunanta.
Firgigit ta mike tana Raba ido sai ta gansa a gabanta Tuni jikinta ya Fara rawa tana kokarin tashi ya Rike duka Hannuwanta yana fadin"Ki natsu mgana zamu yi..!
Duk da ta natsun ammh ta kasa kallonsa Kanta na kasa tana kallon yadda ya rike da hannunta sosai.
Cikin Taushinsa yace"Ya jikin ki..?
Fata kin sami lafiya..?
Kai ta gyadamai alaman eh Cikin bude murya kadan yace"Da baki zaki amsamin..!
Sai da runtse ido kafin tace"Eh da sauki..!
Kai ya kada kafin yace"Ba inda yake miki Ciwo..?
Kai ta kara dagamai kafin kuma da Sauri tace"Ba ko"ina..!
Shuru ya gifta na wani Lokaci kokarin Kwace hannunta take yi yaki Sakinta wani yanayi take ji Daya riketa shi kuma sai faman kai da kawon mganar yake yi kafin yayi shahada ya kira sunanta.

Amina..!

Amsawa tayi ammh bata Dago ba shima bai Damu ba cikin Taushin lazafi yace"Abunda ya faru Tsakaninmu Sirrinmu ne ko..?
Yafada yana kallonta kanta na kasa bata yarda ta Dago ba ta gyadamai kai Cikin jin nauyi shima ya cigaba da Fadin"Yauwa to kuma kinsan duk wanda yake fadan sirrin aure Allah zai kona sa ko..?
Ba kyau nasan an fada muku a islamiyanku ko..?
Nan ma kai ta gyada mai kafin ya cigaba da Fadin"To ina so abunda ya Faru Tsakamin mu ya tsaya iya mu Biyu..Kada ki sake ki Fadama kowa kin jini ko..?
Sai alokacin ta Dago ta kallesa suna Hada ido tayi saurin maida idonta kasa shima Fuskewa yayi kafin yace"Kin ji ko baki ji ba Amina..?
Cikin sanyi tace"To Allah fa..?
Ai ya sani ko..?
Mamakinta ya kamata sai bai nuna mata Cikin yanayinsa yace"Eh Dagani sai ke sai Allah..Daman ai shi yana Sama kuma yana kallon Duk abunda muka aikata..!
Bana so ki fadama kowa..Koda Hajiya ce ko mallam ko Aba ko Hannatu da Hamida. !
Kai tsaye tace"Harda Mamanmu..?
Da Sauri yace"Har da ita kada ki Fadamata in kuma kina so Allah ya Konaki Ranar Lahira shikenan..!
Yafada da sigan ya Tsoratarwa Amina mamakinsa ya kamata me ya maidata ne..?Sauma kiramana shashasha kenan..! Da bata san me take yi ba da zata bama wani wannan Labarin mai kunyar Fada ita ba Haka take ba ko da ya ganta yarinya tana da wayau..!
Shi a dole zai mata wayau sai abunda ya bata Dariya har sai da ta Murmusa kafin tace"naji insha Allahu bazan Fadima kowa ba..!
Jinjina kai yayi Cikin jin Dadi kafin yace"Good naji Dadi..Ki kula da kanki kinji ko..?Kirika wanka sau uku ko Biyu arana sannan ki rika shan mganinki kin ji ni..?
Nan ma kai ta gyada mai ba Zato kawai taji ya saka mata kudi a Hannunta ganin yan Dubu Dubu yasa ya Zare ido kafin tayi mgana ya mike yana fadin"Ki rike su a hannunki..Ni yau zan koma..!
Zaro ido Amina tayi kafin tace"Ina..?Madina..?
Kai tsaye yace mata"Eh tafiyar ma bata yuyu bane da Tuni na tafi..Jafar zai kawo miki waya zamu rika mgana ..!ina dai gargadinki kada ki Fadama kowa..!
Amina bata ma jinsa Tunaninta na kan yadda zata zauna ita kadai agidan nan gashi bata san ina gajeran matarsa taje ba tun ranar bai kara mganarta ba..kafin ya ankara Amina ta Fashe da kuka cikin mamaki yake kallonta kafin yace"Kukan me kike yi..?cikin kuka tace"Wlh bazan iya zama agidan nan ni kadai ba Tsoro nake ji ka maidani gida..!
Kai Tsaye yace"Nima? naso hakan sai dai? Hajiya da maallam bazasu bari ki koma ba..!
Amina na Jan majina tace"Gidammu zan koma bazasu sani ba..!
Dariya mganarta ta basa da sai ya Dara kafin yace"In jiwa..? ai da gidanku da gidan mallam Duka Dayane Dole zasu sani..Ki daina kuka zan kira Hajiya ko Hannatu sai tazo ta Zauna Dake kafin Sakina ta Dawo..!.
Jin sunan Hanne Daya ambata yasa ta bar kukan ta Dago tana kallonsa kafin tace"Da gaske..?
Kai ya gyada mata wani mikewa tayi kafin tace"Yauwa harda Hamida don Allah ya Danmallan kaji..?
Ashe tasan sunansa kallonta yayi kafin yace"Wato ku hadu ku fara rashin ji ko..?
Kin san dai yanzu ba da bane ko..?
Da Sauri Amina tace"eh wlh babu abunda zamu yi..!
Kai ya jinjina mata kafin yace"Shikenan sai su zo..!
Tsalle ta Daka tana Hawaye tana Dariya zafi taji a kasanta yasa ta Duke tana Wash wash Kallonta yayi kafin yace"Ki rika kula da kanki fa..Kina da Sauran Rauni..!
Bata Dago ba ta mikamai kudinsa tana Fadin"Babu abunda zan yi da kudi..!.
Shi kuma yace"Ki rike a hsnnunki. zaki koma makaranta Dis Coming monday ki rika yin kudin Break sannan in kina Bukaar wani abu in Sakina ta Dawo ita zaki rika tambaya kina jina ko..?
Kai ta gyadamai ammah aranta tace Tab wannan matar muguwa din.
Afili kuma cewa tayi"Allah ya kiyaye hanya..!
Ya amsa da Amen yana kallonta kanta ya Dafa kafin yace'Allah yayi miki albarka..Na tafi sai in kuma na Dawo..!
Sai kuma taji kamar kar ya tafi yana mata Kirki na kwana Biyu wayarsa ya Dauka anan wajen kayan kallo ya Fice ta rakasa da kallo sai da ya Dade da Fita sannan ta koma ta Zauna da kudi a Hannunta tayi Tagumi haka kurum taji kamar kar ya tafi sai dai kuma taji Dadin da su Hanne zasu zo Dadi ya isheta.!
Shi kuma yana Fita Tasha ya wuce Direct Allah ya taimakesa ya samu Motar kano ta kusa cika ita ya shiga kuma Motar nada Lafiya sun yi gudu kuma koda biyar tayi yana Filin Jirgin Aminu kano,bayan yayi sallah ne ya kunna wayarsa ya Kira Hajiya..

******

Hajiya na Cikin Bedroom dinta tana Duba littafin 40 Rabbana Hanne na Tsaye awajen Wardrope dinta tana gyara mata kayanta Jiya mai wanki da guga ya kawo wayar Hajiya Dake kan madubi ta fara kuka alamun kira Hanne tafi kusa da wayar yasa Hajiya tace ta miko mata.
Tana Dauko wayar tace"La Hajiya ya Danmaallam ke kiranki..!
Hajiya ta ijiye abunda ke hannunta kafin tace"To ya natsa kenan tunda ya kira..!
Bata Tsaya Duba lambar ba ta Daga Kiran Lokaci Daya tana amsamai Sallamarsa cikin Sanyinsa ya gaisheta ta amsa tana Fadin"Kun sauka lafiya..?Mallam nata kiran ka bai samu ba Nima har da Safe na gwada layinka nachan ban samu ba..!
Cikin Taushinsa yace"Hajiya ai ban tafi ba..Sai yau ne zamu tafi jirgimu zai tashi da karfe takwas na Dare. !
Hajiya ta Bude baki kafin ta Dago wayanta tana kallon Lamba sai Lokacin ta Lura lambarsa ta nan ne saboda ta chan Danmallam2 ta sakamai.
Cikin mamaki tace"Ikon Allah to meya faru ba wanda yaji labari don ko da Safe Jafar ya shigo nan nake tambayansa yace shima bai samu wayarka ba..!
Umar yace"Matsalan hazo ne Hajiya shiyasa tafiyar bata yuyuba aranar..!
Hajiya tace"To Allah yasan hakan shi yafi Zama alheri..!
Ya amsa mata da Ameen kafin yayi shuru itama jinsa shuru yasa bata yi mgana ba sai da taga bai da niyar mgana sannan tace"Danmallam lafiya kuwa..?ka kira kuma kayi shuru..?
Ya sosa kansa kafin yace"Hajiya ina Filin jirgi kanon tun dazu..!
Hajiya tace"Madallah Allah ya Tsare..ya wajen su Aminar ina Fatan Lafiya ko..?
Cikin Kasa da Murya yace"Suna lafiya Hajiya..Daman zence ne in ba Damuwa Hannatu da Hamida su tafi yanzu su je su zauna da ita gidan ba kowa..!
Hajiya tace"Bangane ba kowa ba Sakinar fa..?
Kai Tsaye yace"Bata nan Hajiya..!
Bata Damu da tace ina taje ba tace"Allah ya kyauta..To yammh tayi kuma mallam baya gida sannan Gobe jumma'a suna da makaranta Danmallam..
Kai Tsaye yace"Hajiya kiyi hakuri su bar makarantar ta gobe su je su kwanan mata Biyu..In sakina ta Dawo Shikenan sai su dawo gida..kinga tayi kankanta da Zama ita kadai.. sannan ita ma Ranar monday sai ta fara zuwa makarantar..!
Hajiya tace"Shikenan bari na Tura su yanzu Daman na bari ne sai Asabar sai su hakura da Haddar su je mata tunda kuma ga wannan laluran bari na nemi ko Uzairu ne ya kai su sabod maallam da idi ya fita..!
Danmmallam yace"Uzairu ya Dawo ne..?
Hajiya tace"Eh jiya ya Dawo..!
Kai Tsaye yace"Hajiya ki basu keys din gidanan su tafi dashi..!.
Hajiya bata da bin Diddigi kai Tsaye tace shikenan daganan sukayi sallama ta bisa da Fatan isa Lafiya..tana gama wayar Hanne data kasa kunni taji ta cikin jin Dadi tace'Hajiya wajen Amina zamu..?
Hajiya ta mike tana fadin"Eh da naso sai jibi ne ammh yace kuje yau sakinar bata nan..!.
Hanne ta Daka Tsalle tana Murna Hajiyw tace"Daman na gama Hadamata komai jiya ma kinsan a kawo Dinkunanta da mallam yayi mata Sabbi yanzu shiga gidan Sa"idu kice ma Balaraba zaku wajen Amina in tana sako ta bada..!
Ai da gudu Hanne ta fita Tana murna Hajiya kuma ta fara Hadaa Sabbin kayan da mallam ya Dinkama Amina kala goma da Hijabai sai ita kuma ta mata Turaran wuta da Humra sai Dambun nama dasu Samosa duk an yi package dinsu sai kamshin girki kala kala har da curry har da su Cake sannan ta Siya mata Sabbin panta da sikat da Vest.
Ba jimawa sai ga Hamida da Hanne kamar bakinsu zai Tsage saboda murna Hamida ta Dauko kayanta kala Biyu Hanne ta bama Hajiya Turaran Tsinke guda Daya a ledansa wai inji mamanmu akai ma Amina..
Hajiya mamaki ya kamata ko jiyan nan Sa"idu ya sake fadaa mata ya bama Balaraba kudi ta yi ma Amina siyayyan abun Bukata shiyasa ta aika mata ammh sai taga wannan abu haka..?
Abun ya bata mamaki ace wajen Amina fa za"aje koda Sa"idu bai ce ya bata kudi ba ta Dauka kayan da zata Hadama Amina sai yafi ma wanda ta Hadamata ammh sai bata saka kokonto aranta ba ta barshi a kila bata siyan mata bane tukunah sai Daga baya..!
Hajiya batace komai ba ta Hada Cikin kayan sannan ta Dauko musu keys din gidan ta basu sannan tace Hanne ta Diban ma Amina sinasir din da sukayi da Miya su kai mata jiki na rawa suka Diban mata a coolers suka saka miya Dabam sai murna suke yi Hajiya ta Jaddada musu ranar? Lahadi idi zai Zo ya Daukesu sannan taja kunnensu da su natsu da sakon su gaida Amina..bata yi gaban kanta ba sai da ta kira mallam sukayi mgana da Farko cewa yayi"Hajiya yara nan su kadai agida kina ganin zai yuyu.?
Kodai Aminar ta dawo gida kawai har Sakinar ta dawo..!
Hajiya tace"Hakan ba

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login