Showing 42001 words to 45000 words out of 265571 words

Chapter 15 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28903

ta maida get din ta Rufe suna Shashen ya jafar ne suna ta Hayaniya amaran Dayake Duka yan"uwan Hajiya daga Maiguduru ne sukayi musu Lalle da Kitso da kuma gyaran jiki nan suke kwana Anty Shamsiya yau chan gida zasu kwana ita da Fadila.
Daganan da suka fito sai da suka kusa gida suka Daina gudu suka Duka suna Hutawa Amina ta Dago tana Haki tace"Ya Abidar nan muguwar yar bakin ciki ce..!
Ta hanamu shiga mu gani ance ana ta mu su gyaran Amare..!
Hanne tace"Eh su yakura ne fa suma tun ranar da sukazo hajiya ta turosu nan..!
Amina tace"Ai dai zamu gansu gobe duk Tsiyanta nifa daman tunda naji muryanta nasan sai ta bamu mtsala..!
Zafira tace"bata da kirki ne..?
Amina ce"Ko kadan..Bata da mutumci ya Abida kina ganinta haka..!
Gabadayansu dariya suka saka Amina ta Cigaba da Fadin"Ke kinga gidansu Hanne..?Kaf ba mai mutumci yasin..!
Hamida tace"Kai Amina ga ya D'anmalam ai bai taba Dukanmu ba..!
Amina tayi jim kafin tace"Shi kuma wannan dama dukan yake yi da Mganarsa..!
Hanne da Hamida suka Kalli juna suna Danne Dariya Amina ta gansu ta Hararesu tana Fadin"Munafukai..!
Zafira tace"Me ya faru ki bani labari..?
Da Sauri Amina tace"Wlh kuka Fada mata sai nayi muku Rashin Mutumci..!
Dariya suka kara saka mata ta kwalo musu ido Zafira na magiyan su Fada mata Amina ta Faki idonsu tace"Wayyo bayanku maciji..!
Ai bata gama Rufe baki ba suka Zura aguje tabi bayansu tana Dariya.
Allah ya taimakesu sanda suka Dawo an shiga Sallar mangariba sai suka Lallaba suka Shige gidan Baba Malam.
Shashen Hajiya ba waje duk ya cika duk da wasu suna Kitchen din gidan suna ta soyan kaji su da su Baba Lami yan aikin gidan.
Karsahenta dai Shashen Hajiya uwa suka Shige sukayi salla adakinta ita bata ma nan tana Shashen Hajiya taje suna mgana..
Sallar kadai sukayi suka Fito su leka chan su leka chan har shashen Anty Amarya sai da Amina tace suje saboda tana son ta kara ganin gulma
Akwai suna shiga suka iske Sakina da Sarood zaune kugu Daya Jidda na Kan Cafet tana ta Hada Turaran wuta da Sabulun Salo cikin wasu kananun Robobi ita da wasu Daga cikin Dangin Anty Amarya..basu ga Sa"adatu ba bata nan tatafi kunshi an samu Sake.
Hanne ne kadai da Hamida suka gaida su Sakina banda Amina Data yi keme keme Anty Amaryan bata Falon.
Anty Sarood ta ganesu tana ta yi musu Mirmishi.
Sakina taga Amina na wani kallonsu Daya Daya yasa tace"Ke..Baki da kunya ko..?
Baki iya gaisuwa bane..?
Amina ta yamutsa Fuska kafin tace"Na gaisheku..!
Sakina tace"Karya kike..Hanne kadai da Hamida suka gaishemu da wannan yarinyar..!
Ta fada tana nuna Zafira.
Amina ta Tura baki batayi mgana ba Jidda ta dago tana kallonta Kafin tace"Wai Amina daman baki daina wannan Rashin ta idon ba ko..?ko ni ai baki gaisheni ba..?
Amina ta yi wani jim kafin tace"Ina yininku..!
Daga haka ta juya tana Jan hannun ZAafira Dake kusa da ita.
Sakina ta rike baki kafin tace"'Yarinyar nan bata da kunya..!
Amina na kunkuni tace"Eh din ai na gaisheki tunda kuma ba Duka miki zan yi ba..!
Da karfi tayi suna ji ta fice Jidda ta girgiza kai tana Fadin"Kamar ba yar gidan Baba Sa"iduba kaf ya"yan gidanan ta fita zakka..Allah ya shirya..!
Sakina batayi mgana ba baki kawai ta Tabe ta juya tana ma Sarood mgana Wacce ta maida hankalinta Sakina na jin Labaraci tun anan balle kuma Da suka koma chan Zama da Larabawan yasa yaran ya zauna mata sosai.
Kitchen suka shiga suna neman abinci sun samu Jallop din shibkafa da aka Dafa da Rana.
Amina idonta na kan manya manyan Baho cike da Naman kaza da Naman rago duk am soya Amina da nama Tuni Ranta ya biya.
Akitchen din sukaci abinci suna cikin ci Amina tayi ma Hanne Rada"Yasin sai na saci naman chan..!
Hanne tace"In aka kamamu fa..!
Amina tace"Dillah bamai ganinmu..!
Har suka gama cin abinci Amina na Tunanim mafita Su baba Lami na Kitchen da sauran mutane suna ta aiki kowa Hankalinsu baya kansu Anty Nasara ce ta shigo ta gansu yasa tace"Me kukeyi a kitchen..?
Kuje waje mana ku sha iska..!
Dole suka fice Hanne nama Amina Dariya ita kuma tayi Fuska
Shashen Hajiya suka koma suka samu chan gefe suka zauna bama wanda ya Lura dasu Amina aranta tana Takaichun yadda in ana sha"ani bamai bi ta kansu aranta tace ai suma sun girma sun wuce yara yanzu.
Suna nan har akayi sallar Isha"i suka tashi sukayi salla.
Sai alokacim Hajiya ta gansu tace"kuna nan ashe..?na zata kuna gidan Sa"idu ne..!
Hanne tace"Tun dazu muna nan..!
Tana Sauri ne ana mata mgana yasa ta wucesu Amina tace"Kowa baya bi ta kanmu..!
Hamida tace"Wlh fa kallemu kamar wasu almajirai..!
Amina tayi dariya kafin tace"Almajiran ne mana duk inda mukaje ana koranmu..!
Hanne ce ta ma Amina Rada a kunne tana Fadin"Kin fasa satan naman ne..?
Amina tace"A"a
Ku tashi muje..!
Haka suka sake ficewa Kitchen din Amina ta leka taga ba kowa sai su Baba lami su kuma suna ta Hidiman yanka Albasa suna Hira Amina ta yafito hanne tana Fadin"Ku tafi daga chan..Ni zan shiga na Debo mana zan taho..!
Hanne ta mika mata wata bakar Leda Data Dauko daga Dakin Hajiya tace"Zubo mana anan..!
Zafira ce tazo zatayi mgana Amina ta mata alaman tayi shuru Hanne ta mata rada tana fadin"Ke nama Amina zata sato mana..!
Zafira tace"Yauwa daman wlh tun dazu miyauna ya tsinke..!
Amina ta Sadada ta shiga kitchen din ta Duka ta Bude ledan ne ta rika Zuba Nama Har sai da ta Kusa Cika Hanne da Zafira suna daga bakin kitchen din suka hango Anty Amarya zuwa da Sauri Hanne tace"Amina Ga Anty Amarya nan ki taso..!
Jin haka yasa ta taso da gudu su kuma sun riga sun ruga har tana bangaje Anty Amarya,Da tayi baya tana Fadin"Ke ke..Waye anan..!
Ina Amina bata tsaya ba sai Aharaban gidan inda su Hanne ke jiransu Anty Amarya bata ga Fuskar Amina ba.
Ta shiga kitchen tana yi ma su Lami Fadan suna barin yara na Shigowa.
Haraban gidan akwai haske tunda an kunna Gen yasa Amina ta jasu suka shige wani dan lungu Dake Wajen kofar Shiga Shashen mallan da dan Duhu kadan suka ZAuna Amina ta Fito da Naman Hamida ta zaro ido tace"Amina kin Debo da yawa in aka gane fa..?
Amina ta tura wani nama bakinta Tunda naman sa ta Debo na kajin suna kusa da Baba lami yau gidan Gonar Baba malam yasha Diban kaji da Shanaye.
Sai da ta cika bakinta sannan tace"Dillah kefa kin cika tsoro..Abu da yawa wazai gane..?
Zafira ta mika hannu zata Diba Amina ta make hannunta tana Fadin"Kada ki samin hannu ko na Hanaki wlh..!
Jin haka yasa ta Dakata Amina ta Dauki Tsoka Hudu hudu ta basu Ta bama Hanne Biyar ta Dauki Sauran tana Fadin"Mai sata ke da wannan..!
Hamida tace"Kai Amina naki yafi yawa..
Amina ta balla mata Harara tana Fadin"To Sarkin korafi..Dayake ke kika je kika Debo naman..!
To wannan ma in baki so bani kayana..!
Tafada tana mika mata hannu Hanne tayi Saurin cewa"Hamida karbi abunki..Mun ji Amina tunda ke kika Debo Dauki wannan..!.
Amina ta murguda baki kafin tace"ko baku yarda bama..In mutum yaji Haushi yaje ya Debo nasa. !
Hamida tasan da ita take yi ammh bata tankata ba suna cin namansu Zafira ke fadin"Wai shanaye nawa aka yanka da kaji..!
Duk gidajen nan fa akwai Nama ko"ina ka shiga. !.
Amina tace"Waya sani Zafira..?kila sun kai dubu kajin Shanayen kuma kila goma..!
Tafada tana Tura naman bakinta Hamida tace"Haba inaga ma sun fi..Kinsan in ana Biki haka ake ta Yankosu ana shigowa dasu..!
Zafira tace'Cab...ai gidan Gonar ta kare..!
Amina tace"Ke..kina da Hankali kuwa..?Kinsan adadin Dabbobin Dake gidan gonar nan ta baba malam..?
Ke babban waje ne fa na taba gani a Wayar Ya jafar da yazo yana nuna ma su Mamanmu na rantse da wanda Raina ke hannunsa gari guda ne..!
Hanne ta karbe da cewa"To yaushe zamu je mu gani..?bamu taba zuwa ba..?
Amina tace"Kuma fa hakane..?to ammh Aba chan yake zama fa..?ya zamu yi mu je chan Hadeja Road ne fa..?
Hamida tace"Nidai ba ruwana..!
Amina tace"Sai me..?ke dai kin cika Tsoro..Hanne bari nayi shawara na Rantse koda bala'i sai mun je mun gani ko da zamu dawo a yankamu ne..!
Hanne tace"A"a fa ni wasa nakeyi..!
Amina tace"Ke fa sai an je..Inaga ma gobe saboda bama wanda ya Damu damu..!
Hanne zatayi mgana kenan sukaji mgana a kofar Falon Baba maallam gabadayansu suka Leka suna ganin Ya Uzairu ne ya fito Daga Falon mallam din Bayansa ya Shamsu ne sun saka Takalmansu sun nufi barayin da Dakumansu suke
Amina ta juyo tana Fadin"Jaruba..Daman ya Uzairu ya Dawo ne..?
Hanne tace"Eh mana tare suka zo da Ya Zulfa..!
Amina tace"Harda Ya Nazem..?
Wannan karon Hamida ce tace"A"a shi naji Ya Zahra na fadin sai gobe yace zai taho yana da Karatu gobe..!
Amina tace"Mugayen gidan.com zasu Taru Lokaci Daya bala"i..!
Hanne tana Danne Dariyanta take Fadin"Har na tuna ya Nazeem sanda ya miki Dukan Tsiya Lokacin muna aji hudu kin Tuna. ?
Amina tace"Kan bala"i ina zan mata..Ranar ai mariya na Tsungula ya kamani Shine ya fitar dani gaban aji kusan awa daya nasha ya manta dani ne na Daga Murya nace Tattasan da ka shanya ya isa Bushewa sai kazo ka kwashe..!
Gabadayansu suka saka Dariya Hamida tace"Kin ga kwashewa kuwa..Amina kin Daku fa hannu. Ya Nazeem..!
Amina ta Ciji yatsa Kafin tace"Kuma Wlh har yanzu ban yafe ba Wuta bal bal har kabarinsa..!

"kai su waye anan..?

Mganarta ta Katse ne sanda aka Dallaresu da Filita Lokaci Daya da mgana suka Tsorata gabadayansu sukayi Tsumu Tsumi.
Ya Uzairu ne zai fita shago ya Siyo katu yaji mgana daga bayan shine ya Haskasu da wayarsa.
Karisawa yayi gabansu yana kallonsu Daya bayan Daya ya ganesu mamaki ya kamashi me suke anan..?
Cikin Tsawa yace"Su waye anan..?
Hanne ce baki na rawa tace"Mune ya Uzairu..!
Amina kuma namanta take kullewa a leda yace"Ke miye wannan..?
Daidai Lokacin da su ya jafar suka fito daga Falon Baba Malam daman tun Fitowarsu masallacin Sallar isha"i suka Dumgumo suka shigo.
Bayansa Ya Nasir ne sai ya Da'nmalam Daya fito Daga karshe.
Jin mganar ya uzairu yasa Ya jafar Daya sanya Takalminsa yake fadin"Kai Uzairu lafiya..?kai da su waye..?
Juyowa yayi yana fadin"Wlh yaya zan wuce naje siyan kati naji mgana ta nan ina Haskawa naga yaranan bansan Uban da sukeyi anan lungun ba Cikin Duhu..!
Dukkansu matsowa sukayi shi da Ya Nasir banda Ya Danmallan Dake gefe yana Danna Wayarsa.
Gabadayansu suka Haskesu da Fitulan wayarsu Ya Nasir yace"Lalle nema yaranan to ku fito don kaniyanku..!
Ba musu suka mike suka firfito Amina ce ta karshe tana Boye abunda ke hannunta ya Uzairu ya jawota yana Fadin"Bani abunda kike Boyewa..?
Baki ta Tura kafin tace"Bafa kom..!
Bata karisa ba ya make bakinta yana Fadin"Bani kafin nayi kasa kasa Dake mara kunya..!
Hannunta Dafe da baki da mikamai ya karba Daidai sanda Ya Jafar ke fadin"Me kuke yi anan da Daddaran nan..?
Gabadayansu sun kasa mgana Ya Nassir ya fara Duba bayansa yana Fadin"Inaga sai sun ji ajikinsu..Kai shamsu Dubamin Sanda don Allah..!
Ya karishe Fada da karfin daya Janyo Hankalin D'anmallan kansu ya Zura wayarsa gaban Aljihun farin yadin dake jikinsa Riga da wando.
Shamsu Daman tun farko ya fito jin haka yasa ya shiga Dakinsu ya Fito da wata Bulala mai kyau katuwa da ita ta duka yaran mutane A islamiya
Ai Hanne da Hamida na ganin ya mikoma ya Nasir har ya Fara Nade Hannun riga suka Duka harda Zafira Data fara fadin"Wlh ba komai..!
Sai kuka ya Uzairu ya Bude ledan sai ga Nama da Sauri yace"Ya jafar nama ne aledan nan..?
Gabadayansu suka ce Nama..?
Cikin mamaki Har da ya D'anmallan Daya kariso wajen basu sani ba.
Da Sauri zafira tace"Eh nama ne..Dama Dama..Amina ce ta sato a Kitchen shime muka zo nan ta san mana muna ci ammh Wlh bamu yi komai ba..Amina ce ko Hamida..?
Hamida da Hanne sun kasa mgana Amina na Tsaye ko gizau.
Ya Jafar yace"ai ta saba indai Satan Nama ce..Amina ta saba..!
Ya D'anmallan sai Lokacin ya Fahimci mganar ya kuma kare ma su Amina Dake wajen kallon idonsa ya Fada kanta yadda take wani Juya ido.
Aransa yace"Again..?satan nama..?
Meke damun yarinyar nan..?
Ya Nasir ya kalli Amina yana Fadin"Anan gidan ne kike mana Satan nama..?kin ce abaki an hanaki ne..?
Ya karishe fada cikin Tsawar dayasa Baba Mallam da Aba Dake cikin Falon zaune suna mgana sai da sukaji.
Amina kuwa baki ta Murguda kafin tace"Ni ba barauniya bace..Ba sata nayi ba..!
Ya Nasir yaga sanda ta mai haka yasa ya Daga Bulalar ya Shimfida mata yana Fadin"Karya zan miki..?kuma ni kike juyama baki zaki gane yarinya kwana Biyu jikinki na kaikayi..!
Ya Jafar yace"Dake ta shegiya bakinta baya mutuwa..!
Amina ko ko gizau ya kara Lafta mata wannan karan da karfi tace"Ai ba Sata nayi ba..ni ba barauniya bace..!
Dukanta yake tana mgana su Hanne sun koma gefe har sun fara Hawaye..
Ya Danmallam mamakin Taurin ran yarinyar yake ganin da Har yanzu ko Dukawa batayi ba kuma bakinta bai Daina mgana ba
Su ya shamsu na gefe suna Dariya.
Ya Danmallam yaga dukan yayi yawa yasa yace"Kai Nazir bar dukanta hakanan mana..!
Ya Jafar yace"Ka bari ya Daketa baka ga bata da kunya ba ai tare sukayi Laifin da yan"uwanta meya su ba"a Dake su ba..!
Sai ya kasa mgana Idanuwanta yake kallo ko kwallah basu Tara ba kuma bata tare dukan ba,Idonta kyam ba ko alamin nadama ballatana ta bada Hakuri.
Yana auna Shekarunta ne har ya isa ta Zama kangararriya irin haka..?
Yana cikin wannan Tunanin yaji mganar Baba Malam a sama yana Fadin"Kai kai Nasiru..Kaga naka nan..?ka samu jaka ne dake dukanta kamar ka samu namiji Dan"uwanka..?
Sai Lokacin suka Lura dasu shi da Aba suna Tsaye ran Malam ya baci da azama ya kariso wajen Har Alkyabban Dake jikinsa na neman Rinjayansa.
Gaban Nasir ya tsaya ya Fizge Bulalar yana Fadin"Sau nawa zan gaya muku ba kyau Horo da duka..?Wlh???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? banta Hora ku da duka ba sai Nasiha mai yasa kuma bazaku yi haka ba..?
Ya nasir kansa na kasa yace"Baba ra..!
Hannu ya Dagamai Lokaci daya yana Fadin"Bana son jin komai..Bana son Sarkaci kai Umar agabanka suka Tasa yarinya karama da duka baka Tsawatar musu ba..!
Danmallam ma ya kasa mgana Dakyar yace"Kayi hakuri Baba..!
Aba Dake gefe yace"Baba da barsu sun mata Hukunci Amina ce..Amina ai bata jin mganar kowa..!
Aran Danmallam yace"Kenan ta gagara..!
Baba Mallam ya Dagamai hannu yana Fadin"Kaima ka fita idona Sa"idu..!
Jin haka yasa suka fara basa Hakuri ko kallonsu bai yi ba ya Juya ga Amina Data ga Baba mallan ta fashe da kuka Tana Fadin"Ce min fa yayi barauniya Baba..Ni kuma bana sata Daga na Diba naama shikenan..!
Baba malam ya rikota yana Fadin"Bai kyauta ba..Mamata ai ba ta sata..Kuma naman da kika Diba ai na Gidanku ne ba wanda ya isa ya hanaki daina kuka Share hawayenki kinji..!
Yana Fada yana goge mata Hawaye Ya Danmalam mamaki ya cikasa ya Tabbata ko cikin kannensa bai taba ganin Baba mallan yayi ma wata haka ba..Kenan ita wannan Dabam take.?
Su ya jafar ko basu yi mamaki ba sunsaba ganin haka.
Har su hannen haka ya taso su ya Damka musu Amina yana Fadin ku shiga Cikin gida..!
Amina tace"Gidanmu muke kwana nan ya cika..!
Baba mallam ya kalli su shamsu kafin yace"Ku rakasu sai kun tabbatar da sun shiga gida kana ku dawo..!
Hakanan basu so ba suka tasa su Amina suka rakasu gida ya shamsu kam harda Tsaraban rankwashi.
Baba malam bai Tsaya Sauraran ban Hakurin su ya jafar ba ya koma Falobsa Ransa bace.
Aba ya Sauke Numfashi yana Fadin"Ku tafi gidajenku..Yau baba malam ransa ya baci..An taba Amina..!
Ba wanda yayi musu suka juya wajen Motocinsu ya Danmallam dai na tsaye aransa yana ayyana wasu abubuwa kafin ya Tabe baki kawai.


Don Allah mu ding yi ma junanmu Uzuri kusan hakan nan ba zan ki Typing ba sai da wani Dalili Biki naje bani agida sai jiya da yammah na Dawo bana cikin Natsuwar da zan iya Rubuta wani abu shiyasa aka samu Tsaiko..!





*Janafty*

*TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janaftyd'?*



*

Lallabawa sukayi suka shige Dakin da suke kwana suna jin Hayaniyar su ya Jaleela a chan Tsakar gida,da kuma Hayaniyar Mutane,Har alokacin suna Tsakar gidan suna kamallah aikin su.
Suna shiga Dakin Zafira ta yaye Hijabin Jikinta ta zauna Dabas kan Cafet din Dake Dakin ta Dago tana kallon Amina Dake Tsaye kyam takaicinta Daya yadda Ya Uzairu ya karbi Namanta bai bata ba Shi yafi kona mata zuciya ba Dukan Ya Nasir ba.
Zafira tace"Amina ke kam baki jin Duka ne..?
Amina ta wani kalleta a kaikace kafin tace"Me kika gani..?
Zafira tace"Gani nayi kina Tsaye sai Dukanki ake yi ko kiyi Tunanin Guduwa ma ballatana ki bada Hakuri..!
Hameda da gajiya yasa har ta kishingida tace"Tab Aminan ne zata bada Hakuri..!ai mutun Daya Amina na taba ganin ta bama Hakuri..!
Hanne na gefen ta ta karbe da Fadim"Yaya..Yaya ce kadai Amina ke bama Hakuri bayan ita ko Aba Tsayen nan take mai .Zuciyarta kamar ta Kafuran Farko..!
Zafira ta jinjina kai kafin tace"Tabdijam Haka kurum na zauna ayi ta Jifgana kamar wata Jaka..!
Amina ta Daga idonta Sama kafin tace"Duka ai baya kisa..Daya na kisa da Tuni ba Sauran Amina Zafira..Sannan mganar na bada Hakuri ma bai taso ba..Me nayi..?Amina bata bada Hakuri matukar tasan ita keda gaskiya..!
Zafira tace"Uhmm..Ko dai aljanu gareki. ?su suke saka ki wannan Taurin kan Amina..?
Amina ta mata kallon Tara sau ra kwata kafin tace"Sai dai in naki ne suka Dawo kaina yanzu .!
Da Sauri Zafira tace"Ni bani da Aljanu..!
Amina ta tari numfashinta tana Fadin"Nima haka..!
Daga haka ta samu chan Lungu Bayan ta Nanannde Hijabin jikinta tayi matashi Dakin ba Katifa Cafet ne kawai sai tarkacen kayansu da suka Kwaso zuwa nan baya ta juya musu aranta Allah ya isa kawai take antayama Ya Nasir da ya uzairu kafin ta Muskuta tana Fadin"Ai shima ba Zubar da naman zai yi ba ci zai yi..Wlh In na yafe Allah Tsinan..!
Suna jinta ba wanda ya tanka mata suna Hiransu sama sama Tsakaninsu Amina ko kala bata kara cewa ba tun tana jinsu sama sama,Har sanda Hanne tace"Naga fa ga Ya D'anmalam Dazu da su ya Nasir suka Turkemu..!
Hamida tace"Nima na gansa ammh bai yi mgana ba..!
Hanne tace"Baida Hayaniya ne..duk acikin Yan gidanmu yafi burgeni..!
Hamida tace"Gaskiya..!
Amina na jinsu batace komai ba Domin kwarjinsa ma ya isa yasa kakasa mai gaddama Dole ace baida Hayanjiya.
Har barci ya kwasheta ba ita ta farka ba sai da taji an Fara sallah Cikin Wata Zakin murya cikin Sanyi da Haiba Muryan Ya D'anmallam ne tunda ya Dawo Duka Khamsin Salawatun shi ke badawa ko da tatashi ta iske Hamida da Hanne na Sallah har da wasu ma yan gusai adakin suna Bin Jam'i.
Tashi tayi

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login