Showing 162001 words to 165000 words out of 265571 words

Chapter 55 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28896

kamar yana jinta ko yana ganinta.
Yanzu Ta rage tsoro tunda Tare da su Hamida take kwana sannan koda aka shiga Damina ko ana ruwa Tsakar Dare ba ruwanta tana makale bayan Hanne ko Hamida hanka??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????linta kwance.

A jidalinta kam babu abunda ta Rage sai Dambe ne kadai ta Daina ammh Fada a makaranta da siyan fada ko bada ita akeyi ba sai abunda yayi gaba Ballatana gata ga Hamida ga Hanne bata da wani Danuwa ranar ma A Hadda suka yi fada da Samira ta kan kujeran zama Amina ta mike ta Chakume Wuyan Hijabin Samira zata Jata da Dambe Mariya ta kada baki Tace Amina yanzu fa kin girma tunda ke matar aure ce wannan abun da kike yi bai kamata ba..Ku su hanne ku Fadamata gaskiya in zataji to..!
Amina sai taji ta Muzanta Ido ya Dawo kanta sai taji kamar ta Shake mariya ta kalleta ta murguda mata baki kafin tace"Ubanki na aura ammh ko..?
Wannan mganar yasa mariya ta kai kara wajen Mallam Datti akan Amina ta Zagi babanta Case din da sai da ya Jafar yazo makarantar mallam ya aikosa ya kashe mganar Tunda Mallam Dattin ya kira mallam awaya ya Fadamai.
Ranar ya Jafar yaso ya Daki Amina sai Mallam ya hana ya kuma yi musu gargadin? har Abada Amina ta wuce Duka awajensu..ko ba domin darajan auran Dake kanta ba Domin Darajan Danmallam Dake mijinta bazai ji Dadin su daketa ba in yaji Labari.
Ya kuma fada musu suma Amina Uzuri Amina har yanzu yarinya ce dole ya kyaleta ita kuma sai ya Bita da Nasiha tamai alkawarin Insha Allahu bazata kara ba,Daga dai ranar ta kulla Gaba da mariya sannan Sa"adatu ta sha Habaici kala kala Domin ita ta yada Labarin Hanne da Hamida su dai yan bada Hakuri ne Amina bama jin mganar su take yi ba suna dai bata Bakinsu ne.

Hajiya sun yi mgana dashi Danmallam din tana chan maiduguri yana so ya kara mata mgana? ammh kuma ya kasa ita kuma tana Sane ta bari ne sai ta Dawo tamai bayanin abunda mallam yace.
Har Haj.uwa sai da ta Fadamawa itama tace shawaran mallam tayi saboda Kada a rabama Amina hankali Daga karatunta,aranta kuma Tana Tunanin meyasa Danmallan ya Damu da Amina alhalin kowa yasan wannan auran ga yadda yazo sai dai ta kasa sanun amsa.

Sati Daya Hajiya sukayi Idi yaje ya Daukosu suka Dawo Mamanmu kuma sai da tayi kwana goma sannan ta Dawo Amina kuma Hajiya na Dawowa ta Tattara ta riga komawa gidanta tana kwana sai su hadu da Sakina ammh basa ma juna mgana Sakina gabadaya Tsanar Amina take ji Saboda gani take yi komai ya Faru ita ce sila Anty Amarya tace ta cika gajen Hakuri ta Daina kiranta in bata da mgana mai Dadi Ita kanta Anty Amarya a Rude take abubuwa duk sun shagule mata Tafiyar mamanmu Gusai sun hadu a Dutse sun koma wajen malamaminsu ya Tabbatar musu da cewa Umar zai dawo ya tafi da Sakina Sannan Burinta zai cika itama mamanmu ya Fadamata Sa"idu na hannunta sai abunda tace suka Zubemai makudan kudi Anty Amarya ta koma Gumel ita kuma ta koma Gusai saboda kada a Fahimci Tafiyarsu Daya.

********

Umar sunyi mgana da Sarood itama ta yarda kila shafan Aljanun ne suka fara amfani da mganin da ya siyo mata a Islamic Chamet na irin abunda suke Hasashe shima ta bangaransa ya Dake? da Addu"a ammh bai kara Jaraba kusartar ta ba ya bari sai ta gama amfani da mganin sannan.








*Janafty*


*TFZB2011*

*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488*


Bayan Sati daya da dawowar su Hajiya Daga maiduguri Ranar wata lahadi da misalin karfe goma na Safe sai ga Aliyu a falonta Danmallam ya aikosa tun daga Dutse har gumel wajen Amina.
Hajiya mamaki ya cikata Lokacin da Ta fito falo suka gaisa da Aliyu yake sanar da ita yazo neman Amina ne mamaki bai bar Fuskar Hajiya Babba ba ta kalli Aliyu Dake zube saman Cafet din falon nata kansa a kasa cikin ladadinsa kamar abokin nasa
Sai da ta gyara zama kafin tace"Amina..?
Cikin sigar mamaki kansa na kasa yace"Eh Hajiya..Yace nazo ne na kawo mata waya yana so zasu yi mgana..
Hajiya tayi wani kayattacen mirmishin su irin na manya kafin tace"To ban da abun Danmallan don wannan sai ya Tadoka tunda ga Dutse har Gumel..haka ake yi..?
Ai da ya kirani sai na basa Aminar suyi mgana sannan ni nace zan kirasa nayi mai bayanin yadda mukayi da mallam kan wayar da jafar ya kawomin sai na manta zuwana Bikin nan sannan da na dawo ma ban zauna ba Sabga tayi yawa..!
Aliyu kansa a kasa bai ce komai ba shima so yake ya gama da Hajiyar ya fita ya Tsitsiye Shehi yaji Dalilin sa na neman yarinyar daya gama Cema kwaila kazama.
Hajiya tacigaba da Fadin"Tashi ka tafi abunka Aliyu Amina bata nan suna Hadda Yau ma inaga da wuri zasu dawo Saboda hutu zasu yi sun fara Jarabawar tun awanchan satin ne In ya kiraka ka Fadamai ya kirani muyi mgana..!
Aliyu kansa na kasa ya mike yana Fadin"Shikenan Hajiya Allah ya kara girma mungode..!
Ta amsa da Ameen da Fatan ya gaida iyalansa daganan ya fice zuwa shashen maallam yamai sallama suka Hade da Anty Amarya ya gaisheta cikin Ladabi ta amsa tana kallonsa cikin mamakin ganinsa da Safe haka sai dai bata Tsawaita mamakinta ba Sanin Aliyun yana zuwa gaida Hajiya da mallam Lokaci bayan Lokaci koda Danmallam din baya kasar
Shashen mallam ya koma yamai sallama zai koma domin nan ya fara shiga suka gaisa bai dai zauna bane ganinsa suna mgana da Aba yace bari ya shiga ciki ya gaida Hajiya Mallam bai kawo ma kansa shima wani abu ya kawo Aliyu ba sanin Yadda yake Darajasu Dalilin kawai suna iyayen Abokinsa Umar.
Sallama sukayi yana ta sakamai albarka da Fatan Allah ya kaisa gida Lafiya kiran Danmallam bai shigomai ba sai da ya bar Gumel ya dau hanyar Dutse Gefen titi ya samu yayi fakin sannan ya Daga kiran nasa Daga chan bangaran Danmallan yayi mai sallama kamar yadda kowa yasan shi da zarar ya Dauki waya da sallama itace Farko a bakinsa
Aliyu bai wani amsa sallamarsa ba yace"Shehi wai miye sirrin ne..?
Umar yace"Sirrin na mene..?
Aliyu yace"To gani nayi ka bi ka Rude kan karamar yarinya sa"ar yarka ta Fari kuma kwaila..kuma kazama ka tadani Tundaga Dutse zuwa gumel haka Hajiya ma ta Dinga mamakin wannan aikin naka..!
Umar ya Dafe kansa dagachan bangaran kafin yace"meyasa ka bari kuka Hadu da Hajiya..?
Aliyu yace"Dole kuwa mu hadu don Daga Falon mallam shashenta naje neman Amina ta tabbatar min da batanan suna makarantar Hadda..!
Umar yace"Kash..Da tace haka sai kayi Tahowarka ba sai ka fadamata Dalilin zuwanka ba..!
Aliyu yayi wata Dariya kafin yace"Ai aikin gama ya riga ya gamu Shehi tuni na Rattafamata komai tace in munyi mgana Dakai na sanar maka ka kirata zaku yi mgana .!
Umar yayi shuru kafin yace"Kai dai baka da biyan Bukata duk ka bata komai ni fa kunyarta nake ji shiyasa ban kirata ba ita da mallam..!
Aliyu yace"Oho zakace haka mana Tunda na gama Biya ma Bukata akwai ai watarana ba agama ba..!
Umar yace"Naji bakomai dai nagode zan kirata yanzu..!
Aliyu yace"Ni fa baka Fadamin sirrin ba..!
Umar yace"Wani sirrin kenan..?
Aliyu na Dariya yace"Sirrin abunda ya susuta ka kan Aminatu mana..!
Umar ya saki karamin Tsaki kafin yace"bansani ba..!
Aliyu ya saka Dariya kafin yace"To to..Nagano Sirrin ma..Shiyasa jiya daka kirani bakace min wannan kazamar yarinyar ba kai Tsaye ka kira sunanta Tabbas yanzu ta tashi Daga kazama kwaila ta koma Sweet Amina..Ko Honey ce..?
Umar ya tsaki again kafin yace"Kai fa Dan iska ne..!
Daga haka ya Datse kiran Aliyu yabi wayarsa da kallo yana Dariya sosai in ya Tuna sanda aka aurama Umar Amina yana ta fada yar cikinsa ne ina zai kaita sai gashi kaji sa shuru ya shiga komar yara ya kasa sukuni.
Duk da yayi matukar mamakin yadda Komai ya faru Tsakanin Amina da Shehi sai dai bai Tsananta ba Sanin Tsakanin miji da mata sai Allah ammh Shehi ya bani a wajensa ya Dinga Tsokanarsa kenan.
Yana Mirmishin ya Tada motarsa ya bi hanya yana kara Dariyan Abokin nasa yana kuma Fatan yasa Amina ta mai mugun kamun da sai ya raina kansa.!

Bayan Tafiyar Aliyu Hajiya tayi ta Tunanin me yasa Danmallan ke son mgana da Amina haka da har ya kasa Hakuri..? Bata samu amsar ta ba sai tayi Tunanin kila yana so yaji Lafiyanta ne sannan ya tambayeta ko tana Bukatar wani abu daganan ta watsar da Tunanin ta koma Bedroom dinta tana gyarawa ba Dadewa ta samu kira Daga Danmallam bayan ta Dauka sumgaisa kamar yadda suka Saba sai kuma yayi Shuru yana jin kunyar yayi mata mgana ta san Halinsa Tunda ita ta Haifesa.
Yasa ta gyara Zama tana fadin"Dazu Aliyu abokin ka yazo..akan kai ka aikosa ya kawo ma Amina waya zaku yi mgana ko.?
Dakyar ya iya amsa ma Hajiya gani yake kamar zata Fahimci abunda ya Faru Tsakaninsa da Aminar.
Cikin Dattakonta ta cigaba da fadin"To nace yayi tafiyarsa Sabgoginsa ka taso mutum Tunda ga nisan Duniya Danmallam..! Ai sai ka Kirani muyi mgana ko ba Haka ba.?
Kai tsaye yace mata"Kiyi hakuri Hajiya..
Cikin Ladabinsa bata Damu ba tace"Ni ba laifi kamin ba..gani nayi ka basa wahala..Daman ina ta so na kira ka nayi maka bayanin Dalilin Dayasa ban bana Amina wayar nan ba duk da ni nace ka siya mata mgana mukayi da mallam ya nuna min Rike waya ga Amina yayi sauri sannan Duba da har yanzu akwai kuruciya a tare da ita..hakan zai Dauke Hankalinta har ya Taba karatunta da muke Fata ta Samu,ya nuna min na bari sai zuwa gaba in kazo ka tafi da itan sai ka siya mata wayar Lokacin tana gabanka zaka kula da Motsinta yanzu kuma ya nuna min gaskiya a"a shiyasa kaji Shuru ban bata wayar ba tana nan na ijiyeta..!
Cikin gamsuwa da mganar ta yace"Hakane Hajiya..!
Hajiya tace"To kaji yadda mukayi da mallam da Dalilin dayasa kaji shuru..Sannan yace in kana son jin Lafiyarta ne ka kirani ko mallam din sai in ta na nan sai abata ku gaisa..!
Danmallam yace"Shikenan Hajiya Allah ya kara girma..!
Hajiya ta amsa da Ameen kafin tace"suna Hadda ammah ina ga bazasu Dade ba in sun Dawo zan kiraka sai na Hadaku..!
Cikin Ladabinsa ya shiga Fadin"Allah yasa agama Lafiya Hajiya Allah ya kara Nisan kwana..!
Ta amsa da Ameen suka rabu bayan ta Tambayi Iyalansa da ayyukansa.
To sun ma gama wayar ba Dadewa wajen azahar sai ga su Aminan sun Dawo suna ta Murna an basu Hutun Sati ukun Dadinsu Daya gobe zasu fara Exam din second Semister a makarantar boko satin daya gabata Gabadaya Revision sukayi.
Amina ke fadin Dama islamiya ma ta bata da Hutu ai da sun ji Dadi.
Ba"a basu Sakamakon su ba sai Sun dawo Hutu sannan.
Anan Shashen Hajiya sukayi sallah Sukaci abinci Hajiya na ciki bata san Amina da Hamida sun koma gida ba Tana zuci zucin ta Kirata sai ta Kira Danmallam din ta Hadasu ko da ta Fito sai Hanne kawai ta gani a Falo ita ke Fada mata Su Amina sun tafi gida kai Tsaye tace Hanne taje ta kira mata Aminar.
Hanne ta mike ta saka Hijabi ta tafi tana zuwa ta iske su acikin Dakinsu har Amina ta kwanta bata ga mamanmu ba tana cikin Dakinta ta kwanta in ji Hamida jawaad ke ta wasa da Karamar kwallo a Tsakar gidan.
Da Farko Amina Dataji Hanne na Tashinta kin tashi tayi sai da tace mata Hajiya ke kiranta sannan ta Mike tana fadin"Kice Wlh Hanne..!
Hanne ta mike tana fadin"Au nace ma Wlh..!?
To ki zauna kin ga tafiyata..!
Amina ta mike tana fadin"Tsayani Hanne mu je..Fatana Allah yasa ba gida zata saka Idi ya kaini ba..!
Hamida da Hanne suka kalli juna kafin Hanne tace"To in chan din ne fa..? Ai kince gidan mijinki ne..!
Amina na saka Hijabi batayi mgana ba sai da ta gama sakawa sannan ta Dago Tana fadin"Ni yaushe na Fada..?
Allah ya isa na, wuta bal bal in ban Fada ba..!
Hamida na Dariya tace"Daman chan Allah ai ya ishi kowa Amina..!
Harara ta balla musu kafin ta bangaje Hamida ta wuce fuu hamida da Hanne suka.bita da kallo Hanne tace"Kamar an kara mata bala"i wlh bayan auran nan..!
Hamida tace"Kowa ma haka yake fadi..ya danmallam zai yi mganinta bari su koma Madina ki gani nan ta raina achan Ubanwa zata mawa .!
Hanne na Dariya tace aifa Daganan ta bi bayan Amina zuwa gidansu.
Koda Taje Amina da Hajiya na kuryan Daki Hanne na shiga Hajiya Data Kira Danmallam bai Dauka ba ta kalli Hanne ta nuna mata kofa Tana fadin"Jirata afalo..!
Hanne ta Tura baki kafin ta fita Amina ta Fakaici idon Hajiya tayi ma Hanne gwalo ita azatonta wani abun Dadi Hajiya zata bata sai da wayar Hajiya ta shiga kidan larabawa taga Hajiyqn ta Dauka ta mika mata tana Fadin"Karbi Mijinki ke son mgana Dake..!
Ta fada Lokaci Daya tana Ficewa Daga Dakin Harda Rufo mata kofar Bedroom din Amina gabanta ya Fadi tabi wayar da kallo ga sunan Danmallan nan baro baro na kan Layi sai jikinta ya fara rawa aranta tace na shiga uku ni Amina Allah yasa ba wani Abu akace mai nayi ba..
Jikinta a sanyaye ta kara wayar kunne Daidai Lokacin da Sanyayyiyar Muryansa ta Doketa Cikin Sallama da Hausansa daya Cakude da Larabci.
Sai da ya kara maimaita Sallamar sannan ta amsa Bakin da jikinta na rawa Tun kafin ya gama rufe baki Tace"Ina yi..yini..!

Ajiyar zuciyar daya sauke har sai da ta jisa a kunnenta Dayaji muryanta sai yaji Salama da natsuwa Cikin Taushinsa yace"AMINA...!
sai taji kamar yafi kowa iya Fadar sunan nata jin yadda ya kirata ita bazata iya tuna ko yama taba kiran sunanta ba Haka ba, jin tayi shuru yasa ya kara cewa"Amina kina lafiya..?
Cikin Sanyin Jiki tace"Na"am..eh lafiya kalau..!"

"Ya jikin ki..? Ina fatan kin warke babu kuma inda ke miki ciwo..?
Ya fada kai Tsaye domin baya Fatan ace wani abu kuma ya tashi bayan Tafiyarsa kunya ta kama Amina ta Dukar da kanta kamar yana ganinta ta kasa mgana sai gabansa ya Fadi da Sauri yace"Ko da wata matsala ne..?
Da Sauri tace"A"a na warke..!
Afili ta Furta"Alhamdulillah..!
Kafin yace"Naji Dadin haka ina Fata kamar yadda kikamin alkawarin baki gayama kowa ba ko..?
Sai da ta gyadamai kai kafin tace"Eh ban fadama kowa ba..!
Cikin jin Dadi yace"Dakyau naji Dadin Haka..Ya karatu fata kina maida Hankali wajen karatu..?.
Da Sauri tace"Eh yau ma mun yi Hutun Hadda..Gobe ma zamu Fara Jarabawa a boko..!
Kai ya gyada kafin yace"Allah ya bada sa"a..ki rika maida hankali kinji ko..?
Ta gyada kai ya cigaba da Fadin"Sannan ban da wasa ban da Fada ban da gujeguje ke yanzu ba yarinya bace kin tashi Daga su Hamida ke matar aure ce ba Daya kike Dasu ba kina jina ko..?
Nan ma kai ta gyada mai yace"Baki da baki ne..!
Ba nace ki daina min mgana Da kai ba .!
Da Sauri tace"Naji insha Allahu..!
Ajiyar rai ya Sauke kafin yace"Kina Bukatar wani abu..?
Tace bakomai kai Tsaye yace"Ki rika gaida Sakina in kun hadu tana gaba Dake kinji ko..?
Amina ta Tura baki kafin tace"Ni fa in na ganta batamin mgana sai tayi ta Hararana har zagina ma tanayi..!
Cikin mamaki yace"Ita Sakinar..?
Amina tace"Eh shiyasa nafi son zaman nan fiye da chan sannan achan ina jin Tsoro da Daddare bana iya barci don Allah ka Fadama Hajiya ta rika barina ina kwana anan in ka Dawo sai na koma achan..!
Kawai sai ta sakamai kuka sai yaji Hankalinsa ya tashi meke Damun yarinyar nan ne Cikin Tausasa Murya yace"Naji ki daina kuka zan mata mgana..Daman baki daina Firgita cikin barci ba..?
Tace mai eh sai da yayi shuru kafin yace"Ki samu mallam yau da Daddare in ya natsu ki Fadamai abunda kike jin in zaki Firgita kin ji ko..?
Tace"Na Fadamai..?
Yace"Eh ki Fadamai sannan mganar Zagin ki da Sakina ke yi kada ki Fadama kowa har su Hajiya zan mata Fada insha Allahu zata Daina ke dai in kin koma gidan kun Hadu ki rika gaisheta saboda ko bakomai Tana gaba Dake kuma a islamiya an koya muku yin biyayya ga na gaba da ku ko ba Haka ba..?
Tace eh ya cigaba da fadin"To ki rika bata girmanta kin ji ko..?.
Ta amsa da toh bai Tsawaita mganar ba yace"Zan ce ma Jafar a Cefanan wannan watan ya siya miki Goldenmorn da Cornfkles Saboda Saukaka miki Wahala sai ki Rika sha in zaki tafi makaranta..!
Tace "To nagode..!
Ya amsa ta da Fadin"Kada ki damu komai kike Bukata kada ki tambayi Hajiya ko mallan ki yi ma Jafar mgana ko kuma ki Dauki wayar Hajiya ki kirani kinji ko..!
Nan ma tace mai da toh tagode Dagnan yace ta maida Hankali a karatunta ta amsa mai Daganan ya mata sallama ya kashe wayar.
Tabi Wayar da kallo Tana Tura baki wai ta rika gaida Sakina Tab wannan mara mutumcin ne zata gaisheta..
Shi kuwa sai da sukayi mgana yaji Hankalinsa ya kwanta har ya natsu ya Cigaba da Duba Takardun Dalibansa da sukayi gwaji.
Da suka gama wayar kunya ta Hana Anina fitowa sai da Hajiya ta Shigo Daukan abu ta ganta zaune tayi shuru tace"A a Mamah tunda kun gama wayar ki fito falo hanne na jiranki mana sai ki zauna ke kadai..!
Jin haka yasa ta mike ta mikama Hajiya wayar, ta karba ta Fice da Sauri Hajiya ta bita da kallo tana Mirmishi a Cikin aranta tana Fatan addu"an su Allah ne ya karba na amitar da Ruhin Amina da Danmallam waje daya.

Amina na fita Hanne ta taso tana Tambayanta da wa tayi waya Amina ta balla mata Harara kafin tace"Bansani ba..!
Hanne na Dariya tace"Nasani Ya Danmallam ne..ko..?
Amina ta mata wani kallo kafin tace"In ma shine sai na Fada miki..?
Sirrin miji da mata..!
Hanne ta saki Dariya kafin ta Ja Hijabinta tana fadin"Bari naje na gayama Hamida..Sabon Update..!
Amina tayi Tsaki kafin tace"Ai ke Hanne mijinki ya shiga uku..duk wanda ya aureki ya auran ma kansa sai kin hada Fada a Family din mijinki Saboda munafuncinki..!
Hanne bata bi ta kanta ba ta fice Amina tayi zamanta Falon Hajiya chan sai gasun dawo Tare Hamida sai kara maimaita abun da Hanne ta gayamata take yi Amina

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login