Showing 201001 words to 204000 words out of 265571 words

Chapter 68 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28962

Fadin"Wlh ya Danmallam Amina tana da kirki sai wanda ya Zauna da ita ya sani...Tana da son yan"uwanta sai dai akwai abu Daya Amina tana da riko in ta Tsaneka sai Alllah sannan tana da Fada da Tsiwa kuma bata Laushi ko bata da gaskiya sannan ga son jin gulma,Amina fada ko ba nata bane siyanta take yi a makarantar boko da Islamiya ba malami ko Dalibin da baisan Jidalin Amina ba,ba wanda ta Kyale tana da Fara"a sai dai bata Daukan Reni bata kuma son arainata kan Hamida da hanne Amina Zata iya yin komai tasha Fada saboda mu kuma duk wani abu da ake yi Amina ce gand leader din mu.
Ya Danmallam ga ni Amina wata Hudu ta bani Hamida kuma wata uku ta bata ammh nuna wa take kamar ta Girmemu Amina bata san Faduwa ba bata nuna gazawarta Wlh ko su ya Abida ban shaku dasu yadda na shaku da Amina ba tunda muka taso bamu taba Rabuwa ko na kwana Daya ba,Shiyasa Rashinta ya ke sakamu cikin Wani hali komai baya mana Dadi..!

Hamida ta karbe da Mirmishi tace"kuma ba"a zaman minti goma da ita ba"ayi fada da ita ba..tafi Fada dani Fiye da Hanne saboda ni bana gani na kyale Hanne kuma bata da yawan mgana,Mu yi fada mu Shirya hakanan muke zaune duk duniya ba wanda yakaimu sanin Amina sannan mun san Halinta sai muka ci Mganin zama da ita, jidalin Amina ni da Hanne kadai muke iya Daukan ta, ko Ciwo tayi kowa sai yaji wani iri saboda Amina mai Fara"a ce sannan tana da Dadin zama ga wanda ya santa sai dai kawai Fada da Zafin rai sannan bata Daukan Reni Haka Aminene take bata da tsoro bata Shakka Kirarinta badai ta mutum ba sai Allah..!
Ko abunda ya faru na Aminu Tsausayi ne wlh ba Halin Amina bane nan ta shiga bashi labarin soyayyar ta da Aminu tundaga farko Har karshe da abun da ya Faru Hamida ta kareshe da Rantsuwan wlh tallahi ya Danmallam Tsautsayi ne ammh wannan ba Halin Amina bane barta da Jidalanta ammh Namiji baya gabanta soyayyarta da Aminu kaddara ne ta Ubangiji..!
Da Dukkan Hankalinsa yake sauraranasu duka labaransu suna shiga kansa wasu labaran na Amina abun Dariya ne wasu kuma ya Dauki wasu abubuwa da mganar Data Fadamai akwai kamshin gaskiya ko wani yaro akawai irin yarintarsa ammh na Amina yayi yawa wannan Rashin Tsoro da rashin jinta yayi yawa ba nata bane ita kadai da gaske an kara mata ne duk da abun ya Tarda Halinta ne ya gasgasta mganar ta Dalilai da dama sannan ga abunda ya Lura dashi a wajenta lokacin da ya kusanceta din nan ya Fahimci akwai matsala sannan ga mgangan su Hamida sosai yaji tsausayin Amina da wani Kaunarta na shiga ransa bai sani ba..
Mganar Aminu kuma mallam yadan Fadamai kadan Daga Cikin abun da ya faru Lokacin bai wani mai da kai ba kan mganar tunda alokacin yana ganin Aaminar kamar ta riga ta gagarane aransa kuma sai yaji ya baci da jin Labarin yadda su Jafar suka Dinga Dukan mai mata gaskiya ransa ya baci da Yana Kasar sai ya hanasu ai wannan abun yayi yawa kamar sun sanu jaka su bazasu Fahimci wani abu kan Amina ba..?
Yayi mamakin da ko mallam bai Taba kaawo wani abu acikin Ransa ba sai dai kila wani abu Allah bai Cika bayyanasa da wuri ba sai Tafiya tayi tafiya mganar Aminu kuma bai Damu ba yasan ba son shi Amima ke yi ba yarinta ne da kuma kaddaran auransa da Amina shi kamar ma taimakonsa yayi sannan da kuma karfin rabon dake Tsakaninsa da ita

Mirmishi yayi har Hakoransa suka bayyana kafin yace"Wato Aminene dai ikon Allah ce badai ta mutum ba sai ta Allah..!
Hamida da Hanne sukayi Dariya suka Dukar dakai shima Dariya yayi yana tuna wai tace ma malamar corper dinsu tana warin maza kawai sai yaji wani abu mai gardi da Zumudi kan Amina na kara mamaye ransa
To ai a jidalin nata zata zama uwa..!
Lalle akwai kallo sannan Jidalin akwaishi kam
Nan ya samu ya lallaba su hanne yace zai hadasu suyi mgana da Amina ammh bai sanar dasu inda take ba sun ji Dadi da sanyi tunda Amina dai tana Lafiya sannan tunda yace zai hadasu susan bazai musu karya ba sannan yace kada su fadama ko Hajiya mganar da sukayi.
Adaran yayi ma Hajiya mganar zuwa Abuja Hajiya tace ko da yaushe ya shirya yaje mana ya ganta..
Kansa na kasa yace zai sanar da Mallam jibi sai ya tafi gobe zai je Dutse shi da su Sarood su gaida Aliya matar Aliyu tana asibiti Ciki na bata Wahala...
Hajiya ta jajanta kai Tsaye tace ma Danmallam ya Dauki Aliyu ya rakasa Abujan mana.
Cikin mamaki yace"Hajiya kin manta kin ce ko shi kada yasan komai..?
Hajiya tace"Ka sanar dashi nasan shima bazai sanar da kowa ba..Bai kyautu kaje kai kadai bane..!
Ko Jiya sai da nayi ma Sa"idu Tsiya kawaicinsa yayi yawa bai Taba Tambayana ina Amina ba ko ina na kaita ba.?
Anya akwai Uba irin Sa'idu kuwa..?
Cemin yake yarda da nayi Dake Hajiya yarda kika rikeni Tsakani ga Allah na Tabbata duk inda Zaki kai Amina Za"a kula da ita kuma bazaki kaita inda Za"a Cutar da ita ba .!

Danmallam mirmishi kawai yayi bai ce komai ba Tsakanin Baba Sa"idu da Hajiya ko mallam baisan Tsakaninsu ba ballatana shi da ba mazauni ba sun Dade suna Hira da Hajiya kafin ya mata sallama Shashen falon ya koma sukayi mganar Tafiyarsu Dutse gobe da zuwansu Abuja shi da Aliyu mallam yace yana da kyau hakan Aliyu ai Aminini sosai sannan ya bada Sakon gaisuwarsa ga Mamarsa Amina.
Daya fito daga wajen Mallam shi da Nazeem suka yi hira sai after 10 ya koma gida Sarood ta kwanta Sakina dai na Zaman jiransa ya riga yaci abinci shashen mallam shiyasa bai ci wanda suka shiryamai ba yasan Daman abunda take mawa shi har mamaki take basa zafin nema na kawo samu ne..!
Tunda ya Dawo bata barsa ya Huta ba koda yaushe abu Daya ce mata akayi haka ake samun Ciki..?
Koda yake duba da Cikar Burinsu ai yasa tama Fita daga hankalinta Kada ya Danne mata Hakkinta yasa ya Biye mata kuma duk Shawaran Anty Amarya ne Ta Dake ta maida Cikinta Datayi barinsa.
Washegari karfe tara na Safe suka Dauki Hanyar Dutse shi ke Driving din Sakina na gidan gaba Sarood na baya sun isa da wuri Ajiyan aka Sallami Aliyan tana gidan chan suka wuce Direct bayan sun ci abinci sun huta sai mazan suka shiga Cikin gari suka bar matan agida
Sakina da Aliya suna mgana da Hausa suna Yamutsan fuska suna zunden Sarood, ita kuma tana kallon su tana washe baki batajin me suke Fadi Daga baya ma tashi sukayi suka shige Ciki suka barta ita kadai afalo kamar mayya su kuma sai bayan La"asar suka Dawo abokansu suka ziyarta da sukayi makaranta tare da aiki ya kawosu Dutse da zasu dawo suna Hanya Danmallan yace gobe da Safe ya zo zai rakasa Abuja Aliyu bai kawo komai ba Tunaninsa wani abun zai kai Umar din Abuja.
Yasa bai matsamai da Tambaya ba ya amsa masa da toh Allah ya kaimu.
Bayan La"asar suka Dauki Hanya bayan su Aliyu sun rakosu da Fatan isa Lafiya da suka Dawo gidan mallam suka Sauka sai aranar suka shiga gidan Baba Sa"idu suka gaisa da mamanmu shima adaran ya shiga shida Aba suka gaisa da ita sai kallonta yake yi yana Nazarinta haka kurum daman shi tun Farko kirkirta bai mai ba sai kuma ta kara Dora kanta azargi da Aba ya shiga Shashensa ta fara tambayansa Amina harda sharan kwallarta na karya wai Hajiya taki sanar ma kowa inda takai Amina..
Mirmishin yayi kafin yace mata shima bata Fadamai ba sai ta fara sallallanmi tana Fadin Allah yasa to dai lafiya.
Har ya mata sallama ya fita yana Auna mganganunta Biri dai yaso yayi kama da mutum a kaunar datake ma Amina in har na gaskiya ne Amina Bazata kai wannan wattanin bata nan ba bata wani damu ba gaskiya bai yarda da ita ba daman mutum ya cika Kirki wani Lokacin mugu ne.
Sai dare ya kwashi matansa suka koma gida adaran ya Fada musu gobe zai je Abuja wani aiki zai kaisa ba su Damu ba ita kanta Sakina bata kawo komai aranta ba ta Dauka dai aikin zai kaisa kamar yadda yace.
Washegari kuwa agidan mallam suka Hadu da Aliyu bayan ya gaida su Hajiya suka Dauki Hanya,Hajiya ta bata Goriba da su Rama da zogale da kulu su gauta da yalo da Daffafiyar gurjiya akaima Amina sun yi mgana da Aisha ta fada mata abincin zamani Amina bataci sai na gargajiya.
Danmallan ya taho da Tsaraban Amina tare da Ruwan zam zam din daya riga ya karanta mata duka ayoyin dake karya sihiri aciki sannan da Sauran addu"o"in Tsari Domin ya yardan ma kansa Amina ba ita kadai bace.
A motar Aliyu sukayi tafiyar dayake sun tafi da wuri sha Biyu suka shigo Abuja Usman mijin Aisha Danmallam ya Kira yayi musu kwatance cikin Lokaci sai gasu a anguwan maitama Dayake gidajen akawai lamba sai gasu agidan Usman ya Fito ya tarbesu daman yana gida ya samu dan break yana Hutawa kuma shima sai da Safen nan Ya Dannallam ya kirasa ya fadamai suna tafe kuma yace kada ya Fada su Aisha..!

Sai da suka iso gidan ne Aliyu yaga Usman sanna ya kalli Umar yana Fadin"Daman gidan Aisha zamu zo..?
Ko wannan ba mijinta bane..?
Lokacin Usman din yayi gaba suna Binsa abaya zuwa Cikin gidan.
Danmallam yace"Eh ammh ba wajenta nazo ba..!
Aliyu Cikin mamaki yace"To wajen wa kazo..?
Ai naga har sako Hajiya ta baka ka kawo mata. !

Kamar bazai yi mgana ba sai kuma yace"Zaka ganta ita wacce nazo Dominta..!
daidai suna shiga kayattacen Falon na gidan Aisha.







*Janafty*


*TFZB2020*

*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*

Har cikin babban falon gidan Usman ya kawosu yana musu maraba suka samu Daya daga cikin kujerun falon mai zaman mutum biyu suka zauna suna kallon falon ko'ina tsab sai tashin kamshi yake yi sai talabijin dayake ta babatunsa shi kadai cikin Tashar Arewa24.
Usman kitchen ya wuce Direct saboda gida ba wanda ya tashi sai Saude mai aiki shima kiran Danmallam ne ya tashesa bayan ta gaisheshi yace ta kawo Ruwa da lemo akwai baki a falo ta amsamai da toh Cikin girmamawa.
Yana ???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?fitowa ya zauna saman kujera mai zamam mutum daya suka kara gaisawa da Danmallam da Aliyu.
Sannan Usman ya mike yana fadin"Bari na mata mgana..Gidan ba wanda ya tashi..!
Da haka ya nufi Bedroom dinsu shi kanshi ai kayan barci ne masu taushi ajikinsa Aliyu ya bisa da kallo har ya bace ma ganinsa Umar ya kallah yana kara nazari da Tunanin me suka zo yi gidan Aisha..?
Shi dai yasan ko gidajen su Jafar a kirga zuwan Umar ko Nazir kila sau Daya ya taba Taka Lagos in bai manta ba bama shi kadai ba ko su isu isu matan Mallam bai yarda su rika Bin gidajen juna ba sai da kwakkwaran Dalili ballatana shi namiji kuma in bata ma da Lafiya ne ya tabbata sai dai Cikin su Hajiya za su zo bashi ba Gabadaya mamaki ya kamasa daya kasa mgana shi kuma Umar kansa ya Jinginar jikin kujera Idanuwansa a Lumshe fatansa da Burinsa yaga Amina yaga cikisa Dake Jikinta Da yanzu yakai wata shida.

Usman Cikin blanket ya Samu Aisha ta nade tana barci yaye blanket din yayi yana kiranta.

Sweety..!

Dakyar ta Bude ido cikin Barci Tana Fadin'"Darling ka barni nayi barci don Allah..!
Kafarta ya matsa yana Fadin"Baki fa mukayi..!
Bude ido tayi da Sauri tana Fadin"Baki kuma..?
Da sassafan nan..?
Mikewa yayi yana Fadin"masu muhimmaci ne kuma ba Safe bane wajen 12pm fa yanzu rana tayi!
Mikewa tayi tana mamakin wasu irin baki ne haka sai ta saka aranta yan"uwan Darling ne ammh Daga barayinta bata tsammani haka ba.
Dogon Hijabinta ta Zurma na sallarta ne kan kayan barcinta Doguwar riga ta Sako Silafas dinta na yawo Cikin Gida ta fito shi kuma yana Biye da ita a baya har Cikin Falon.
Wadanda ta gani ne yasa ta Tsaya Cak tana kallon Usman baki Bude Dariya yayi mata ya koma ya zauna yana Fadin"Suprise..!
Saboda murna sai ta kasa zama Cikin wani yanayi a muryanta tace"Ya Danmallam .!
Ya Aliyu..!
Tafada Cikin farimciki suka kalleta gabadayansu suna mata Mirmishi ai da gudu ta nufi Danmallan ta Rumgumesa daga Zaune saurin Kwacewa yayi yana Fadin"Miye haka kanar wata yarinya..?
Tana yar Dariya tace"Allah ya Danmallam nayi murnan ganinku ne ko Jiya mun yi mgana da Hajiya bata fadamin zaka zo ba..!
Kai Tsaye Danmallam yace"Ban tabbatar da tafiyar ba nima..!
Kasa ta koma ta zauna tana gaishe da Aliyu ya amsa cikin Fara"a sannan ta gaida Danmallan ya amsa mata ta Tambayi sakina da Sarood yace"Duk suna Lafiya sarood da ita muka zo Tana gumel..!
Aisha tace"Allah Sarki..Sannun ku da zuwa gaskiya ammin zuwan bazata kuma Harda Darling aka hada baki ko..?
Tafada tana Hararansa da Sauri Aliyu yace"Kada ki ga Laifinsa ba ruwansa ko ni da ya Daukoni Tundaga Dutse bai Fadamin gidan nan zamu zo ba..Ga mai Laifi nan yayanki..!
Yafada yana Hararansa da bai masan yanayi ba,Aisha zatayi mgana kenan sai ga Saude da Faranti Cike da kayan ruwa da Lemo Aisha ta karba tana Fadin"Bari nazo Kitchen din Saude yayyina ne suka zo..!
Ta amsa cikin Fara"a tana gaishesu suka amsa mata sannan ta fice Daga Falon taja Center Table din Dake Falon ta Dora musu akai tana Fadin"Ku fara da wannan yaya..bari a sama muku abun karyawa..!
Aliyu na Dauka goran ruwa yace"Tab ai mu nan sai da na Rana..ni kinsan ban cika irin wannan abun na bature ba..Sai dai shehi kila shima bai karya ba ya fito..!
Sai yanzu ya Hararesa Yana dan kallon Usman da hankalinsa baya kansu yana kaa wayar hannunsa ya karkata daidai saitin kunnensa yace"Kaima kenan Dake da mata Daya kayi karin ka agida ballatana ni Dake da Daya biyu uku..!
Ya Fada yana Kirgasu da Hannu Aliyu na Dariya yace"Ba shakka..!
Usman ya mike yana isa kusa da Aisha a hankali yace"Kefa ba waJen ki suka zo ba.Wajem Amina nefa ammh kin Tsaya kina ta kallonsu..!
Kanta ta Dafe ta juya tana Fadin"Murna ce ta sa na Rude Darling..!
Mirmushi yayi mata sai bai bita ba yace ma su Aliyu bari yazo ya tafi ya basu wuri kada ya Takura musu.
Amina na Dakin yakaka kwance akan gado tana barci yakaka kuma na Saman Darduma ta daidaici gabas tana Ta lazimi tun bayan data gama Sallar walha ko Hijabin jikinta bata Cire ba ammh sai faman gyangyadi take yi.
Aisha ta shigo Dakin da Sallama yakaka ta amsa cikin Fara"a tana Fadin"Aisha kin tashi..?
Gaban yakaka ta Durkusa tana amsa mata Lokaci Daya da gaisuwa Ta amsa tana Tambayan Tashin Usman tace mata Lafiya Amina ta kalla data yi kwanciyar gefe saboda Cikin jikinta tace"Yakaka ita wannan bata tashi bane..?
Yakaka tace"Tun dai da ta koma bayan Sallar asuba bata tashi ba..Kinsan ta da barci kuma kila Cikin mganin da likitan ya bata akwai na barci ne inaga..duk da dama tun jiya naganta tana tura baki tana kunkuni bansan me aka mata ba.
Aisha tace"To ina ga...,Yakaka ai Takwaranki jidalinta tashi yake yi ko ba"a mata komai ba..
Yakaka tace"A"a yafi dai tashi in an Tabamu..!

Ya Aisha tayi Yar dariya kafin tace"To ai tashi zatayi yanzu yakaka mijinta ne yazo..!
Yakaka ta zaro ido Lokaci Daya tana Fadin"Wani mijin nata..,?
Ya Aisha ta mike tana Fadin"Ya Danmallam mana yakaka..!
Yakaka sai ta mike tana Fadin"Allahu akbar kice bakin Madina garin manzon Allah Sallahu alaihi waasallam..Zuwa haka ba sanarwa..?
Ko daman kin san da zuwansa..?
Aisha tace"Bai fadamin ba yakaka..!
Yakaka na gyara Hijabin tace"Ahto bari na fita mu gaisa ki tasheta in ta Tsaya wannan kunkunin nata kice na tafi kwace mijin sai ya cike ta Hudu dani ya Rufe kofa..!
Ya Aisha na Dariya tace"To yakaka .!
Ta fice tana Fadin"Tadata ta taso ai barcin ya isa haka..!
Ta fice abunta ita kuma ya Aisha ta dan Daki gefen katifa tana kiran sunan Amina sai chan ta jita ta dan Dago kai Cikin barci ta Bude idonta ya Aisha tace"Dilla ki tashi barcin ya isa haka..!
Amina zata sake juyawa Aisha ta Make mata hannu tana Fadin"Ya Danmallam ne fa yazo Amina..!
Da sauri ta dan mike zaune tana Fadin"Da gaske..?
Ya Aisha ta mike tana fadin"Ko nace ya shigo ne..?
Amina ta Tura baki batayi mgana ba Ya Aisha tace"Suna falo suna gaisawa da yakaka ki Sauya kaya ki sako Hijabinki ki fito ku gaisa..!
Daganan ta fice Daga Dakin Amina ta Bita da Harara tana kunkuni tace"Ba"aza afiton ba sai yau ne ma zai zo wajena tunda ya dawo ya manta dani ya samu guzumayen matansa ko kirana bayayi..!
Ashe Fushinta datake yi kenan tun jiya Saboda sau daya suka yi mgana Daya Dawo.
Aisha na fita falo ta iske yakaka sai Hira suke sha da Aliyu Har da ya Danmallam da bai mgana Dariya kawai tayi yakakace fa balle ai yasanta Saboda in suna waya da Amima yana jin mganarta sannan sun taba gaisawa sau biyu da ita kuma ai Hajiya ta Fadamai akwai kakar Usman agidan tun kafin ta kawo Aminar.
Tana ganin Aisha tace"To ina takwaran tawa.?
Na ganki ke kadai..?
Aisha tace"To nidai na tasheta na Fadamata ban sanin mata ba..!.
Yakaka tace"Kajimin shegentaka ace maka ga mijinki ya taso daga wata uwa Duniya domin ka sai ka Tsaya Sakarci..?
Ahtto ni dai dan madina tunda Takwaran tawa tana ja maka aji gani sai ka Rufe kofa dani mu Daga garin manzo sai dai taji asalansa..!
Dariya Aliyu yayi tsohuwar farat Daya ta shiga ransa sai da yana ta mamakin waye wannan da Aliyu yazo gani..?.
Saboda shi bai taba sanin Amina bata nan ba..
Danmallam ne yace ma yakaka"Shikenan baaba..Sai mu tafi Dake ai ni naga Amaryata.
Ta washe baki tana Fadin"ah to in ita bata so..Ai ni ina son abuna..Daman ita naso na raka garin na manzo Tunda na mata fashin Mijin ai shikenan kowa yayi ta kansa..!
Har Aisha sai da ta Dara yakaka ta mike tana kallon Aisha kafin tayi mgana sai ga Amina ta shigo Falon da Karamar sallamanta tana Tura baki Sanye take

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login