Showing 123001 words to 126000 words out of 265571 words

Chapter 42 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28887

na daya da Labarina na ta fita zaka,Nagode ma Allah domin baiwarsa ce kuma ikon sa ne bazan Tsawaita mgana ta ba kun riga kusan yanzu aka fara wasan akwai tarin abubuwan da zasu faru a kashi na Biyu na cigaban wannan labarin a baya naso nayi sa Cmpt dinsa Hardcopy ne ammh Sakamakon Rikon Wasu masoyana yasa na amince zan yi sa Softcopy ammh da Sharadin in kun siya Over 150 a paid group sannan bazan fara posting ba sai nan da Sati Daya zuwa sama in na gama Hutun dana Dauka ga masu son su Fara payment din su zasu Biya N500 Via 0552179550 Jamila umar Gt bank sai a Tura Shedar biya ta wannan lambar 09069067488, masu Turo kati kuma sai ku Dauki hoton katin ku Turo kai Tsaye ta wannan lambar 09069067488,Mutanenmu na Niger kuma zasu Tuntubi Kausar aglan Nissa ta wannan lambar +22796562223 sai na jiku ina gaida masoyana a ko"ina afadin Duniyar nan wanda na sani da wanda ban sani ba..Sannan ina mika jinjinata ga Groups din da suka yi sharhi kan wannan labarin da masu sharing dinsa da yan Wattpadian dina Allah ya saka da Alheri Allah ya bar zumunci Maassalam*


*TFZB2001*

*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yad'ashi..Pay N500 via jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan Lambar 09069067488*

Yana dafe da kansa kwata kwata baisan motar ta kwacemai ba sai da yaji ta fara yawo a kan titi sannan ya dawo hayyacinsa yana kokarin kamo Sitiyarin motar ne Amina Data ke kuka cikin karan sautinta taga wata babbar mota tayi kansu gadan gadan sai gabanta ya fadi,Kukanta ya Dauke da batasan sanda tayi tsalle sai gata jikin Danmallan cikin rawan jiki Ta kwalla kara tana Fadin"Wayyo Allah babbar mota...!
Wani bakinciki da takaici su kusa kasheshi,bai samu damar mata mgana ba sai da ya daidaita Motar sannan ya gangara gefen hanya yayi parking kafin ya juyo yana kallon Amina wacce ke rike dashi Saboda Tsoro ran sa bai kara baci ba sai da yaga gabadaya Hawayenta da majinanta ta gama gogemai saman kafada wani irin kallon kyama da Haushi yake binta dashi ita batama Lura ba saboda bata cikin natsuwarta ga Halin datake ciki ga Razanan da tayi na ganin babbar Mota ta nufesu gadan gadan.
Ganin sai zare ido take yi taki sakinsa yasa ya saki wani siririn Tsaki kafin ya Daka mata tsawa yana fadin"Ke...!
Sai alokacin ta dawo Tunaninta ta Dago tana kallonsa ganin irin yadda yake Hararanta ne yasa tayi saurin Sakin rigarsa data cukwikwiye da hannayenta ta koma kujerarta ta zauna da Duwawunta tana maida Nunfashi Lokaci daya da ruwan hawaye suna gudu Bisa kumatunta.
Ransa ya kara baci da ya kunna Hasken motar yaga yadda Maikon hannunta ya sakamai Shatin Datti ajikin Rigansa baisan sadda ya kalleta cikin bacin rai yana fadin"Ke wata irin kazamar yarinya ce mara natsuwa..?Ko sau daya tak a rayuwarki bazaki yi wani abu da zai nuna ke mace bace..?
Yafada yana kallonta cikin Idanuwansa da suka fara sauya Launi Saboda bacin rai.
Bata dago ba kanta ta kara maidawa kasa tana sharan kwallah kalmar kazaman daya fadamata bata Dameta ba kamar yadda yace mata mara natsuwa duk sanda ya fadamata haka sai ya sakata kuka yanzu ma Kukan ta fara Tana neman kara baremai baki da Sauri yace"Kika kuskura naji ihim dinki Wlh sai kin raina kanki..kinsan Zafin hannuna kuwa..?Baki sani ba na su Jafar kika sani to kika bari kika kaini bango da wannan banzan kukan naki wlh in na mareki sai bakin ki ya juya Hagu..Uselesss kawai..!
Yafada Cikin Kufuluwa acikin ransa yana Faman kokuwa da yanayinsa Gabadaya an kuntatama rayuwarsa yanzu banda a kashesa da ransa Lokacinsa bai ba..?yi ta ina zai iya zama da wannan yarinyar..?Kukanta kadai ya isa yasa Hawan jini ya kamashi..!

Ko kara kallonta bai yi ba ya maida kansa wajen kokarin tada Motar ammh sai me sai yaji kukan na kwace mata da sauri ya juyo yana kallonta Cikin mamaki ganin haka yasa tayi Saurin saka Hijabinta ta Danne bakinta Hawaye kamar famfo suna zuba bai mata mgana ba ya tada Motar suka hau kwalta ya fara Tafiya kenan kawai yaji ta bare baki ta saki kuka Da waani karin mamaki ya kara Binta da kallo yama rasa me zai ce mata,Hannunsa Daya rike da Sitiyari Daya kuma Dafe da kansa yana Bin ta da kallo ji yake kamar ya Tsaya a hanyar nan yayi wurgi da ita kalli Daga gidan mallam zuwa gidansa yarinyar nan har ta fara chazamai kai.
Saboda bacin rai baisan sadda yace"Au kukan kike yi ko .?
To wai ma tsaya me akayi miki ko kuma uban me kike so..?
Cikin kukan tace"Ni kamaidani gida..bazan iya kwana wajen da ba Hanne da Hamida ba..!
Harara ya jefa mata kamar ya Daketa Haka yake ji Cikin Fusata yace"To anki a maidake din..Sai kiyi abunda zaki yi in kin isa..Haba..Wannan iskancin ya isheni wlh bazaki je kina Damuna da wannan kukan banza naki ba mganinki zanyi..!
Amina sai ta kara wage baki tana Fadin"Wayyo ni..Hanne...Yiyiiyiiii..Hamida..Wajen su zan je na shiga uku..Yiyiiyiiii..!

Reras fa hake ta kuka Danmallan yayi zaune kawai mganarsa ta kare Ya rasa ma abunda zai ce mata kawai ya Cigaba da Tukinsa bayan ya Dauke kansa,Tsabar bala"in yarinyar nan kansa har ya fara saramai ina Dalili ganin bata yi shuru ba yasa ya Daka mata tsawar da yasa ta kama bakinta Cikin Daga Sautinsa yace"To baza ki koma wajen su ba ko zaki yi kukan jini ne..Salon ki je chan ku cigaba da yima mutane iskanci da raini ko..?
To anan ni zan gyara miki zama wlh in baki min shuru da bakin ki anan wajen ba..Daganan Gidan gyaran Hali zan kai ki inda ake ladabarta da kangararrun yara marasa jin mgana irin ki sai kinyi kwana arba"in cikin mari kinji ma na Rantse..!
Amina ta kallesa tsab tasan zai aika sai hankalinta ya fara tashi maimakon tayi shurun daya ce sai kawai ta Duke kasan Mota hannunta Bisa kai ta rushe da wani kukan dayafi wadanda tayi sauti da kara Fadi take"Don Allah kayi hakuri..Don Darajan iyayenka kayi hakuri..!
Wlh kadan ya rage bai Bugama wani mai adaidaita ba saboda yadda Ihun ya shiga kansa ransa yakai kololuwar baci in ya zauna acikin motan nan zai iya ma yarinyar nan Lahani yasa baisan sadda ya Gangara gefen kwalta ba ya faka Motar a fusace ya Bude bangaransa ya fita Amina kuwa ta zata ita ya tsaya ya Daka yasa ta koma ta Lafe jikin kofa tana Rufe bakinta Cikin kuka sai taga ya fita ya Rufe kofar da karfi kamar zai ballah.

Bayan Motar ya koma ya Dafe kansa cikin wani yanayi yake maimaita Hasbunallahi wani'imal wakeel..!
Bai saurara ba sai da yaji ya Dawo Cikin natsuwarsa ya zai yi da wannan Fitinanniyar yarinyar da ke neman chajamai kai..?
Wlh bazai iya zama da yarinyar nan ba Tun aTarihin rayuwarsa bai taba Daga Sautinsa irin na yau ba bai taba Fada irin na yau ba ko Sakina ta batamai rai baya Biyemata yana da Hakuri da kawaici sai ta Dade tana abunta bai Dago ya kalleta ba shi in ya tashi nashi Lokaci Daya zai yi shikenan kuma ya huce ballatana Sarood da bata da Hayaniya banda ma dan matsalan da suka samu da zasu taho Bikin nan.
Karamin Tsaki yaja kawai afili yana kokarin samo ma kansa mafita Visar sa zai yi kokari ta fito Cikin Satin nan ya kara gaba kafin yarinyar nan ta kai shi bango yayi mata Dukan mutuwa Tunda ya Lura Baba mallam ya gama batata sannan su jafar ba Hukunci suke mata ba wani Burauban nata Harda iskanci da rashin natsuwa.
Ya lura ba yarinta bane Tsabar iskanci ne da samun wuri banda haka kamar ita tasan ta iya waya da Saurayi a boye har suna haduwa..?ai shi sanda Mallam ke fadamai yana ta fadin yarinta ke damunta jinsa kawai yake wannan abun ya wuce yaro yayi sa tana Sane da duk abunda ta aikata shine Hajiya ke son ya kwasheta ya kaita Madina wlh ya tabbata watarana sai ta jawo silar abunda zai sa a Dauresa in ma bata yi sanadiyar barowarsa kasar ba gabadaya bama.

Yana cikin wannan Tunanin wayarsa Dake gaban aljihun rigarsa ta Dauki kara,Daukota yayi ganin mai kirasa yasa ya saki ajiyar rai da salama da sauri ya Daga kiran yana Fadin"Ka kira alokacin Dayace Aliyu..!
Ko sallama bai tsaya yayimai ba Tsabar Tashin hankali
Aliyu dake zaune afalon gidansa ya gyara zama yana fadin"Shehi ango..Angon Sixty.. Tsabar Rudewar ne yasa yau Shehi ya manta da sallama..?

Ya fada cikin shakiyancinsa Umar ya Saki karamin Tsaki kafin yace"Salamu alaikum..Na sha"afa ne Aliyu kaina ya Fara ciwo wlh..!
Aliyu yajisa cikin wani yanayi yasa yace"Meya faru ne..?
Baka koma gidan bane ko baka je gidan Mallam din bane..?
Daman sunyi mgana Kafin ya fita Daga gida
Cikin Kar ya Sauti yace"Na je gidan mallam..Bakasan wani abu ba..yarinyar nan fa suka hado da ita Aliyu..!
Aliyu yace"Wata yarinya..?
Danmallam ya Dafe kansa kafin yace"Kazamar yarinyar nan mana..!
Aliyu yace"Nifa ban gane wata yarinya ba Sakina wai kake mgana..?
Yafada cikin Danne Dariyansa Umar ransa ya baci cikin Haushi yace"Sakinar ce kazama Aliyu..?
Amina fa nake maka mgana da nace maka Hajiya ta matsa sai ta tare yau din nan abu kamar za"a gudu..Ko kuma ana jirana Aliyu..!
Aliyu ya saki yar dariya kafin yace"Au to..Kaine ka fadi sunan yarinya kaki kana ta fadamin kazama ni to ya zan yi na ganeta..?
Wai yanzu kana nufin kuna tare..?To tana ina..?
Yafada daidai sanda Aliya matarsa ta shigo Falon ganin yadda yake zaune yana waya ne yasa jikinta ya bata da Umar yake mgana Hararansa take ta kasan ido domin itama tashin Datayi Da Sakina taje Daki sukayi mgana Wlh tafi sakina Jin kishi da wannan auran Rainin da Umar yayi haba in ba Raini ba wannan kazamar yarinyar ta ina zata iya hada miji da ita komawa baya ne wlh,Ta fadama Sakina kada ta Sake ta bari ta shigar mata Dakin miji sai ta zata sun zama Daya da ita kenan sai dai ta nemi Dakin kwana Tun da Sakinar ta fadamata Labarin Tarewar ranta yake bace Har Aliyun taji Shima Haushinsa take ji tunda ya shigo take fadin rai yana ganin haka shima ya shareta bai bi ta kanta ba.
Ganin yadda ta zubamai ido ne Umar na fadin"Wlh Aliyu yau kadai dana Dauko yarinyar nan har na fara gajiya..Can u just imaging kuka take min amota har tana wayyo Allanta har barazanar kaita gidam mari nayi taki yin shuru kafadamin ya zanyi..Wlh kaina har ya fara ciwo na rasa ya zanyi..?

Yafada lokaci Daya yana Dafe kansa dayake Saramai Tun dazu Aliyu, Aliya yaga tana kallonsa yasa ya mike yana Fadin"Shehi me yayi zafi..?
Kai da zakayi lallashi sai ka Bige da zuwa gidan mari..!
Yafada yana Dariya Lokaci Daya yana Ficewa daga Falon zuwa bedroom dinsa yana jinta tana raka sa da fadin"Girma dai ya fadi wlh..!
Shi yasan kan mganar domin tun da yadawo take sakin tsaki Lokaci bayan Lokaci sai tace an dai ji kunyar Wlh mutum ya rasa wazai aura sai yar Cikinsa ko batayi mgana ba yasan da Umar take so take ya tankata shima yau gidan nasu ya koma yakin Biyafara banda mata ma mata ne ina Ruwanki da batun gidan wata kai abun na bashi mamaki..!
Sai da ya shiga Dakinsa ya kulle sannan yace"Ina jinka..na baro Falo ne..kasan nima yau gidana irin gidanka ne..Aliya na taya Sakina kishin ka yo musu amarya da karamar yarinya wai kama raina su..!
Ya karishe fada yana yar Dariya Umar ya saki hanci kafin yace"Bangane tana taya ta Kishi ba..!?
Nan Aliyu ya labartamai abunda ya faru Danmallam ya shafa gemunsa yana Fadin"Meyasa mata suke da karamin Tunani ne..?,Ita Aliya Daman haka take..!To yau in kai in zaka kara aure ya kenan..?
Inaga baka ba kara aure Aliyu..!
Aliyu yace"Wane ita..?Har ta isa wlh tallahi sai dai in banga wacce nake so ba..Ina da sha"awar kara aure Shehi in kaga ban yi ba to hakan na cikin Abunda Allah ya Tsaramin ne..!
Umar yace"Lalle akwai yaki..Aliya zata cin na ma gidanka wuta..!
Yafada yana yar dariya Aliyu yace"In ta fasa..Ni fa ba irinka bane da zan zauna anamin iskanci ban ci ubam Mutum ba..Wlh ban kai ka Hakuri ba Umar..Ina da kawaici ammh ba kowani Lokaci ba yanzun ma Daka ga na kyaleta Lokaci na bata in ta bari na tankamata sai ta raina kanta ni ba Sakaran Namiji bane ka sani..!
Umar na yar dariya yace"Allah dai ya kyauta..!
Aliyu ya amsa da Ameen kafin yace"Wai ina ka barta ne..?
Umar yace"Tana cikin mota..Kaina ya fara ciwo wlh kukanta zai sakamin Dagaaawar jini Aliyu..!
Agogon Wayarsa Aliyu ya Duba kafin ya maida wayar kunnensa yana Fadin"Shehi Dare fa yayi..Pass 9 goma ta kusa..ka lallabata tayi hakuri kasan Rabuwa da gida..kuma kada ka manta aure yakin mata..Sannan ita ga yadda abubuwa suka zo shehi Dole tayi kuka..Gata yarinya ce karama Kasan kaima sai ka kara Hakurinka sannan Hajiya da Mallam sun zama gatanga gareta Dolene ko baka so kayi Hakuri da ita na dan Lokaci ne nan da wani Lokacin in ka fara cin amarci kana jin Dadinta zaka bani Labari mutumina..!
Danmmalan ya saki Tsaki kafin yace"Ammh dai Aliyu kai mutumin banza ne.. ko..?
Bai jira amsar sa ba ya katse kiran yana Fadin"Ko kunya Bai ji..Yana mganar wannan abun da wannan yarinyar..!
Tsaki yayi kasa kasa kafin ya maida wayarsa aljihu sai da ya bata Lokaci kafin ya Dawo Motar budewa yayi ya lekata ganinta nan kasan kujeran ta Dunkule yasa ya shigo Motar karan Rufe motar ne ya Dawo da ita cikin Tunanin data Fada na gata chan agidan kangararru an sakamata mari.
Tana ganinsa ta zabura tana Kokarin kara sakamai kuka wani banzan kallo yayi mata kafin yace"Ki bari naji ihim dinki ki gani..Wlh na rantse yau sai kin kwana gidan mari karyan iskanci kike da rashin kunya chan akwai Uban ninki a tacewa..!
Bakinta ta kama tana Hawaye Tsawa ya Daka mata kafin yace"Tashi ki hau Kujera..!
Da Sauri jikinta na Rawa ta koma ta zauna tana Danne Bakinta ko kara kallonta bai yi ba ya Tada Motar suka fara tafiya Amina ko Tsoron za"a kaita gidan mari ga kuma tsoron zata je wani gidan inda ba Hamida ba Hanne Ta tsorata dashi duk muguntar su ya Jafar tana ganin ya Darasu tunda su basu taba cewa zasu kaita gidan mari ba,Shiyasa duk son kukanta ta bame Bakinta gam sai da na zucci a haka suka iso gidan Danmallam Dake kofar arewa.
Yana hon megadi yazo ya Budemai get din gidan ya sulala da Motarsa parking space sai da ya gama Daidaita motar kana ya kashe ta ya Fito har Lokacin Amina na zaune ta kasa Motsi sai da ya fita yana gaisawa da Buzun megadinsa yaga bata fito ba kai ya girgiza Booth ya Bude ya Fito da Kayanta ya ijiyesu nan Kofar Falon kafin ya isa wajen motar ya Bude mata Murfin yana fadin"Sai nace ki fito sannan zaki fito ko me kike nufi..?
Dasauri ta fito tana faman sharan kwallah ko kallonta bai yi ba yayi gaba ya barta nan tsaye yana kallonta bai ce mata komai ba ita kuma Tsoro take ji kada tayi wani abu yace zai kaita gidan mari duk da bata taba zuwa ba,Ai Baba mallam na kai ziyara Lokaci bayan Lokaci yana zuwa tare da Aba ko su ya shamsu har jawad an sha zuwa dashi tana jin labarin yadda ake gana musu azaba abakinsu ina zata yi wani abu wannam mara Imanin ya mikata chan kafin Su Baba mallam su ji labari su je su karbota ta kusa mutuwa..!
Shi kuma yana ganinta Tsaye yayi kamar bai ganta ba Yasan in ya bar mata kayan bazata iya Dauka ba yasa ya Fara Dauka yana shigar mata dasu Cikin Falon gidan
Yazo Daukan na karshe ne ya Dago yana kallonta cikin Haushinta yace'"Shima sai nazo na kama hannunki na shigar dake gidan sannan zaki shiga..?
Jin haka yasa tayi saurin wucewa gaba shi kuma yabi bayanta.
Tana shigowa Falon suka hada ido da Sakina data fito daga Dakinta Cikin kwalliyarta Less ta saka riga da Sikat sun kamata ta shaba kwalliya kamar wacce zata je gasan kyau na Duniya bakinta Cingam ne tana Taunawa kas kas kafarta cikin wani takalmi mai Dubu kallon kallon suka tsaya yi da Amina cikin kyama da wani Tsana take kallonta ita kuma Amina sai ta kasa gaba ballatana baya saboda ganin Sakina shima daya shigo ya ganta sai yayi kamar bai ganta ba Tun bayan tafiyar Anty mgana bata Kara Hadasu ba Dakinta ta shige shima ya shiga nasa har ya je amsa kiran Mallam bai sata a ido ba jidalin Dake kansa sun ishesa inda zata gane da ta barsa ma yaji da abunda ke Damunsa..!
Ta gefen Amina ya raba ya wuce ko barayin Sakina bai kallah ba Dakinsa ya Nufa zai Bude yaji a kulle Cikin mamaki ya juyo yana kallon Sakina kafin yayi mgana ta wucesa zuwa kan Daya daga cikin kujerun falon ta Zauna ta Dora kafa Daya kan Daya Tana cigaba da Taunan cingam tana kas kas..!
Ransa ya baci ganin Amina Tsaye awajen yasa ya sausauta Cikin sanyinsa yace"Waya kulle Dakin nan Sakina..?
Ina key din..?
Sakina ta kallesa Cikin wani Bakinciki yau ita ce ke shakan Numfashi da wannan yarinya a matsayin Mijinsu Daya gaskiya Umar ya gama Cutar da ita.
Kai ta kauda batayi mgana ba ya kara Sausauta Murya yana fadin"bada ke nake mgana ba Sakina..?
Sakina ta wani kallesa a karkace kafin ta Hura bakinta ta saki kwan cingam din Dake Binta ta wani Rausayar Dakai Cikin Wani yanayi tace"Makullin na hannuna..Ni kuma na kulle Dakin..!
Bai ji mamaki daman yasan ita zata kulle ba kowa ba cikin son kara nazarinta yace"Saboda me yasa kika Kulle Dakin bayan na Fadamiki Hajiya tace yarinyar nan ta zauna aciki..!
Sakina ranta daman yana bace ne ga Kishi kawai sai ta mike tana fadin"Wlh Umar baka isa ka Tozartani ba..Ni zaka wulakanta bayan auran wannan yarinyar da kayi ban ce komai ba..Shine saboda a kara Kuntatamin sai ace Dakin mijina zata zauna..? To wlh bazata sabu ba...Ko Mijin bazan raba da wannan kuchakar yarinyar ba ballatana Dakin miji..Bazai taba yuyu ba..!
Tafada tana bayyana bacin ranta Hannu kawai ya kama a

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login