Showing 132001 words to 135000 words out of 265571 words

Chapter 45 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28936

Fadin"Abinci ya yi saura..?
Cikin mamaki tace"Menene..?
Yana Tafiya wajen Dinning yace"Zuba ma yarinyar chan a filet ki shigar mata dashi..Sannan Daga yau ki rika Dafa abinci da ita kin ji ko..?
Sakina kadan ya Rage bata Danna ma Umar ashar ba sai ta Tuna mijinta ne ammh sai da ta Hararesa kafin tace"Nine ma zan rika girka mata abinci ina aika mata Dashi Daki ko..?
Kai Tsaye yace"Haka nace..!
Sakina ta kallesa Daga sama har kasa kafin tace"Saboda wani Dalili..? Ka manta kai kace Matsayina da nata Daya ne..?
Bai son doguwar mgana yasa yace"Saboda ita yarinya ce..Kuma Amana ce a wajenmu..!
Sakina ta yi shewa kafin tace"yarinya kuma suka aura maka ita..?
Amana kuma ai takace ni dai ba wanda ya bani wata amana..!
Gani yayi zata raina masa wayau yasa yace"Su wa kike mganar sun auramin ita cikin Raini Sakina..?
Yafada yanayinsa na sauyawa ganin haka yasa tayi saurin cewa"Ni fa ba su nace ba..kawai dai kai ma baka taki adalci ba..Zan Dafa abinci ammh wlh bazan Dafa mata na Bita dashi adaki ba in ta fito shikenan in bata fito ba ita ta sani..!
Tana gama Fadin haka ta Mike Dauke da wayarta zata shige Dakinta ya Daga Muryansa yana fadin"bazaki zuba mata ba kenan..?
Juyowa tayi kafin ta kallesa Duk da ta tsorata da yadda ya Hade ransa ammh wlh bazata zauna tana Boyin boyin Amina ba, yasa kai Tsaye tace"Eh..Kai ka zuba ka kai mata tunda ta zama Dolenka ammh bani Sakina ba..!
Daga haka ta shige ta barsa ya bita da kallo bayason Fitina ne yasa bai bi ta kanta ba ya isa ga kular abinci ya Dauki Filet ya Bude ya zubama Amina Daidai ya rufe ya Daukar mata Ruwan gora guda Daya mganar Mallam kawai yake tunawa yasa zai taimaketa kada Cutar yunwa ta mata Lahani fatansa Visar? sa ta fito wannan Satin ya saka kafa ya tafi sai yaga karyan iskanci daga ita har Sakinan sai su kashe junansu shi ba ruwansa.
Sanda ya koma Daki tayi wanka sai dai abun haushi kayan jikinta ta maida nan kasan Cafet ya ijiye kayan hannunsa yana hararanta? kafin yayi mgana ma ta mike jikinta na rawa tana fadin"Ban..baga kayan bane..!
Ghanas dinta ya nuna mata yana Fadin"Ai kinsan kayanki ne acikin nan ko suma sai na ciro na saka miki..?
Da Sauri ta girgiza kai ta wuce sumi sumi wajen jakunkuna ta Duka ta Bude Daya taga Littafan makarantar ne aciki sai da ta Bude Dayan ne taga kayan a goge sai da tayi hawaye tasan aikin Mamanmu ce ko Hamida aranta tace Allah sarki Hamida da hanne ina kewarku..!
Wata Doguwar riga ta Dauko na Material sai bakin dankwali,zata maida ta rufe yace"Ciro wani Hijabin ki Cire na jikin ki malama..!
Ba musu ta ciro aranta ta kudira ta gama mai gaddama gashi mara imani ga mganar Aba ayadda take din nan bata fatan ta kara yin wani abun da Aba zai yi Tir da ita,Tayi alkawarin har Abada an dai kaimasa kararta.
Kayan ta Dunkule Cikin Hijabinta ta gabansa ta wuce zuwa Tiolet chan ta Sauya kayan ta Sake fitowa da na hannunta yana Dakin bai fita ba ganin zata maida masu Dattin Cikin jakar yasa yace"ke wai meke damun ki ne..?
Masu dattin zaki maida Ciki kuma..?Common maida su Tiolet akwai kwando Dogo ki saka aciki nan zaki rika tara kayan Dattin da kika cire..!
Sumi sumi ta koma ta saka a inda yace sannan ta kara fitowa abinci ya nuna mata yana fadin"Ki zauna kici..Wannan shine na karshe da zan kawo miki abinci ruwanki ne ki Fita ki nema ruwanki ne ki zauna da yunwa..Kin ga dai ishara ko..?,Ita yunwa ba"ayi mata Taurin kai..!
Ba musu ta zauna Daman yunwar take ji dan Tea din Data sha ta Amayar dashi kama hanyar fita yayi kafin ya Juyo yana kallonta har taja Filet din gabanta Hararanta yayi ta kasan ido take kallonsa kanta na kasa cikin Sanyinsa yace"Ki tabbatar kuma kin sanya duka kayanan cikin wardrope bna so na kara ganinsu anan wajen kin ji ko baki ji ba..?
Da kai ta gyada mai kafin tace"To..!
Bai kara mgana ba ya fice ya ja mata Kofa kamar tana jira ta Fara cin faten Dankalin hannu baka hannun kwarya sai da ta da shi duka ta kora da ruwa sannan ta kara da sauran Tea din Dazu su Amina har ana lashe Filet,Sai Lokacin taji ta dawo daidai Ajiyar rai ta Sauke ta yaye Hijabin jikinta tana kara shan iska sai da ta huta sannan tatashi taje ta wanke hannu,ko ta kan Filet da kofin batayi ba ta fara Bude kayanta tana watse su a kasa domin bata son ya sake shigowa ya gansu Allah kadai yasan me zai mata in batayi abunda yace ba tana Tunanin su ya jafar ne mugaye sai yanzu take fahimtar akwai wanda ya Shafe su a mugunta ya Danmallam Tana da tabbacin daga shi har shegiyar gajerar matar nan tasa basu da Imani gwara ta bisu a sannu su wanye Lafiya.

A wardrope din ta saka kayan kamar yadda yace,ba komai acikinsa sai Rigar barci Daya da Jallabiya guda Biyu Saman Madubi kuma sai Tararuka Amina ta matsar da su gefe ta saka kayanta aranta tana fadin ita yar Saudi bata ijiye kayanta anan ba kenan..?
Har da littafan makarantar ta da takalmi da jakar Cikin wardrope ta Nausa su ta hada da ghanas din duka ta Tura kada dai yazo ya gani kafin ta gama bayanta ya kage ta koma ta zauna bakin gado tana Tuna Hamida afili ta Furta"Allah sarki Hamida kin sha Fadamin watarana baki tare dani zan tuna dake..Sai gashi Kaddaran data Rabani dake ko kwana Daya ban yi Cikinta ba na Tunaki hamida..!
Sai hawaye ta tabbata da Hamida na nan tare da ita duka wannan aikin ita zatayi Kan gadon ta koma ta Dunkule tana kukanta na fama sai da taji sanyi ya isheta ne sannan ta tuna batayi sallar mangriba da isha"i ba..dole ta mike ta koma Tiolet din ta Dauro alwala tazo ta Daidai ci gabas tayi sallarta tana idarwa ta kwanta nan Saman Cafet din tana Tunanin rayuwarta a wannan gidan,Sai kuma ta fara kuka kewar yaya ta isheta Sai kuma ta ji mutuwarta ta dawo mata Sabuwa sai kuma ta tuna da mamanmu da su Hamida sai kuka wiwi har barci ya kwasheta tana kuka bata sani ba.
Da safe tana tashi da filet da kofunan taci karo tana idar da sallar asuba ta makara sai da gari ya waye ta tashi ta Dauke duka harda goron ruwa ta fara Tunanin in da zata kai domin in wannan dan bala"in yazo ya gani kashinta ai bushe.
Yanke shawaran fita tayi ta kai kitchen daman ya sa mata sabon suna wai kazama ai in yaga wannan sai ya kara kiranta da Hujja..
Koda ta fito shuru falon ba kowa sai da ta leka ta tabbatar da ba kowa sannan ta fara Tafiya Sadaf Sadaf zuwa Kitchen ai tasan hanyar tunda sun taba zuwa.
Tana shiga kitchen din nan ma ba kow????      

                  ! " # $ % & ' ( ) * + , - . / 0 1 2 3 4 5 6 7 8 9 : ; < = > ? @ A B C D E F G H I J K L M N O P Q R S T U V W X Y Z [ \ ] ^ _ ` a b c d e f g h i j k l m n o p q r s t u v w x y z { | } ~  ? a sai dai tas kitchen din ba Datti kamar ba"a girki a wajen saman Cabinet din kitchen ta ijiye kayan hannunta ta juyo kenan zata fito suka kusa cin karo da Sakina data ganta sai da gabanta ya fadi ta ja baya tana Zare ido.
Sakina Dake sanye da Riga da wando na plazo ta kalli Amina Daga sama har kasa cikin kaskasci kafin tace"Me ya kawo ki kitchen dina..?
Amina ta kalleta taso tace ne bata sani ba ammh kuma bata da wannan karfin gwiwan yanzu ta kanta take yi yasa batace mata komai ba ta raba ta gefenta zata fita ran sakina ya baci ta Finciki hijabinta ta Dawo da ita baya ta Shake mata wuyan Hijabi tana Fadin"Ke don ubanki ni nake miki mgana kina sha min kamshi..?
Tafada tana Zare mata ido Amina ta kalleta ammh ta kasa mgana aranta Tana Tunanin Sakina tazo Lokacin da Bazata iya maida mata martani ba..Ammh ta bari wanchan mara imanin ya tafi wlh bata zagi Aba a banza ba sai ta rama mai.
Ido ta dago karaf suka hada ido da Danmallam dake tsaye daga falo yana kallonsu yana sanye da Jallabiya baka da Hula Cashaba ce a hannunsa kamar Dawowarsa kenan daga masallaci.
Amina tana ganinsa sai da gabanta ya fadi da sauri tace"Kiyi hakuri abu na kawo..!
Sakina zatayi mgana kenan taji Muryansa daga bayanta yana Fadin"Saketa Sakina..!
Sai Lokacin ta juyo tana kallonsa sannan ta saketa ammh sai da ta Murje mata kafa da takalmin Dake kafarta Amina taji azaba ammh bata nuna ba Da sauri? ta fice Daga kitchen din kamar ta kifa ko barayinsa bata kallah ba ta koma Dakin datake tana shiga ta Dafe kirji tana Sauke Numfashi kamar wata mara galihu haka ta koma saman cafet ta zauna tayi Tagumi bata son hawa gadon ne bata saba da irin shi ba sannan ta saba kwana cikin mutane,akwai watarana ma da ita da Hamida suke kwana agado daya hamida tayi ta mitan ta matseta ammh Amina ta mata Burus wai ga inda Rayuwa ta kawota ita kadai kamar mara galihu.
Tunda ta shigo Dakin bata kara jin motsin su ba sai chan rana Sakina ta shigo Lokacin har barci ya fara Fizganta koda ta Bude ido sai taga ta Dungurar mata da Filet din abinci tayi Tsaki ta fice Daman yunwar Amina take ji domin tayi alkawarin daina zama da yunwa in ta mutu Danmallam da matarsa basu da asara.
Data gama da Filet din ta fita takai kitchen bata ga sakina ba yasa ta Tsaya ta Bude Fridge ta Dauki ruwa ta sha ta Koshi ta koma Daki da Daddare ma Sakinar ta kawomata Fuskar nan tata kamar Hadari saboda hadewa,Ta ballama Amina Harara Dake zaune taba kallonta sai da ta fita taji Dariya ya kamata aranta tace bani kadai yake ma Mugunta ba harda matar tasa tasan badomin shi ba Bata isa Sakina ma ta kalleta ba..
Kamar ta sani tun abunda tace mai jiya da Daddare ya dinga Daure mata shiyasa sai ta ganshi sai ta zuba abincin ta kaima Amina tana cika tana batsewa shi dai ko kara bi ta kan Sakina bai yi ballatana Amina,ita kuma Sakina Dadinta Daya ganin Aminar da ita da banza duk daya a wajen Umar sannan suna waya da Anty Amarya tana fadamata komai ita tace tarika bama Amina abinci ba komai suke da nasara..
Washegari tun safe Umar ya fita kan mganar Visa dinsa kano yaje tunda ta chan zasu tashi sai dare ya dawo an samu Visar nan da kwana Hudu zasu tashi,Farinciki ya ishesa sai kuma aranar yaje chan Gida bayan tafiyarsa da Amina sun hadu da Aba yayi ta mai fadan kada ya saurarama Amina in tayi mai wani abu yayi mganinta kada ya Ragamata shidai bai ce komai ba.
Taya ya zai biyema Aba ya taba Amina hajiya ko mallam su ji labari ai sai su Tsine mai ya samu dai ya lallaba ya kara gaba ba"a gansa ba ballatana ace wani abu.
Tare da mallam sukayi sallar isha"i Daganan ya shiga cikin gida ya gaida matan mahaifinsa,Shashen Hajiya ne na karshe,ya shiga tana zaune afalo tana gyaran farcenta ya zauna nesa da ita a kasa suka gaisa tana tambayansa Amina yace tana lafiya.
Shuru na wani Lokaci kafin ya muskuta yana fadin"Hajiya na samu Visa ina ga nan da kwana hudu zan tafi..!
Hajiya ta Dago tana kallonsa kafin tace"Allah ya kaimu..Allah kuma ya Tsare..!
Kansa na kasa ya amsa da Ameen kafin Hajiya tace"Yanzu ba da ita Sakinar zaka koma ba kenan..?
Kai Tsaye yace"Eh Hajiya..!
Hajiya tace"Ai shikenan ma da nazata da ita zaka koma nayi ma mallam mganar Hamida da hanne su koma chan su taya Amina zama har ku dawo..!
Yana jinta bai ce komai ba tacigaba da Fadib"Ammh tunda ta na nan shikenan..Sai dai kafin ka tafi zaka siya mata ko karamar waya ko Danmallam..?
Kansa na kasa kafin ya Dago yana Fadin"To Hajiya sai a siya mata..!
Hajiya tace"Ya kamata gaskiya tunda kaga itama Sakinar nada wayarta. sannan in ka tafi chan sai ku dinga mgana ta wayar da zaka siya mata hakan zai fi..!
Danmallam dai nasa cewa to ne Domin Gata kan Amina ta fisa gata a wajen su Hajiya.
Shuru ya kara giftawa na wani lokaci kafin tace"yaran nan ma yan"uwanta har yanzu basu saki da kewar Amina ba..Nace zasu je mata cikin Satinan tunda ma zaka tafi bari in ka tafi sai su tafi su mata ko kwana Biyu ne nasan zataji Dadi..!
Dan mallan kansa na kasa aransa yace"Zataji dadi tunda abokan iskancin nata suna kusa da ita..!
A fili kuma bai ce komai ba Hajiya ta shiga Fadamai zata je maidguri Cikin watanan yar yagana zatayi aure ya Dago yana fadin"Hajiya daman tana da wata ya agabanta ne..?Na dauka Suhailu ne kadai autanta..!
Hajiya tace"A"a tana da karamar ta zaituna itace zatayi aure..!
Bai wani damu ba yace"Allah ya kaimu hajiya..Allah ya bada zaman lafiya ke kuma Allah ya kaiki lafiya ya Dawo Dake..!
Ta amsa mai da Ameen kafin tayi mgana Hanne da Hamida sun shigo Falon suna ganin ya Danmallam suka natssu suna gaishesa ya amsa yana kallonsu ganin yadda sukayi wani iri Hajiya ta kalle su tana fadin"Nasha chan zaki yi kwanciyar ki hanne..!
Hanne batayi mgana ba kanta na kasa Hamida ce tace"ni ce zan kwana anan Hajiya..!
Hajiya tace"Shikenan yau dai kun ma Balaraba Yaji..Ita kadai sai jawadu..!
Basu ce komai ba kansu na kasa Hamida ke taba hanne ita kuma taki mgana Hajiya ce ta gansu Dariya tayi kafin tace"Ku sha kuruminku..Karshen sati zaku je kuga Amina..!
Baki suka washe suka hada baki wajen Fadin"Da gaske hajiya..?
Hajiya tace"Yanzu ma muka gama mgana da yayanku..!
Suka wani daka Tsalle suka Rumgume juna wani kallo yayi musu dayasa suka natsu waje daya ganin haka yasa ya mike yayi ma Hajiya sallama ta amsamai tare da cewa"Kace ma Amina su hanne na nan zuwa zasu zo mata da sako tayi hakuri..!
A kasan makoshi ya amsa ma Hajiya kafin ya fice Daga Shashen yana jin ihun yaran bayan ya fita kai ya girgiza kaawai.
Falom Mallam ya koma sukayi sallama shi da Aba ne suna mgana Daganan ya shiga motarsa zuwa gida koda ya koma Sakina ta gama komai taci kwalliya tana jiransa ta tarbesa ta taimakamai yayi wanka ya sauya kaya suka fito saman Dining suna cin abincin sai alokacin ya kalli Sakina yana fadin"Kin kaimata abinci..?
Sakina ta amsa mai da kai,Yaji dadin haka kai tsaye yace"Allah yayi miki albarka..!
Tana Mirmishi mugunta ta amsa mai da Ameen Ameen domin ta gama wasa wukanta jira take ya saka kafa ya Tafi sai Amina tayi nadama wlh.

*********

Washegari..
9:30am.

Adaidaita ta shiga yana ta Gudu da ita kamar zai bar garin gumel da ita sannan naga ya Tsaya bakin hanya inda ba yalwar giftawan abun hawa Fitowa tayi sanye da Hijabi Dogo har kasa ga Nikab a Fuskarta karamar Jakarta ta Dauko ta bashi kudinsa kafin ta fara tafiya ta mike wata Hanya tayi tafiya sosai kafin ta fara Hango ta tana zaune saman wani Dutse tana jiranta sai da ta tazo gabanta sannan tace" Aci balbal Fitilar sharri..Ko babu mai kina kai safe. Kwalba ko kin fashe da sauran sharri kibiyar ajali kike mai Ratsa rigar karfe..Madina ikon Allah gabanki Fari bayanki baki..!gaba salamun baya salamun damisa mai maida Fatar kura nama..!

Wata irin Dariya Anty Amarya ta saki Lokaci Daya tana mikewa tsaye hannu ta bama ta Tsayen suka tafa ji kake tas..kafin tace"Ban kai ki sharri ba Dayyaba..Domin ni daman chan ban taba aron Fuskar salihai ba..ke kuma fa kin fini zama kwalbar sharri..An aminta Dake kin ci Amana sannan a yarje miki kin yi ha"inci..!
Tare suka kara saka Dariya kafin ta yaye Nikab din data Rufe fuskarta sai ga Mamanmu ta bayyana..!
Cikin wani yanayi tace"Babu abunda zan ce da ke madina..Sai Allah ya Cika miki naki Burin..!
Saura kadan na gama mallakan Sa"iduna a hannuna madina kiris ya rage .!
Anty Amarya dake sanye itama da Dogon Hijabi tace"Kwarai naga alama..Ammh meyasa kika batamin Lokaci kinsan tun yaushe nake tsuggune anan wajen ina faman jiranki..!?
Mamanmu tace"sai da ya fita sannan na samu na fito daga gidam..Kinsan dai yanayin da ake ciki..Lokacin da yaya nan ne nake samun fita akai akai in nace zan shiga gidanku yanzu kuma gida ni kadai ce Hamida na makaranta ita da jawaad..Kuskure kadan zan yi sai kiga na bata komai..!
Anty Amarya tace"kiyi hanzari ina kan hanya ne..!
Ba musu ta Bude Jakarta ta Dauko Kudi masu yawa ta Damkama Anty Amarya tana fadin"Shashashan wai fa bani yayi nayi ma Amina siyayyan kayan amfani shine nayi sama dasu..!
Anty Amarya tayi dariya kafin tace"Shegiya Balaraba...!
Mamanmu tace"kul..Dayyaba nake in kika Kirani balaraba kamar kin Ragema Kwalba sharri ne..!
Tare suka kasa Dariya kafin Anty Amarya tace"Mallam fa ya fara korafin kin Daina zuwa yanzu sai dai nazo ni kadai kada ya fara Tunanin ko dan kin Samu Biyan Bukata ne..!
Mamanmu tace"ki kai masa wannan kudin na karin kudin aiki ne..Mganar zuwana kuma in zaki koma dani zamu koma nace miki nan da Sati Biyu zan je gusai bikin gidansu..Sai na Fake da Guzuma na Harbi karkasa..!

Anty Amarya tayi dariya sosai kafin ta Fito da jakarta babba ta Tura kudin aciki kafin tace"Shikenan bari nayi hanzari..bana so nayi Dare..!
Kallonta tayi kafin tace"Kwana zaki yi..?
Kai Tsaye tace"Eh in nayi Dare sai gobe zan dawo..Zuwan daman na Sakina ne so nake Mallam yayi aiki kan Umar ya koma da ita madina..!
Bana son zamanta da wannan shegiyar Yar taki..!

Mamanmu ta bata rai kafin tace"A"a fa ki bari madina..Allah ya Tsareni ni Uwar Zulfa nake da Zahra kuma uwar Hamida...!
Anty amarya tayi dariya kafin tace"Mamannu...Mamanmu ..!
Tana kwaikwayon muryan Amina aatare suka fashe da Dariya suka tafa Kafin mamanmu tace"Uwarta na kabari..!
Wani Tsari kika rakata ne ni ban kara ma bi ta kanta ba tun sanda ta bar min gidana..!
Anty amarya tace"Tsarin auran ya zo a banza ya kare a banza..Domin Sakina ta tabbatarmin ita da banza Duk Daya suke awajensa..Kinga kenan haka zata gaji da zama har mallam da Hajiya da suka kulla abun su gaji su Rabashi..Sannan nace ma mallam ya kara mata rashin kunya da Tijara tayimai ya Sako shegiya..!
Mamanmu tace"Ni kuma Daga Lokacin zan karata gaba..Bana son na kara bude ido na ganta agidan nan har Abada gidanan nawa ne ni da ya"yana..!
Anty Amarya tace"Kadan zaki jira..Burinki zai gama cika..!
Ni ce dai naga Tafiyata akwai Tsawo..Burina

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login