Showing 63001 words to 66000 words out of 265571 words

Chapter 22 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28943

ke kika fada!
Hamida tace"Ni kuma..?
Amina ta Bude baki zatayi mgana keman Idonta ya Fada kansa yana Tsaye Daga Kofar gidansu bai yadda sun kariso da Motarsu ba Tana baya Nura ke ciki yana kallon Ikon Allah
Sun fi awa Daya suna wajen nan agaban idonsu Motan makaranta tazo ta Sauke su Amina suka Firfito.
Ko alama bata manta dashi ba gani su Hamida sukayi hankalinta ya koma Chan gabansu yasa suka juya suna kallonsa yana Tsaye sanye Cikin Riga da wamdo bakake sai ya Dora Farar Jaket ya saka F.cap ya Rufe Fuskarsa sai dai ya Janyeta kadan.
Amina cikin mamaki tace"Laaa..Kai ne..!?

Mirmishi ya sakar mata kafin yace"Nine..Amina kina Burgeni..!
Fadin haka da yayi yasa ta washe baki ta fara takawa gabansa shima ya tako suka Tsaya daidai kofar gidansu Amina Hamida da Hanne suka saki baki suna kallonsu.
Amina Hannu ta Fara tafawa tana Fadin"Kai..Daman ina neman ka..?Ashe kai mawaki ne bansani ba..?
Ido ya zaro yana kallonta kafin yace"A ina kikaji..!?

Kai Tsaye Amina tace"A wayar wata yar ajinmu mana..naji suna mgana suka ambaci mai irin sunanka nace anunamin Hotonka kuma Wlh kai ne..Yauwa daman ina ta so na Fada ma su hanne don Allah ba kai kace ina Burgeka ba..?
Kallonta kawai yake yi yanjin wani Farinciki sai da ya ganta ya kara ganin yarintarta tana mgana ko Tsayawa ta kasa yi.
Kai ya gyada mata yana kallonta juyawa tayi ta riko hannun Hanne da Hamida ta kawo gabanshi tana Fadin"Yauwa don Allah sake fada musu..Kila su yarda..!
Tafada tana wani juya ido Dariya abun ya basa cikin gyara Tsayuwarsa yace"Amina Kina Burgenii..Wani ya Taba Fada miki u are so Beautifull..!
Amina taji wani Sanyi acikin ranta Cikin Alhafari ta kalli su Hanne da mamaki ya sa suka kasa mgana tace"Kun ji ko..?ai in na Fada muku sai kuce Karya nake..Nima fa ina Burge mutane
Kunga wannan babban mawaki ne yana tare dasu Umar.m sharif..!
Dasu Ani nihu kasan su ko kilama abokan ka ne..?
Take Fada tana kallonsa Cikin Dariyarta Kai ya gyada mata Cikin Dariyarta yace"Ai Ani nuhu abokina ne..yama ce yana gaisheki..!
Ido ta zaro kafin tace"Da gaske.?
Ya sanni ne..?
Yana Danne Dariyansa yace"Sosai ai yasan Amina..Amina ta Gumel abakin Aminu..!
Amina ta Dafe kirji Murna Duk ya Cikata Hanne taja gefen Hijabinta tana Fadin"AMINA kada wani ya fito fa ya ganmu fa.?
Hamida kuwa uwar tsoro sai waige take yi kafin tace"Amina kin sanshi ne..?
Hijabinta ta Fizge kafin tace"Dillah..ku na sanshi fa..Shagon chan muka hadu kwanaki da mamanmu ta aikeni..!
Har yace ina Burgesa ko..?
Tafada tana wani juya ido Kai ya gyada yana kallonsu Hamida kafin yace"Sosaima
gaskiya kuma Laifin ku ne da baku taba Fada mata ita din abar Burgewa bace!
Amina ta washe baki kafin tace"Kun ji ko..?yauwa gayamusu..Ni da suke cemin ina naga abun burgewa
Sai ma na gundiri mutane da Halina..!
Tafada tana bata Fuska da Sauri yace"Kada ki damu..Ni kina Burgeni..!
Hamida taga Amina ta Zake da yawa hannunta ta Fincika tana Fadin"Amina kada wani ya ganmu fa..?
Hanne tace"Bawan Allah don Allah ka tafi jidalin Amina ne kawai..In wani cikin yan gidanmu ya ganmu Dakai yau mun shiga uku..!
Amina ta kwace hanmunta tana Fadin"Dillah sai me..?iyaka duka ne kuma baya kisa..!
Hanne tace"Baba Mallam kinsan baya nan bamu da maceci sai Allah Amina..!
Wa kika taba ganin ya tsaya da wani..?ko su ya Abida kin taba gani..?
Amina ki shiga Hankalinki..!
Sai kuma tayi shuru ta tsaya tana kallon Hanne kafin tace"Kuma fa hakane..muje..bawan Allah sai an juma..Yauwa don Allah ka kara gaida min Ani nihu..!
Hamida tace"A ina kikasan Ali nuhu mu da ba kallo muke yi ba..?
Amina tace"Dillah Ani nihun ne baki sani ba..?dan wasam hausa fa ki bari gobe zan nuna miki hotonsa a bakin Unity ashagon nan ma kusa da shagon Bola gasu nan kala kala!
In Tana mgana Nishadi ke kamasa Shiyasa ya shagala yana kallonta baisan sun wuce ba suna gabda Shiga gidan ya Daga Muryansa ya Kirata.

Amina..!

Dukkamsu suka juyo suna kallonsa Cikin wani yanayi yana kallonta yace"Wlh da gaske nake yi kina Burgeni...
Sannan KUma..INA SON KI..!
DAM!!
dukkansu gabansu ya Fadi Amina ta zaro ido ya sake Daga mata kai kafin yace"Wlh da gaske nake ina sonki.!
Zan dawo ki jirani..!
Yafada yana kallomta Hanne da Hamida ta kallah kamar sun ga abun Tsoro suka Rumtuma suka shige gidan da gudu kai ya girgiza kafin ya Furta"Finally dai na gano abunda ke Damuna
Son yarinyar nan nake yi..!
Daga haka yajuya ya fara Tafiya wajen Mota Nura na ganin haka ya Tuko motar zuwa gabansa da azama ya Budamai gaban Motar ya shiga ya maida ya Rufe suka fara barin anguwan ammh Idanuwam Aminu na kallon Kofar gidansu Amina kamar tatafi da ransa Nura na binsa da kallonn Tsausayi.
Nura ya kada kai kafin yace"Ina muka Nufa Oga..?
Idanuwaansa na shigewa kamar mai barci yace"Mu koma Hotel..Nura son yarinyar nan nake yi..Bazan koma kano ba sai na samu Soyayyarta..!
Nura yace"Ta wata hanya..?
Dokar gidansu ce ba sa soyayya kuma na Fada maka..!
Bai damu ba kai Tsaye yace"Koma ta wata hanya ce
zan sakata ta soni
In ta soni komai mai sauki ne..!
Nura ya kasa mgana ya fara Tunanin Amina mayyace ta kama Ogansa.

Su kuma su Amina a haraban gidan sukaci Burki suka tsaya suna maida Numfashi.
Hamida tace"Amina mutumin nan bai da Hankali ammh ko..!?
Hanne tace"Ke ina ga wasa yake mata..!
Duk Amina na jinsu karo na Farko yau aka taba cewa ana sonta acikin Idanuwaan Aminu gaskiya ta gani ita kanta Zuciyarta ta kasa Fassara yanayinta yasa ta Biye ma su Hamida da Fadin"Bai da hankali..Inaga bai da hankali..!
Kai suka gyadata mata atare suka Furta"Gaskiya bai da hankali..!
Da haka suka watsar da mganar sukanufi Cikim gida Ammh banda Amina ta kasa goge Kalaman Aminu ko wani juyi tayi acikin Ranta sai taji muryansa.
Amina..Kina Burgeni..Kuma WLH INA SONKI.!
Batasan Dalili ba taji abun ya zauna acikin ranta sannan tana ji tana so ta kara ganinsa taga wannan Gaskiyan Data gani acikin idonsa..!




Mafarin komai...!






*Janafty*


*TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janaftyd'?*



*
Da gaske yake yi Duk abunda ya fito Daga cikin zuciyarsa bai gasgasta haka ba sai da ya koma kano ya kasa zama kwana uku yayi ya saka Nura ya Tukosa zuwa Gumel,batare da Amina ta sani ba yake Bibiyanta ahotel yake zama In garin Allah ya waye zai zo kofar gidansu Amina Daga baya domin yaga tafiyarsu makaranta da Lokacin dawowarsu da Lokacin Tafiyarsu islamiya wasa wasa sai da yasan komai na Amina sannan yana Bibiyan dukkan Motsinta,Batare data sani ba Nura gajiya yayi ya koma Abunsa Tunda yaga alamun Ogan nasa ya kamun da gaske.
Baya sati bai shigo Gumel ba,Duk saboda Amina zai zo ya ganta yaji Sanyi aransa koda bata gansa ba koda bata sani ba ya gama yardan ma kansa Amina ta shiga ransa ta samu matsugunnun da bai zai iya cireta ba komai nata yana Burgeasa ne..
Amina bata son Aminu na binta ba Ba kuma wai don ta manta da mganarsa ba akowani Shafi na Tunaninta kalamansa bai bace mata ba sai dai Tundaga Ranar bata kara yarda sun kara mganar da Su hanne ba suma sun Dauki abun a wani abu dabam shiyasa suka watsar da mganar suka Cigaba da Harkokinsu.

Bata taba katarin ganinsa ba,Sai watarana sun dawo daga islamiya,Idi bai zo Daukansu ba Motar tana ta basu matsala ya shamsu ya Tarkasu su ya Abida ne ke baya su kuma suna gaba su uku kamar koda yaushe Sa"adatu na baya tare da sabeeha da Umaima ya shamsu da su ya Akilu suna bayansu sun taso su gaba Kafa kafa Hira suke a tsakaninsu Labarin littafi Amina ke bama su Hannu kasa kasa suna Dariya sun kawo kofar masallacin Baba mallam kamar an ce ta Daga kanta sama ta Hangosa abakin Masallacin yana Tsaye cikin irin Shigarsa kamar ko yaushe da Jaket baka Baki ta saki da Hanci tana kallonsa Cikin mamaki Farinciki yaji yau daya ganta ta gansa Hannu ya Dagamata Lokaci Daya da Mirmishi.
Su hanne sun juya suga me take kallo kamar ya sani ya Duka kamar yana Gyara igiyan Takalmi sai basu gansa ba Amina suka koma suna kallo kafin Hamida tace"Wa kike kallo Amina..!?
Sake kallon wajen tayi sai kuma taga bashi a wajen ta fara waige waige Ya Nasir ta gani yana Daukan Buta sai ta Fara Tunanin ko gizo yake mata yasa tayi saurin cema Hamida bakomai..!
Ta Dauka bashi take gani ba sai da washegari ta kara ganinsa Lokacin sun fito zasu islamiya,shima ya Ganta ya kuma mata Mirmishi gani na ukun da tayimai da Safe ne Ranar asabar zasu tafi Hadda ta fito tana jiran Hamida jikinta ya fara rawa Yana Daga Tsallaken su chan bakin wani gida Wannan karon bayan Mirmishi har sai da ya Daga mata hannu ta fara Tsorata tana Tunanin kodai ba Mutum bane Kila aljanine Datake ganinsa a ko"ina kuma ta kasa Fadama ko Hanne haka kurum bakinta yayi nauyin data gaza Furta komai.
Daga Lokacin kuma duk sanda ta fito gida sai tayi waige waige ko zata gansa sai dai bata kara ganinsa ba sai ta yadda da Tunaninta kila gamo tayi da aljani.
Harta da su Hamida sun fahimci kwana Biyu Amina ta rage karkasashinta da suka tambayeta sai tace bakomai basu damu ba sanin Halinta Lambo take halinta na tashi ne Lokaci bayan Lokaci kamar mai Bugawar jinnu.
Bata kara ganninsa ba sai bayan Shudewar kwana Hudu tsakani ta kara ganinsa a gabda gidansu Ranar Wata Laraba sun dawo daga makaranta,Gidansu Hanne ta Tsaya sai da tayi sallar mangariba Hanne ta Rakota Mazan gidan duk suna masallaci Baba Mallan na wa"azi
Har hanne ta rakota kofar gidansu suka Tsaya suna mgana yana Daga gefe basu ganshi ba har Hanne ta juya ta koma gida ita kuma ta juya zata shiga gida Taga mutum yasha gabanta.
Ta firgita taso ta yanka Ihu ne sai ya Hasko hasken wayarsa lokaci Daya yana fadin"Nine..Amina..!
Taji muryansa ai ta Haddaceta kamar Karatu Cikin tsoron da bata taba jiba ta fara waige akwai hasken a wajen Karo na farko taji mganar su Hamida in wani ya zo ya ganta fa..?
Abu ne da bai taba Faruwa ba..!
Tana ji yana Fadin"Amina kin bani Wahala..?wlh da gaske ina sonki..baki ga yadda na koma saboda ke ba...?

Yake fada yana kallonta da Dukkan Zuciyarsa Jikinta ne ya fara rawa domin taji motsi tunani take ko wani ne zai fito Daga gidansu ta manta ba kowa Aba bai dawo ba kuma Ya Jafar yana masallaci wani Firgici ne ya shigeta Dayasa ta Damki hannun Aminu suka sha kwanar Dake Tsakanin gidansu gabanta ne ke Dukan uku uku kamar ta rike kaya haka tayi saurin sakinsa kafin tace"Don Allah ka daina bina..Kaga bansan ka ba..Ka daina Bibiyata kada kajamin mtsala..!
Take Fada acikin idanuwanta yake ganin Tsoron wanda Daga gani tsoron ya shigeta Lokaci Daya.
Cikin Gyara tsayuwarsa yace"To in na Daina Binki ni ya zanyi..?
Wlh tallahi kin ji rantsuwan Musulmi ina sonki Amina sonki ya hanani zaman waje daya ki kalleni koda yaushe ina garin nan na kasa zaman Kano ballatana Yola koda yaushe korafin Nenne na ta daina gane kaina kuma Wlh duk kece Sila..!
Yadda yake mganar ne yasa ta ke kallonsa acikin idanuwansa ta Hango gaskiya aciki.
Sai dai ta tsorata wannan wani abu ne da bai dace yana Faruwa akanta ba Arude tace"Meyasa sai ni..?ni fa karamace akwai yayyina ga su ya Abida duk bakace su ba sai ni..?
Kai Tsaye yace Mata"Ni ban sansu ba ni ke na sani..kuma ke Allah ya Saka Kaddaran haduwarmu Amina..!
Amina ta zaro mai ido tana Fadin"To wlh ahir dinka da bina..Kada ka sakani Cikin mtsala in Aba ya Sani ko ya Jafar ko ya Nasir wlh kasheni zasu yi..!
Ka rabu dani Amina ba kamar matar da ka sani bane yarinya ce ni ban gama karatu ba..!
Da sauri yace"Nasani zan jiraki Amina da gaske nake ina sonki kuma na Rantse zan aureki..!
Amina ta Dafe kirjinta tana Fadin"In wani ya sani zaka jamin bala"i daman nayi suna..Amina tayi suna ka rabu dani don Allah ban san me kake fada ba..Don Allah ka tafi ka kyakeni..!
Yaji Rokonta bayaso ya ja mata matsala yasa ya ciro katinsa Daga aljihun wandonsa ya mika mata yana Fadin"Zan tafi badomin na tafin kenan ba..Zan tafi ne saboda kin Rokeni sai dai zan dawo zan rika Binki duk inda nasan zan ganki Amina banfara sonki da wasa ba Wlh..Wannan kati na ne da Lambobin wayata aciki duk sanda kikaji kina son mgana Dani ki samu waya ki kirani zan zo..!
Kin karba tayi ta noke hannunta Tana Fadin"Kasheni kake so ayi in aka ganni Dakai..?
Kai ya girgiza mata bai yi mgana ba illah Hannunta Daya kama ya saka mata katin kafin yace"Ba abunda zai faru..Ki sani Aminu Buba yana Tare Dake acikin kowani Bugawar Numfashinki Amina na barki Cikin Aminci..!
Daga haka ko waige ya Fice Daga Kwanar Jikin Amina ya fara rawa ta Murza katin hannunta.
A.A Buba tagani ajikin katin da address dinsa da jerin Lambobinsa kamar ta yardaahi sai kuma ta Fasa taji Ranta na janta data adana katin Kilan watan watarana yayi mata amfani yasa ta Dunkule katin a hannunta sai da ta leka ta Tabbatar daya tafi kana ta fito ta shige gida aharaban ta Tsaya tana maida Numfashi Cikin sikat dinta ta Boye katin bata so wani yagani bata Shiryama wannan Jidalin ba yafi karfinta wannan karon..!
Cikin kayanta ta Boye katin Boyo mai Tsawon da ba wanda zai gani kuma koda wasa bata taba Fadama su Hanne ba.
Bai yi karya ba Tun da karancin Shekarunta Ta Fahimci Aminu na cikin Duka bugawar Numfashinta ta Rage Walwala da yawan mgana Tun ballatana data Daina ganinsa data Kulle ido zata kwanta shi take gani da kuma Kunnuwanta na Sauraran Muryansa bata son so ba..Sai dai ta Fara Fahimtarsa a karance karancen Datakeyi sai dai tasan Shekarunta basu kai ta bama wannan a Tsarin a rayuwarta ba yanzu. Jadalin Gidansu soyayya ko manyansu basu yi ta ba ballatana ita saboda haka wannan Tunanin baya Cikin muhallinta.
Su hanne da Hamida sun gaji da korafin Chanzawar Amina ranar Tana jinsu da Hanne ta shigo tana Fadama Mamanmu har yaya tana Tsakar gida alokacin Hanne take korafin sauyawar Amina.
Zeenatu na wanki abakin Famfo tace"Nima na ganta kwana Biyu ba Tsiwa nace kila aljanun Salahancinta ne suka sauka..!
Hamida tace"Allah Nafi son Aminar mu ta baya..Wannan shurun shurun bana sonshi..!
Hanne tace"Ko ya Abida sai da tace Amina ta sauya..Sai Hajiya tace Hankali ne tayi girma yazo..!
Mamanmu najinsu tace"Kwarai da gaskiyan Hajiya..Hankali da Natsuwar da'ake mata gori ne Allah ya bata yanzu..!
Hamida tace"Mamanmu Amina kamar tayi gamo fa..?ko Aljanun Dare ne suka bata tsoro kinsanta da Fitan Dare ko tsoro bataji..!
Ya zeenatu ta saka Dariya tana Fadin"Waya sani ko ta hadu da Cika Lora..!
Gabadayansu suka saka Dariya Har Yaya Dake gyaran kubanta acikin Ranta tana Fatan Hankalin Amina ne yazo kada ace shurunta wata Tsiyar take shiryawa kamar yadda ta Saba.
Amina nadaga cikin Daki tana jinsu Mirmishi tayi ta Furta"Gamo nayi Hamida..Tabbas na gamu da jidalin Danike kira ni Amina..!

Satuttuka sun zo sun shude har an shiga wattani Amina bata kara Haduwa da Aminu ba,Sai abun yadan Fara Sakinta ta fara dawowa Daidai ta Fara Dawowa da walwalwarta har ya Zeenatu na fadin"Daman ai na Fada muku wanchan watan Salihan ne suka zo mata..!
Lokacin baki ta Murguda mata tana Fadin"ni bani da Aljanu..!
Sun saba gwara suyi mgana ta maida su ko Ya ya Amina ta sauya suna ganin Alamunta sannan in zasu fadi gaskiya basa jin Dadin ganinta asanyaye.
Har ta manta dashi ranar jumma"a Bayan La"asar Mamanmu ta aiketa ta kaima Hajiya kuka da aka aiko musu dashi mai kyau Daga gusai bata so zuwa Hamida ce ba Lafiya Cikinta na ciwo yasa Mamanmu ta matsa sai taje.
Tana Tura baki ta saka Hijabinta ta Fita Tana ji ya Zeenatu na Fadin"Mamanmu Amina fa bakinta take Tura miki alamun bazataje ba..!
Mamanmu tace"Zeenatu fita daga idona..Bana son sharri..!
Sai da ta Murmusa wani Lokacin bata san in akace ta zabi Tsakanin Mamanmu da yaya wacce zata zaba ba..
In tace zabi zatayi to sau goma mamaanmu zata zaba itace komai nata,Laifinta Dubu sai ta kare mata Ita da baba mallam Har Abada bazata manta dasu ba shi baya samun zama yanzu saboda suna ta zuwa gwaruruwa Da'awa ko ya zauna na dan kwamaki ne kuma suna makaranta sun Dade rabon da su samu Zama da Baba Mallam din Hakika tana kewarsa.
Leshin Bikin su ya Zulahait ne ajikinta da Farin hijabin mamanmu Dogo ita nata duk sun Yamutse ba guga.
Mamanmu ta wanke mata Hamida ba lafiya balle ta goge mata ya zeenatu kuwa ko mamanmu ta saka kafin ta Goge sai taci zagi da Mita da Dunguri in ma Zata gogen kenan
Lokacin data fito kanta na kasa ko alama bata gansa ba Kamar inuwa taji daga gefenta da kuma jikinta ya bata ana kallonta Tana Dagowa suka Hada ido.
Gabanta sai da ya fadi gabanta ta kallah Masallaci yana kulle ne Baba Mallam baya gari ba kowa sai yara Dake wasa da Famfo bakin masallacin bayanta ta kallah ba kowa yasa ta fara Sauri ta shige gidansu Hanne bata san ya Biyota ba Muryansa taji.

"In kika shiga baki Tsaya munyi mgana ba..Wlh zan biki cikin gidan..!

Amuryansa tasan zai aikata abunda ya Fada yasa ta Tsaya tsoro take ji wannan Jidalin yafi karfinta in wani ya ganta kashinta ya Bushe ko Baba Mallam bai isa ba sai su ya Jafar sun kusa Kasheta.
Ta daga kafa taga yana Binta sai ta Rude kawai sai ta Mike maimakon ta shiga gidansu Hanne shima yabi bayanta kafa kafa har sai da suka sha kwanar Layin kamar tana jira ta Dakata azafafe ta juyo tana Kallonsa Cikin Juya manya idanuwanta Tace"Kayi wa girman Allah ka daina Bina..Zaka jamin bala"i..!
Waka taba ganin yana Tsayawa da wani agidanmu..?
Kada ka jamin bala"in in ba so kake akasheni in wani ya ganmu tare ba..!
Yadda yake kallonta yasa ta gane baya Fahimtarta yasa ta Damke Ledar hannunta zata Ruga da Sauri ya riko Gefen Hijabinta Amina taji kamar ta Yanka ihu ballatana ma dataga wata Mota kamar ta ya Nasir da sauri ta Fizge Hijabinta tana Fadin"Innalillahi..Ka sakeni don Allah..!
Da sauri ya saketa Lokaci Daya yana Fadin"Zan kyaleki Amina..Ammh sai kin jiyo kin kalleni kin ga yadda Sonki ya maidani..?
Kamar bazata juyo ba yanayin muryansa yasa ta juyo tana kallonsa kallon ya shiga har cikin jikinta tana jin kamar Zazzabi zai kamata.
Ya rame sai dai ya kara Fari Wayarsa ya zaro yayi wani Danne danne ya kara

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login