Showing 258001 words to 261000 words out of 265571 words

Chapter 87 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28888

yana mgana sai magiyan kiran sunan Amina yake yi tayi kamar bata ji ba, Hankalinta ma na kan bama Mallam Nono kamar yana Kiran Dutse..!
Fadi yake yi "Noor don Allah ba don Halina ba kiyi mgana..!
Amina haba Amina..Haba Amina da Allah fa nake hadaki..Nasan kina jina..!
Kiyi mgana saiki fadamin Laifina i Promise you zan baki Hakuri..!
Kinji Amaryata..!
Amina tayi wani Dariyan rainin Hankali har sai da yaji aranta tace su Amarya an ji jiki ai baka san ni Amarya bace sau na nuna maka matsayina..!
Yakaka na bakin kofa baki ta saki Tana Bin Amina da kallo Har Danmallam ya gaji da magiya ya Datse kiran Sannan ta kariso Dakin koda Amina ta ganta bata Damu da taji ko bata ji ba yadda ta yi nisan nan Mallam ko Hajiya ne kadai zasu saukar da ita Su kuma tana da Tabbacin ya Danmallam bazai bari su sani ba..!
Mallam ta karba ta miko mata Aba Amina ta karbeshi tana bata rai tace"Ni wlh na fara gajiya yaran nan duk sun gama tsotseni na fara yamushewa..!.
Tafada tana wani Tura mai Nonon a baki ruwan nonon ya kawo yaran ya Shake ya fara Tari Yakaka tayi Saurin Ijiye mallam Kan gadon Amina ta karbesa ta Daga sa sama tana shafa Bayansa Cikin Lallashi Lokaci Daya Tana Hararan Amina data kauda kanta Gefe kamar bata ganta ba..!
Cikin Ikon Allah aka samu yayi barci ta Lallaba ta kwantar dashi gefen Dan"uwansa sannan ta Dawo kan Amina tana Fadin"Ashe zama na Dake bamai amfani bane Amina..?.
Ina ga gwara nayi tafiyata sai ki zauna ki yi yadda kika ga Dama..!
Yakaka ta fada Cikin bacin rai ta Juya da Niyyar Tafiya Amina ta mike ta Riko Hannunta tana Fadin"Haba yakaka me kuma ya faru..?
Yakaka ta juyo tana Hararanta tace"tambaya ta ma kike me ya faru ko..?
Ai kina Sane Mijinki ya kiraki kin Dauka kina ji yana mgana kin yi banza Dashi Sannan kina bama yaro nan Nono kina mai mugunta kina so ki kashe ya"yanki ne..?
Kada ma kiyi Tunanin domin kun samu matsala da Babansu kike jin Haushin su yaro ina ruwansa..?
Sannan ki Sani yaki dan zamba ne Amina kuma abunda Hakuri bai baka ba Wlh Tsiya bazai taba baka shi ba. !
Kawai sai Amina ta saka kuka ta sanya Tafukan Hannayenta ta rufe Fuskarta dashi tana wani irin kuka mai cin rai Kukan Daya Dade yana Damunta aranta sannan Hade yake da Kishi da Takaicin D'a Namiji.
Yakaka sai Tsausayinta ya kamata ta Jawota jikinta ta rumgumeta tana Buga bayanta alamun Lallashi.
Amina sai ta Bude muryanta tana kuka sosai har da Shessheka.
Yakaka na Dafa bayanta Lokaci Daya Tana Fadin"Kidaina kuka Amina. bari kada yaranki su tashi su ga kina kuka. !
Gefen gado ta zaunar da ita tana Share mata Hawaye Amina ta Dago Tana kallon yakaka Lokaci Daya tace"Yakaka meye laifina da ya Danmallam zai min wannan wulakancin..?
Yakaka tace"Me ya faru ne..?
Amina tace"Kan mganar komawarmu Madina tare ne Lokacin da zai koma ai kinsan dani zai tafi Daga baya sai Hajiya ta hana tace sai nayi jarabawa Sannan yara sun yi kwari ko..?
Yakaka tace"Eh anyi hakan..!
Amina na sharan kwallah ta Cigaba da Fadin"To shine fa yazo ya sameni wai sai naje na samu Hajiya nace ni zan Bisa..Ina aka taba yin hakan yakaka..?
Tsakanina ga Allah fa Hajiya matsayin uwa take gareni tana da kimar da zata yanke Hukunci kan abunda ya Shafeni nayi shuru da Bakina Saboda bazata taba aikata abunda zai zama Cuta gareni ba..!
Yakaka tace"Kwarai Amina..Daga ke har Danmallam din Hajiya ta isa ta Zartar da komai akan abunda ya Shafe ku batare da kun Daga ido kun kalleta ba..!
Amina na kuka tace"To shine fa Dalili Saboda nace mai ni bazan iya zuwa nayi ma Hajiya musu ba..Hajiya tamkar uwa take gareni tamin abunda ko Uwata Data Haifeni sai haka Tayaya zata ce ga abunda ya kamata kuma na bata kunya..?
Na fadamai bazan iya ba shima yayi hakuri nan da wata Biyar komai ya Daidaita sai in na koma chan ba Jeka ka Dawo shine yayi fushi Yakaka ya tafi ya Dauko Sakina fa ya tafi da ita yakaka Wlh kin ji rantsuwan musulmai bansan ya tafi ba ko sallama bai mim ba ballata nasan da Sakina zai koma in ya gayamin zan Hanasa ne ai matarsa ce Tare na gansu..Ammh sai yaki Darajani ya saka Kafa ya tafi ya manta Dani Ko waya bai tabamin ba sai acikin kwanakin nan duk wani abun na yaran nan ko kayan abinci sai dai su ya Jafar su kawo ni bai taba mgana Dani ba..Sai yanzu ya san Dani..?.
Yakaka ina Laifina domin naki Sauraransa don Allah..!
Amina ta karishe Fada Cikin kuka Yakaka ta jinjina kai kafin tace"Gaskiya Umaru bai kyauta ba..Nima da Hajiya ta Fadamin da Sakina ya tafi sai da naji ba Dadi to ganin baki min mganar ba yasa nima ban miki ba..!
Amina na jan majina tace"Yakaka ki Duba mganar nan ina Laifina aciki..?
Yakaka tace"Baki da Laifi Amina ai Hajiya tana gaba da Umar bama ke ba..Sannan abunda babba ya Hango ai yaro ko Rimi ya hau bai isa ya Hango ba.Sannan ta yaro kyau take bata Karko..kiyi hakuri Ki kara Hakuri ke Macece sannan shi Mijinki ne kuma Shugabaanki ne kina kasan shine biyayya ya zama Dole gareki Ki yi Hakuri ki Sauraresa kiji ko dame yazo..!
Amina ta mike cikin Wata murya tace"Yakaka kiyi hakuri bawai bazan Saurari mganarki bane..A"a naji mganarki sai dai nayi Rantsuwan bazan Taba sauraransa ta waya ba..In ya matsu ya tako yazo ya Sameni in yana so na Sauraresa ammh matukar yana Chan wajen wadanan matan nasa bazan taba Sauraransa ba..Ya zauna dasu Tunda su ya Zaba..Zai gane muna mata ya tara..ga inda suke nan suke bata mawa su nuna an musu ba Daidai na rantse ga Allah Sai na nuna mai ni ba abanza nake ba Sannan nafi karfin yamin wannan wulakanci yaci banza. !
Ta karishe Fada tana Huci Yakaka tayi Dariya kafin tace"Na tabbatar miki da zai zo..mu ai ba"a isa a wulakantamu ba..Na goyi bayan ki nuna mai kema kina da Muhimmanci..!
Yakaka ta bama Amina goyon baya Sai dai ta mata Fada tabi komai a Sannu sannan ta Sasaauta.
Ana cikin wannan Tsukin Ya Ikram ta Haihu Amina sai taji Dadi tunda basu Fara Neco ba Da ita akayi suna ya Zulahait ne kadai tazo sai ya Fatima Sauran duk basu samu zuwa ba,Kuma har alokacin Danmallam bai Daina Kiran Amina tana banza Dashi ba Shi kuna yaki Hakura ita kuma Taurin kanta bazai barta ta Saurareshi ba..
Suna waya dasu Hanne har Hamida yanzu tana da ciki sannan bata Taba Fada musu ga abunda ke faruwa ba tadai Samar dasu sai ta gama Jarabawa zata bi ya Danmallan madina sai Tsiya suke mata wai wa ya ga Amina a madina ita kuma tace sai ma sun ga ta Saje da Larabawa..!
Sun Fara Neco dinsu cikin Nasara wani Lokacin da Yakaka suke zuwa makarantar in suna kuka takan fito ta basu Nono malaman makaranta su kansu mamaki suke Amina ce ta zama uwa ta kuma natsu kamar ba ita ba Tsakaninta da kowa sai gaisuwan mutuntawa Kamar ba itace a ka sha Gwagwamarya da ita ba Daman Haka Rayuwa ta gada
Danmallam kuma Amina na Neman ta Hauka tashi ko barci ba yayi yasa ya nemi Tahowa sai dai bai sami Dama ba Sai karshen wata Yasa sai ya bari karshen wata in yazo sai su yi ta kare shi da Amina yarinya karama zata chazamai kai da Rigimanta Shi yana ganin Rigiman mata ammh na Amina na musamman ne ita kadai take Fushi Dashi yaji ya Damu yanzu hakama Duk ya kasa sukuni har su Sakina sun Fahimci wani abu na Damunsa ya Dade da Samin Amina nada Jidali Sai dai baisan haka take da Taurinkai ba sai yanzu da ta nuna mai Sai yaji yana raina ta ashe ta wuce nan sannan kuma yana raina matsayinta aransa sai yanzu yasan Amina ta fita zakka ko acikin zuciyarsa komai in da tayi Birgesa take yi.
Bai yi shawara da kowa ba ya nemi Visa suma su Sakinan sai ana gobe zai Tashi ya Sanar dasu zai je Nageria Duk da bai Fada musu ba susan wajen Amina zai je basu ji Haushi ba Matarsa ce sannam kuma uwar ya"yansa.!
Washegari yabi Mota zuwa Jidda Sannan Daganan jirgin Dare yabi zuwa Abuja,washegari suka sauka Filin Jirgin Nnamadi azikiwe Dake Abuja da yammah sallah kadai ya Tsaya yayi ya hau Motar Haya zuwa Gumel batare da ya kira kowa ba. !motar bata gudu sosai basu isa Gumel ba sai Dare misalin Karfe Tara a masallacin Anguwan ya Tsaya yayi Mangariba da Isha"i sannan ya nufi Gidan Amina get din na Rufe Daman bai Dauki megadi ba ta cikin gida ake Rufewa..wayar Amina ya Kira Duk da yasan bazata Dauka ba Haka ya Dinga jera mata Kira bata Dauka ba.
Sai ya Hakura ya koma yana Faman Buga get din Amina na Dakinta kwance ita da ya"yanta har sun gama Hira da yakaka ta nufi Dakinta ita kuma tazo tayi wanka yaran daman yakaka ta musu na yammah ta Gaji yau English sukayi tun Safe sai yammah suka Dawo Har yaran sun gaji suna shan Nono sukaji Ruwan zafi suka fara Barci itama barcin Take ji Tana Fitowa wanka tayi salla ta Saka Rigar Barci masu Taushi Riga da wando ta saka Hula ta kwanta wayar ma na chan gefen gadon kuma tana Silent ne shiyasa ma bata ji ba Sannan har buga gidan bata jiba sai Yakaka ce Data fito Daukan ruwa a Kitchen taji kamar ana Buga gida.
Sai ta Tsaya ta kara Saurarawa taji Dai da Gaske ne har zata leka Amina sai kuma ta fasa jikinta ya fara rawa tana Tunanin waye ne da Daddaran nan..?
Sai tayi tunanin ko su Jafaru ne..?
Yasa ta Dauki Tocila ta fita har Haraban gidan dayake an Dauke wuta tana fitowa taji buga get din anan ne yasa ta karisa jikin kofar tana Fadin waye..?
Danmallan Dayaji muryan yakaka sai Hankalinsa ya kwanta Cikin Muryansa mai Sanyi yace"Ni ne Yakaka..!itama ta gane Muryansa Cikin mamaki tace"Danmallan..?
Yana mirmishi yace"Nine yakaka..!
Da Hanzari ta Cire sakatan kofar get din sai gashi ya bayyana a gabanta Har ya shigo tana cikin mamaki ita ta koma ta kara kulle kofar get din ta Juyi Tana Fadin"Danmallam zuwa ba Sanarwa haka.?
Danmallam ya shafa kanshi bai ce komai ba yana Sanye da yadi mai Santsi riga da wando kansa ba Hula sai Sumar kansa data Fara Tahowa yana gaba tana Binsa a baya har Cikin Falon gidan sannan suka gaisa yaga gidan da Duhu Lokaci Daya yace"Yakaka Sun Dauke wuta ne..?
Yakaka tace"Da yammah nan suka Dauke ammh nasan zasu dawo dashu..!.
Danmallam yace"Yakamata aa Hada muku Solar Duhu ai ba Dadi..!
Yakaka tace"Dayake ma suna barin wutar..Sannu da zuwa kasha Hanya...bari na kawo maka ko ruwa na yau bamu yi girki ba Takwara makaranta ta wuni sai da zamu Dawo ne muka biya gidan mallam muka Dauko waina gatanan in zaka ci na Zubi maka...
Danmallam yace"Bakomai yakaka wanka ma nake so na farayi..!
Yakaka tace"Eh to ya kamata shiga Ciki Aminar na ciki ina ga sun kwanta daga ita har yaran sun gaji..ya amsa mata da Toh ya juya kenan Tace"ahf kaga na manta ya wajen su Sakinar ne da mai juna Biyu..?
Fatan dai suna Lafiya..!
Danmallam ya juyo yana amsa ma yakaka da Lafiyarsu kalau sannan ya shige Dakin Amina a gaban gadon ya Tsaya kawai yana kallon Amina tana Barcinta Cikin kwanciyar Hankali ta saka Hannunta ta rumgume ya"yanta su Aba yake mamakin girmansu da kibansu wani Annuri na shiga cikin Ransa yana kallon Amina aransa yana auna yarda yar yarinyar nan ta Hanashi Sukuni
Zama yayi gefen gadon bayan ya Sauke karamar Jakar Hannunsa yana kokarin Dauke hannun Amina kan yara saboda ya Samu ya Daukesu Caraf ta Rike Hannunsa da Karfi Lokaci Daya tana Bude idonta sai ya Fada kansa suka kura ma juna Ido na wani Lokaci shi na murnan ganinta ne da wani sonta da sha"awarta ita kuma na Bakin ciki da Takaici ne Daya Taimaka wajen Dakushe Zumudinta.
Kauda hannunsa tayi ta mike Zaune Fuskarta ba Fara"a tace"Mallam Lafiya..?
Girman Idonsa ya kara yana kallinta Cikin mamaki kafin yace"Mallam kuma..?
Kawai sai taga ma zai raina mata wayau ya sake kai hannu zai Taba yaran da Sauri ta make hannun nasa ya Dago Cikin mamaki yana kallonta kafin yace"Amina ni kike bige ma Hannu don zan Dauki ya"yana..?
Amina tamai wani kallon Tara saura kwata kafin ta sauko Daga kan gadon batayi wata wata ba ta Dauki Aba ta goya ta saka showel din Dake gefe ta Daureshi dashi sannan ta Dauki Mallam a Hannunta ta juya zata bar Dakin da Sauri ya mike yana kiranta,

"Amina..!

Da farko taso tayi Ficewarta ne sai kuma ta ja ta tsaya bata juyowa ba Da Hanzari ya taka har gabanta ya ja ya Tsaya yana Binta da kallo ita kuma ta Kara Hade rai cikin mamaki yace"Me kika yi haka?
Amina tace"Dani da ya"yana bamu da Muhalli a wajenka..saboda banga amfani Daukan su da zakayi ba..!
Baki ya saki yana kallonta Duk da yasan za"a rina Daman rigima sai wacce ya gani sai dai bai nuna ya karaya ba ya mika mata hannu yana Fadin"Bani su..Sai muyi mganar Daga baya..!
Amina ta kallesa Daga Sama har kasa kafin tace"Wadanan ya"yan Amina ne sai ka bari in Sakina ko Sarood dake da Mutumci a idonka sun haifan maka sai ka Dauka..Bani waje na fice kafin Raina ya kara baci kaga abunda baka Taba gani ba wlh..!
Sai mamakinta ya kamasa yadda take kallon Tsabar idonsa tana mai rashin kunya sai ya tsawarta mata yana Fadin"Ban sauke kaina kasa don ki raina ni ba Amina ki shiga Hankalinki..!.
Wata Dariyan Rainin Hankali ta sakamar kafin ta raba ta gefensa ta Fice Daga dakin ransa ya baci yabi bayanta yana Fadin"Amina ki dawo nace..Nace ki dawo ko..?
Amina ko Sauraransa batayi ba ta Fada Dakin Yakaka shi bai yi zaton Yakaka na Dakin ba ya bi bayanta kawai sai suka Hada ido da yakaka Amina na Tsaye ta Cika kamar ta Fashe Daman Yakaka tasan yadda Amina ta Zuciya Danmallan bazai ji Da Dadi ba.
A matsayinta na Babba yasa ta mike Daga zaunen Datake ta mikama Amina Hannu tana Fadin"Bani yaran..Ki koma ku cigaba da Rigimarki kada ku saka yaran da basu san me Duniya ke ciki aciki ba. !
Sanda ta Fadi haka sai Danmallam yaji kunya ya koma da Baya ya fice Daga Dakin Amina sai ta sakama Yakaka kuka ita kuma ta karbi Aba ta kwanto Mallam Dake baya tana Fadin"Ban son Sakarci kin gama kuma Nuna mai Matsayinki ya tako ya Biyo ki sai ki Bata wayonki..?
Maza Share hawayenki kada ki sake mai kuka kije ki karbi Lallashin shi ko Banza yasan Darajan ki yanzu..!
Amina ta Share Hawayenta sannan ta juya ta Fice Yakaka ta bita da kallo aranta tana Fatan Allah ya Daidaita Tsakanin Ma"auratan..!
Amina na komawa Dakin ta iske shi Zaune gefen gado yayi Tagumi yana ganinta ya taso zai riketa ta kauce ta sakamar Jajayen idanuwanta tana Fadin"Bana so..Kada ka tabani..!
Sai ya Janye mata Kan gadon ta koma ta kwanta ta Juyamai baya sai kawai ya koma ya zauna ya kara yin Tagumi.
Yana mamakin Amina zata???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? Haukatasa ganin kamar ma batasan yana Dakin ba yasa ya Sauko Ya Duka a Gaban gadon inda yake kwance yana Kiran sunanta..!

Amina..!
Noor..!

Kamar yana kiran Dutse haka tayi mai yasan Laifinsa yasa ya fara mgana"Amina kiyi hakuri Ana Asif..Nasan ban kyauta ba da na tafi ban Fada miki ba..Ammh kema ai kinsan kin batamin ko..?
Kamar tana jiransa ta juyo Lokaci Daya ta Mike zaune tana Fadin"Au nama bata maka ko..!?
Saboda ban je nayi ma Hajiya Rashin kunya nace zan bika ba ko..?
To ai da nayi hakan da nagane bani da wayau domin ka nuna min Tabbas ku maza baku da Tabbas haka zan bika kuje ku Hadu da matanka kuna wulakantani Tunda ka nuna musu ban da Daraja..duk lalacewar naka ai naka ne. watarana Hajiyar dai itace Uwata kuma wajenta zan koma bari kaji na Fada maka har yau ban yi Nadaman Kin binka ba..Indai kan Umarnin Hajiya ne da kai ma ta isa Dakai bama niba..!
Ta fada tana bayyana bacin ranta Danmallam sai ya kasa mgana yana kallonta Amina taji hawaye sun kawo mata sai tama kasa Cigaba da mganr
Danmallam ya Bude baki yana Fadin"Amina n...!
Dakata..!
Tafada tana Dagamai Hannu kafin ta kallesa Tana fadin"Ba sai kace min komai ba..Ka nuna min matsayina amfanina ya kare Tunda kamin ciki na Haihu ni Aikina kenan shiyasa Domin ka nuna min ni din ba wata bace yasa ka Dauki matarka kuka koma Tare bansani ba.?
Saboda ka nuna min in ban bika ba kana da Biyu irina ko..?
To ai bakomai yanzu ma sai ka koma wajensu ni ban kira ka ba sannan ban aika maka da katin gayyata ba..!
Daga haka ta juya zata kwanta ya riketa da karfi tana so ta kwace jikinta yaki barinta sai ma gadon da ya hau ya Rumgumeta sosai Duk yadda taso ta kwace kanta yaki barinta sai kawai tayi Lamo sai kuka Danmallam ya kamkameta yana Fadin"kiyi Hakuri Amina na Tuba nabi Allah..Na biki..Nasan ban kyauta miki ba ni Haushina da na shirya tafiya Dake kika bi na..Wlh Amina na kasa zama in baki kusa dani ina Bukatarki kusa dani Amina..Noor ina sonki..Wlh ina kaunarki ki yafemin..!
Amina ta kara sakarmai kuka Tana Fadin"Baka sona ka nuna ka fi son matanka akaina..!
Yana kara riketa cikin jikinsa yace"A"a kada kice haka.. Kema kinsan ina sonki..Tunda na koma bana cikin natsuwata na gama Fushin na Sauko na nemeki baki bani Daman kare kaina ba..Sannan ki duba na kasa zama a madina saboda ke..Hankalina ya tashi ko Barci bana iyawa..!
Wannan duk ba so bane. ?
Wannan duk bai sa kisan kina da Daraja ba..?
Amina na jinsa ta masa banza sai Faman mata rantsuwa yake yi yana Lallashinta Amina na karamai Bore Gajiya yayi ya Hade Bakinta da nashi Duk yadda taso ta hanasa ta kasa Domin itama ai ta gyaru tana Bukatar Mijinta a kusa da ita tun ana Lallashi har aka Sauya salo Danmallan yadda ya Samu Amina yasa sai da ya raina kansa kuka reras ya Dinga rairamata Albarka kuwa tashashi har sai da tagaji Sai da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login