Showing 219001 words to 222000 words out of 265571 words

Chapter 74 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28906

masa kwanciyar hankali da Zama lafiya da wadata..!
Danmallan yayi Tagumi kafin yace"Sai kuma me zaki Roka..?
Amina tace"Sai kuma na roki Allah ya bama mijina Wadata na alheri Allah ya Zaunar damu lafiya Allah ya karamana kaunar juna ya shiryamana abunda Zamu haifa ya bamu ikom Musu Tarbiya bisa Amana da koyarwan addinin islama..!
Ayadda take mgana sai da yaji ajikinsa Cikin mamakinta yace"Wani mijin naki..?
Kai Tsaye Amina tace"Kai mana Hubby..dole zan gode maka..Domin kaima ka bani Taimako wajen dawowa da Rayuwata daidai sannan ka aureni Cikin wani yanayin da bakowani Namiji zai iya ba..Nagode kwarai Allah ya baka ikon yimana aldaci..!
Danmallam sai yaji kamar yayi kwallah ashe haka Amina ke da Hankali..?
Kai tsaye yace mata"Ameen Ameen Noor..Allah yayi miki albarka Allah ya Saukeki Lafiya insha Allahu Buriinki Zai Cika kin ji ko..?
Ta amsa mai Cikin jin Dadi,Shuru na wani Lokaci kafin taji yace"ANA BEHABBIK YA NOOR.....!
Amina ta ji mganar kamar Daga sama yasa tace"Me kace..?
Shi a tunaninsa bata ji me yace ba Sabida Labarci ne ya fada sai yayi saurin cewa"Bakomai..!
Kawai sai ta murmusa batace komai idonta ya kawo kwallah haka suka gama Hirarsu sukayi sallama Suna gama wayar ta rumgume wayar akan Cikinta tana Fadin"Ina son babanku..Wlh nima Ana Behabbak Hubby Umar..'
Hawaye ya kawo mata tayi saurin sharewa tasani tana son mijinta so mai tsanani data bata san yaushe ya fara ba Sannan yadda take kishin sa ko matansa basu kaita ba shiyasa ta Tsani ko jin sunansu kamar ma ya sani in suna Hira baya mata mganarsu shine zaman lafiya.
Washegari suka tafi asibitin tunda yanzu duk sati suke zuwa saboda Cikinta ya tsufa.da suka Dawo ne suka Tsaya Shagon salloon aka musu gyaran kai da Gyaran kafa Daman Amina ta Fadama Ya Danmallan yace kada tayi kitso ta bar mai gashin nan yafi son ya gansa haka ya fi bashi sha"awa ita kuma Amina duk abunda Zata Burgesa shi take yi bata Damu da kowa da komai ba sai shi sai Cikinta ke gabanta.

*******

Ana saura Kwana goma Bikin su Hanne Oder din kayan Dakin su ya iso har da Na Amina,Kowacee kuma Dakinta inda zata zauna aka wuce mata dashi Hamida dai yayarta Zulfa taje ta taimakama ma"aikatan aka Gyaran kayan aka saka komai a muhallimsa anan zaria zata zauna Gaskiya Layout.
Ita kuma Sa"adatu Gombe Kanwar Anty Amarya A"i sai Haj Nasara da Hajiya Babba suka je aka gyara Inda Sa"adatun zata zauna Sai washegari suka Dawo na Hannatu kuwa Haj.Uwani ce taje da Anty Amarya har Yola suka yi Jerin su,Tunda sun tafi da Kayan Kitchen din da Hajiya ta siyama Hanne da Hamida duka da Sauran na Hamidan da Mamanmu ta siya a mota ta saka ta aika ma Zulfa bata bari ko su Hajiya sun sani ba kada ta bar wata kafar da Za"a Zargeta.
Har Zulfa sai da tayi mata mganan ina ta samu kudin siyan wannan kayan saj tace ai kiwo tayi a gusai da Bikin Hamidan yazo sai ta saida tayi wannan Hidimar da ita Zulfa sai ta yarda bata kawo Tunanin komai ba na wajen Hajiyan wajen mamanmu aka barsu da niyar sai ranar Daurin airan in za"a wuce da Amarya sai a wuce dasu.
Bangaran gidan Amina kuwa batare da kowa ya sani ba Daga Hajiya sai Aliyu sai Mallam suka san an kawo kayan Dakin,Hajiya da bata samu kiran yar"uwanta yagana ba saboda Nisa Mallam ma yace ta kyalesu Fadila matar Nasir ta nema tare suka gyara gidan Amina ya fito Tsab komai an saka mata Labule ne kadai ba"a saka ba Aisha zata zo dasu Tunda tace ta siya ma Amima masu kyau oder dinsu tayi daga Dubai.
Har kuma aka gama gyaran gidan Fadila bata san ko gidan waye ba,Tunda dai Hajiyan ta nemeta da Nasir bai sani ba,sai bata ma Fadamai ba Tunda bata da Hayaniya,ta kama Bakinta tayi shuru ammh bata taba kawo Tunanin gidan nan da komai na Cikinsa na Amina bane Aliyum ma Data gani Tafi Tunanin ko nashi ne ko na wani nashi kila.
Shirye shirye ta ko"ina ya kamkama ana cikin kwanakin Bikin ne Sakina achan Madina tayi Zazzabi har da su Amaye amaye ana zuwa asibiti aka gwadata sai Ciki dan kimanin wata Biyu da kwanaki Labarin da ya yadu a Nageria abun mamaki shi Danmallan Da mallam kadai sukayi mgana ya fadamai hajiya ma mallam ya manta bai Fadamata a bakin Haj.Nasara take ji.
Anty Amarya haka take yada mganar Cikin tana Hura Hanci Hangowa kawai take komai ya kare ana gama auran Sa"adatu zata fara kokarin ganin bayan Haj.Uwa Ita kuwa daman Dariya take mata domin ta tabbatar da cewa kamar sauran shima haka zai bi Rariya Hajiya dataji labari Fatan Allah ya Tsayar tayi mata har aranta bata Fatan wannan karon Sakina ta rasa Cikinta ai mugunta Fitsarin Fako ne mai shi yake ci.
Amina ma taji labari abakin ya Aisha itama tace Sadiya ta kirata ta fadamata Amina sai taji Abu acikin Ranta ammh bata yarda ta Furtamai abunda taji ba shima kuma bai taba mata mganar ba sai mganar tafiyarsu Dayace Ranar Litini Jirginsu zai taso Daga jidda da Daddare zuwa Nageria shi da Sakina da Sarood.
Da farko yaso Sarood ta zauna Hajiya Dataji mganar tace bai yi adalci ba Sai dai Sakina ta Zauna shi kuma baya son Rigima yadda Sakina ta ke Hura Hanci da Cikin jikinta da kuma wannan sha"anin in yace ta zauna ai sai ta nemi mai hayaniya sannan yana da kudi a Hannunsa yasa kawai yaga gwara su taho gabadaya sannan yana su dan jima tunda hutun karshen shekara ne.
Su kuma su Amina suna ta shiri Ya Aisha bata siya ma Amina komai da kudin da Usman ya bata ba Daman kuma ta Bude Banki zuwanta Abuja sai da sukayi mgana da Hajiya tace ta barmata kudinta tunda kusan komai ta siya ma Aminar itama Aishan ta siya mata Zannuwan gado da sauran kayan Kitchen su blander Toster da Sauran su sai kayan Kamshin girki su kayan gyara kuma sai dai inda ta Haihu sannan har da Yakaka zata tafi gumel Usman baya nan yana Lagos za"a Yi Bikin Direba ne zai kawo su da kayan su.
Amina ta rasa Bakin godiya Data ga Uban kayan lefenta da kayan da ya Aisha ta siya mata sai da tayi kwallah Tace Gudummuwar malam da Hajiya ne suka Dauke ma Danmallam lefe tasani ba"a taba kawo lefen kowa ba sai dai in kaje gidanka ka gani ammh Sai gashi ita da nata Lefen zata koma Allah Sarki Rayuwa daman ai abunda ya baka Tsoro watarana shi zai sakaka kuka.
Ranar Talata da yammah Jirgin su Damallam ya sauka Filin saukan Jirage na kano Aliyu yazo ya Dauke su shi da Jafar suka kawo su Gumel gidansu suka sauka.






*Janafty*
*TFZB2024*

*Ki biya ki ??????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????????karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*


Saboda Gajiyan tafiya yasa ko washegari basu fita ko"ina ba Har shi Dannallam din bai iya fita ba sai Ranar Laraba suka zo gidan mallam Lokacin baki daga nesa duk sun fara Hallata irin su ya Fatima da su ya Nazifa,Mutanen Jordan kuma Suma Jiya suka iso Goggo Husai da Jadwa Sannan aranar Hidaya matar Nazir da Jaleela suka sauka suma da yammah kuma sai ga Mutanen Parthercourt su yaya zahra,Gida fa masha Allah ya fara shiga da Dangi na nesa dana kusa Sakina saiwani Hura hanci take yi tana iyayi ita a dole mai ciki sai Tsirfa take yi kala kala Saboda Sarood wanda ita batama nuna ta damu ba,Bangaran Anty Amarya kuwa itama Sai harkokinta take yi Cikin jin Dadi Saboda ai tana ganin ita yanzu bata da wata matsala ga Sakina na da Ciki gashi Zata aurar da Sa"adatu duk da abaya bata so hakan ba ammh zuwa yanzu ta hango hakan a matakin Nasararta.
Aranar bata koma gidan Danmallam ba nan ta kwana wai bata son kamshin Gidansu Danmallam ko ta kanta bai bi ba ya Dauki Sarood suka koma sai da Safe bayan sun Karya sun yi wanka ya Dawo da ita.
Aranar da Safe yan gusai suka iso da su ya Abida,ya zulaihat su ya Zeenatu da ya zulfa da su ya Ikram dukkansu duk sun iso domin in ba irin wannan Sha"anin ba baka samun damar zuwa gida har ka dan yi kwanaki mallam baya barin su suzo sai da wani Dalili mai karfi.
Hidaya wannan karon data zo Shashen Hajiya uwa ta sake sauka kamar yadda ta saba Hajiya bata nuna komai ba ko a Fuskarta,Shiyasa Hajiya uwa ta saki jiki anata kai da kawo da ita sai dai ta ciki na ciki in sun Hadu da Anty Amarya su rika ma juna kallon baki isa ba ita Hajiya Uwa Dariya Anty Amarya ke bata in taga tana wani iyayi saboda dai tasan Cikin Sakina ma wannan karon sai yabi Rariya kamar sauran ita kuma Anty Amarya tana takama da mallam yace Wannan matsalan ta kau har Abada.
Hajiya babba kuwa bata bi ta kansu ba harkan gabanta kawai take yi,Shashenta itama ba Matsaka tsinke Danginta yan maiduguri sun iso suma kwansu da kwarkwatansu Tunda ai Auta Hajiya zata aurar wannan karon Ita in kaga tana mgana ko Shawara da mallam ne ban dashi ta daina yarda da kowa Tunda ta lura yanzu Rayuwar ga yadda ta zama sai addu"a kawai wanda bakayi Tsammani ba sai ya Cutar dakai ko Hajiya Nasara da bata taba kamata da wani abu bata Saki Jiki da ita ba an ce Sau Daya ruwa yake dukam mutum yayi hankali ita kanta ya Daketa kuma tayi Hankalin Sosai.

Achan gidan Aba kuwa shima yana cike da Baki na nesa dana kusa yan Gusai Dangin Aba da Dangin mamanmilu Wannan karon yadda taci Burin Bikin nan yasa gayyata ba kama hannun yaro har da wadanda basu zo nasu Zeenatu ba sun zo wannan karon Mamanmu sai shiga take tana Fita Domin tun jiya ta fara sawa tana Cirewa Da Sabbin kaya Bakinta kamar zai Tsage saboda Fara"a kanta na Fashewa duk inda ta shiga ana Balaraba sannu da kokari Allah ya Biyaki da Aljannah.
Tana amsawa da Ameen tana kara jin Dadi ita ta samu Duniya,Domin yadda ta amshi kudade hannun Aba Allah kadai yasan yawansu data Mika hannu bai gaddama yake bata sannan Duk abunda tace ko bai kwantamai ba ta ZAuna Hajiyar banza ai yanzu ta sha gabanta ballatana wani chan Tsoho mallam da kansa A tunanin ta ayadda ta ci wannan Burin bata taba Hasaahen ko kawo kanta da wani abu zai iya faruwa da ita da zai Tsawarwata wannan Burin nata ba ita kawai har kan gabanta take yi Ranta Fes da Tunanin Burinta ya Cika sannan tana kan cin Duniyarta ne kamar yadda ta Tsara.
Abunda bata sani ba suna nasu ne Allah ya riga ya gama nasu..Basu sani ba Ranar tonon asirinsu ya kusa zuwa..Dama dama ace suna da sani da Allah wlh kafin Ranar hakan duk zasu gudu kafin bayyanan boyayyun Fuskokinsu.

Bangaran Amare kuma suna gidan su ya jafar Kamar yadda aka saba Su da sauran yan"uwansu su ya Zeenatu ya Abida ya zulaihat da su ya Ikram da su ya Sadiya har sa"adatu bata ware kanta ba wannan karom duk suna Tare ya Aisha Kadai ce bata iso ba,Abida tayi ta Kiranta sai tace mata tana tafe yau komai Dare insha Allahu.
Hanne da Hamida kam sai a hankali duk sun yi wani irin sanyi su Ya Abida nata musu tsiyan Amare,gwarama Sa"adatu ta saki jikinta ana ta harkokin yin Meatpie din walima da ita tunda su ya Abida ke yinsa anan gidan shi da Donut,su damuwar su Daya ayadda? biki ya zo ammh ba Amina sannan ai Hajiya ta musu alkwarin Amina zata zo ammh basu ganta ba ko da Safen nan da suka je gidan sun mata mgana ta musu Dariya tace kada su damu Amina Zata zo insha Allahu.
Ya Danmallan kuma tunda suka Dawo basu hadu dashi ba Sunga dai Sakina,shima a shashen Anty Amarya,Sai sarood dake shashen Hajiya tuni Sakina ta Daina janta kusa da ita da sun iso garin zata janye mata sai dai ka ganta zaune bangaran Hajiya tana Bin kowa da kallo in taga mutum kuma ta fara mai Mirmishin ta din nan tunda ba jin abunda mutane ke cewa take yi ba.
Misalin karfe Daya na Rana Hajiya ta kira Wayar Danmaallam yana gida alokacin domin tun bayan da ya kawo Sarrod ya koma ya kwanta Gidan mallam ya cika da Hayaniya damam sun gama mgana da Aliyu kenan shima suna tafe shi da matarsa da ya"yansa sai Jibi asabar zasu koma sai ga Kiran Hajiya daman tunda ya Dawo ban da gaisuwan da sukayi Jiya basu yi wata mgana ba gwara ma mallam sun samu zama shi da Aba sun yi Hira sosai saboda gidan ya cika da Jama"a banda ma shashen Hajiya bai shiga ko"ina ba.
Da Hanzari ya sake yin wanka ya sauya kaya Cikin shigar Wani Farin yadi Dinkin riga da wando na Zamani da Hula,Allah ya taimakesa ko da ya iso ana salla nan masallacin mallam Duk da bai samu duka ba ya samu Raka"a Biyu mallam ma baya nan ya Shiga Cikin Collage din Gumel ta Fce suna da taron da aka gayyaceshi.
Ya Shiga gidan cike da Mutane Kansa na kasa yana gaisawa da duk wanda ya Hadu dashi har Falon Hajiya inda ya Duka yana gaisheta da goggon ninsu na maiduguri,sauran yara yaran matan kuma suna gaisheshi yagana ne tace mai Hajiya na Ciki yasa ya tashi ya shiga sarood na Dakin su Hanne ta shiga Sallah shiyasa bai ganta ba.
Koda ya shiga Dakin Hajiya suna waya da ya Aisha Shi dai baisan me tace ba yadai ji Hajiya na Fadin"Shikenan Allah ya kawo ku Lafiya zaku iya tasowa yanzu..Munyi mgana da mallam kafin ya fita..!
Daganan sukayi sallama shi dai yana Duke agabanta kansa a kasa Hajiya ta gama wayanta ta juyo tana Fadin"Mutanen madina..!.
Kansa ya shafa yana fadin"Hajiya mun same ku lafiya..!
Hajiya ta amsa da Lafiya lai daganan suka gaisa da Tambayan Hidima shuru yadan Biyo baya kafin Hajiya ta gyara Zama tana fadin"Kun yi mgana da Amina tunda ka dawo..?
Kansa na kasa yace"Eh Sau daya mukayi mgana da ita Hajiya..!
Hajiya ta jinjina kai tana Fadin"Daman kan mganar tahowar su ne ita da Amina..Sun gama shirin su? ni na Tsaidasu saboda Wani Dalilina..Naso Da sun sauka Amina ta wuce gidanta sai mallam yace bai kamata ba nan zata sauka tukunnah Shiyasa sai na sauya Shawara yanzu dai nace su taho ita da Aishar ne da Aminar sai yakaka da zasu zo tare da Direba..!
Danmallan kansa na kasa yace"Allah ya kawosu lafiya..!
Hajiya ta amsa da Ameen tana Fadin"Yau dai abunda muke Boyewa zai bayyana..Amina Zata dawo ammh ba ita kadai ba da abunda kowa zai yi mamaki..!
Shidai bai ce komai ba kansa na kasa Hajiya tace"Shikenan tashi kaje kiran da nayi maka kenan daman..!
Ba musu ya mike yayi mata sallama ya Fice yana tunanin murnan da Amina ke Ciki jiya da sukayi mgana sai shagwaba take mai kan sun gama shirinsu Hajiya tace su Dakata shi ya Lallasheta da fadin kada ta damu da ita za"ayi wannan sha"anin.
Yau kuma bai samu ya Kirata ba,Zumudin tafiyar ne yasa ko kiransa ma batayi ba sun dai yi mgana da Aisha da Safe kan asibitin da Amina ke zuwa awo sun je sun amso Takardun duka report dinta sannan ya basu shaidar ko a ina Amina zata Haihu in suka nuna wadanan takardun Babu matsala.
Yaji Dadin Hikimar Aminar da Mijinta Saboda shima yana Tunanin ba lalle Amina ta koma ba,Duk da Hajiya bata fadamai ba ammh ai tace gidanta zata Zauna ta Haihu tayi jegonta.
Yana fitowa daga shashen Hajiya suka ci karo da Anty Amarya ta fito Daga kitchen nan suka gaisa har tana cemai bazai shiga ya duba Sakina bane..?
Sakina na ciki kwance Zazzabi ya rufeta bai damu ba yace zai mata waya mata sun yi yawa ya samu ya fice aransa kuma bai yi niyyar kiranta ba ai tasan dashi tun shekaran jiya bata nemesa ba Shima ya shareta ai ba ita kadai garesa ba balle ya Damu sannan Ciki kuma ai ba kanta Farau ba shi Allah ya tuba ma ko ZUMUDI bai yi ba wannan karln to me za"a a nuna mai shi da ke da mai Ciki haihuwa ko yau ko gobe..?
Ai karyar barazana kuma ta kare yadda ta ke wani tsirfa ma mamaki take basa shiyasa tunda suka zo tace wajen Anty Amarya zata zauna bai damu ba Ko a kwalar rigarsa.
Dakin su Uzairu ya shiga suna taba Hiran inda yake sarvice daya ke shima ya Dawo shima da Safen har shamsu ya iso Dazu shima wannan Bikin fa na musamman ne kowa da kowa yana nan Saboda bikin mata ne kuma Sune na layim karshe daga su sai maza su Nazeem in sun tashin yin kenan nan kusa Har Mutanen bazanga mata da basu Cika zuwa ba sun zo wannan karon Bikin su Hamida kan kowa yasan yayi goshi.
Sun Dade suna hira dashi tare sukaci Abincin Rana da Hajiya ta aiko musu dashi Tunda tasan suna cikin Gidan sai La"asar suka fita Danmallam ya bada salla bayan sun idar ne sai ga Aliyu sun iso ya fita ya tarbesa Suka gaisa da Aliyu ya Dauki karamin yaronsu Hammad ita kuma Aliya da yar macen da Cikin jikinta Daya fara fitowa suka nufi Cikin gida.
Sai da ta fara zuwa shashen Hajjya suka gaisa har taga Sarood tana ganinta ta fara bashe mata baki taga wanda ta sani ammh Aliya ko kallonta batayi ba Ko Dadewa batayi ba ta baro Shashen Hajiya zuwa na Anty Amarya wajen sakina daman sun yi waya tun kafin ma su fito Daga gida.
Anty Amarya sai ina ka saka da Aliya take yi ita kuma Sakinar na kwance Dakin su Sa"adatu wai bata jin dadi Zazzabi ne ya rufeta Ammh ganin Aliyan sai ta mike tana wani yamutsa Fuska.
Aliya na kallonta tana Dariya tace"Masu Ciki..Yan Laulayi..!
Sakina tayi far da ido kafin tace"Kedai bari tunda muka iso ban jin Dadi..komai ma baya min Dadi..Chan gidan fa warinsa tadamin Hankali yake yi na baro

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login