Showing 30001 words to 33000 words out of 265571 words

Chapter 11 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28878

yana Fadin ina Yaya Danmallan ya Samo Balarabiya mai kyau haka sai da bai tanka ba ya Fice Daga Falon.
Hajiya ta kalli SAROOD tana Fadin"Maraba lale..Kariso mana..!
Hanne ta saka Dariya tana Fadin"Hajiya wayace miki tana jin Hausa..?
Hajiya tace"Oh to..To ku da kuke yara yanzu kwakwalwar ku take ku mata mgana da labarci kuce tazo ta zauna ai batayi ta tsayuwa ba..!
Aisha ce taje ta kamo hannunta tana mata Sannu da zuwa Cikin Harshen Larabci batayi mamaki ba Sanin Daman Umar ya fada mata zataji dadin zama a Nigeria Domin agidansu akwai masu jin yarenta
Har kan Daya Daga Cikin kujerin Falon ta zaunar da ita sai dai bata Zauna ba ta Zame ta Zauna akasa Cafet kanta na kasa Umar ya fadamata Shashen Mahaifiyarsa za"a kaita Shiyasa kanta na kasa ta shiga gaida Hajiya da Harshenta Hajiya na jin Larabci tun abaya don ma Shekaru da kuma Rashin yinsa Lokaci zuwa Lokaci.
Cikin jin Dadi ta amsa mata da Tambayan Hanyan ta amsa da Alhamdulillah kanta na kasa Muryanta Dadi Cikin Harshenta.
Hajiya ta kalli su Aisha tana Fadin"Aisha ce mata ta tsshi a kasa..Ta zauna kan kujera..ke kuma Hanne kwashe kayan nan kikai Dakin ku..Ki kuma Shiga Kitchen ki Hado mata Ruwa da Lemo..!
Daga haka ta wuce zuwa Dakinta Aranta tana Tunanin to wacece wannan yarinyar da D'anmallam ya Taho da ita kuma kai Tsaye a bata Masauki a shashenta da wannan Tunanin ta karisa Dakinta bazatayi gaggawa ba koma me ke ciki tasan Malam ya sani Tunda tasan yaronta bazai Taba zuwa da wata garin nan batare da Izinin Malam din ba..!
Kowacce tayi abunda Hajiyar ta sakata Hanne ta kwashi kayan zuwa Ciki Aisha kuma tace mata ta Hau kujera sai taki Mirmishi Kawai tayi.
Kafin Lokaci an cika gabanta da Ruwa da kunun ayan da sukayi Jiya da Daddare.
Bata taba ko Daya ba tana gefe kanta na kasa tana wasa da adon Kwalliyar Dake Cikin Jakarta Hanne da Ya Aisha suna gefe suna kallonta kowacce aranta tana ayyana kyau kamar ita tayi kanta wannan Balarabiyar da Tambayan Ina Ya Danmlam ya samota..?
Hajiya tana Shiga Bedroom dinta Wayarta Dake kan gado na neman Dauki tana Dubawa taga D'anmalam ne,Da Sauri ta Dauka Tana Fadin"Danmallam kun iso Lafiya..!?

Dagachan Falon Baba Malam Baba Sa"idu na zaune akasa kusa da Baba Malam Dake kan kujera Cikin Farin Raawani suna mgana shi kuma yana Daga chan gefe kamar zai bar Falon kansa na kasa yana Shafa Sumar kansa da bata da yawa.
Cikin Tattausan Muryan da ban taba jiba wacce ta Chakule da Labarci Yasa bata fita saosai kamar yana Koyonta yace"Mun sauka lafiya Hajiya..!ya muka Sameku..?
Hajiya tace"Duka muna Lafiya..!
Sai kuma Shuru ya biyo baya Hajiya Bata Damu ba Sanin Halinsa ko Waya ya Kirata sai ya bata Lokaci kafin ya ce wani abu bayan sun gaisa.
Kamar ana Fizgan mganar Daga bakinsa yace"Hajiya kinga Bakuwa ko..?
Hajiya tace"Eh fa..Yanzu na Dawo Ciki Shamsu yace kai kace ya Kawota Shashena..!
Karkaace kai yayi kamar mace kafin yace"Eh Hajiya..Aisha na kusa ko Hannatu..!?
Hajiya tayi mirmishi tace"Suna Falo Tare da Bakuwar D'anmallam ko na fita na kirasu ne..?
Sai da yayi shuru jin bai yi mgana ba yasa tasan yana jin nauyin yace ta kai musu wayar ne yasa ta Nufi kofa tana Fadin"Kada ka damu..bari na fita na kai musu wayar..!
Da kamar yace ta barshi bari ya Kira Sarood din ammh Hajiya Har takai Falon ji kawai yayi tana Fadin"Lafiyanku kuka zauna kuka tasa Bakuwa agaba kuna kallo..?bana son Shanshanci..Ke Aisha karbi Waya yayanku na son mgana Dake..!
Tafada tana mika musu wayar ganin yadda suka wani tasa Bakuwa gaba suna kallon Dariya sukayi harda Hanne yana ji sanda tace"Wlh Hajiya tana da kyau baki gani ba..?
Hajiya ta tsaki kafin tace"Bangani ba..!
Daidao Sanda Aisha tamai Sallama Cikin Girmamawa ta gaisheshi ya amsa Lokaci Daya yana Fadin"Ke da Hannatu meyasa bakuje makaranta ba..?
Da Sauri tace"Yaya ai muna Jarabawa ne.kuma yau bamu dashi ni da Sadiya da Ikram duk muna gida Hanne kuma sun gama Jssce suna gida suma sai an koma Firstime..!
Kansa ya kara shafawa ya manta fa ko Dazu Shamsu ya fadamai haka da sukaje Dutse suka Daukosu Daga Filin Jirgi,Dayake ta Kano suka Sauka Daganan suka Hawo Jirgin Daya kawosu Dutse.
Cikin Muryansa mai Cike da Zati yace"Kunga bakuwa ko..?
Tace"Eh yaya..Mai kyau da ita wlh ya sunanta..!?
Dan Bakinsa ne ya Motsa kafin yace"Sarood..sunanta batajin Hausa ki rika mata Labarci yanzu dai me kuka bata..?
Kai Tsaye tace"Ruwa da abun sha..Muka fara bata yaya..,!
Kamar bazai yi mgana ba sai chan yace"Aisha ki kaita Dakin ku kice mata tayi wanka..Ta huta tukunnah kina jina..?
Da Sauri tace"To yaya..!
Kai Tsaye yace"Mika mata wayar na Fadamata..!
Ba musu ta mikamata tana Kallomta Tace"Yaya..!
Karba kwwai tayi ba Domin ta gane ba tana kara a kunne taji muryansa Nan da nan ta washe baki basu san me ya Fadamata ba suka ga ta mike Lokaci daya tana mika Aisha wayar Ita kuma tayi gaba sai gata tana Binta abaya Har Dakinsu Hanne ta Bisu da kallo kawai
Har Toilet din sai da Aisha ta nuna mata sannan ta Fice ta barta bayan ta ja mata Kofar Dakin Hajiya ta shiga ta Isketa tana Duba wani Turaran wuta da aka aiko mata Daga garinsu Maiduguri duk da yanzu Saboda Rashin Zaman lafiya Danginta duk sun Dawo Cikin maiduguri wandanda suka Rage Mahaifinsu ya Dade da Rasuwa.
Mikama ta wayar Tayi Hajiya ta karba? batayi mgana ba ita bata wannan Shisshigi sai Aishan ne tace"Hajiya Dakin mu yace na Kaita tayi wanka ta Huta..!
Kai kawai hajiya ta gyadamata bata ce komai ba ba irin su daya da Aisha ba Abida ba mai Shigen Surutu ba da hannatu,yasa bata Dameta ba ta fice ta barta sai Faman Raba Turarenta take zata Bama abokan zamanta Sauran ta aika ma su mamanmu Dashi haka Hajiya take Ko sun san da abu ko basu sani ba Sai ta Dibar musu wannan Kirkin nata kowa yana Girmamata Saboda shi.

Sanda ya gama wayar ajiyar Zuciya ya Sauke lokaci Daya yana Sauke wayar Daga kunnensa,kusurwan Falon Mallam yake kallo inda Cabet din Jerin Littafansa suke,Tunani yake yi yazai yi ya Sanar da Hajiya ya kara aure..?ga Halin da Sakina take Ciki Tunda ya Fadamata an Daura musu aure da Sarood take kuka taki cin abinci ta Daina mai mgana Har yau da suka so gida Allah ya gani bai taba son Sarood ba ammh Tana da kimar da bai isa ya Wulakantata ba.
Daga Bayansa yaji Baba Sa"idu na Fadin"UMAR Baba mallam na mgana..?yace ko baka gama wayar bane..?
Jin Haka yasa Lokaci Daya ya Dago kansa Tare da Juyowa Ya fara Tako Doguwar Kafarsa Zarara saman Tattausan Cafet din Dake Falon Malam din
Tsarki ya Tabbata ga Shugaban Hallitun Duniya..Domin Tsabar kyau da Zati da kwarjini wajen bawan Allah nan,Shi ba Fari bane kuma ba Baki ba Fatarsa wani irin Fatace mai kalan Haske kamar na yan Moroci Tattausa Saboda jin Dadi da Hutu tana Sheki Dogon Namiji ne wanda ake Kira Ingarma yana da Fadin Kirji Daga Kafadunsa zuwa cikinsa ya Bude,FUSKARSA doguwa ce Sambal masu Dauke da matsaikatan Idanuwansa da Gashin gira dana Ido..Hancinsa Dogo ne ammh ba Sosai ba wanda ya karamai kyau da Zatinsa Sannan Bakinsa Zagaye da Saje baki wanda ke karamai kwarjini Daga kasa kuma gemunsa wanda yabar gemu kadan wanda bau wuce kamu Daya ba.
Wanda ya Dace da Zagayyen Bakinsa mai dan Fadi kadan da Tudu,yana Sanye Cikin Pakistan Riga da Wando na yan Saudiya Rigar Tawuce gwiwansa Sannan wandon bai rufe kwarin Kafansa ba Kansa Sanye Cikin Hula irin ta Larabawa karamar nan wacce iyakarta rabin kansa mai Kulin Gashin Sakan Hulan Daga sama Wanda ya ba Sumar kansa Daga kasa zuwa sama sama Bayayyana Duk da ya Asketa ammh gatanan tayi kwance gwanin Burgewa sannan Goshinsa ga Bakin Tabon sallah nan wanda ke karamai kwarjini da Haiba.
UMAR YUNUS ABDURRAHAMAN BAZANGA kenan Namiji kwara Daya Tal da Bayan Sa"idu Mallam ke matukar kauna acikin Ransa a Cikin Jerin ya"ya ashirin din da Allah ya basa mai tarin baiwa da Allah kadai Daya Hallicesa ya sani mai kimanin Shekaru Talatin da Takwas zuwa da Tara aduniya.
Har ya kariso ya zauna Kusa da Baba Sa"idu Baba Malam da Baba Sa"idu basu daina kallonsa ba.
Suna kara yaba kyan zatinsa ko su kansu kwarjini yake musu Tabbas Qur"ani ba karya bane kana ganin Mahaddacinta kake ganewa Saboda Natsuwar dabam take.
Kansa na kasa Cikin Muryansa mai Zaki yace"Afuwan Baba..na kira Hajiya ne..!
Baba Malam ya gyada kai kafin yace"Kace Shashenta ka Sauki bakuwar taka ko..!?
Kansa na kasa ya gyada kai Baba malam ya cigaba da Fadin"Hajiya ko bata san mutum ba ita din mai karamci ne..Zata karramata matuka..!
Baba Sa"idu yace"Sosai shiyasa nace a kaita chan kaawai..!
Baba Malam yace"Da kaji an ambaci Hajiya Jikin ka na rawa ka yabeta..Ina mamakin yadda ZAINABU ta kwacemin SA"IDU NA..!
ya karishe Fada Cikin Zolaya.
Baba Sa"idu na Dariya Danmalam kuma Mirmishi kawai yayi.
Kafin Baba Sa"idu yace"Haba dai..Ai Tsakanin Uwa da d'a akace sai Allah baba..Kuma haka Tsakanin Uba da Dansa sai Allah har Abada Sa"idu na Baba Malam ne ba shi ba duk wadanda ke karkashin sa naka ne Baba..!
Baba Mallam Zuciyarsa kamar Farar takarda ya gyada kai kafin yace"Allah ya albarci Rayuwarka Kai da iyalanka Sa"idu..!
Suka amsa shi da Umar atare,Kafin Baba Malam yace"Ni na hana Sa"idu ya Fadama Hajiya komai..na bari sai ka zo..Ko sauran abokam zaman nata ban Sanar da kowa ba..Ina Fatan ka Fadama ita Dayar iyalin naka ko..?
Kansa na kasa yace"Eh na sanar da ita tun muna chan..!
Mallam yace"Dakyau haka ake so..Allah ya zaunar daku lafiya..Sai ka zama jajirtattacen adalin zama da macen Fiye da Daya sai Adali Umar..Bana jinka nasan bazaka taba aikata wani abu mara kyau ba..Sannan itama Diyar Kattab din indai Halin Mahaifinta ta Biyo Har Abada bazakayi nadama ba..!
Baba Sa"idu yace"Allah ya sa...!
Kansa na kasa shidai bai ce komai ba basu Damu ba Sanin Halinsa Shuru Shuru bai da Hayaniya.
Baba Malam ne ya kalli Baba Sa"idu yana Fadin"Sa"idu ka tafi wajen aika..Nima anjuma kadan zani Gidan Sarki Tun jiya Sakon sa ya isoni yana son ganina..Umar kuma ya shiga Cikin Gida ya gaida iyayensa zuwa anjuma sai mu zauna gabadaya domin a gabatar da Bakuwar data shigo Cikinmu Gabadaya..!
Baba Sa'idu ya jinjina kai yana ma Malam Allah ya kiyaye Hanya.
Tare sukayi mai Sallama suka Fice shida Baba Sa"idu sun Dade aharaban gidan suna jingine jikin Motar Baba Sa"idun suna mgana kafada na gugan kafada Malam na daga cikin Falonsa yana Hangesu ta Wandow Falon Lokaci Daya ya saki kayattacen Mirmishi.
In ka gansu kamar wasu yaya da kaninsa uwa daya uba Daya ya Tabbata abunda bazai iya Fadamai bane yake Sanar da Sa"idu Akwai Shakuwa da Fahimta a Tsakaninsu Yana Daukansa kamar kaninsa Shima yana Daukansa kamar yaya kuma Uba agaresa
Sun dan jima suna mgana kan yana Fadamai bai Tsara Karin aure yanzu ba, sai dai kana naka Allah na nashi ne Baba Sa"idu na ta bashi Wasu Shawarwarin kafin suyi sallama ya Shiga Mota ya wuce Gidan gona yayinda Shi kuma ya Fara takawa yabar Filin Haraban gidan zuwa Shashen Hajiya ammh Kuma Ransa da da Kallonsa na Shashen Anty Amarya yana Tunanin ko Sakina ta Daina kukan..?ya manta Rabonsa Daya ga taci wani abu sai ruwa kawai..!











*Janafty*
*TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janaftyd'?*

*Sadaukarwa ga Halima Yusuf gwarzo (Besty) Alherin Allah ya kai miki a dukkan inda kike*


*
Cikin Tafiyarsa ta natsuwa ya karisa Shashen Hajiya babba kamar yadda yake a ka"idarsa sai ya fara isa shashen Mallam sun gaisa sannan sai ya shiga cikin gidan Daya bayan Daya ya Bisu ya gaishesu.
Hajiya na cikin Dakinta har alokacin Daya shigo Aisha ce da Hanne har Lokacin afalon yana Shigowa Cikin Sallamarsa da Muryansa mai Zaki da Sanyi a koyaushe,Lokaci daya da kamshin Turaransa na Arab yayi musu Sallama..!
Gabadayansu suka mike Cikin Fara"a da Murnan ganinsa domin sun Dade basu gansa ba Tun Karshen wanchan Shekara sanda yazo Lokacin Duba Hajiya ce Datayi ta Fama da Kafa suna makaramta basu gansa ba kuma Kwana Biyu yayi ya koma.
Hannayensa duka Sanye Cikin Aljihun wandonsa ya Kariso Tsakiyar Falon gabadayansu har suna Hada baki wajen gaisheshi da yanayin Natsuwarsa ya kallesu yana amsa gaisuwarsu yana kara ganin girmansu acikin Idanuwansa.
Kai Tsaye yace"Hannatu Aisha meyasa baku je makaranta ba..?
Da Sauri Aisha tace"La yaya bana Fada maka ba..!
Sai Alokacin ya tuna da Sauri yace"ohm.Sorry na manta..Allah ya bada sa"a..!
Suka amsa da Ameen gabadayansu sai kuma yayi shuru yana kara nazarin Falon kamar me neman wani abu basu Damu ba Sanin Halinsa Sannan babu wani Shakuwa sosai a Tsakaninsu Tunda shi Babba ne sannan Lokacin da suka taso baya kasar yana Madina so zamansa Dasu bashi da yawa ammh duk da Haka yana da Kwarjini da baiwar da kowa ke girmamasa,ba Duka yake yi ba ba kuma Fada ba,Shi ina ma ya zauna ballatana yayi Hukuncin ..?in yazo kuma bai wani Dadewa yake komawa sai dai AllAh ya riga ya bashi wannan girman kuma ya Dauka kamar yadda In mallam yayi mgana bamai Musamai haka shima mgana Daya zai yi Cikin kwanciyar Hankali da Salama kowa zai shiga Taitayinsa bawai bashi da Sakewa bane, bai da yawan wasa da Dariya sannan bai da mgana ballatana Hayaniya yana da Matukar Sanyi Sosai a lamuransa.
Kamar ma ya manta daasu acikin Falon Saboda yadda yayi Shuru bai kara mgana ba sai chan ya kalli Aisha kafin yace"Ina bakuwar ku.?
Da Sauri tace"Na kaita Dakinmu na nuna mata Tiolet tana ciki na barta Tun dazu..!
Kai ya gyada kadan kafin yace"Ina Hajiya..?

Wannan karon Hanne ce ta nuna mai Dakinta tana Fadin"Tana ciki Yaya..!
Bai tsaya kara mgana ba ya Kama Hanyar zuwa Dakin Hajiya Cikin Natsuwarsa kannensa suka Bisa da kallon Sha"awa Duk cikin gidan nan ba kamarsa Sai dai abiyo bayansa.
Sai da suka Tabbatar da ya shiga Dakin Hajiya sannan Hanne ta Juyo Tana Fadin"Ya Aisha kinga yadda Ya D'anmalam ya kara kyau kuwa..?Wlh nima ina son naje Madinar nan Watarana..!
Aisha tana jinta batace mata komai ba illah ta Cigaba da Duba Littafin Dake Hannunta Hanne bata Damu ba Sanin Halin Aishan itama din mai Sanyi ce.
Hajiya na Tsaka da kasafin Turaranta Taji Sallamarsa Cikin Sanyi da Haiba Lokaci daya da Kamshin Turaransa mai Sanyaya Zuciya batasan Lokacin data saki Mirmishi ba Cikin Farinciki ta amsa sallamar tasa tana jaye kayan gabanta Lokaci Daya tana mai maraba.
"Maraba..Maraba..Maraba da Danmallam maraba da bakin madina Bakin Larabawa..!
Sai alokacin hakoransa kadan suka Fito yana Mirmishi gaban Hajiya ya Duka kansa na kasa yace"D'anmallam dai Hajiya..?Har yaushe ne zaki Fara Kirana da Umar ne..?Alhalin Baba Sa"idu Sa"idun sa kike kiransa Hajiya..!
Hajiya na Dariyan Farincikin ganin Yaronta ta kauda mganar da cewa"Masha Allah..Danmallan me kuke ci a Madinar ne.?gabadaya ka Sauya ka koma kamar Balaraben chan..!
Kai kawai ya gyada yana Shafa Gemunsa kafin yace"Hajiya bakomai..Sai nasaran addu"an ku gareni..!
Hajiya tace"Hakane..Allah ya kara Tsareka Allah ya Dafa maka Allah ya albarkaci Rayuwarka..!
Ya amsa da Ameen kafin ya Dago yana Fadin"Hajiya baki ce Allah ya bani Zuru"a ta gari ba..!
Hararansa tayi kafin tace"Ko ban Fada ba..Ina maka wannan addu"ar D'anmallam..!
Daman yasan haka zatace yadda Hajiya ke kunyarsa ko Ita Bafullatanane sai haka Tambayan kowa da kowa yayi tace duk suna Lafiya,Shuru ya biyo baya shi bai ce mata ba itama yasan bazatace ba Hajiya nada wannan Halin bata matsa ma Mutum akan abunda tasan Dole zata saani Shiyasa bata ce masa komai kan Sarood ba shima bai ce mata ba.
Kansa na kasa yana Duke ita kuma tana Cigaba da Zuba Turaranta Ganin Yaki zama kuma yaki tashi yasa ta kallesa tana Fadin'Ka zauna mana..Kada Tsugunnen ya gajiyar Dakai..!
Kai ya girgiza kafin yace"Hajiya Ina da gajiya ajikina..So nake na shiga na gaisa da su Hajiya uwa..Kafin naje nayi wanka na Huta..!
Kai ta gyada kafin tace"Hakan ma ya kamata..Mallam ya fitan ne..?
Kansa na kasa yace"Bai riga ya fitan ba ammhh yace yanzu zai fitan..Muna ma nan Haraba ni da Baba Sa"idu yanzu ya wuce gidan gona..!
Hajiya tace"Sa'idun Zainabu da Malam..ya shigo mun gaisa tun zuwansa..!
Bai yi mgana ba ita kuma ta kallesa tana Fadin"Dame zaka Karya..?nasa dai yaran sun yi maka Sinasir da waina..Bansan kuma me zamu ba wannan bakuwar ba kasan ku achan ba irin Cimar mu bane naku..!
Sai alokacin ya Dago kafin yace"Da kuli Hajiya..?
Kai ta gyadamai tana yar Dariya shima Mirmishin yayi yana Fadin"Yaushe Rabona da waina da kuli Hajiya..?Naji dadi sosai su dafamin ruwan Tea da na"a na"a,su hadomin da waina din ita kuma Sarood su hada mata Tea su soya mata Kwai is ok..!
Hajiya bata wani Damu ba tace"Shikenan.Ammh a Shashen mallam zaka Huta..?ko yanzu zaku isa gidan naku..?
Da Sauri yace"Sai Dare hajiya..Dakin su Shamsu zan yi wanka na Huta zuwa an juma..!
Hajiya tace"Na manta ne da na saka su Akilu sun gyara maka Dakinsu Nazem ka Zauna aciki..!
Kai ya kada kafin yace"Bakomai Hajiya nan din ma ya isa..!
Hajiya tace"Ai shikenan..!
Yana kallonta Kafin yace"Hajiya Turare kika fara saidawa..?
Hajiya tace"A"a Goggonku Yakura ta aikomin dashi shine nake rabawa zan aikama sauran iyayanka Sauran kuma na matan Sa"idu ne..!
Danmallam ya Murmusa kafin yace"Su yaya suna Lafiya..!
Hajiya tace"Duka suna Lafiya..!
Daganan sukayi shuru hirar ta kare ya Dade kafin ya tashi ya mata sallama ya Fice,Bayan ya fito su Hanne sun zata zai nemi Sarood sai dai bai ce musu komai ba ya Fice bayan Fitarsa Hajiya ta leko tace Hanne ta Dafa Ruwan Tea ta soya kwai ita kuma Aisha taje wajen Shamsu ta karbi key din Dakin Su Nazem ta dan gyarama Danmallam ya samu wajen da zai karya ya Huta.
Dukkansu da toh suka amsa Aisha tatashi ta saka Hijabi ta Fice,Hanne kuma ta shiga Kitchen.
Daga Dakin Hajiya Shashen Hajiya Uwa ya isa Tana ganinsa Cikin Fara'arta ta fara mai maraba itama Dukawa yayi yana gaisheta ta amsa tana Fadin"Umaru basai ka jira mu zo sannu da zuwa ba..!
Kansa na kasa bai ce komai ba tayi Dariya ya tambayeta yaran tace kowa Lafiya sai ga Umaima ta fito ta gaisheshi ya amsa yana kallon Hajiya uwa kafin yace"jikinta ya daina tashi ko..?
Hajiya Uwa tace"To ya dai yi Sauki Umaru..!
Kai ya jinjina kafin yace"Allah ya kara afuwa..Nazo mata da wasu manganuna in na Huta zan kawo mata ta fara amfani dashi mu gani..!
Hajiya Uwa ta fara mai godiya yana amsawa Har ya fice tana Rakasa da addu"an haka take ita tana da Kirki kamar Hajiya take.
Daganan sai bangaran Haj.Nasara itama

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login