Showing 78001 words to 81000 words out of 265571 words

Chapter 27 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28953

na aikata Bata sani ba..Ba Laifina bane Soyayyace ta jani inda ta kaini Ina sonka ammh kayi hakuri mu Kareta anan akuma yau Aminu...Don Allah kayi hakuri..!
Kuka take kamar ranta zai fita Aminu yaji kamar ta Chakamai mashi da Sauri ya Mike yana Fadin"Bazai taba yuyu ba Amina..Ina bazan iya Rabuwa Dake ba..Laifinki ne da kin bari na gabatar da kaina da Duk haka bai Faru ba..!
Yau ba sai gobe ba zan bayyana kaina Amina insha Allahu ke Rabona ce..!
Jin kalamansa yasa ta Mike da Sauri Har tana neman faduwa tace"Kada kayi haka..Lokaci ya kure abunda zaka aikata bazai kawo mafita ba Amin..!
Yana Kokarin Hana Idanuwansa zubar kwallah ya ke kallonta ta Duhun wajem Cikin wani yanayi yace"Menene Mafitan AMINA..?
Kada kice mafitan itace na Hakura Dake..Wlh in haka ta faru Zan Lalace Amina akanki ki taimakeni kimin Rai don Allah..!
Yake fada sai Hawaye Gwiwansa ya saka a kasa yana Rokonta Kada ta barsa Amina ta Rude batasan sadda ta saka Hannu ta Dago Kafadun Aminu ba Cikin kuka take fadin"Don Allah ka tashi..Na shiga uku..!

Yana Dagowa bai yi wata wata ba kawai ya jawota ya Rumgume kam kam kamar wani zai kwaceta alokacin Inda tasan sanadin wannan Rumgumar Zanen kaddaranta zata fara na Tabbata da Amina bata amince ba in da Aminu yasan sanadin wannan Rumgumar Amina zata haramta garesa da har Abada bai yarda yazo ba..Sai dai ina bakin Alkalami ya Riga ya Bushe..!
Amina ta kasa yin wani motsi ballatana ta kwace jikinta Tayi luf akirjin Aminu yana Fadin"Bazan iya Rayuwa baki ba Amina..Kinsan ina sonki..kinsan ina sonki in kika barni ina zan saka kaina..?
Amina alokacin Tunanin bai bata ta kwace jikinta ba,tsausayin Aminu da soyayyarsa ya Rufe mata idon da bataji bata gani.
Alokacin wani al"amari ya Faru wanda ya Faruwarsa ya Fallasa abubuwa Dadama kuma ya Watso wasu sirruka a waje alokacin kuma Zanen kaddaram Amina da wanda Allah ya Turo mata cikin Rayuwarta ya fara..!
Suna cikin waannan yanayin suka ga an Dallaresu da Hasken Fitila Lokaci Daya Cikin Muryansa da ko barci Amina Take bazata taba bace Mata ba yace"Su waye anan..?

Dam..!

Gabanta ya amsa hakama na Aminu arude ta Dago kanta Daga Kirjin Aminu karaf Hasken Fitilan ya Hasketa Tar Cikin Faduwar gaba da wani yanayi ya Jafar ya Zaro ido Cikin Tsawa yace"AMINA..!!!

Yadda ya Kira sunan ne ya Girgiza Zuciyar Amina Hanjinta suka Cure waje Daya kuma har Alokacin Tana Rike da Aminu shima yana Rike d ita Rudewa yasa sun kasa Sakin juna..!
Hamida Daga cikin gida ta kalli Hanne tana Fadin"Hanne gabana na Fadi..Inaji ajikina mun rusa komai fa..!
Ita kanta Hannen Jikinta rawa yake gabanta na Fadi Cikin Tsoro tace"Nima Hamida..Na farajin wani iri na fara Nadama fa Hamida..!
Hamida ta Bude baki zatayi mgana kenan Muryan ya Jafar ta shiga kunnensu sanda yake fadin"Innalillahi Amina me zan gani..?
Iskancin naki har yakai kikawo wani kato a kofar gidanku kuna shanshanci Amina..!
Dam gabansu ya fadi atare suka kalli juna suka zaro ido kafin suyi Rige rigen Lekawa ta kofa sai da suka kusa Sakin Fitsari a wando ganin ya Jafar Tsaye bakin lungun da su Amina suke ya Hsskesu da Hasken Fitila Fuskar nan kamar an aikomai da Sakon mutuwa.!
Hamida ta Damke hannun Hanne suna karkawa Lokaci daya suka Hada Baki wajen fadin"Mun shiga uku..Mun kara saka Amina acikin Bala"i..!
Agaban idonsu ya jafar ya taka ya Shiga lungu sai gani kawai sukayi ya Tunkudo Amina saida Hijabin jikinta ya Hardeta ta Fadi yaraf Cikin Fitan Hayyaci ya saka kafa ya Shureta yana Fadin"Tashi Tashi munafuka yau Allah ya Toni asirinki..Daman wannan Idanuwanki bakomai a Cikinsu sai iskanci Kee Amina yarinyar dake Rumgume da wani kato Amina..?
Tashi muje gaban Aba na Sanar dashi Abunda nagani tashi nace don Ubanki kafin nayi miki illah yanzu nan..!
Yafada yana kokarin kara Shurinta da Sauri Aminu ya rikosa Cikin wani yanayi yana Fadin"Kadaina Dukanta..Don Allah ka Tsaya ka Bincika wlh ba abunda kagani bane gaskiya..Ina son Amina kuma auranta zan yi..!
Ya jafar ya Fincike hannunsa bai yi wata wata ba ya Daga hannu ya Sharara ma Aminu mari lokaci Daya ya Nunasa da yatsa yana Fadin"kai har kana da bakin mgana Lallatacce kamar ka..?Allah ya isa Tsakanimu dakai Tunda kayi Samadiyar batamana kanwarmu kuma kabar kofar gidan nan kafin na Fito da matasan gidanmu su Illata ka yanzu nan..!
Shi bai Damu da kansa ba Amina yake kallo tama kasa kuka Zuciyarta ya Soye ta riga ta sani ajikinta tanaji Ba wani Tsumi ba Dubara ayadda ya Jafar ya gansu Allah ne kadai zai iya Fitar da ita shiyasa ta kasa motsi ko mgana!
Yana so yayi mgana bakinsa yayi Nauyi yana ji yana gani Ya Jafar ya isa ga Amina ya taso ta Bai yi wata wata ba ya Daga hannu Dama da Hauni ya Dauketa da maruka da sai da ta Koma ta Kife kamar zata Fadi ya Fizgota yana Fadin"Muje agaban Aba da mamanmu mai kareki..Ki Fada musu Tun yaushe kika fara Wannan Lalacewar Amina..!
Ya karishe Fada yana ingizata gaba,Aminu ya taka ya Bisa ya Dagamai hannu yana Fadin"Karka Nuna min iskanku na yan Tasha..Nima In akabi ta wani Fanni na Fika tashanci wlh zan kara Dauke ka da mari Kaji ma na rantse in baka bace Daga gani na ba..!
Ayadda Ya Jafar yake zai aikata Abunda ya Fada din sai ya koma baya Cikin Raunin Murya yace"Amina komai zai yi Daidai..Zan tafi Yola...su Alhaji Baba zasu zo nema min Auranki..!

Amina tana jinsa tana so,tacemai kada yayi haka,ammh kuma a wannan gabar bazata iya mgana ba Domin mganar bata da wani amfani..!
Hamida da Hanne suna jin Bude gidan ya Jafar suka Rumtuma zuwa Cikin gida ba inda jikinsu baya rawa Saboda Abunda zai iya Faruwa yau..!
Haka Ya Jafar yake iza keyar Amina kamar wacce tayi sata Yana tafe yana Dukanta Fadi yake"Amina kece Rumgume da wani kato..?
Yaushe kika fara wannan lalacewar..?
Yana Fadi yana Dukanta Saboda Wani Bakinciki ke kara kamasa in ya Tuna da yadda yaga Amina Rumgume jikin wani kato..!
Hanne da Hamida Dakinsu Hamida suka Fada suna Haki ya Zeenatu na kwance ta Mike tana kallonsu,Cikin wani yanayi tace"Lafiyarku kuwa..?
Kasa mgana sukayi jin Muryan ya Jafar Tsakar gida yana Kiran sunan Aba gabadayansu suka kara Tsurewa Hamida da Hanne suka kamkame hannun juna,Saboda Tsoro ya Zeenatu ne ta Mike tana Fadin"Muryan Ya jafar nake ji..?
Meya faru kuma..?
Tafada tana mikewa Tsakar gida ta Fita Daidai Sanda Aba ya fito shi da Yaya Sai kuma Mamanmu data fito Daga Dakinta Dankwali a hannu Tana Fadin"Lafiya hayaniya me nake ji..!
Ya Jafar Amina ya Tura gaban Aba sai da ta Fadi cikin Fushi yake fadin"Aba Gatanan ta fada muku tun yaushe ta fara Lalacewa..Yanzu nazo zan karbi mganin da za"a shafa ma mai sunan Mallam akansa kawai naci karo da yarinyar nan Rumgume ajikin wani Dan iskan kato ajikin gidan nan Aba..!
Gabadaya jikin Aba sai ya fara rawa Yaya,kuma Kirjinta ne ya fara Lugude Yayinda Mamanmu ta saka Salati tana Fadin"Innalillahi...!
Haka kawai take fada Hanne da Hamida dake cikin Daki suka kalli juna suka Gwalo ido,ya Zeenatu kuma zuciyarta sai da ta amsa Amina bazatayi haka ba Halinta bane..!
Ba wanda ya Lura da Aba Jiri ya kwashesa sai da ya Saka kafa ya Ture Amina Dake gabansa takasa kuka sai na Zucci Domin kukanta bazai taba Cetonta ba..!
Kadan ya Rage bai Fadi ba Yaya tayi Saurin Rikosa ta fashe da kuka Bango ya Dafa yana Fadin"Jafar fitarmin da ita Daga gidana..Ka fita da ita ban Haifi Dan da zai zamenin zakka ba ta ficemin Daga gida..!
Yake Fada sai hawaye Sharr Mamanmu ta Fashe da kuka tana Fadin"Na shiga uku ni balaraba..In ka Koreta ina zataje Abbansu..?
Wlh Amina bazatayi haka ba Halinta bane..!
Ta karisa wajen Amina ta Dago tana Fadin"Amina ki tashi ki fadamusu karya ne..Abunda Jafar ke fada ba gaskiya bane..!
Da manyan Idanuwanta Take kallon Mamanmu Lokaci ya kure bazata iya kare kanta ba batasan sadda tace"Gaskiya ne Mamanmu..Gaskiya ne ya ganni..Rum..Rumgume..!
Bata karisa ba Mamanmu ta Dauketa da Mari Cikin kuka take fadin"Karya ne..Ba gaskiya bane..!
Take Fada tana kuka kamar Ranta zai Fita Zuwa Lokacin hatta Hanne da Hamida sun fara kuka Aba kuma Yaya na Rike dashk Dafe da Bango Yana Hawaye..!
Ya Jafar ya kalli Aba yana Fadin"Aba kadaina kuka..Wannan yarinya Dukan mutuwa zan mata yanxu nan..Wai har dan iskan yaron yana Fadin sonta yake yi zai aureta..!
Aba ya girgiza kai yana Fadim"Na Rantse da wanda Raina ke hannunsa bazan aura ma Amina wannan yaron ba..Jafar Amina bazata samu abunda Take so ba..bata isa ba..!
Yafada yana jin wani Takaichi da Bakinciki Ya Jafar Cikin mamaki yace"Dama kasan shine Aba..?
Aba ya jinjina kai yana Bama Jafar Labarin abunda ya faru bai gama ba Ya Jafar ya Finciki Amina ya Fara Dukanta yana fadin"Kafin ki kashemana Uba ke zaki fara Binsa Amina..!
Dukanta yake yi kamar Allah ya aikosa Ba wanda ya hanasa Yaya kuka take tana rike da Aba Dake fadin"Hadiza kamani muje ciki..Jiri nake gani..!
Ya Zeenatu ma kuka take tana Fadib"Mamanmu ki cece Amina ya jafar zai kasheta..!
Mamanmu Dukewa tayi tana Fadin"Jafar kadaina Dukanta don Allah..Jafar kabari..!
Take fadi ko jinta bayayi sai ma Karisawa da yayi ya karyo ganyen Bishiyar Dake Tsakar gidan ya Shiga Lafta ma Amina wacce bata kuka ko kadan sai na Zuucii awannan gabar ta gagara tana jin kada ma wani ya Ceceta abarta ta Mutu ta huta ta saka Mamanmu kuka da Yaya,Aba ma yana kuka Saboda ita ai bata da wani amfani acikin wannan Rayuwar..!
Hanne ce Jikinta na Rawa da wayar Hajiya Dake hannunta ta Kira Baba Mallam wanda mamaki ya kamasa ganin Hajiya zaune gefensa suna Hira Cikin mamaki yace"Yau kuma Zolaya kike ji ne Abu..?
Kallonsa tayi kafin tace"zolayar mene Mallam..?
Wayarsa ya nuna mata yana Fadin"Kirana akeyi da wayarki fa..!
Cikin mamaki tace"To lafiya..?Wayata tana Daki na barta fa!
Jin haka yasa bai ce komai ba ya Daga Kiran kukan Hanne ya fara ji tana Fadin'Baba Kazo gidan Baba Sa"idu..Ya Jafar zai kashe Amina da Duka kazo da sauri..!
Baba Mallam Zumbur ya Mike Cikin tashin hankali yake tadin"Hajiya Wani abu ya sake faruwa..Muje gidan Sa"idu..!
Hajiya ta fara salati Hankalinta tashe ta Rarumi hijabinta ta saka Baba Mallam na kan gaba suka Fice Daidai Anty Amarya ta fito zuwa shashen Mallan taga fitarsu Cikin gaggawa tasan ba Lafiya itama sai ta Rufa musu baya ganinsu sun shiga gidan Baba Sa"idu yasa aranta tasan ba Lafiya Domin Baba Mallam baya zuwa gidan Baba Sa"idu haka kurum wani abu bai faru ba.
Cikin azama tabi bayansu Domin tana son Taga abunda ke faruwa..!
Abunda Su Baba Mallam suka gani Sai da Hankalinsu ya tashi Ya Jafar yayi m Amina Dukan kawo wuka Baba Mallan ne ya karbe sandan Hannunsa yana Fadin"Jafaru ashe baka da Hankali ban sani ba..?
Ya jafar na haki yace"Baba Mallam so take ta kashemana iyaye da bakincikinta..Shanshancinta ya wuce Tunanimku yau fa ganinta nayi a nan kofar gidan Rumgume jikin wani kato Mallam..Amina fa nawa take..?
Har ta gama lalacewa haka bamu sani ba..Shine kafin ta kashe su gwara ita ta Fara Binsu..!
Karaf manganganun akunnin Anty Amarya Data shigo Salatinta kawai akaji Tana Fadin"Innalillahi wannan yarinyar Tabbas zakka ce..Iskancinta nata har yakai haka bawanda ya sani..?
Kallonta kawai sukayi kowa ya kasa mgana Hajiya,Amina ta Duka ta Rumgume jikinta Duk ya Fashe da Duka Fadi take"Jafar kayi dukan ganganci..Ba haka akeyi ba..!
Mamanmu na gefe tana ta kuka ita da Zeenatu harta Jawaad Dake barci hayaniya ya tadashi ganin Dukan da Ya Jafar kema Amina sai shima ya Fara kuka..!
Baba Mallam Hankalinsa ya tashi Ya kalli Jafar yana Fadin"Ina Sa"idun..?
Da kyar yace"yana Dakinsa..!
Baba Mallam ya wuce gaba yana Fadin"Hajiya ki taikama Mamana..Kai kuma muje Ciki..!
Da haka ya tasa Jafar suka shiga Falon Aba Hajiya kuma Da Mamanmu suna Hawaye suka Daga Amina da Idanuwanta basa Buduwa Sai faman wash Wash take da kananun kuka Kilama ya Tardagata inji Hajiya Zeenatu ta kama musu suka yi Dakin Mamanmu da ita sai Lokacin Hamida da Hanne suka fito ganin Halin da Amina ke ciki suka Hade kai suna ta kuka Anty Amarya Fadi take"Ruwan zafi za"a Dafa ayi mata gashi..Allah ya kyauta bai mata karaya ba kinsansu in suka Fara Duka kamar mahaukata..!
Hajiya taji kamar ta Make bakinta sai dai batayi mgama ba batama san ya akayi tasan wani abu na Faruwa ba domin Anty Amarya sai dai ta Fadama wani Halinta..!
Ashashen Aba kuwa Baba Mallam suna shiga suka gansa kwance kan kujera Takure yana rawan Sanyi Fadi yake"Hadiza sanyi nakeji ki sakamin bargo..!
Baba Mallam ya Duka agabansa yana Fadin"Ashh Sa"idu me zan gani haka..?
Yana jin muryan Baba Mallam ya Bude ya Rarrafa ya tashi Zaune yana Cijewa Baba Mallam ya rikesa Hannunsa ya kamkame yana Fadin"Baba don Allah ina so cikin Almajiranka masu karatu ka Tallata Amina in akwai mai so..Bana so wunin gobe ya kare ban aurar da Amina ba..Ina jin tsorom wani abu ina Fargaba kada watarana Bakincikinta yayi ajalina..!
Baba Mallam yace"Baza "ayi haka ba kana cikin Fushi Sa"idu.
Mu Tsaya mu bincika zuwa gobe zan yi mgana da Mamantawa kan yaron Dake zuwa wajenta in har ya Chanchanta zan bashi Mamana..!
Jikin Aba na rawa yace"A"a Baba..Na riga nayi Rantsuwa ko bayan Raina Amina bazata samu abunda take so ba..Bata isa ta fita Zakka ba..Kada ka Saurareta Nidai ko Waye ka aura mata ta bar gabana na Daina ganinta ko zan samu Saukin Abunda nakeji..!
Baba Mallam yayi shuru yana kallon Baba Sa"idu ganin haka yasa ya kara Rike hannunsa sai Hawaye sharr yana Fadin"Kada kace A"a Baba Mallam
Kayimin wannan alfarman a mtsayin ka na Uba gareni ka yafemin in har ahalima suna goga maka bacin suna ka yafemim..!
Ya karishe Fada Cikin kuka,Da Jikin kowa saida yayi sanyi Baba Mallam yace"Kul..Kar na Sake ji..Kai jinina ne Sa"idu har gaban Abada..Kada ka Damu Zan aurar da Mamana kamar yadda ka Bukata sai dai bazan mata auran kaskasaci ba kafin waye wan garib gobe Allah zai bayyanamana Mijinta mafi Alherinta aduk inda yake Sa"idu kayi hakuri kada ka aibatata kila ita irin Tata Kaddaran kenan..!
Aba bai Sake mgana ba Tari ya Sarkesa kamar zai sheka Ya Jafar da Yaya suna Rike dashi yaya kuka kawai take Yadda take ji aranta baya Misaltuwa ita ta Haifi Amina Radadin da kowacce uwa take ji in Wani Daga Cikin D'anta ya zama zakka..!

Ganin Halin da yake ciki yasa Baba Mallam yace su tafi asibiti haka kuwa akayi Ya Jafar ya Tuka Motar Mallam dashi da Yaya suka tafi asibiti da Aba su Hajiya kuma suna tare da Amina da tasha gashi Ta samu Targade a Hannunta na Hagu da gocewar kashi a Kafarta Mamanmu da Hajiya suka Shafe mata da man zafi tana Hawaye sunayi Mamanmu ma kasa zama tayi ta koma Cikin Bedroom dinta tana kuka Anty Amarya na nan bata tafi ba da anyi abu sai ta Tafa Hannu tana Fadin"Oh..Allah dai ya shiryamana..An haihu dai a Ragaya..!
Sai da Hajiya ta gaji ta tanka mata da Cewa"Ki kama bakinki Domin kema Uwace..Akwai Sa"adatu da Sabeeha agabanki bakisam ina Kaddara zata kaisu ba!
Jin haka yasa ta Fara Fadin Hajiya na mata Mugun fata Cikin gatsali tace"Allah ya Tsareni kowa yasan ya"yana basu fita zakka ba..Daman ai wanda yasiya Rariya yasan zata Zubda Ruwa..!
Ba wanda ya kara bi ta kanta kuma taki Tafiya kamar mayyah har sai chan Dare Baba Mallam ya Dawo Jinin Aba ne yayi sama An bashi gado ya Jafar na wajensa zai kwana sai alokacin suka koma gida bayan Baba Mallam ya kwantar ma da Yaya da suka Dawo tare ita da Mamanmu hankali da kalamai masu sanyaya rai sun Daina kuka Amina kuma ta samu barcin Wahala Baba Mallam yace zuwa da Safe mai gyaran Targade zai zo ya gyara mata.
Sanda suka koma gida Dagashi har Hajiya sun kasa Runtsawa Fadi kawai Take"Na kasa gane meke Faruwa Mallam..?
Nasan Jafaru bazai yi karya ba..Nasam jikina na bani Amina ba haka take ba..!
Baba Mallam yace"Wani al"amari ne da Allah kadai yasan me ya Lullube aciki..!
Nan ya shiga Fadamata yadda sukayi da Baba Sa"idu ta sauke Tagumi tana Fadin"Kai..wata sabuwa to menene Mafita..?
Baba Mallam yace"zan kwana Istikara Zuwa Safe Boyayyan al'amarin zai bayyana Hajiya kema ki tayani..!
Da kai ta amsa mai,Tabbas sun kwana Gayama Allah Hajiya ce ma wajen Uku na Dare ta kwanta Baba Mallam sai karfe 4 ya iya barci saman Darduma bai tashi ba sai da yaji wayarsa Dake cikin Aljihunsa na Ringing yayi Zumbur ya Mike yana Lalubota yaga DANMALLAM.. !
Ne ke kiransa ajiyar rai ya Sauke ya Daga wayar da Sallama Dagachan bangaran Umar ya amsa cikin Sanyinsa yana Fadin"Baba..Nasan yanzu asuba ne a Nageria shiyasa na Bugo Domin na samu ladan tashinka Duk da nasan kila ma kana masallaci..!
Baba Mallam ya Mike a kasalance yana Duba agogon bangon Bedroom dinsa 4:55pm na asuba..!
Cikin karfin gwiwa yace"Na makara yau Umaru..Naji Dadin kiranka Allah yayi maka albarka..!
Ya amsa da Amen Cikin Farinciki kafin suyi sallama suna gama wayar Baba Mallam yayi kasake na wani Lokaci kafin Lokaci Daya Mirmishi ya mamaye Fuskarsa Hajiya ya kallah Dake barci ya karisa ya Bubbuga Gefen gadon yana Fadin"Hajiya..Hajiya..!
Mika tayi Cikin Tattatusan lafazi yace"Ki tashi mun makara sallar asuba..!
Mikewa zaune tayi tana Mutsike ido Lokaci Daya tana Fadib"Mallam kasamu mafita kuwa..?
Wlh da yarinyar nan na kwana araina ita da Sa"idu..!
Cikin Mirmishin data kasa gane masa yace"Kada,ki damu..Cikin ikonsa ya kawo mana Mafita tashi kiyi sallah ki shiga gidan Sa"idu ni kuma Daga masallaci asibiti zan tafi na Dubasa..!
Kai ta gyadamasa tana kallonsa ya saka akyabbansa da Rawaninsa ya Fice acikin ranta tana Tunanin wata mafita Mallam ya samu wannan Fara'ar dake fuskarsa ta bayyana Koma wata Mafita ce ta zauna sosai acikin Ran mallam din.!


Ina godiya sosai masu sharhi yan wattapad ina gaisuwa..!



*Janafty*

*TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janaftyd'?*

*
Suna idar da Sallar Asuba Baba Mallam bai Tsaya ba Ya Nasir ya Tukasa zuwa asibitin Tunda shima nan ya sallaci sallar asuba Ya jafar tun Daran jiya ya kirashi ya fadamai kafin su tafi sai da Baba Mallam ya Umarci Shamsu daya kira Mallan ya"u mai Dori yazo ya Duba Amina..!
Haka kuwa akayi gari na waye bakwai na safe Ya shamsu yazo da mai Dorin,Koda yaje Hajiya Babba tana gidan Amina jiki yayi Tsami sai faman kuka take ashe kadan tayi Domin wajen gyaran Targade da Goshewar data samu sai da ta raina kanta sai da su Hajiya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login