Showing 213001 words to 216000 words out of 265571 words

Chapter 72 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28893

tsiyan suke kusa sai a wuni ana Rigima ko kuma ta rika mai kananun kuka ya tafi chan ya manta da ita saboda yana da matansa achan shidai baki yake bata yana kawo mata Uzurinsa sannan take hakura kadan shidai fa yaga Jidalin Amina ganin idonsa ba Labari baa.
Dayake bata da matsalan kudi a waya Ya Usman na saka mata haka ma ya Aisha sannan ko kudin da ya Danmallam ya barta mata bata taba komai aciki ba sannan su ya Aisha bata karbi kudin ba tace Aminar ta ijiye a Hannunta tunda bata Bukatar
Komai na Bukatar Rayuwa babu abunda ya Aisha da ya usman suka Rageta dashi.
Mganar siyayyan Kayan Haihuwan kuwa Hajiya ya kira sa suka Tattauna yace zai turo mata kudi cikin satin da sukayi mgana Jafar ya kawo mata kudi 100k daga ya Danmallam,ita kuma bata taba komai ba sai ta nuna ma mallam shi kuma sai yace ta bari ya kara wani abu akai sannan yayi mganar Hada lefen da Umar bai samu hada mata ba mai zai hana a Hada ayi mata gabadaya..?
Sai Hajiya taga haka ya chachanta sai tace mallan din ya Kira Umar din suyi mgana haka akayi shi ya kirashi yamai tuni kuma ba domin ya Tunaamai ba sam ya manta yace zai Turo wasu kudin a kara dasu ammh zai siyan mata wasu kayan anan,Duk da bai da wani kudi a Hannunsa sosai bai Fadama mallam ba ammh shi mallam din ya Fahimci haka saboda Biyayyah Umaru garesa yasa kawai yayi ma Aba mgana aka fitar da kudi Dubu Dari hudu ya damkama hajiya yace a Hadama Amina lefe gangariya da kayan Haihuwa Bakin Hajiya yaki Rufuwa Amina ta fita Tsara Sai dai Danmallam yaji mganar kudin da mallam ya bada abakin Hajiya mamaki yasa ya kasa mgana Daya Kira mallam zai yi mgana sai ya hanasa albarka kawai ya sakamai tare da Fatan Cigaba da aminci a Rayuwarsa..
Danmallan kamar yayi kukan karamcin mallam agaresa wani kaunar mahaifinsa yana kara shiga ransa mallam kuma yasan tun bayan da Umaru ya tsaya da Kafafunsa bai Taba karban wani abu Daga garesu ba Sai ma shine da alherinsa baya yankewa koda dayake wani kasar Sannan yanzu Iyalai sun mai yawa ga Zama inda kasarsa ba akwai kashe kudi Sosai shiyasa yayi mai wannan karamcin domin ya nuna mai jin Dadin yadda ya amshi Umarninsa da Mutumci na auran Amina kuma ya riketa Bisa gaskiya da Amana.
Hajiya ita kanta taji Dadin hakan Sannan ai Dannallam ya chachanci komai a wajensu saboda Biyayyarsa,batare da Sanin kowa ba ta Kira Aisha sukayi mgana ta kuma Tura mata kudin duka 500k din tace a siya duka abunda ya kamata Hade da kayan Haihuwa ita kanta Aishar tayi mamakin uban kudin sai dai Tasan Amina ta Chanchanci dukkan gata yadda Hajiya da mallam ke sonta.
Duk ta Online tayi duka Siyayyan Tundaga kan akwatina da Sauran kayan Size din Amina kadai ta karba Duka har na bbys din ta Online ta siya so take sai ta gama Hada komai a kawo mata tunda anan Abujan matan mai saida kayan take Direba kadai zata bama Sako ya karbo mata.
Ko Amina bata san da kayan ba sai da aka kawo kuma na Jarirai kadai ta nuna mata ita da Yakaka Lefen kuma Damam Hajiya tace kada ta nuna ma kowa,Amina ita bata ma wani Damu ba Damuwarta ta Haihu Lafiya saboda ta fara Tsoron yadda ake fadin Haihuwa take Yakaka tayi ta saka albarka tana fadin basu da Tsara ita da takwaranta.
Acikin satin da Aisha ta gama Hada kayan Hajiya tazo ta Duba Amina ta kuma ga kayan wannan karon ma banda Mallam ba wanda yasan da zuwanta Amina taji dadin ganinta ta makaleta har da Hawayenta Hajiya mamaki ganin yadda Amina ta koma sai ya kamata ta fara Tunanin anya Mutum Daya ne acikin Amina ganin yadda girman cikinta ya wuce misali Har Aisha sai da ta ma mgana batace komai Sai Dariya datayi Hajiya bata kwana ba kamar wanchan zuwa Idi ya koma da ita bayan tayi ta ma Yakaka Godiyar irin kulawar datake bama Amina ta kawo mata kyautan Turaman Zani guda Biyu da Turaruka Yakaka nata godiya Hajiya ta tafi bayan ta sanar da Aisha ta bar duka kayan a Hannunta In Lokacin isan su gumel yayi zata mata mgana..!
Batare da kowa ya sani ba Danmallam ya yi ma Aliyu mgana ya neman masa gida anan gumel,yana so zai siya wannan karon bai nemi Jafar ba ballatana Nasir ko Aba ko Hajiya da mallam basu sani ba Aliyu kuma bai Fadamawa kowa ba an samu gida flat mai kyau da Tsari an gama ginasa kenan wanda aka bama kyautar kuma yace zai saida ne,An yi Ciniki Miliyan shida Tunda gidan bai da wani girma Bedroom biyu sai falo sai kitchen sai Haraban gidan karami shigar mota Biyu,To bayan ya fadama Danmallam kudin sai da akayi kwana uku ya Turomai kudin Saboda sai da ya Saida wani Share dinsa na harkan Saida gold da suke yi da wani Abokinsa Balarabe ne Riyad yake zaune Tare sukayi karatu shi sai ya koma kasuwanci,to shi yayi ta ma Danmallam Sha"awar fara kasuwanci har dai ya yarda ya saka Hannun Jarinsa suna dan yi tare to Kuma ba Laifi yana samun Alheri saboda Tasowar Hidimar Dake gabansa ya sa ya Karbi duka share dinsa Daga Hannun Abokinsa nasa.
Ya turo ma Aliyu kudin gidan sauran kuma ya rike a Hannunsa,Daman yana Tunanin siya ma Amina gida Saboda wanchan bazai Dauke su ba gata Zata Haihu tana Bukatar wajen da Zata zauna ita da abunda ta Haifa daman yana Tunanin yadda zai yi abubuwa sun mai yawa sai ga Tallafin mallam Daya Dauke mai hidimar Hala ma Amina lefe sai shi kuma yace bara ya wanke masu Hajiya zuciya da wannan gidan duk da daman akwai Sharadin siyan ma Amina Gida Tsakaninsa da su Hajiyan.
Gidan yana nan a anguwan Babura ne Dake garin Gumel makullan gida da Duka Takardun suna Hannun Aliyu ne tunda Shi yayi komai Yaso Umar ya Fadama mallam sai yace zai Sanar dasu sai Lokaci yayi yasan Tabbas Hajiya bazata bar Amina ta Haihu a Abuja ba gida zata Dawo da ita to yana so in ta haihu bazata zauna gidan Baba Sa"idu ko gidan mallam ba Insha Allahu sai dai ta Zauna agidanta.

Ana cikin hakane Mallam ya tara Su Hajiya duka matansa ya sanar dasu Cikin watan nan manema auran su Hanne da Hamida da Sa"adatu zasu zo su gana dasu basu yi wani mamaki ba Daman ai su san tunda sukayi jarabawa a SS2 susan mallam bazai zuba musu ido ba aurar dasu zai yi Anty Amarya ce kadai ta nuna Damuwarta ta kalli Mallan tana Fadin"Mallam nawa duka duka yaran nan suke..?
Shiyasa naso da ka bari sai wannan shekarar su zana jarabawar tasu kamar yadda duka yaran gidan nan suke yi..!
Mallam yace"To ai nasu tsarin ne yazo ahaka sun gama zaman me zasu yi..?
Kuma daman tun kafin haka suna da mgana akansu ai bazan zuba musu ido suna zaune haka ba sannan da kike mganar yara su hannatun ne yara..?
Ko basu kai sha takwas ba nasan sun kusa ko Hajiya..?
Hajiya na gefensa tace"Ai sun ma Shiga a watan musulunci mallam..Su kansu sauran yan"uwan nasu suna Sha takwas wasu sha tara ake aurar dasu nake ga..!
Mallam yace"Ahto .Nidai na fada muku ku sanar da yaran ku su fara Shiri Insha Allahu bikin kuma zai kai karshen watan gobe ne bazan Dauki Lokaci ba..Su kuma su Akilu na yi ma Wani abokina Dake Jami"ar ABU mgana zai tuntubamin in sun samu gurbin karatu chan zan tura su tare. !
Hajiya ta amsa da Allah ya bada Sa"a ya kuma yi albarka Hajiya ita da Hajiya Nasara Hajiya uwa dai duk yadda takai ga Boye Damuwarta Sai ta bayyana Mallam nata aurar da duka ya"yansa ya manta da Umaima ne .?
Bai taba mganarta ba ya Jingineta gefe ba boko ba islamiya sannan ba mganar aure Tunda ta ke ganin ta kusa Cika Burinta sai kuma Umaiman yanzu ne damuwarta.
Ita ke da mallam yau yasa su Hajiya suka fice suka barta sai da suka shiga Ciki bayan yayi wanka yayi shirin kwanciya ta kallesa tana Fadin"Mallam naji kayi mganar auran su Hanne ne..?
Ban ji ka saka Umaima aciki ba..?
Na zata wannam karon zaka Hada da ita ne..?
Sai da ya Zauna gefen gado ya dora kafafunsa saman gadon sannan ya Fuskaceta???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~? yana fadin"Umaima da bata da Lafiya Uwani..?.
Kuma ma ba wanda ya kaawo min mganarta ne har yau shiyasa kikajini shuru da ita..Sannan ni fata na ta samu Lafiya sai komai ya Biyo baya. !
Sai hajiya Uwani ta saka kuka tana Fadin"Haba mallam domin Allah ya Daura mata wannan Laluran sai kace bazatayi aure ba .!
Ai sai ita ma ka hadata da mijin daya Dace da ita kamar yadda kake ma Sauran ya"yanka har da ma wanda ba Naka ba. !
Ta karishe Fada tana kuka kallonta kawai yake yi yana Nazarin mganarta Mimirshi yayi kafin yace"Uwani..Kinsan Kalmar wlh Rantsuwa ce..?
Ta daga kanta ya Cigaba da Fadin"To wlh tallahi ban taba Tallata ya"yana ba ko ya"yan Sa"idu ba Duk Cikin yaran da na aurar dasu zuwa akayi aka sameni mganar ana son aure Cikin iyalaina abu Daya nake yi shine ni nake Zaban wacce ta Dace sai nace na bama wane na bama wane kaza..Sau Daya tak na taba Aikata haka kuma shine na karshe da yardan Allah mganar Umaima kuma ni bazan zama mara adalci ba kamar Zalunci ne na aurar da ita da wannan laluran batare da sanin wanda zai aureta ba Saboda haka in Bukatar hakan ya taso Lalle to sai an Bude komai a Fili in wanda yazo neman auran yaji ya gani Shikenan Uwani nima zan so ganin na gama Sauke Nauyin aurar da duka ya"yan Matan da Allah ya bani..!
Daga haka bai kara mgana ba sai ma mganinsa na Ciwon kafa Daya Dauka yana Shafa ma kafarsa tasa.
haj.Uwani tayi jagale tana kallonsa kafin ta Cigaba da matsan kwallarta Hujjan mallam ai ba Hujja bace in ya bata da ita yadda ake ganin girmansa ai bazata wulakanta ba ammh Saboda An ga gazawarta ne kowace mata za"a gama kwashe ya"yanta ita kuma ko Oho.
Ranar haka suka kwana kowa da Abunda yake sakawa aranta,Da Safe data koma Shashenta ta Kira Batula ta Sanar da ita komai tana Fadin"Batula Hankalina ya fara tashi..kannen bayan Umaima mallam aurar dasu zai yi tana Zaune. !
Batula tace"Mafita kawai ki shiryo kizo Tsafe mu tafi Niger wajen mama..Bazamu bari aga gazawarmu b...!
Da wannan shawarar Haj.Uwani ta Zauna adaran ta tambayi mallam zuwa Tsafe bai hanata ba yace Allah ya tsare ya bata kudi 20k da zata tafi da harda kayan abinci yace ta tafi dashi gidansu tana ta godiya idi ya kaita washegari bai kwana ba Aranar ya Dawo.

Cikin Satin da mallam yayi ma su Hajiya mganar auransu hanne Tuni Labari yakai ko'ina tunda su hannen har masu auran dake wani garin iyayansu sun fada musu hanne da Hamida Hajiya ta kirasu ta Fada musu duk da daman ai susan haka zata Faru ammh sai da jikinsu yayi sanyi aure fa?tunda sukaji mganar basu da wani Walwala daman Amina na nan ne itace Cikin kowani yanayi bazata taba bari su damu ba Jidalinta kadai ai ya Ishesu Allah sarki Amina suna kewarta sun gaji da jiranta da saka ran Dawowarta har sun cire rai ma.
Bangaran Sa"adatu kuma kuka ta Dinga ma Anty Amarya wai bata son aure yanzu sai da Anty Amarya ta kusa Dukanta sannan ta kyaleta Domin ko ta kai wacece ita bata isa taja da Umarnin mallam ba Sadiya yayarta Anty Amarya ta Fadamawa ita kuma ta Kira waya aka bama Sa"adatun ta mata fada shiyasa Sa"adatun tadan Saki ita kanta Anty Amarya bata so ba ammh to ya ta iya..?
Mallam in ya Fadi mgana ai bamai Tada ita kuma sai Allah...
Mamanmu da Aba ya Fada mata Murna ma ta Farayi zata yi Biki na kece raini wajen aurar da autarta hamida Saboda Tasan mallam gangariyan mazaje masu Nagarta yake aurar da ya"yansa da nasu garesu Shiyasa bata da wata Damuwa in akwai abunda Hajiya da mallam ke yi suna Burgeta wannan Sadaukarwan nasu ne, basa numfasawa sai sun ga duka ya"yan agidan auransu mai Cike da Nagarta ne Shiyasa da Anty Amarya ta Kirata tana Korafin auran yayi kusa sai da Mamanmu taji Haushinta da Tunanin tana Bakinciki to in ba Haka ba menene. ?
Yara sun gama karatu to me zasu jira ai sai aure ammh tana neman ta nuna Bakinciki akan hakan,Sai dai bata Damu ba sanin ko me Anty Amarya zatayi Mallam dai bazai sauya mgana ba Sannan ai ita kakarta ce ta yanke saka Tunda tana ta amsan kudade wajen Aba da sunn siyama Hamida yan kayan kitchen tunda kayan gado da Sauransu mallam ke musu kowa ya sani ai ita fa Duniya sabuwa aranta tasha Fadin ko yanzu kasuwa ta Watse mata ai dan koli yaji Riba...

Har Abuja sun ji Labarim auran su Hamida da hanne watan Gobe Aisha da kanta ta fadama Amina aranar Amina wuni tayi bakinta har kunne Domin ta Jiyo kamshin zuwanta Gumel sai dai takaicinta Daya bata nan ai da mutane sun ga Hura Hanci a Bikin Hamida da hanne ko su ya Abida sai ta rama suma wulakancin datake musu in ana Biki ita ko Cikin jikinta bata Duba ba hango kanta kawai take suna Kara"i ita dasu Hanne Tun kuma Daga ranar bata da wani Hira sai wannan Bikin yakaka har ta gaji da Haddace Labarin Bikim nan a bakin Amina shi kanshi Danmallam Topic din kenan kullum sukayi waya sai tace ranar Bikin su Hanne Hmm kaza kaza yana so yace da Cikin zaki yi kaza..?
Yana tsoron ya ballo ma kansa Ruwa sai dai yana Tausayinta in Hajiya tace bazata zo ba ya zatayi..?
Ai ya tabbata wannan Jidalin na Amina in ta fara shi ko mallam to sai kila sai dai shin zai iya lallashinta yadda taci burin Bikin nan ya tabbata bata ci burin haihuwarta haka ba.
Shima ai yasan da labarin bai Fada mata ba Tunda Mallam ya fadamai haka Hajiya ma duk sun yi mganar su sakina ma bashi ya fada musu abakinsu ma yake jin suna kara zencen yace musu Hakane Sakina sai Murna take yi Nageria tayi kira abu nasu to Har Sarood ta Shirya wannan karon sai tazo itama shi dai ko ci kansu bai taba Ce musu ba kan Bikin ya zuba musu ido ne kawai yana kallon ikon Allah.
Haj.Uwani kusan sai da shafe wajen kwana goma sannan ta Dawo ta saki Ranta ana ta sha"ani da ita Domin mama tace mata ta kwantar da Hankalinta ana gama wannan Bikin Itama Umaima za"ayi nata to shi yadan Sanyayamata rai sannan tana chan Tsafe Uzairu yazo gida Ya kwana Biyu bata nan daga Chan Delta in da yake Bautar kasarsa har ya tafi bata Dawo ba sai da sukayi mgana ta waya.
Haka take shigema Hajiya ana komai da ita Hajiya bata taba nuna mata tasan Wacece ita ba ta barta ne sai Ranar kin Dillaci domin ta nan zuwa Ranar da Allah zai tona musu asiri a bainar nasi.
Mazajen su Hanne sun zo kuma sun gana dasu,Manemin Sa"adatu ya fara zuwa Dan gombe ne ma"aikacin Costume mahaifinsa ne sukayi karatu da mallam a kano,Sai kuma na Hamida Dake lecutring anan Kango Abu Zaria shima yazo Cikin Daliban mallam ne da ya koyar da Mahifinsa tun zamansa a zaria yana Dalibi ma alokacin.
Sai na Hanne da Shine Karshen zuwa Haifaffan garin Adamawa kuma mazaunin yola ne.
Dukkansu ba wacce bata yaba da Zabin Maalllam ba,sai hanne da tun taga ta ganshi take kuka cikin Damuwa kuma taki Fadan Daliinta Hamida ne kadai ta sani kuma ita din ma batayi Zencen da kowa ba.
Shiryen Shiryen Biki fa ya kamkama ta kowani bangare mamanmu ta fi kowa Shiri domin tayi alkawarin kece Raimin da bata taba yi ba sai a bikin Hamida Autarta duk tana Barikin cewa Jawaad ne Autanta wanda yanzu suka fara JSS1 Shi da Sabeeha a kasan ranta ko nan bata ma kaunarsa bataki shima ya mutu ta koma Daga ita sai Sa"idu ko ba ko Hajiya ta Daukesa ta daina ganinsa kamar yadda ta Dauke Amina daga gabansu.
Danmallam da kansa ya Kira Mallam ya fadamai zencen gidan daya siya ma Amina mallam yaji dadi ya dinga sakamai albarka shi ya Kira Hajiya ya Fadamata addu"an da Danmallam ya sha kamar Hajiya zata goyasa albarka kuwa ya shata har sai da ya kusa kwallah yana Tunanin wanda bai Sakama iyayensa ba Allah kuwa zai barsa. ?
Aliyu yama mgana ya kawo ma Mallam Takardun gidan sannan ya Dauke shi da Hajiya kai suka ga wuri Hajiya kamar tayi kuka fadi take"Allah ya tsareka Danmallam..ya yalwata arzikinka..Allah ya Jibanci lamuranka Allah ya kara budi na Alheri yadda ka faranta mana ka rike Amina da Amana Allah kai ma Allah ya rike Hannayenka cikin Aminci..!
Mallam ma haka ya dinga sakama Danmallam albarka sai Tsausayinsu ya kama Aliyu da sukayi waya da Umar ya fadamai irin albarkar da ya sha Wajensu Hajiya Danmallam ya murmusa yana Fadin"Aminene ta mallam da Hajiya ce..Suna shiga farinciki matukar aka kyautatamata kuma kaunar Baba Sa"idu ce ta Shafeta. !
Aliyu yace"Ai kacigaba da kyautatama Amina..ka riketa Amana har ya'yanka sai albarkar Hajiya da mallan ya bisu..!
Umar ya saki kayattacen mirmishi kafin yace"Insha Allahu..!
Hajiya ta kasa auna farincikinta Daga ita sai mallam suka kara tsara kayan Gidan Amina kamar yadda mallam yayi alkwarin yima Amina kayan Daki kamar sauran yan"uwanta haka kuma akayi tare da nasu hanne aka bada Oder din kayan gidan sannan Hajiya ta Tsara in kayan sun iso ya"yan yagana yayarta zata kira ta bata aron su su biyu bayan sun tambayi izinin mazajensu su zasu taimaka mata cikin Sirri su gyarama Amina gidanta Sabida tana so duk ranar data dira agarin ta iske komai ya kamallah.
Hajiya ta kudiri niyyar sai da wannan Bikin Amina zata bayyana sirin Boye zai bayyana a kuma Lokacin take Fatan Allah ya bayyana mugayen Fuskokin Dake tare dasu domin ba Shakka bayyana Amina da Ciki Sai ya Razana su kuma ita ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login