Showing 234001 words to 237000 words out of 265571 words

Chapter 79 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28941

juya yana kallonta Baki Sake Nazeem da Uzairu suka kalli juna suna mai Nuna Tsanatsanin mamaki.
Baba mallan yana kallom Haj.Uwani har ta kariso Falon Idanuwanta sum kode saboda kuka ta Zube gaban mallam Tafashe da kuka Lokaci Daya tana Fadin"Nasan ko ban fallasa kaina ba kasan Abunda nake boyewa..!
Don Girman Allah Mallam ka yafemin..Ni ce nayi ma Umar kuruciya shi da Nazir suka kasa zama kusa dakai sannan ni na mai da Nasir mara amfani a wajenka..Ni nake Hana Cikin Sakina Zama mallam duka nice na aikata hakan..!
Ta karishe fada Cikin kuka Baba mallam yayi wani mirmishi Takaici kafin yace"Kema saboda ki same ni dani da Dukiyata ko..?
Haj.Uwani kanta na kasa tace"Mallam kayi hakuri..Idona ya rufe..Burina naga ya"yana ne gaba akomai..Hajiya tasha gabana a wajenka..Sai nayi Tunanin in ya"yanta suka sha gaban ya"yana na gama yawo..Shiyasa na nemi Cikar Burina ido rufe..Ina da wata Bokanya Da muke cema Mama a Niger take ita take min aiki..Sannan ita ta bankadomin sirrukan Marliya da Balaraba,ita ta bani mgani na saka ma Sakina a tea tasha ita da Sarood har da Amina ma na bata..Ammh sai gashi na ganta da Ciki wanda Mama ta tabbatar min da cewa ko sun samu Ciki sai ya zube..!
Ta karishe fada tana gunjin kuka ai Kowa a Falon sai ya kasa motsi ashe abun bai kare ba..?
Hajiya Cikin Zubar Hawaye ta kalli Uwani Tana fadim"Saboda mene..?
Meyasa kika zabi ki kashe rai Uwani..?.kinsan girman Laifinki kuwa a wajen Allah..?
Haj.Uwani na kuka wurjajan tace"Saboda Mama ta fadamin maallam na Matukar son Umar Sannan ya"yansa da zai haifa sune masu soyuwa a wajensa shiyasa na hana matansa su Haihu shi Nazir bai da wani Tasiri ne shiyasa ban Damu dashi ba..Dalilina kenan na daya sa na Tura Nazeem ya rabu da Sa'idu a kan Harkokin dukiyar mallam Burina shine Nazeem da uzairu su zama kan gaba aduka Dukyarka ni kuma na zama nice gaba da Hajiya tunda ya"yana ne akan komai..Wlh sharrin shedan ne ku yafemin don girman Allah sai yau nayi nadama na Fahimci Zakaran da Allah ya nufa da Cara ko ana muzuri ko ana Shaho sai yayi..!
Kuka take kamar ranta zai fita Mallam ya Datse Hakoransa waje Daya Cikin Bakiimciki,Sai ga Hawaye sharr na zubar ma mallam hawayen Tsausayin kansa da Bakincikin yadda iyalansa suka Gurbace suka gurbatamai zuru"a.
Hajiya ce ta share Hawayenta tana Fadin"Allah ki kayi ma Laifi shi zaki roka uwani..Allah ya gani ban Taba Zama Daya daga Cikin ku da wata manufa ba Shiyasa Allah ya nuna muku iyakarku..Kun ga dai ku baku isa kuyi abunda Allah bai yi ba ko..?
Amina tsohon Ciki gareta Haihuwa ko yau ko gobe ina Mganin da kikace kin bata..?
Sannan ita kanta Saratun Ciki gareta yakai Wata Hudu ni nace kada a fallasa mganar Cikin ina mganin da kikace kin bata itama..?
Sannan ke marliya ina Sihirin da kikayi ma Danmaallam..?
Kin Fahimci in Allah yace kun yafakun bawa bai isa ba. !
Sai kallo ya koma kan Sarood da mamaki Sakina kuma cikin ta taji yana Juya mata saboda Tsabar Tashin Hankali.
Hajiya ta cigaba da Fadin"Daga karshe nagodema Allah da komai naku ya kare a kanku..sannan ina kara Fada muku ni ban Dogara da boka ko mallam ba..Ni Allah na rike shiyasa na Gagarara har yau har gobe..Kuje Allah zai muku sakamakon abunda kuka aikata Hakkin Rayukan da kuka kashe kuka gurbata bazai taba barin ku ba..!.
Hajiya ta fada tana juya baya Lokaci Daya tana sharan Hawaye..
Nazeem na kuka uzairu da shamsu nayi ganin yadda iyayen nasu ke kuka suna neman gafara.
Nazifa har muryanta na Dishewa.
Hajiya Nasara sai kuka take yi tana Fadin"Wlh ban taba sakama kaina Bakinciki ba..Da zuciya Daya har ga Allah nake zaune da kowa..!
Kawai sai ta saka kuka Mamanmu da Anty Amarya da Haj.Uwani Duke suna kuka neman gafaran ya"yansu da Su mallam ammh ba wanda ya kallesu yan gusai kuwa haka suke aibata Mamanmu suna kirarin bazata gama da Duniya Lafiya ba.
Tashi tayi tana kuka tana Rangaji ta isa gaban su Amina ta Duka tana kuka tana Fadin"Don Allah Sa"idu kai da ya"yan Yaya ku yafemin..Sharrin Shedan ne nasan na cutar daku..ammh ku yafemin ku yafemin ko domin Darajan su Hamida..!
Tafada tana kokarin rike Kafafun Aba yayi Saurin janye kafarsa ya juya baya yana Fadin"Bazan taba yafe miki ba Balaraba..Insha Allahu sai kin girbi Abunda kika shuka..!
Sai Hawaye Mamanmu ta Dukar da kanta tana Kuka tana kokarin rike Amina fadi take"Amina nafi cutar dake don Allah ki yafemin..!
Amina bata yi sanya ba ta mike da katon Cikinta ta saka Hannu ta Dago mamanmu Tsaye kowa mamaki ya kamasa Ammh basu gama mamakin ba Amina ta Cire Hannunta ta Zabga ma Mamanmu mari kafin ta taso ta kara mata a Hannun hagu kafin ta kara tasowa ta kara mata

Sai da ta Durkushe kasa,su Hamida sai kuka ba bakin mgana ba kuma wanda ya Hana Amina.
Cikin hucin kuka da Hawaye ta nuna mamanmu tana Fadin"Marin farko na kashe mana uwa da kika yi ne..!
Mari kuma na Biyu na yadda kika Lalata rayuwata ce..!
Mari na uku kuma na Aba ne..Na yadda kika Raunana masa zuciya..Tsakaninmu Dake BALARABA allah ya isa..Bazamu taba yafe miki ba..!
Amina tana Fada tana kuka sai kuma ta fara kokarin Sulalewa Numfashinta na Sarkewa kafin su ya jafar su farga Ya Danmallam yayi saurin isa gareta ta Fada Jikinsa jijjigata ya fara yi lokaci Daya yana Kiran sunanta.

Noor..!
Nooor...!

Sama sama ta jisa kafin ta Bude ido ta fara ganin fuskarsa Cikin Fitan Hayyaci tace"Hubby...!

Da Sauri yace"Na"am Noor..ki tashi kada ki tafi ki barni na shiga uku..Ina zaki tafi baki tsaya kin taramin zuru"a Daga Tsatsonki ba..?
Tana kuka ta wani kamkamesa Ta fashe da kuka yau Dannallam ba kunya Hajiya bana Mallam da sauran mutanen Dake Falon ya kamkame Amina kamar zai maidata Ciki yana jinsa kamar yana yawo a gajimare kukanta na Dafa mai rai kamar ya Dawo da abunda take ji akansa bayanta yake shafawa a Hankali alamun Lallashi.
Kallo sai ya koma kansu Hajiiya ta saki Mirmishi haka ma Mallam da su Ya Aisha Goggo Husai tace"Ajiyan Allah..Gaskiya ne Amina ta FITA ZAKKA acikin gidansu sannan ko azuciyan Mijinta ta fita zakka..!
Tafada tana sharan kwallah Aba ma kallonsu yake yi yana jin bakincikinsa na dan raguwa,lokaci Daya yana kallon Mamanmu da wani kallo kallon kin gani..?
Baki da yarda zaki yi Alkwarin Allah ne ya cika..!
Sakina kuma sai taji kamar wani abu na Bin katafunta tana shafa kasanta tadago da hannunta taga Jini..Sai ta Zaro ido..tana kokarin mikewa jiri ya kwasheta ta zube kasa sumammiya..!
Allah ya riga ya Rubuta har ta koma gq Allah bazata taba haihuwa ba..
Shi bawa bai isa ya kankare wannan kaddaran ba..!
Cikin ya sake zubewa kamar yadda Sauran ma aka rasasu..!









*Janafty*

*TFZB2027*


*Ki biya ki karanta cikin Salama kiyi ma girman Allah in baki biya ba kada ki karanta sannan kuma kada ki yada'ashi..Pay N500 via Jamila Umar gtb 0552179550 ko katin waya ta wannan lambar 09069067488*

Su sadiya suka ruga da gudu wajen Sakina data fadi sumammiya jini na malala ajikinta,A"i kanwar Anty Amarya ta riketa lokacin Da ta ga jinin dake malala ta kasan Sikat din Dake jikin Sakina sai ta fashe da kuka.
Ita kuka Sadiya kuka Jidda kuka Sa"adatu kuka,Anty Amarya ta taso hankalinta a tashe tana kuka zata rike Sakina,Anty A"i ta Daga mata Hannu Cikin kuka take fadin"Marliya kada ki kuskura ki taba Sakina..Kije Abunda kika aikata kawai ya isheki ko Alhakin Sakina ya isheki..!
Daga haka tace ma Sadiya ta kamata Sakina suje asibiti da ita da yan"uwansu dake Dutse duk suna falon komai ya Faru Anty Amarya tana ji tana gani suka fice da Sakina Daga falon haka ma su Jidda suka Fice suka barta ko gizau Sa"adatu ne kamar zata tsaya sai kuma ta juya tabi bayansu tana kuka Anty Amarya nan ta Sulale tana gunjin kuka.
Ganin yadda gabadaya Falon ba wanda yabi ta kan abunda ya faru,Har ta dashi Danmallan din kuwa yana rike da Amina bai Saketa ba ballatana Hajiya da mallam da wannan yanayin bai gama Sakin su ba..
Bakajin komai ba sai tashin koken koken su ya Zulahait kamar ransu zai fita,da kukan Mamanmu da na Hajiya Uwa,haka suke kuka kamar ransu zai fita.
Nazeem ne ya fara mikewa Idanuwansa sun kala sun yi jajir Saboda yanayin dayake ciki Cikin wani yanayi ya kalli Uzairu da ya kasa tashi Har da kwallah shi sai da ya Zubar jin abunda Mahaifiyarsu ta aikata.
Cikin Kaushi yace"Uzairu tashi mu tafi..Zaman mu bai da amfani a nan wajen...in muka ci gaba da zama anan wurin zuciyata zata iya bugawa..!

Uzairu na jin haka ya mike yana Bin Hajiya Uwa da wani kallo kallon Tsana da Bakinciki kafin ya juya zai bi bayan Nazeem daya fara tafiya zai bar Falon da Sauri Hajiya uwa ta kira sunayensu suka tsaya batare da sun juyo ba.
Haj.Uwa ta rarrafa zuwa inda suke Tsaye Cikin kuka take fadin"Meyasa zaku juyamin baya. ?
Kada ku manta duk abunda na aikata Saboda ku ne..Wlh duk abunda na aikata Saboda ku ne..!
Kuyi hakuri ku yafemin Don Allah..!
Sai kuka har tana Dukewa saboda kuka,Nazeem ne ya juyo a fusace yana Fadin"kada ki kara jingina Zunuban ki da sunanmu..Tunda nake dake ban taba Fada miki ina son zama a Karkashin Baba mallam ba..Ko Uzairu ma nasan ba Ra"ayinsa bane Meyasa kafin ki fada wannan Halin baki zauna Damu kin tambayi Ra"ayin mu ba..?
Me kika nema kika rasa..?
Me Hajiya ta rage ki dashi ita da ya"yanta..?
Me Baba mallam ya rage ki dashi..?
Wlh Tallahi ban taba jin kunyar Hajiya da mallam ba sai yau mugin Halinki yasa na kasa Hada ido da yan"uwana..!
Ya karishe fada yana Sharan hawaye Uzairu ma haka cikin Hawaye yace"Mommy meyasa kika Zabi wannan Rayuwar..?
Baki taba Tunanin Sharri dan aike bane..?.inda ka aikasa nan ko min Daren Dadewa zai dawo maka..?
Wlh ko Kaffara bazan yi ba Shiyasa kanwar mu Umaima take cikin wannan Jarabawar saboda irin abubuwan da kika aikata ne ta ke Fuskata..!mommy kun Cutar damu Kin sakamu jin kunyar Mallam da Sauran yan"uwanmu..Nasan Ya Nazeem bai Fada miki ya samu aiki da wani kamfani a Lagos ba,Sannan ni kuma ,masters dina zan koma bamu da burin komai sai muyi karatu mu nemi na kanmu Muma watarana mu taimakama iyayanmu da abunda muka Tara na Halaliyarmu..!
Ya karishe fada Kamar zai Saki gunjin kuka kawai sai ya juya ya fice Nazeem ya mara mai baya Haj.Uwa ta bisu da Kuran sunanyensu ko waiwayo ba wanda yayi..nan ta durkushe tana wani irin kuka mai sosa rai Shamsu na Zaune ya mike shima cikin wani yanayi yazo gabanta ya tsaya sai ji kawai tayi ya Kira sunanta da Sauri ta Dago sai dai ganin kallonta Dayake Binta dashi yasa jikinta yayi sanyi.
Kallon tsana da Bakikciki yake Binta dashi da tir da ita bisa yadda ta Aikata wannan abun kunya.
Juyawa yayi kamar sauran zai fita Ta saka Hannu ta rike kafarsa ya juyo ya Fizge Kafarsa ya fice da Sauri yana Sharan kwallah Haj.Uwa ta Dora hannu akanta tana Fadin"Na shiga uku na Lalace..!
Kaico na..Kai co na..!
Wajen Nazifa ta nufa itama kawai sai ta kauda kanta tana kuka Haj.Uwani ta riko hannunta tana fadin"kema gujemin zaki yi nazifa..!
Kada ku manta ni mahaifiyarku ce..!
Duk abunda nayi yau saboda ku ..!
Bata gama mgana ba Nazifa ta kwace Hannunta tana kuka Cikin kukan take Fadin"Ki daina kokarin dora mana Girman zunuban ki..Kin sakamu jin kunya Mommy..Nayi nadamar kasancewarki mahaifiyarmu ayau..Kin cucemu kin bar mana Tabon da har abada bazamu taba mantawa ba..!
Tana gama fadin haka ta mike da gudu itama tabi bayan yan"uwanta tana gunjin kuka suka bar Hajiya tana wani irin kuka,kukan nadama da nasani mara amfani.
Ita da Anty Amarya da Mamammu wanda ko Tsausayi basu bama kowa afalon ba.
Baba mallam sai da ya Dauke kwallah a kwarmin idanuwansa kafin yayi gyaran murya yana fadin"Duk Sboda Dukiya ce yasa kuka kai kan ku ga Halaka..?
Shirka acikin gidana da zuru"ata..!
Allah ya tsaremana imaninmu..!
Bayaso ya cigaba da mgana Rauninsa ya bayyana yasa ya Dakata,irin su Goggo Husai ne da su yakaka suka iya amsa da Ameen ko Hajiya kanta na kasa tana sharan hawaye.
Mallam ya cigaba da fadin"Kun Saka ido kan Dukiyar da baku san Wahalar da Sa"idu ya sha wajen tarata ba..Rana iska damina yana Tsaye da Amana kan Dukiyata..Dai dai da Rana Daya bai taba gazawa ba..Sai yau rana Daya komai Dayake faruwa saboda ita ce..?
Daman an ce Dukiya da mata sune abun shagala anan duniya..to bari in sanar daku abunda baku sani ba ko nace wasu basu sani ba..Gabadaya Dukiyata Rabinta mallakin Sa"idu ne..Rabi ne nawa shekaru kusan uku da suka gabata ribar da muke samu da nashi aciki..Na saka Lauyoyi sun yi Rubutu ko yau na Fadi na mutu Rabin Dukiyata na Sa'idu ne ya Chanchanta ya kuma Dace domin yafi wahala da ita Fiye dani dana mallaketa..!
Ya karishe mganar cikin wani yanayi,Sai kallo ya koma wajen Baba mallam,Kar Baba Sa"idu da Ya"yansa su ji labari cikin mamakin jin kalaman Baba mallam..
Baba Sa"idu dake jikin Jafar ya Dago Cikin Rauni yana Fadin"Baba mallam ammh...!
Hannu kawai ya Daga masa yana Fadin"Basai kace komai ba..Wannan ba mgana bace..Tuni an tabbatar dashi Tuntuni takardun komai yana nan a Rubuce..Sa"idu kai D'a na ne..Har yau gobe kana nan a matsayin Babba yaro na..Kafin na same su kai na Fara samu har gaban Abada bazan manta da karamcin Mahaifinka gareni ba..Kafin na Fara sanin kowa Ku na fara sani kai da Hajiya..Dole ku zama wani jigo nawa abunda baku sani bane ba boka ko mallam ba..nan Duniya ba wacce zata kai matsayim Hajiya a wajena..Hajiya ta zauna dani Tun ina amsa sunana Yunusa ban tara komai ba kuma ban da komai ban isa komai ba,ban kai ko'ina ba sannan ba wanda ya sanni..Itace ta wahala dani ta Zauna dani tun ina malamin zaure ta jure yawon gari gari da nake yi domin Da"awa sannan ta jure abubuwa da yawa akaina,Itace ta Fahimceni Fiye da kowa acikin ku..Sannan duk abunda na kawo mata Zata karbesa hannun Biyu bazata taba korafi ba,dukkan ku da na aure ku Hajiya bata taba Daga Bakinta akan hakan ba..Ban taba kawo mgana ta tsallaketa ba yadda ta Daukeni Allah ne kadai ya sani..Bayan ita sai Sa"idu Shima yazo ya wahala dani, wahalan da ko ya"yana basu yi dani ba..Har gaban Abada Hajiya da Sa"idu matsayin su bazai sauya a wajena ba..!
Duk Kokarin mai kokari bai isa ya Ture abunda Allah ya kafa ba..Shiyasa duk kan sharrin ku ya koma kanku..Allah ya gani ban taba cutar daku ba..Ammh tunda kuka Zabi ku cutar damu bazamu ce komai ba..Sai dai zamu bar ku da Allah mai Fitowar rana da Faduwar ta,Kamar yadda ya Fallasaku yau..Sannu sannu zaku amshi Sakamakon a Hannunku..!
Ya karishe Fada yana kauda kai Daga kallon Anty Amarya da mamammu Dake kuka kamar ransu zai fita.
Gogggo Husai tace"Hakkin rai bazai barsu ba mallam..!
Mallam yace"Tsakanin su da Allah ne wannan Husai..Basu isa su kashe rai ba..Saboda basu ke Kashewa su raya ba..Duka na Allah ne..Allah daman ya Rubuta Lokacin Hadiza yayi..Ko ba Sanadi zata rasu a wannan ranar..Allah ya rubuta Hakan Wa"adinta ya kare..Ammh sune Sanadin hakan
Cutar da sukayi ma Sa"idu da ya"yansa kadai aka bar Balaraba da Marliya sai ya hanasu zaman Lafiya a Duniya..!
Goggo Husai tace"Allah ya isarmu..Allah ya sakama Sa"idu..!
Take fada tana kuka Yakaka na gefe tana jinjina kai mamaki duk ya cikata wannan aikin duk agidan malami kamar Mallam yunus..!
Tsoron Allah ya kara kamata da tsoron rayuwa. !
Amina ko na jikin Danmallam tana Shesshekan kuka shi kuma yana ta lallashinta su ya jadwa na gaban Aba suna ta gunjin kuka.
Mamannu ganin Aba ya juya baya su Jadwa ma sun juya mata baya suna kuka sai ta rarrafa wajen Zulfa kafin ta kariso ta mike ta isa gaban Aba ta Zauna tana kuka Daya bayan Daya suka koma wajen Aba da yan"uwansu suka zauna suna kuka suna Binta da kallon kyama..hamida ce ta mike tana wani irin kuka kallon Mamanmu take Idanuwanta sun juye.
Mamammu ta rarrafa gabanta ta rike Kafafunta tana fadin"Hamida kema kada ki gujeni..Wlh sharrin shedan ne da Sharrin so..!
Hamida ta yi wani mirmishi kafin ta Saki Dariya kamar mahaukaciya.
Cikin Dariyan take kallon mamammu cikin wata murya tace"Tunda kike aikata wannan Muguntar naki baki Tunawa damu ya"yan ki ba..?
Baki Taba Tunanin watarana abunda kika aikata zai taba mu ba..?
BALARABA KO NACE DAYYABA..ki sani Duk abunda kika aikata kanki zai Dawo..Ba yaya kika kashe ba kanki kika kashe ba Amina kika lalata ma Rayuwa ba ya"yanki kika lalata ma Rayuwa Kika gurbatamu kika Wulakantamu..Duk abunda kika aikata tare damu ya"yanki zamu girbeshi..!
Ta karishe fada cikin Kuka lokaci Daya da dariya kamar wata Mahaukaciya kowa sai ya koma kallonta cikin mamaki da Tunanin me ya Sameta .!?
Mamanmu ta fara kokarin mikewa ta Rumgume Hamida cikin Fitan Hayyaci ta tureta Sai ta fadi kasa cikin muryan kuka tace"Kada ki kara tabani..baki sanni ba..Ban sanki ba..Tsakaninmu Dake sai Allah ya isa..Bazamu taba yafe miki ba kin cutar damu kin Cutar da kanki.Da izinin Lahi sai kin lalace sai Allah ya wulakantaki..Sai Allah ya Dai'daita Rayuwarki sai Allah ya tsarwatsaki BALARABA..!
ta karishe fada cikin wani yanayin da sai da ta bama kowa Tsausayi Amina ta Baro Jikin Danmallan Tsausayin Hamida ya kamata kafin ta karisa wajenta Hanne ta isa ta rumgumeta tana kuka tana fadin"Hamida ki daina Fadin haka don Allah ki daina. !
Hamida na gunjin kuka take fadin"Ya zan yi Hanne..?
Ina jin zuciyata kamar zata fashe..Kamar zan yi hauka.!
Muryan Amina taji a bayanta tana Fadin"Ki rika maimaita innalillahi wa"inna ilaihirraju"un acikin ranki zaki samu Sauki..!
Hamida ta saki Hanne ta karisa gaban Amina tana Fadin"Innalillahi wa"inna ilaihirraju"un Amina da wane ido zan kalle ki ina jin kunyarki..?
Take Fada tana kama kanta sai tayi suu kamar zata fadi Amina da Hanne sukayi saurin tarota ta fada jikinsu haka suka kankame juna su uku suna ta kuka kamar ransu zai fita.
Kowa afalon sai da ya Tsausayamusu suna yi su ya zulaihat nayi bamai lallashin wani.
Mallam ne ya mike yana kallon Hajiya yace"ki Rarrashi yaran nan Hajiya..kukan ya isa haka..Allah ya Tsaremu..!
Ta amsa da Ameen Idanuwanta sun kada kafin tace"Cikin wannan halin da suke ciki za"ayi Daurin auran..?
Mallam ya gyada kai yana Fadin"Insha Allahu ba fashi..!
Ba wanda ya kara mgana Baba mallam yana gyara Rawaninsa yace"Sa"idu tashi muje shashena..Tashi ga Kafafunka da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login