Showing 111001 words to 114000 words out of 265571 words

Chapter 38 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28960

wando tazarce anyi Dinkin zamani na matasa masu ji da kansu sai hula zanna bukar Zaran yanayin aikin shaddan Jikinsa kafarsa cikin Bakin Rufaffan Takalmi na Fatar damisa sai bakin agogon Fata Dake tsitsiyan hannunsa na Hagu bashi ke mganar ba Aliyu Dake kusa dashi yake saurareshi shi key din Mota ne ke hannunsa yake kadawa Lokaci bayan Lokaci yana Sassauta yanayin Fuskarsa.
Sai da gaban Amina ya fadi da Sauri ta kauda kai ta sani ita bata isa tace Ya Danmallam ya dace da ita ba Tazaran Dake Tsakaninsu mai girma ce,kana kallonsa zaka hango Tsantsan kamala Dattako da sannin addini sannan uwa uba kwarjinin da Haiba ta mutumin da yasan addini sosai da sanin ya kamata sannan da yana kyau, kyau irin na fatan kowacce mace zabinta ya kasance haka..!
Bata son mgana saboda ranta ya riga ya baci shiyasa taja karamin Tsaki ta kauda kanta sai ma ta kara Sauri ta shige gidan bata son wata mgana ammh Hanne da Hamida sai suka saka Dariya har suna Tafawa Allah yasa Zafira na baya tare da yan garinsu.
Hamida ta kara riko gefen Hijabinta tana Fadin"Amina ki kallesa mana..Kai wlh ya Danmallan yayi kyau matuka..!
Amina ta Juyo a Fusace daidai sanda suka shiga get din gidan Baba mallam tace"Ba mijina ba..A"a ubana ne..Nace sai dai Ubana Hamida haba..Kin Dameni..!
Hamida da hannu suka kalli juna suna kunshe Dariya Hanne tace"Mijinki ne..Kuma ko bakomai ya Danmallan yana matsayin Uba ne agareki..!
Amina ta kalleta shekeke kafin tace"Allah..?Aiban yi mamaki ba..Kowa ya ganni yasan auran son zuciya yayi da yar cikinsa..!
Hamida da Hanne suka zaro ido Hanne tace"Amina kin ma kanki karya..Kaf gidanan ko ya Nazir bai kama kafar ya Danmallam akomai ba wlh..Baki magodema Allah ba kin Samu miji Kamar sa bama..!
Cikin Hargowa Amina tace"Ban gode ba..Domin bani nayi tallar kaina ba..Da kike mganar duk gidanan ba kmarsa to ni ina ruwana..Kinsan dai ina da Aminu..Kudi kyau nasaba ga yarinta bai isa ya nuna mai ba..!
Sai kawai ta saka musu kuka abunda basu taba gani ba in ta Tuna da Aminu bata iya Boye rauninta har Abada bazata taba mantawa dashi ba ko wani Hali yake ciki yanzu Allah masani..!
Jikinsu yayi sanyi suka kasa mgana ganin su zafira suna kokarin shigowa ne yasa ta juya ta fara tafiya suka mara mata baya Hanne na Fadin"Allah baki Hakuri Amina..Ammh aragama yayana ko Saboda ni..!
Amina ta Daga murya tana Fadin"Saboda ke..?ai ke din ba Mutumcinki nake gani ba Hanne..Ki kyaleni kada ki Tunzurani na yi miki Tijaran da zaki ji Haushina..!

Hamida tace"Hanne abar mganar..!
Daga haka suka kyaleta har shashen Hajiya sun shiga ba Dadewa sai ga Amaran da yan gusai,ba kamar wanchan karon ba Amina wannan karon batayi ra"ayi ba shiyasa da su Hanne suka ce tazo su raka amaran Nasiha Shashan su Haj.uwani da Nasara da gidan Aba Amina tace sai sun dawo ita ba inda zata jin haka sai suma jikinsu yayi sanyi suka ki binsu Zafirace dataga sunki zuwa sai ta Bisu.
Basu fito ba sai da Zafira tazo tana Fada musu amare zasu tafi ssannan suka fito Lokacin ma suna Falon Mallam ana musu nasiha da bankwana sai fito da kayan abinci su Ya Akilu suke motocin amaran suna kwasa suna sakawa acikin Booth ya Zeenatu Tawagar angoyen ta suna shirye harda mace Daya wacce zata tafi da amarya suka zo ya Abida dai tafi gata tunda su Anty Amarya na chan sai gobe zasu dawo..
Suna wajen sai gasu Haj.Nasara da Hajiya babba da goggo yakura sun fito dasu,kafin su ma mazan ne suka fara fitowa su ya uzairu da su ya Nasir ya Danmallanm da abokinsa Daga baya suka fito baba mallam da Aba sune ke rike da Amaran zuwa motocinsu Ba yau aka saba biki agidan ba ammh wannan na Dabam ne kamar yadda amaren suke na Dabam haka suke ta kuka kamar ransu zai fita Zeenatu da Abida.
Ana fito dasu suka kyalla ido suka hango su Amina suka kwace daga rikon Baba mallam suka nufesu Abida ta Rukunkume hanne tana kuka Zeenatu ta rumgume Amina da Hamida tana kuka duk da sun girmesu sune sakon su na kusa dasu akwai shakuwa sosai a Tsskaninsu.
Amina bata taba tsammanin zata yi kuka domin su ya Abida zasu tafi gidan mijinsu ba ammh yadda suke kuka suna rike su ne da kuma yadda Hamida da hanne ke kuka sai Amina ta fara Tsausayin kanta tana Tunanin in da gaske ne ta auri ya Danmallam kenan watarana itama zata iya Tsintar kanta cikin wannan yanayin sun bala"in bata Tsausayin da batasan sadda ta fara kuka ba takamkame Zeenatu suna kuka ita da Hamida ganin haka yasa Abida da Hanne suka zo suka hade suka yi Rumfa suna ta kuka kamar anyi mutuwa sai kallo ya koma garesu hajiya bata awajen ta koma cikin gida Haj.Nasara ne sai dangin mamanmu dana Aba na gusai.
Baba mallam tsaye kawai yayi bai ce komai ba ya jafar ne ya fara fada shi da ya Nasir suna fadin iskanci banza kukan uban me suka hadu suna ma mutane..!
Baba mallam ya kallessu yana Fadin"Ku kyalesu suyi kukan rabuwa da kannensu da gidansu..Gida fa ba kamarsa kuma aure ai yakin mata ne ko domin ku din maza ne shiyasa baku san wannan Raunin ba..!

Jin haka yasa sukayi shuru ya Danmallam bai ma san abunda ke faruwa ba suna haraban gida azatonsa amaren sum mika Aba kuma an kirasa a waya ya kebe agefe.
Haj.Nasara ne ta kalli Baba mallam tana Fadin"Maallam Uku tayi fa..Tafiyace kuma agabansu..!
Goggo yakura tace"Abidar kuma Angon yace jirgin karfe hudu zasu bi zuwa chan kuma ta Dutse zasu tashi..!
Baba mallam bai ce komai ba ya juya yana fadin"Ina Umaru..?
Ya Jafar yace"Yana daga cikin gida mallam..!
Kai Tsaye yace"Kiramin shi..!
Ba musu ya juya ya shiga ya kirasa sun ma hadu dasu ne zasu fito ya fadamai kiran mallan din sun fito kenan sai ga su Sakina da Sadiya da Tawagan yan"uwansu sun fito su ga Tafiyar amaran.
Daman Aliyu ya rako zai koma sai ga Kiran mallam sai ya isa wajensa yana zuwa Mallan ya dafa kafadarsa yana Fadin"Ka ga matarka da kannenka chan sun hade kai suna ta kuka. taimakeni ka lallasomin su kafi su Jafar sanyi su yanzu sai su ce zasu kai musu hannu..!
Inda mallam ya nuna mai yabi da kallo Takaici ya kumesa su din yara ne da zasu zauna suna ma mutane kuka kamar wasu marasa hankali sai karin wani takaicin wai matarsa shi fa har ga Allah ya Dauka Sakina ce da farko sai da ya kalli wajen yaga su hanne ne Tunanin sa ya basa wannan kazaman yarinyar ce bazai iyama mallam gaddama ba yasa ya kada kai yana Fadin"Shikenan mallam..!

Ko kafin ma ya isa garesu su ya Zulaihat sun isa suna faman lallashinsu su saki juna Sakina na gefe ta kame tana kallon kowa Daya bayan Daya sai ta ga Danmallam ya isa wajen yana mgana batajin me yake fadi,Ranta ya baci kishi ya Rufemata ido ganin Amina awajen badai ita yaje yana Lallashi ba..!
Sadiya ce tace"Ya sakina ga ya danmallam chan yana Lallashi..!
Bata tankata ba ta wuce fuu sai da ta isa wajen ne sannan taTsinkayi mganarsa yana fadin"Haka kurum zaku zo kuna ma mutane kukan banza..?
Kukan jin dadi kuke yi ko na menene..?Ko kuma an dake ku ne..Dillah ku sake su bana son Sakarci..!
Cikin Kiftawan ido suka Saki junansu suna Cigaba da gunjin kuka Daya bayan Daya ya kallesu kafin yace"Kowacce ta kama bakinta kafin nayi kasa kasa daku..!
Bai gama rufe baki ba suka yi shuru suna ajiyar rai Amina da Hanne suna rike da hannun juna kansu na kasa Amaran ya kallah sun yi Dama dama da Hijabinsu da hawaye da majina kafin yace"ku kuma ku wuce ku shiga mota..!
Da sauri ya Nazifa tace"Bari mu rikesu..!
Haj.Nasara na Dariyan su Amina tace"Danmallam da ka roki mallam ya bari su je koda kai Zeenatu ne zasu ji Dadi..!
Ko amsata bai bata ba illah su Amina Daya kalla cikin Taushinsa yace"Haj.Ba inda zasu je me zasu je suyi kuka..?Kowaccen ku ta koma cikin gida kuma ku cigaba da kukan ku gani Tunda anyi mutuwa ne..!

Sum sum suka mike hanya maimakon su koma gidan Baba mallam sai suka koma gidan Aba ko motsin kirki sun kasa Baba mallam baya wajen ya koma Falonsa shi da Aba
Sakina ranta yayi Dadi ganin ba mgana mai Dadi Umar ke fadama su Amina ba sai ta saki Fuskarta.
Su Haj.Nasara suka ssaka amaran Amota tare da rakiyan yan gusai da yayyinsu da kannensu suna kuka kamar ransu zai fita suka mika hanya sai Fatan Allah ya Kiyaye su.
Kafin La"asar kofar gidan ya zama wayam ba Jama"a Danmallam gidansa ya koma ya Huta Aliyu kuma ya koma Dutse dazu.
Hankula basu kwanta ba sai da Amare suka natsu adakinsu Jidda na Tare da Ya zeenatu a Kaduna sai gobe zata koma kano hakama Abida sai Dare suka sauka su Anty Amarya sun gama gyara komai gidan Zahra suka koma zasu kwana sai gobe zasu dawo..!
Su Amina kuwa ba wamda ya kara ganinsu har aka kwana suna Dakin yaya chan suka yada Zangonsu ammh fa duk sun yi sanyi ba ya zeenatu ba Abida gida yayi shuru sai su kadai kuma aranar ma su zafira suka koma harda ya Jamila,sauran baki ma suna ta wucewa tunda an gama Biki sai kuma Taro ya tashi.
Su Anty Amarya da wuri suka iso wajen La"asar,suka yada zango Shashen Hajiya suna fadamata karan Dangin mallam tunda uban yaron dan bazanga ne kuma matsayin kawu uban yaron yake ga mallam..!
Hajiya Babba ta kudira abu aranta sai dai batace ma kowa komai ba ta bari sai angama Hayaniyar biki sannan zata Furta abunda ta yanke.
Sai ranar Lahadi gidan ya watse harta yaran sun koma gidajen auransu,Ranar Hajiya keda shashen Baba mallam bayan sallar isha"i Mallam da Aba sun dawo shashen mallam din kamar yadda suka saba suna Hira.
Sai ga Hajiya ta shigo Cikin mayafinta yanzu shashen nata ita kadai ce Hanne ta mata yaji tana tare da su Amima agidan Sa"idu.
Lokacin da tayi sallama ta shigo gabadaya suka dago suna amsa mata Mallam ya tareta da Mirmishi yana Fadin"Zainabu abu mai Tagwayen suna..Uwargida sarautar mata..!
Yar dariya tayi batace komai ba Aba ne yace"Kuma Amarya ba..!
Baba mallam yace"A"a uwargidan dai Ni da zainabu ai mun tsufa kodon baka san tsufan ta..!
Aba na Dariya yace"Allah ya kara girma mallam..!
Hajiya na zama gefen mallam tace"Ameen kyalesa Sa"idu..Marliya ce Amarya barni in rike Tsufana..!
Aba yace"Haka za"ayi Hajiya..An watse taro lfiya yau ina sauri ana jirana na fita ban leka mun gaisa da ban gajiya.ba..Angode Hajiya Allah ya kara girma..!
Hajiya tace"Ameen bakomai..Tunda naga ban ganka ba nace uzuri ya rikeka..Ina yaran nan..?Hanne ma tamin yaji wai shashena ba Dadi ba kowa..!
Baba mallam yace"Daman ni na sani..Ranar da Abida tatashi..Sa"idu da Balaraba zasu ja Hannatu..!
Hajiya tace"ba ruwansu mamarkace da Hamida suka jata..!
Mallam na Dariya yace"To shikenan ku kyalesu ke hajiya kiyi zamanki ke kadai tunda kin zama giwar mata ki aurar da naki ki hada har da wanda ba naki ba..Allah ya kara girma da Lafiya Hajiya..!

Tana Mirmishi ta amsa Ameen kafin Aba yamike yana fadin"bari na shiga gida..!
Hajiya ta kallesa tana Fadin"koma ka zauna Sa"idu mgana nake so muyi..!
Ba musu ya koma ya zauna Baba mallan yace"Tunda na ganki daman nasan akwai mgana..!
Hajiya tace"Ina Danmallam..?
Bai shigo wajenka ba..?
Baba mallam yace""Yau kwata kwata ban gansa ba bai shigo anguwan tamu ba..yadai kirani da Safe ya gaisheni..!
Aba yace"Yaje gidan gona yau..Tare mukayi La"asar dashi ma..!
Hajiya ta fito da wayarta tana Fadin"Bari na kirasa.!
Daga Aba har Mallam ba wanda yayi mgana har ta Kira Danmallam bayan sun gaisa tace yazo gida shashen mallam gata nan tana jiransa.
Daganan ta datse kiran Mallam ya koma ya kishingida jikin kujera daman da yaga Yadda Hajiya ta shigo yasan yau Rigima take ji kuma ga Duk alamu kawaicinta ne ya kare kan Umar yau zai sha Fada..!

Tunda ya Dawo daga gidan gona bai kara Fita ba yana gida,Cikin Dakinsa Sakina kuma tana falo tare dasu Sa"adatu da suka zo mata yini,Sallar mangariba ce ta fitar dashi sai da ya Tsaya yayi sallar isha"i a Hanya sannan ya shigo gidan sai kuma yaga su Sa"adatu basu tafi ba ya farama Sakina Fadan meyasa sukayi Dare Cikin Basar da mganrsa tace"Nan zasu kwana fa..!
Kallon bacin rai yayi mata kafin ya kalli Sa"adatun datayi Fiki Fiki da ido yace"Ke mallan yasan kun zo nan zaku kwana..?
Kai ta gyada alamun A"a Harara ya sakar mata kafin ya wuce cikin Dakinsa Uzairu yaso ya kira yazo ya kaisu gida sai gobe yaso ya leka chan din sai ga Kiran Hajiya gabansa sai da ya fadi ba kasafai Hajiya ke kiransa ba yasan akwai wani babban Dalili kuma tace afalon Mallam.
Ko zama bai yi ba ya fito ransa bace Daman shi da Sakinan haka suka zo kowa na Harkan gabansa ya riga ya Dauke mata Tunda ya Lura bai isa da ita ba,Yayi alkwarin wlh bazai koma da ita ba nan zata zauna bashi da kudi bazai matsa ma kansa ba kuma ta nuna tafi son zaman nan din tabbas zata gane bata da wayau..!
Yadda taga ya fito yana cika yana batsewa sai da ta sha jinin jikinta da Sauri tace"Bari na kira Anty ko cikin mazan nan wani yazo ya kaisu..In kuma Idi na nan shikenan..!
Ko kallonta bai yi ba ya fice yana cema Sa"adatu"Dauko Hijabanki mu tafi..!
Daman ita da Sabeeha ne suna Shirye tunda yayi mgana basu ga ta zama ba suka mike tama kasa bin bayansu Saboda mamaki tabe baki tayi aranta tace sai kuma kayita yi ni dai na Riga da na nazo..!
Tsawon mintuna Talatin sannan ya shigo Falon a waje ya ijiye motarsa ya Sauke su Sa"adatu suka nufi Cikin gida yadda ya iske Aba da Mallam ga Hajiya yasa yaji kafafunsa sunyi sanyi Jikinsa ya basa wani Laifi ya aikata Domin Hajiya ko mallam ko Aba suke da Alhakin Zartar da kowani Hukunci..!
Gefe ya zauna bayan yayi sallama kansa na kasa ya gaishesu suka amsa mai Cikin Sakewa har mallam na mai Tsiyan"Umaru na kusa daina ganeka..Ka koma sak Balarabe..!

Ballatana daman shigar Jallabiyace ajikinsa mai Kalan ruwan madara kansa ba Hula gashin kansa ya bayyana..!
Kansa na kasa bai ce komai ba Aba ne yace"Ai yama koma Balaraben Mallam harta Harshensa ya koma nasu..!
Mallam na Dariya yace"Na bar ma Kattab.ni nan ya"yana sun isheni..!
Hajiya na jinsu batace komai ba Sai da ya Dago yana fadin"Hajiya gani nazo..Allah yasa Lafiya..!
Hajiya tace"Eh na ganka..!
Mallam mganar tarewar Amina ne dakace nan da wata shekarar ina so ka ijeta gefe..Ba shawara bace mallam Umarni ne amatsayina ta mahaifiyar Danmallam...Zai tafi da matarsa chan inda yake aiki..!
Daga Mallam har Aba da Danmallam baki suka saki suna kallon Hajiya wacce Daga yanayin mganarta zakasan ba wasa aciki.
Danmallam gabansa ke fadi Hajiya zata Takaitasa ina zai kai wannan yarinyar a yanzu kuma..?
Mallam ne ya katseta da Fadin"Meyasa abaya kika yarda da hakan yanzu kuma kika ce ba haka ba..?
Kai Tsaye Hajiya tace"Kada ku matsa sai kun ji Dalilina don Allah..Bazan Fadama kowa ba..abaya na yarda da hakan ne saboda ina ganin shine Daidai ammh Shekaranjiya na Fahimci munyi kuskure Mallan..anyi mai Wahalar an Daura aure To me zamu jira..!Biki ai ba Dole bane..Saboda haka in zai koma ya tafi da matarsa shine mganata..!
Aba ya bude baki yace"Hajiya hakan kamar ba adalci bane..Shi ai bai yi shirin haka ba..Ta yaya Lokaci daya kuma atakuramai..?
Hajiya ta karkace kai tace"Sa"idu ina da Dalilina..Ni ba shiri nake so yayi ba..Ko ya shirya ko bai shirya ba Insha Allahu da Mamah zai tafi in har na isa Dashi..!
Tafada tana kokarin mikewa da Sauri Mallam yace"Koma ki zauna Zainabu..Muyi mgana..!
Ba musu ta zauna Umar ya kallah yaga kansa na kasa sai zufa yake yi sai ya bashi Tsausayi bai da Hayaniya sam mai Biyayya ne da bin Umarni.
Yasan bazai taba musa mata ba har abada.
Cikin Salama ya kalli Hajiya na wani Lokaci kafin ya koma ya kalli Danmallan lokaci Daya yana Fadin"Umaru kaji abunda mahaifiyarka tace..Kuma bakace komai ba..!?

Sai da ya Hadiye wani miyau mai zafi kafin yace"Mallam bani da tacewa..Duk abunda Hajiya tace shi za"ayi..!
Baba mallan yace"Kana da inda zaka ijiyeta in ka tafi da ita ne..?Ko kuwa zamanta achan bata da takardan zama ba Takura bane..?
Sai da ya Dade bai yi mgana shi kuma Mallam Dubara yayimai su samu su lallaba Hajiya yasan da matsala rana Tsaka ya tafi da Amina gari ba kusa ba kuma ba kasarsa ba sannan abu Lokaci Daya ba shiri..!
Yasa yacemai haka domin ya samu ya kwaci kansa yana so Hajiya tabi komai a sannu sai dai baya so taga kamar yaki Sauraranta da kuma bata goyon baya..
Cikin Dattakonsa yace"Muna Sauraranka..bakace komai ba..!
Hajiya tace"Mallam basai mun jirasa ba..Koda bashi da inda zai ijiyeta sai ya tafi da ita ai ba'a Daji yake kwana ba..!
Da sauri mallam yace"A"a ba"a haka..Ki bari yayi mgana kada ki manta kasar dayake aiki ba Kasar sa bace nan din dai nan ne Kasarsa..!
Dole tayi shuru shi kuwa ya kasa mgana Aba ma haka Domin hajiya Fuska ta Hade ba Fara"a ballatana su ga wani Rahma tana so ne ta Nuna ma Sakina da Amarya Danmallam ya zauna acikinta na wata tara..!

Cikin karfin Hali ya fara mgana yana Fadin"In da son samu ne mallam.Hajiya ta bari in na koma sai na Fara cikun cukun sama mata takardan zama a kasar..sannan da wajen zamanta gidan da nike ciki karami ne Ni da Sakina da Sarood ma maallam maneji mukeyi yayi mana kadan gidana na nan yafisa girma Wlh Tallahi na rantse da Allah in na Tafi da ita zamu Takura mallam..Sai dai bazan iya bijirema Umarnin Hajiya ba..Sai ta fara shiri Jafar zai zo ya kaita ayi mata passport saboda Visa Nan da kwana Hudu nake so na koma..!
Daga Aba har mallam Tsausayinsa ya Rufesu Umar mutum ne mai Ladabi da Gudun bacin ran iyayensa,Hajiya kuwa bata Damu ba illah kada kai datayi tace"Ko ya ya ne dai tunda da inda zata zauna kamar sauran ka tafi da ita..Ka tafi da ita nace UMAR..!

Sai da ya dago kansa jin ta kira sunansa cikin wani yanayi yace"Shikenan Hajiya yadda kikace haka za"ayi..!
Sai kuma ya bata Tsausayi ammh in ta Tuna mganar sakina da yan"uwanta sai ranta ya baci so take ta gani ko

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login