Showing 54001 words to 57000 words out of 265571 words

Chapter 19 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28945

data juyo ta Harari Dakin na mamanmu kafin ta Murguda baki afili tace"Eh din baza"a gaishekin ba..Mutum sai gajarta kamar an kife kwarya..!
Tana jin Sanda mamanmu ke Dariya tana Fadin"Amina ta dai fi Hamida baki ne ita kuma Hamida ta fita Hakuri..!
Tabe baki Amina tayi kafin ta karisa Cikin Kitchen Babban Cooler da suke zuba abinci ta Bude Farar shinkafa Akayi miyar kifi bata wani Dameta ba,Kadan ta Diba ta saka Miyar nan Kitchen din ta zauna taci ta Bude babban Fridge din Dake Kitchen din ta Dauki Ruwa tasha Tana cikin shan ruwan sai ga yaya ta shigo Kitchen din,Kallonta tayi batayi mata mgana ba ta wuce tana Bude Dirowar saman Kitchen din Ko kallon inda Aminar take batayi ba sai da Aminar tace"Yaya duk yau ban ganki ba..!
Bata kalleta ba tace"ina zaki ganni tunda baki je inda nake ba..?
Meyasa baki je makaranta ba..?
Amina tace"Ban fa da Lafiya ne Tun Safe..!
Yaya ta Dauki kulin Ararrabinta Data ijiye ta fice Daga Kitchen din tana Fadin"Allah ya sauwake..Tunda kin ji Sauki ki kwashe kwanuka nan ki wanke yau hamida da Zeematu sukayi ta aiki acikin gidan nan..!
Baki Amina ta Tura afili ta Furta"Hamida bata da mutumci yanzu..Shine ko tamin ko..?
Kyafci tayi domin ta Tsani wanke wanke gwara tayi shara Daman Hamidan take tusama wanke wanken Sau tari ita kuma sai tayi shara to kwanakin nan taga Hamidan ta waye ne sai tace kowa yayi aikinsa.
Batasan komawa Dakin mamanmu Tanayin alwalanta ta shige Dakimsu kayanta kan gadonta Hamida ta Tula mata su baki ta karkace batayi mgana ba bayan ta idar da sallar kan gadon Hamida ta koma ta kwanta tana jin bayanta ya gaji Tunanin yadda zata fita tayi wanke wanken kadai take yi kara narkewa tayi In mamanmu tazo sai tace ciwon kam ya Dawo Dole Dai yaya ta kyaleta Domin mamanmu bazata barta ta fito bata da Lafiya tayi wani aiki ba.
Sai dai addu"arta bata ci ba Domin tana jin an Daga Labulen Dakin ta kara Lafewa har tana wani Nishi Sama Sama Yaya ta kalleta kamar tayi Dariya ammh sai ta kanne Cikin Kaushinta tace"Zaki taso zuwa aikin ki ko kuwa sai na shigo na iskoki kan gadon nan..?
Amina ta tura baki jin Muryan Yaya Kafim ta Mike Zaune tana Fadin"Kai Yaya ciwon kan fa bai daina ba..!
Labulem ta saki Tana Fadin"Ki gama aikin ki in bai Daina ba In Jafaru ya shigo sai ya kaiki Chemist ayi miki Allura..!
Ido Amina ta zaro Kafin ta Diro Daga kan gado afili ta Furta"Na yarda yaya bata Kaunata..!
Yadda ta Tsani Allura kuma sannan ma a rasa wanda zai kaita sai ya Jafar ai data Kade har gayenta an samu mugayen duk sum koma inda suka fito ya shamsu ne sai a islamiya suke Haduwa su ya Jafar kuma sai dai taji muryansu in sum shigo gaida su yaya bataama yarda su hadu tun bayan Watsewar sha"anin suna gida Tunda ba makaranta suke zuwa ba ko Hanne ta rage shiga wajenta itama Ganin haka yasa sai ta kwana Biyu bata shigo ba sai dai su hadu a islamiya da yammah.
Hakanan tana Tura baki tana kunkuni ta fito da kwamukan wanke wanke zuwa Bakin Famfo Dakin mamanmu ta leke bakowa ita ta shiga wanka su Sakina kuma suna Dakin Yaya Daga Tsakar gidan ma tana jiyo Tashin Hirar Sakina da yaya Sarai Sarai ta kwashi kwanukan da suka bata nan Falon mamanmu tana kunkuni ita Kadai.
"Sun wani zo sun bata mana kwanukan sun karamim aiki..Mtsewww..!

Nuku nuku ta dinga yi Saboda Mamanmu ta fito ta hanata sai dai Addu"arta bata amsu ba Mamanmu bata Leko ba sai ma yaya ce ta Leko raka su Sakina suka leka Dakin mamanmu suka mata sallama sai gasu sun fito Tare tana gyara Daurin Dankwalinta Lokaci Daya tana Fadin"Ke Sakina yar"uwar taki bata jin Hausar tamu sai labarcimu kuma bamu kware ba..!
Tafada tana Dariya Sakina ke Fadin"Mamanmu wanda aka Haifa achan yayi Rayuwarsa achan ina zai ji Hausa..?Sai dai hankali zata iya Tunda yanzu ta shigo Cikin mu..!
Yaya tace"Kwarai tunda ta auri Bahauahe ba..koda yake shima ai Danmallam din Harshensa ya Karye kamar Balaraban chan..!
Mamanmu tace"Ai ya Dade fa achan yaya..Ina jin yafi shekara goma ko..?
Sakina tace"Yana cikin shekarata ta ashirin ne fa naji yana Fadi..!
Mamanmu tace"Koda naji..!
Yaya tace"Zai yi fa Tun su Zahra na kanana fa alokacin..!
Ita dai Sarood sai dai tayi ta washe baki in ta tambayi Sakina me akace ne sai Sakina ta gayamata da Larabci Duk da itama ba wani kwarewa tayi ba Harda iyayi ita Adole tana jin Labarcin.
Amina na Tsugunne tana wanke wanke ta tabe baki aranta tace"Allah yasa ma tasanme take fadi..!
Mamanmu ce ta ganta cikin jin Dadi tace"A"ah jiki yayi kyau Amina..!
Dole ta Dago tana yake tace"Eh Mamanmu kam ya daina ciwo..!
Da sauri tace"Masha Allah..To kiyi Sauri ki gama kada mangariba ta Sauko baki gama ba!
Da toh ta amsa batare data kara mgana ba,har suka wuce har korido suka Raka su Sakina suna kara musu sallama da alkawarin agoben kafin su tafi zasu shigo gidan su kara yin sallama.
Tana jin har sanda su mamanmu suka Dawo tana mata Fadan tayi ta gama Ko mgana ma batayi ba da kai ta kara amsaa mata,nuku nuku ta Dinga yi sai tafi minti Biyar bata wanke Kwano Daya,Har Su hamida suka shigo sun Dawo Daga islamiya Ya Zeenatu ne ta kalleta tana Fadin"Har duhu ya shiga Amina kina zaune bakin Famfo alhalin kinsam har Aba yayi Fadan hakan.!?
Amina taso ta dago tace"Ina Ruwanki ne..?
Sai kuma ta fasa ta Tura baki ta Kauda kanta Ya Zeenatu ta wuce tana Fadim"Ke kika sani..!
Hamida ne ma tace"Kin warke kenan..!
Daman jiranta take sai ta mike ta Rike kugu tana Fadin"Ina Ruwanki..Im ma na warke in ma ban warke ba..Duk ba Damuwarki bane..Kada kuma ki Dameni Mutum ba Taimakaa maka zai yi ba sai ya isheka da mita akyaleni ko sai gobe ne in gama ina Ruwan wani..!
Hamida bata tanka ta ta wuce Daki abunta ta ijiye jakarta,Duk tana wajen suka fito sukayi alwala ba wanda ya tankata ta juye Jidalinta akansa itama sai Harare harare take yi karshenta dai kan Jawad ta Sauke Haushinta wai ya Watsaa mata Ruwa haka ta mike ta Rikeshi ta Falfalmai mari har sai da yayi kuka da kuka ya fita masallaci Lokacin Yaya tana Sallah Hamida ce awajen kuma batace komai Domin tasam ba karamin aikin Amina bane ta Dawo da duka jidalin kanta Shiyasa bakinta kanin kafarta ta koma Daki.
Amina har aka Idar da salla tana bakin Famfo bata gama wanke wankenta ba,Yau din ma Ya Danmalam ya bada Sallah Ita Rabonta da gansa tun Ranar Daurin aure da yayi mata wannan Tijaran ta gujema haduwa dashi Shine mutuum na Farko Daya taba Cin Zarafimta bata samu ko Baki ta Turamai ba yana da ta wata baiwar da komai Rashin kunyarka sai kaji Shakkarsa.
Afili ta Furta"a Muryansa kamar mai kirki nan kuwa cikinsa fal Tozarta Mutane..!
Bazata ce taji Sallamamsa ba Daga sama kamar acikin kanta taji Sansanyayyar Muryansa cikin Zatinsa yana Fadin"Waye anan..?
Ya ke fada domin Lokaci akwai Duhu kuma ba"a riga a kunna injin ba.
Kyam Amina ta kame Daga inda take Sai kuma jikinta ya fara rawa da taji Muryansa batasan Dalili ba Bata son Haduwa dashi bata son jin muryansa Domin Fadar mata da gaba Muryansa yake yi sannan Uwa uba ganinsa ba Alheri bane sai ya Tozartata.
Kokarin Fito da wayarsa yake ya Haskata sai Haske ya gauraye Tsakar gidam,Nepa sun kawo Wuta Daidai Lokacin da Idanuwan Amina suka shiga Cikin na Umar Dake Tsaye Gabda da ita yana kallonta kamar yadda itama take kallonsa.
Sanye yake da Jallabiya mai Ruwan kasa da Hula a saman kansa sai Bakin Wandon Dake jikinsa Tunda Jallabiyar bata kaai mai Kasa ba.
Fuskarsa ta kara kyau ya Kara Haske har wani Kiba taga ya karaa mata.
Cikin mamakin ganinta acikin wannan yanayin yake Fadin"Ke me kike yi anan da Mangriban nan..?
Yake Fada yana kara Nazarinta da Sauri ta Sadda kanta kasa ta kasa mgana,Jikinta ba inda baya rawa,Lebenta Kamar ya Nane haka taji ta Kasa mgana s???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?hi kuma Ransa ya fara baci yarinyar nan bata da kunya Rainin Da take yi ma su Jafar shi take so tayi mai yasa ya Dakaa mata Tsawa Cikin Bacin Rai yace"Bada ke nake mgana ba..?Kika bari na nazo wajen nan sai na Lahira yafi ki jin Dadi..!
Ki bari na taso ki gani..!
Tsawamsa shi ya fito da su Hamida Harda Mamanmu da Yaya sai suka ga Danmallamm
Mamanmu ce ta washe baki tana Fadin",A"a Umaru barka da zuwa!
Kallonta yayi kafin yace"Mamanmu me yarinyar nan take yi anan wajen nan har yanzu..?
Mamanmu tace"Amina ce wanke wanke take.!
Katseta yayi da fadin"Haba Mamanmu tana mace?
Da mangariban nan ita Kadai acikin Duhu bata tsoron lafiyarta.?
Mamanmu ta kalli Amina da Kanta ke Kasa tana ta fiki fiki da ido tace"Wlh Danmallam sai da nayi mta magana Tayi ta gama Kafin Dare yayi..Dayake ba Lafiya ne da ita ba..!
Amina taso daga wajen nan Hamida da Zeenatu ku taaimaka ku karisa don Allah ina ga Kan ne ya Dawo mata!
Zeenatu tace"Mamanmu Wlh lafiyarta kalau Aminar ce baki sani ba!
Hararanta tayi Kafim tace"Bazaki yi ba kenan?
Dole tayi shuru bata kara mgana ba Amina kuma kamar mumafuka kanta na Kasa ta taso tsomai Tsomai kamar Wata kazar da aka Cirota Daga Ruwan Zafi Danmallam ya bita da kallo Cikin kyama aransa yana Tunanin yarinyar nan ta wuce Tunaninsa
Yaya ce ta faraa mai maraba tana Fadin"Maraba da zuwan Dan mallam
Ga bakin Larabawa..Lale..!
Jin Muryan yaya yasa ya kariso Cikin Fara"a nan Tsakar gidan ta Shimfida mai Darduma ya zauma suka Fara gaisawa Zeematu da Hamida suka gaisheshi ya amsa kafin mamanmu tazo ta zauna su gaisa Daganan ta koma Daki ta bar su shi da Yaya suna ta Fira
Amina dai tunda ta samu ta shigo Daki bata kara fitowa ba Hamida da Zeenatu suka karisa aikin suka maida komai Kitchen suka share wajem abayin Dakin tayi alwala tayi sallah Ta Haye kan gadonta bata Damu da Kwashe kayanta akansu ta kwanta bata Damu ba

Ya zeenatu ne ta shigo tana ta Fada Fadi take"Wlh Amina ki rika Karisa aikinki..Domin nan gidam ba bawanki..Ni ba Hamida bace Darajan Mamanmu kikaci Wlh..!
Amina na jinta tana Danne Dariyanta Daga kwamcen Tana kallonta kai ta kada kafin tace"Ba Laifinki bane..Mamanmu ce take Daure miki gindin Iskanci Watarana ai ba Maman ko..?
Naga uban da zai zauna kina wannan iskancin bai ci ubanki ba..!
Ita dai bata tanka ba har ta gajii da Mitan ta fice bayan Fitar Danmallam Daman Sallama yazo yi ma su Yaya Gobe Jirginsu na dare me zai tashi zuwa Jidda a Filin Sauka da Hawa na Aminu kano.

Sai da ta ficen ne Amina ta fito da Dariyanta tana Fadin"Allah Sarki..Ya Zenatu kawar ya Abida...!
Hamida ta kalleta kafin tace"Ke kam ki tashi ki gyara kayanki Amina Harda fa Sabbi ciki..!
Amina ta kyabe baki kafin tace"In kin Damu ki gyaramin Hamida!
Hamida tace"Na rantse kuma bazan yi Kaffara ba..!
Tsaki Amina taja Kafin tace"To sai ki kyaleni malama!
Hamida tace"Yau anyi Fada da Mariya da Sa"adatu..Har da Dambe sai da mallam Auwal ya Zanesu..!
Da Sauri Amina ta Mike tana Fadim"Don Girman Allah..?
Hamida tace"Wlh suna Zage Zage..Kinsan Hanne da tsoro sai kuka take yi..!
Amina ta Daka Tsalle har da shewa kafin tace"Ahyayyeee...Yau naji Dadi karshen alewa kasa.
daman ai xaman munafunci baya karko..Tacizi yatsa Kafin ta cigaba da Fadin"Naso yau naje..Da sai na kara Yamutsa wajen munafukai..!
Hamida tace"Gwara dai da baki je ba..!
Amina ta balla mata kafin tace"Ga Shedan ko..?
Hamida kina shigarmin hanci fa ki kyaleni.!.
Hamida tace "Daga Fadin gaskiya..?ai ba karya nayi ba Da kina nan wajen Allah kadai yasan iya inda abun zai kai..!
Amina ta karkace baki kafin tace"Hanne wai me aka mata take kuka..?
Hamida tace"Me kuwa..?tsoro gareta Taga suna Ta kwasan Dambe..!
Amina tace"Aikin banza Hanne banza ce..Meye abun kuka..?
Allah ya Tsareni..!
Hamida dai bata kara mgana ba Domin Har ga Allah taji Dadin da Amina bata zo ba Domin Allah kadai yasan Iya inda Fadan nan xai kai Amina sai ta hau Fadan ta siyeshi ta kara Maggi da gishiri.
Waashegari Da Safe ta shiga wajen Hanne ta iske Su Sakina suna gidan suna ta shirin Tafiya Ya Jafar zai kai su kano Ya Nasir yana da aiki a asibiti.
Amina ta kalli Hanne tana Fadin"Wai ganin ana Fada da Sa"adatun ne kike kuka..?
Hanne tace"Ni bana son ganin ana Dambe ne..Ko ke kike Fada ai ina kuka..!
Amina tace"Wlh karya kike yi..Natan Dai kike kuka ke mai yar"uwa Ki kama Kanki Hanne Domin in kece Dariyama zata yi kina abu kamar wata sakarya..!
Hanne tace"Bakomai naji..!
Kinsan yau su ya Danmallam zasu koma..?
Amina ta tabe baki kafin tace"Jiya sun zo gidanmu naji Mamanmu na Fadin yau zasu koma
Dukkansu zasu koma..?
Hanne tace"eh mana..!
Amina tace"To in suka tafi sai yaushe..?
Hanne tace"Yace ma Hajiya sai wani abu ya taso..Im bai taso ba sai nan da wata Shidda zai zo..!
Amina tace"Allah ya tsare..!
Aranta kuma Fadi take"Allah ya raka taki gona..!
Lallabawa tayi ta gudu gida abunta batama san Tafiyarsu ba su yaya dai da mamanmu sun je sun karayin musu sallama sai yamma suka Dawo suna Fadin wai har ya Jafar ya Kira suna kano basu dai tashi ba sai Dare.
Sai washegari wajen chan Rana taji ana Fadin sun sauka a jidda Daganan zasu hau Mota zuwa Madina ko ajikinta Sai taji kamar wani Nauyi ya tafi Bata ko kaunar ganinsa ma ballatana jin muryansa.

*******

Bayan wata Daya..!

Amina na kwance da Safe tana barci Taji ihun Hamida asaman kanta tana Dukanta Lokaci Daya tana Fadin"Amina tashi..Tashi.!
Next week zamu fara zuwa makaranta an gama mana komai..!
Amina da sauri ta Bude idanuwanta cike da barci tace"ke a ina kika ji..?
Hamida tace"Yanzu naji Ya Jafar yana Fadama Mamanmu..!
Amina tace"Ina zamu koma..?
Hamida tace"Ina kuwa..?Unity...?
karamin tsaki taja kafin ta gyara kwanciyarta Tana Fadin"Yanzu dai chan zamu koma..?nifa na Tsani Unity din nam..Allah yasa banda munafukar nan Sa"adatu..!
Hamida tace"Kema kin sani..Gabadayanmu ne..!
Amina ta Yamutsa Fuska kafin tace"Ban so ba..!
Naso kowa ya kama gabansa..Ke ni fa Wlh nafi son zaman gidan nan akan komawa Shegiyar Unity din nan..!
Hamida tace"Ke yanzu zaman bai isheki ba..?Tab ni Wlh na gaji..!
Amina tace"Da an bari Second Term sai mu fara zuwa..!
Hamida bata bi ta kanta ba ta Fice tana Murna Amina ta Bita da kallon Na Tsausaya.
Da yammah ma sai ga Hanne tazo suna Murna ita da Hamida Amina tun Tana Daukan mganar wasa sai gashi ta Tabbata an kawo musu sabbin kayan makaranta na Senior da Jaka da takalma Da Safa da Sabbin Littafai ya Shamsu yakawo musu nasu Ranar Monday zasu fara zuwa.
Kowa na Murna banda Amina Tsakani ga Allah Hutun bai isheta ba ta so sai Second Time su koma makaranta ammh Ina ba wanda zai bar su su zauna agida ana kallonsu Takaicinta Daya Sa"adatu bata kaunar su na Hada Hanya don bata da yarda zatayi ne kawai.
Har ya Zeenatu sai da ta mata mgana Tana Fadin"Ke Amina Hanne da Hamida na Murnan Jjc yan SS1 KE banga kina yi ba..!
Amina tace"Murnan me..?Unity ce fa..?Daman wata kayan gabas ne ba nan ba..Ni gabadaya makarantar ta isheni..!
Ya zeenatu tace"Kina da aiki..Tun Zamamin su ya Nasir Unity ta kyankyshesu ballatana ke Zuwan yau yau..Yarinya Unity Dolen kowa ne indai D'an nan gidan ne ko dan Gidan Baba Mallam ne..!
Amina baki ta Tura bata kara mgana ba Ganin yadda ya Zeenatu ta zakal kale,Tana ta bayani Hamida na Tayata su adole suna kara yabon Unity a wajenta Tabe baki tayi aranta tace ko Ta Tsani makarantar nan ba Sauyi kowa ban yayi ya gama suma kuma nan din zasu gama..!
Kullum ba cigaba haba don Allah.








*Janafty*

*TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*


*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janaftyd'?*


*
*Jumma"a*
9:00am

Labulen Dakinmu Mamanmu ta daga tana kallon Amina Dake zaune Saman gadonta ta tasa kayan da mamanmu ta gama wanke mata jiya ko fara ninkesu batayi ba.
Hamida na Gefenta itama wajen Dirowarta tana shirya Littafanta Cikin Sabuwar Jakar makarantarta Mamanmu ta kalli Amina Data Zabga Tagumi kamar wacce akace mata nata ya rasu Cikin Lallami tace"Amina baki Fara Ninke kayan nan naki ba ko..?yi hakuri ki adanasu ina aiki ne da na Gyara miki..Kwashesu ki saka cikin Dirowarki in anjuma in nepa sun kawo Wuta Zan saka Hamida ta goge miki sai ki adana Kayanki..!
Hamida na jin haka ta Dago tana kallon Mamanmu kafin tace"Ni kuma Mamanmu..?
Tafada Tana Bata Fuska Mamanmu tace"Eh ke..Ko bazaki yi bane..?
Tunda ita haka Allah yayi ta bata da Zafin nama ku kuma yan"uwanta ne kun fita karsashi ba sai ku taimaka mata ba..?
Hamida bata iya mgana ba ta maida kanta Gefe Amina kuma sai Danne Dariyanta take yi kafin tace"Dama ta barshi mamanmu..!
Bata bi ta kansu ba ta saki Labulan ta koma tana Fita Amina ta Fara Dariya Har tana ma Hamida gwalo kallonta Tayi kafin ta girgiza kai tana Fadin"Kiyi Dariya son ranki..Lokacin ki ne ammh ki sani akwai watan watarana..Da babu mamanmu ba Hamida wlh sai kin raina kanki..!
Kamar ba mace ba komai sai dai ki zauna komai Mamanmu tayi miki ko kuma ta sa muyi miki..!
Tafada Cikin jin haushi Amina ta kara saka Dariya kafin tace"ko ba mamanmu ba gaki ba..?
Hamida ta Harareta kafin tace"Ni kuma sai bazan yi aure ba sai na koma kula Dake..?Sannu Amina yar gata..!
Amina tace"To miye..?Sai ki auri kanin Mijina..!
Karamin Tsaki Hamida taja Amina ta kara saka Dariya tana Fadin"Hamdiya..Hamdiya..Hamdiya..!
Take Fada cikin Sigar waka Da sai da Hamida tayi Dariya tana Fadin"Ke kika sani..Allah yasa ki shiga gidan mai mata Biyu kece na uku..Ya"ya kadai sun isheki Amina..!
Amina tace"jar uba..ya auran ma kansa dai..Mai mata Biyun daya kwashi Amina ai mai Budurwan Zuciya ne..Sai yayi Nadama Tijara ne da Jidali ne zai gani harda na Siyarwa..!
Take Fada tana Dariya Hamida na Tayata Daganan suka shiga Hirarsu Amina na tusa kaya cikin Dirowanta batare data Tsaya Ninkewa ba Hamida tace"Kai Amina mugunta ma harda karan kanki kike yi mawa..?
Amina ta tsaki kafin tace"Ki kyaleni Hamida ni nagaji..!
Hamida ta mike tana Fadin"Zaki ma mike ne yarinya yau ke kike da gyara mana Daki..!
Amina tace"Kan bala balagagge..Ranar fa ni na gyara..?
Hamida tace"Ai ba sau Daya ake gyaran Daki asati ba malama..!
Amina ta Tura baki kafin tace"To nidai na gaji bazam iya ba..!
Hamida ta bita da kallo batayi mgana ba Amina ta cigaba da Fadin"Mutum kamar jaki aiki aiki..Ni wlh nagaji..!
Hamida baki ta rike ta kasa mgana wai Amina na Mganar aiki me takeyi..?
Aiki sai ya

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login