Showing 114001 words to 117000 words out of 265571 words

Chapter 39 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28954

zata bar mata mijin ne kamar yadda tace.
Yasa bata damu ba sai ta saki Fuska kafin tace"Allah yayi maka albarka..!
Ya amsa da Ameen cikin sanyinsa.
Maallam yayi mirmishin su na manya kafin yace"Hajiya..Hajiya manya..Kiyi hakuri zan yi wata mgana ni ba Umarni zan baki kamar yadda kika bama Umaru ba Alfarma zan tayasa riko tunda shi ba"a bashi Dama ba Sa"idu kuma bazai iya tsalleke mganarki ba shima ammh ni ai ina da Damar mgana ko ba haka ba..?
Kai Tsaye tace"Ina jinka..!
Maallam ya gyara zama yana Fadin"Daman zan ce ki yi hakuri don Allah duk da bamu san meyasa kika kawo wannan mgnarnan ba..Maimakon ya tafi da ita cikin Takura Zainabu me zai hana ta tare anan gidansa Dake nan Allah barshi in ya koma ya gama Dukkan shirinsa nima ina goyon bayan yazo ya tafi da ita inda yake aiki Tunda an riga an yi mai Wahalar..!
Hajiya tayi shuru kafin tayi mgana Mallam ya rigata da fadin"Alfarma mukace..Don Allah ayi hakuri ayi mana..!
Yafada cikin sigan lallashi Sai Hajiya tayi Laushi Cikin Dan kauda kai tace"Na amince ammh nima ina da Sharadina..!
Mallam yace"Bakomai tunda kin amince shikenan muna sauraranki..!
Hajiya tacigaba da fadin"Na amince da mganarka..Sai dai Abu Daya nake so in ya tafi bazai Dauki Lokaci ba .In ya Dade sosai wata Biyar ko Shida..Sannan Mamah zata tare agidansa goben in Allah ya kaimu bana son bata Lokaci..!
Mallam yace"Gobe kuma..?anya gaggawa ba aikin shedan bane..?
Da sauri tace"Haka kuma wani Jinkirin matsala ne mallam..!
Ganin yadda ta Cije ne yasa yace"Ammh kinsan nace sai ta yi Jarabawar gama sakandiri ko..?
Hajiya tace"Zata rubuta a Ss2 din ba shikenan ba..!
Mallam yace"Shikenan..mungode..!
Kafin ya maida kallonsa kan Umar yana fadin"kaji mahaifiyarka..na roketa alfarma kuma tayi mana sannan kaji itama sharadinta ko..?
Kansa na kasa yace"Naji mallam..na amince Allah ya shige mana gaba..!
Mallam yace"Ameen cikin gidan naka Dakuna nawa ne..?
Yace"Uku ne sai falo da Kitchen..!
Sakina na cikin Daya da Sarood tazo nace ta bata Daya sai nawa..!
Mallam zai yi mgana Hajiya ta Rigasa da Fadin"Zata zauna anaka Dakin..Mganar jere kuma ba bukata Tunda kowaccensu ba ita ta saka kayan gidan ba..Bana kowaccensu bane..Sai dai ka sani zaka samar ma Amina nata Muhallin anan domin ayi mata Jerenta kamar ko wacce ya' acikin gidanan..!
Mallam bai ce komai ba sai Danmallam ne yace"Insha Allahu Hajiya..!
Ko Aba ya kasa mgana Ganin haka yasa Mallam ya sallami Danmallam yayi musu sallama ya fice Aba ma ya Mike jikinsa sanyaye yayi musu sallama Hajiya ta kallesa tana Fadin"Sa"idu ka sanar ma Balaraba da ita Mamah..Da safe zan shigo insha Allahu gobe agidan mijinta zata kwana..!
Bai da tacewa ya amsa mata da toh ya ficen bayan fitansa mallam bai tada mganar ba domin yasan tana da Dalilinta sha"anin mata sai abarsu.
Aba haka yajema mamanmu da mganar sai ta sakamai kukan nawa Amina take da hajiya zata mata haka bai Saurareta ba ya Kira Amina ya Fadamata Sakon Hajiya ranar su uku kwana sukayi kuka kamar anyi mutuwa kukan sabo da kuma Rabuwa da Amina.
Adaran Mamanmu ta kira Anty Amarya ta fadamata ta Zunduma ashariya tace mamanmu tasan yadda za"ayi Amina ta Bijirema Tarewarta aikuwa da Safe ta kira Amina ta sata adaki tana kuka tana fadin za"a cutar da ita kowace sai da ta gama makaranta aka mata aure banda ita ta Rika Tusa mata mganganu da sai da Amina taga haka din ne ita za"a kwareta an cutar da ita mamanmu tace taje ta samu hajiya ta fashe mata da kuka tace batason tarewan tasan zasu kyaleta Amina ta yarda da hakan domin bata hasko ma kanta ta zama matar aure ba yanzu Haka ta Zurma Hijabi Fuska kozai kozai tasha kuka ko su Hanne basu san ta fita ba
Sai dai tana shiga gidan ta baro shashen Mallam kenan dan lungun Dake tsakanin shashensa da na Anty Amarya taji tashin murya sama sama Abunda yasa taja ta Tsaya sunanta taji ana ambata..!

"Dayyaba..In har AMINA tatare a matsayin Matar UMAR..na sabama Sakina alkawarinta..Alhalin na mata Rantsuwan in har ina Raye auran Amina da Umar haka zai kare a gantale ba Fa"ida..Ammh yanzu komai zai lalacemin in har yarinyar nan ta tare agidan nan Kashin mu ya gama Bushewa Fitar da ita shine babban aiki..!






*Janafty*

*TA FITA ZAKKA..!*
_(Aminene)_
*BOOK 1*

*Wattpad:JamilaUmar351*
*Mallakar:Janaftyd'?*


*
"Gaban Amina ya fadi ras jin Sunanta da mganar da ke tashi akanta Labe ba Dabi"anta bane ammh sai ta kasa yin gaba sai ta ja ta tsaya ta kara kasa kunnenta tana sauraran muryan Anty Amarya Tar tana mgana cikin bacin rai da takaici.

"In ya kulata din fa Dayyaba..?Kada ki manta Namiji ne ko bai kulata domin yana sonta ba na tabbata zai iya kulata watarana saboda Hajiya da mallam..Ayadda yarinyar nan ke da Tasiri a wajensu matukar tatare agidan Umar Tauraruwar Sakina zai koma baya ne..Ni kuma nayi alkawarin matukar ina Raye Sakina ce kadai Mowa agidan Umar..Kuma sai na tabbatar da na cika mata wannan alkawarin Indai bata Haihu da Umar ba alkawari nayi ba wata macen data isa tazo ta Haihu..Ita kadai ce Tauraruwa kuma Sarauniya..!

Amina mamaki ya kara cikata gani take abun kamar amafarki,so take ta Tabbatar da zarginta yasa ta Leka lungun bayanta take hangowa dayake ta Juya bayane tana mgana ta waya,Sai dai ko daga barci tatashi Ko ta baya ko ta gaba zata shaida Duka matan baba mallam ba ta murya ba Daga yanayinta ko kaffara ba zatayi ba Anty Amarya ce sannan gaa ma Muryanta nan na fitowa duk da Bada karfi sossi take mganar ba..!
Baki ta rike tana kara mamakinta Sanda taji tana Fadin"Na bar komai a hannunki..Don Allah ki san yadda zaki yi kada Tariyar ta Amina ta tabbata..In har auransu Kuskure ne to kada ma wannan ya zama kuskure Dayyaba..In ya zama Kuskure zamu yi shekaru kafin mu iya gyarashi..!
Kiyi gaggawan yin wani abu..!

Amina taji kanta ya sara abaya tasan Anty Amarya ta Tsaneta,Ammah bata taba tsammanin Tsanar nata yakai haka ba meyasa bata son ta Tare a gidan ya Danmallam...?Wata zuciya tace Saboda Sakina mana Tunda Diyartace to ammh da wa take waya..?Waye take cema yayi mata kokarin kada Tariyanta ya tabbata..?Ta shiga Rudi Kwakwalwarta ta toshe ta kasa Tunani Abu daya ta kama Anty Amarya bata so ta tare saboda Sakina
Abun kamar almara sai taji kuncin Dake zuciyarta ya yaye Daga rashin son Tarewar zuwa son ta tare din ba son ya Danmallam take ba har Abada Aminu ne aranta Sai dai zata taren sai Taga yadda Anty Amaryan da Sakinan zasu yi da ita munafukam banza Har itace zasu ma Burauba to sai ta taren Uban daya Fasa sai ya Hanata..
jidalinta kadai ya ishesu daga Sakinar har Mijin nata basu isheta kallo ba
Maimakon ta wuce shashen Hajiya Babba kamar yadda Mamanmu ta Tsara mata sai kawai ta fasa ta kada kai ta juya zuwa Haraban gidan tana Tafe tana auna maganganun Anty Amarya tana Tunanin adanginsu wacece Dayyaba..?Ta gama Tunaninta kaf bata ganota ba to wacece take cewa ta bar komai a hannunta..?
Tana wannan Tunanin ta kusa cin karo da Akilu ya fito daga Falon Mallam Sanye da Uniform ajikinsa sai da ta gansa ma ta tuna yau Monday suna da makaranta.
Shekeke yake kallonta ganin ta Dauke kai zata wuce yace"Ke Amina bazaki makaranta bane..!?
Mamaki ya bata suna da son Girma shi da Zubairu gwara ma Akilun ya basu shekara Daya da wani abu Zubairu fa saurin girma yayi Hajiya tace tsakaninsu ko wata Biyar bai kai ba An riga sakashi makaranta Shiyasa ya Tsere musu da aji Daya ammh sai su rika nuna abu kamar sun wani basu Shekaru barin ma Akilun nan dan Rainin Hammata ne..!
Kasa kasa ta juyo tana kallonsa da Kumburarrun idanuwanta kafin kai Tsaye tace"Eh..!
Kallonta yake cikin bude ido yace"Eh fa kikace..To saboda mene ko baki da Lafiya ne..?
Amina ta gaji da yadda ya wani Tsareta da tambayoyi kamar Ubanta Cikin Kufuluwa tace"Bansani ba..!
Baki ya rike yana fadin"Amina ni ma kike cema baki sani ba don Uwarki..?Ni sa"anki ne..?
Daman shi abu kadan zagi kamar ba Jinin Mallam ba
Amina ta Bude manyan idanuwanta kafin tace"Wlh badai uwata ba..!
Ya Zaburo Cikin bacin rai yana Fadin"Sai tawa uwar kenan..!
Ta matsa da Sauri tana kunkumi tace"Ai uwa bata fi uwa ba Ehe..!
Akilu Duka yake son ya kaimata Bai ji Fitowar Mallam ba sai mganarsa.

"kai Akilu kaniyarka nace..!
Matar yayan naka zaka Daka dayake baka da kunya ko..?

Dukkansu suka juya Baba mallam ne Cikin Akyabbansa da Rawani Tsaye kofar Falonsa yana kallonsu Bai ji Mganarsu ba Fitowarsa kenan Daga Daki yaji Akilu na fadin shi Sa"anta ne yana Lekowa yaga zai kai mata hannu.
Akilu na ganin Baba Mallam ya Rankwafa yana fadin"Allah ya kara girma Baba..!
Amina kuwa gaisheshi tayi ya amsa yana fadin"Mamana Daga ina da Safan nan..?
Amina ta sharara karya da cewa"Nazo gaida Hajiya ne..!
Baba maallam ya Murmusa yana kallonta kafim yace"Yar gidan Hajiya..To kin gaishetan ne..?
Amina kanta na kasa ta Daga kai Baba mallam Akilu ya kallah yana Fadin"Bana son na kara ganin wannan Sakarcin..In har zaka Daketa ashe zaka sa ka hannu ka Daki Umaru ko..?
Akilu ya Dago kansa yana kallon Mallam kafin ya juya yana kallon Amina da kanta ya fashe ta Hura Hanci tana Juya ido shifa tun sanda aka Daura auran Amina da ya Danmallam yake Tsausayamai ko shi da yake yaro daidai da ita bazai iya da Amina ba ballatana ya Danmallam wanda bai da Hayaniya mai sanyi ne shi.Ai Tsab zata jazamai hawan jini in kuma ta Hadu da Sauran ciwo Tsab zata Karisa shi Lokacinsa bai yi ba.
Dukar da kansa yayi yana Fadin"Ayi hakuri mallam baza"a kara ba..!
Yaji Dadin haka nan da nan ya saki Fuskarsa yana fadin"Ko kai fa..?Allah yayi muku albarka..!
Ya amsa da Ameen ya mike yana kallon Amina Data fakaici idon mallam ta Zabgamai gwalo Rai ya bata yana Kada mata ido ita kuma tana wani Juyamai ido.
Sai da ya shige Dakinsu sannan Mallam ya kalli Amina yana Fadin"Ina Sa"idu..?
Yana gida ko ya fita ne..Au ga motarsa ma ashe yana gida kenan..!
Amina tace"Eh yana gida mallam
Mallam yace"Yauwa in kin je gida kice mai ina son ganinsa saboda da wuri zan fita!
Amina tace"Mallam tafiya zakayi..?
Mallam yace"Zaria zani Cikin makarantar ABU akwai wani Taro da aka gayyaceni a Depatment din Islamis Studies shine Uzairu zai kaini yau nakeson mu dawo bana so muyi Dare..!
Cikin Sanyinta tace"Allah ya Kiyaye hanya..!
Ya amsa da Ameen uwata Daganan tamai sallama ta wuce ya bita da kallon Tsausayi har yau bai daina jin yanayin kamar bai kyauta ma Amina ba,Hajiya tataso da wannan mganar kuma bazai iya musa mata Ba bataba ja da mganarsa ba yasanta sarai tana da Dalili ammh Tunda bata Fadamai ba bazai matsamata sai yaji ba Jiya yayi istikara akan al"amarin kuma yaga Hasken Amina Tatare agidan Umaru zasu rakasu da addu"an zama Lafiya da Zuru"a Dayyaba..!
Amina Jikinta a sanyaye ta shiga gida ba Kowa a tsakar gidan Har Falon Aba a kulle alamun bai fito ba Sai ta wuce Dakin Mamanmu.
Bata afalo sai ta kutsa kai Uwar Dakinta Kamar yadda ta saba kai Tsaye hankalinta baya tare da ita Shiyasa har bata jin shigowar Amina ba,kalma Daya Amina ta jita Cikin kunnenta.

"Kada ki damu bani nace ba..Ki kwantar da Hankali......!

"Mamanmu..!

Gabanta ya fadi dam jin muryan Amina abayanta Jikinta sai ya fara rawa ckin rawan jiki ta juyo tana kallon Amina Dake kallonta Cikin mamakin ganin yadda take rawan Jiki ga Zufa na keto mata ta saman goshinta.
Cikin Fargaba da wani irin Tsoro tace"A..A..mina yaushe kika shigo..?
Amina tace"Yanzu na shigo mamanmu..!
Tana jin sadda ta Sauke ajiyar zuciya Da sai da ta kalleta,Cikin mamakin ganin yadda tayi Firgai Firgai kamar wacce tayi karya agaban Sarki.
Hannun Amina ta riko Daya jike da Zufa ta zaunar da ita gefen gado tana Fadin"Kin gayama Hajiyar abunda nace..?
Amina ta samu kanta da kasa Fadama mamanmu komai da Farko ta shigo da Niyyar Fadamata har wayar dataji Anty Amarya nayi ammh yanzu sai ta kasa Haka kurum kamar an Rufe mata baki an sauya mata mgana taji ta tana fadin"Eh na fada mata..!
Tana ganin sadda ta washe baki tana Fadin"Yauwa to me tace..?
Amina gabanta ne ya fadi bata so zargi ya shiga ranta Kodai kodai mamanmu ce suke mgama da Anty Amarya Da sauri tace A"a mamanmu ba muguwa bace ba mamanmu bace ba ita bace watace ta Dabam ita Tana yin komai Saboda Farincikina ne.
Da sauri ta Kauda wannan Tunanin da Fadin"Tace na koma gida gatanan zuwa..!
Mamanmu tayi shuru tana Tunanin anya Hajiya zata janye mganar ta kuwa..?
Duk da Mallam da Safen nan Amarya tace ya Tarasu ya fada musu Tariyar Amina ayau dinnan
Ganin kallon da Amina ke mata yasa Ta fashe da kukan makirci tana Fadin"Amina duk abunda kikaga inayi Saboda ke ne .Ina so na ga Rayuwarki ta Inganta kamar ta kowa Amina..Danmallam bai dace dake ba..Matansa Biyu Amina ina zaki iya Kishi da mata Biyu mace ma irin Sakina..Uwarta Kinsani na sani bata Kaunarmu Amina zasu yi komai Saboda su ga bayanki ni kuma na Shirya Saboda ingata Rayuwarki Sai inda Karfina ya kare,na gwammace na rasa komai Ciki kuwa har da Rabuwa da Aba dinku Saboda ke Amina..!
Ran Amina ya cika da Tsausayin Mamanmu arant?????
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
?
 a take jin mamanmu bazata taba Cutar da su ba,da sauri ta Rike Mamanmu tana fadin"A"a mamanmu kada kice haka fa..Insha Allahu saki bazai kara shiga Tsakaninki da Aba ba..Ki daina Fadar haka don Allah bana jin Dadi..!
Mamanmu tana Jan hanci tace"Tun jiya muke tsiya dashi Nidai nace ban yarda ki tare ba sai kin gama makaranta kamar kowacce ya haba..Ai wannan rashin adalci ne shima Maallam din bai Duba ba Gaskiya..Ni bazan yarda ba na Fadamai sai dai koma miye ya faru din..!
Amina tayi saurin cewa"A"a Mallam bazai taba kaini inda za"a cutar dani ba..Shi da Hajiya suma bangarena Jikina ne Mamanmu kamar yadda kike sona haka suke kaunata don Allah na Rokeki kada ki saka baki ran Aba ya baci don Allah..!
Mamanmu na kara matsan kwallah tace"Ni daman ban ce basa kaunarki ba..Bama ke ba Duka Ya"yanmu damu kanmu suna kaunarmu nace ne su Dubaki don Allah kin yi kankanta da Daukan wannan auran..!
Nidai in kina so nayi shuru kada nayi mgana koda Hajiya tazo Aba dinku ya kiraki ko yayi mgana ki Taimakeni ki Fadamai Bakisan wannan Tarewar da auran gabadaya in kuma kika kasa Fada ni zan Tubure nace ban yarda ba Duk da yace in nayi mgana zai yanke igiyar auranmu ban damu ba Zan iya yin komai Saboda ke Amina..!
Amina Sai kuka itama jin kalaman mamanmu Cikin kuka tace"Naji zan fada..Don Allah mamanmu kada kiyi mgana Ran Aba ya baci..na rasa yaya alokacin da bansan Dadinta awajena ba..Kema kuma bana so na rasaki..In kika tafi kikabar gidam nan ina zamu..?Wazai Rikemu..!?
Ni da Hamida zamu lalace mamanmu..!
Da Sauri ta Rumgume Amina Tana Mirmishin nasara kafin cikim karyewan murya take fadin"Bana so a Gurgunta miki Rayuwa ne Amina..!
Haka take fada tana jan majina karshenta dai Amina ce ta share hawayenta tana Cigaba da bama Mamanmu baki har tayi shuru kafin ta kalleta tana Fadin"Tashi kije Dakin ku..Abun karyawanku na Kitchen bari naje Nagani ko Jawad yagama Shirin Tafiya makaranta..!
Daga haka ta mike ta fice tana Dariyan Nasara duk karya ta Fadama Amina tun DAran jiya datayi mganar da Aba bata kara cemai komai ba Shima bai ce mata ba ita shegiya ce da zata bata goma ko Daya bata gyaru ba Saboda Amina ta Samu Sakin Farko ta Tabbata Sa"idu zai iya Sakinta Saboda mallam da Hajiya duk da ta samo kansa din ammh gwara ta Kiyaye in har Makircinta bai yi ba zatace ma Madina ta Kira malaminsu arufe bakin Hajiya da mallam din kan mganar Tarewar kowa ya Huta..!
Amina ma Dakinsu ta koma ta Iske Hamida da Hanne kozai kozAi ba Fara"a kallonsu tayi kafin tace"Miye haka kowacce ido kamar Nama..kunyi wani Figai figai kamar Kajin da aka Tsoma acikin Ruwan zafi..!?

Yake Kadai Hanne tayi mata batayi mgana ba Amina ta Cire Hijabin Jikinta tana Fadin"Mamanmu tace abun karyawan mu na Kitchen Hamida tashi ki Dauko mana..!
Hanne ta Dago daga kwancen Datake tana kallon Amina cikin mamakin kamar ba itace ta kwana kuka ba.
Cikin Dashewar murya tace"An fasa kai ki gidan ya danmallam din ne..?
Amina tace"A"a me kika gani..?
Hanne tace"Naga kin saki jikin ki ne..!
Amina tayi wani Mirmishi, Mirmisshin da ya bama su Hamida mamaki Kafin tace"Ya zan yi Hanne..?
In ba saki Jikina ba za"a fasa ne..?
Daga auran har Komai da komai da suka Faru bani na Tsarama kaina ba Allah ne..bakomai shima wannan din kaddartace..Abu Daya ne zai dameni zan Rabu daku..Bazan iya Rayuwa baku ba zamu daina zuwa makaranta tare zamu daina kwana tare zamu daina Fada zamu daina cin abinci tare zamu daina zuwa Hadda Tare zan koma ni kadai..Wlh in na Tuna haka sai naji kamar zan yi hauka..!
Kawai sai ta saka musu kuka bata so ta Fadamusu abunda taji haka kurum Taji bazata iya fadama kowa ba,suma kansu Abunda ke sakasu kuka kenan suka mike dukkansu suka Rumgumota suna ta kuka suma kukan kewarta suke Amina Bangaran jikinsu ne in Tayi nisa da su zasu shiga uku ne.
Suna wannan kukan sukaji Sallamar Hajiya shiyasa suka Tagaita Falon Aba mamanmu ta shigar da ita sun Dade suna mgana kafin su fito Aba fita yayi yayinda Hajiya ta kalli Mamanmu tana Fadin"Balaraba ina yaran nan suke ne..?
Daman Tun da tazo tana Dakinta Hankalinta yaki kwanciya balle dataga sun dade suna mgana da Aba su ka kuma gama ya fita bai ce mata komai ita fatan ta yasa Hajiya tana Rusa mganar tariyan ne
Shiyasa cikin Damuwa tace"Suna ciki Hajiya..Karki so ki ga yadda suka Tada Hankalinsu hamida da hanne..!
Hajiya tayi Dariyansu na manya ta wuce tana Fadin"Sakarci ne..ai ba Mutuwa zatayi ba..banda abunsu ai suna Tare da ita koda yaushe tunda tana kusa..!
Mamanmu ta Daskare tana Bin bayan Hajiya da kallo me take nufi..,?
Kasa shi ga Dakin tayi sai da taji Hajiya na kiranta sannan ta shiga Dakin taga Amina zaune gaban Hajiya Hamida da Hanne na gefe suna Sharan kwallah.
Cikin Dariya tace"Tayani Lallashin ya"yan nan naki balaraba sun tasani suna min kuka..!
Mamanmu tace"Nima Hajiya da zan samu mai lallashina ina so..Kukan ma ai na yi shi Hajiya..!
Hajiya tace"Balaraba hakuri zaku yi nasan zaku ji mganar Daga sama ko..?to me zamu jira..?,an gama mai Wahalar zaman me zatayi...
Zaman bai da

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login