Showing 177001 words to 180000 words out of 265571 words

Chapter 60 - TA FITA ZAKKA COMPLETE HAUSA NOVEL

11 Dec 2024

28892

gabansu ya fadi ganin Hawaye Kaca kaca a Fuskarta Hannun Jawaad ta Saki ko barayin bata kallah ba Ta nufi Dakin su Hanne tana jin ita da Hamida na Faman kiran sunanta suna tambayanta me ya faru take kuka ko Waigowa batayi ba a yanayin Datake Ciki ba kowa zai iya Fahintarta ta ba Tunda bata da Uwa a raye a Duniya to ta samu kadaicin da zata Zauna Tayi Tunanin makomar ta a wannan Duniyan da Rayuwar data ke cike da Tarin azzalumai maciya amana..!
Tana shiga Dakin ta Ture kofar bata ma iya karisawa Kan gadon ba ta Sulale nan saman Cafet a kofar Dakin Tana Dafe Saitin zuciyarta Daya Dunkule waje daya ga cikinta Daya Cure waje Daya yana murdamata Sosai da sosai Hawaye da majina Har da Miyau haka suke kara kaina akan Fuskar Amina batare data Damu Data Share su ba.

Achan Falo kuwa Hamida ta kalli Jawaad tana fadin"Wai me ya faru ne Amina ta shigo tana kuka..?
Shima ya girgizamata kai kafin yace"Bansani ba nima ina kwallo na ne tazo tana kuka taja Hannuna muka zo nan..!.
Hanne ta mike tana Fadin"Hamida muje mu gani..;
Tare suka Dumguma suka Nufi Dakin suna Tura kofa suka kusa cin karo da Amina atare suka saki Salati Hanne ta Duka gaban Amina tana Fadin"Amina meke Faruwa ne..?
Amina ta runtse ido sai wasu Hawayen ta Dafe saitin zuciyarta Dake mata Zafi bakinta yayi Nauyin da bazata iya mgana ba.
Hamida ta kalli Hanne Cikin wani yanayi kafin tace"Ko zaki je ki kira Hajiya a shashen Baba mallam ne..?
Hanne ta mike tana mai yarda da mganar Hamida da Sauri Amina ta Rike kasan Sikat dinta bata so ta Kira Hajiya domin in tazo bata san me Zata Fada mata ba, ta tabbata ita kanta ba Domin taji ta gani ba ko Duniya Zasu Taru su fadamata Bakaken Halayyar mamanmu bazata taba yarda ba shiyasa ta Dago Jajayen idanuwanta Dakyar tace"Kada ki kirata..!
Hanne tace"To kuma kina ta kuka..!
Amina ta Runtse ido kafin tace"Ba..bani da lafiya ne..!
Hamida tace"Kan ki ke ciwo..?
Daman tasan Amina da Raki ciwo kadan sai ta Fara kuka da Sauri Ta gyada kanta Hanne tace"To ki tashi kici abinci ki sha mgani sai ki kwanta..!.
Saboda su kyaleta yasa tace musu tasha mgani agida Muryanta a Dakushe Hamida ne tace Hanne ta Taya ta su taimaka ma Amina ta koma kan gado tunda bata da Lafiya haka suka taimaka mata ta hau kan gado ta Dunkule ta Runte ido kamar mai barci har Hamida ta Lallube kafarta da Bargo suka fice bayan sun turo mata Kofar sai da suka fita ta Bude idanuwanta Allah Sarki Hamida mai kyakyawan zuciya tunda Take da Hamida bata taba ganin wani sharrinta ba sai Alheri ya zata ji in ta ji Halin Mahaifiyarta..?
Kai Innalillahi Yaya ashe ashe kasheta sukayi Shiyasa ta kwanta Lafiya lau sai gawanta aka gani shin me yaya ta Tsare ma Mamanmu..?
Ta bar mata ragamar gidanta ta bar mata Ragamar duka ya"yan data Haifa ace ko don haka mamanmu bazata Raga mata ba..?
Tunda take bata taba ganin Aba yayi bambamci tsakanin Mamanmu da Yaya ba har tana Kwatantashi Cikin masu adalci Tsakanin matansa.
Ashe ashe alheri yana komawa Sharri ashe ashe haka Duniya ta gada..!
Sai yanzu ta Fahimci Bakin Zaren Ta Dade tana Tunanin da wa Anty Amarya take waya kwanaki tana ambaton sunanta da kokarin Hanata Tarewa a gidan ya Danmalam sai yau Sirrin Boye ya fito Filo ashe mamanmu da Anty Amarya Bakin su Daya..?
Ita tanayin komai Saboda Aba ne ita kuma Anty Amarya saboda Sakina ne..? Ita fa Haj.uwa dataji suna ambatkn sunanta ita me ta ke aikatawa..?! Sannan domin wa take yin abunda take yi har suke Tunanin in zata basu matsala su kawar da ita..?
Lalle Duniya ba abun yarda bace abunda ko a mafarki ko Finfinan India dana Hausa bata jiba ai ko a karance karancen datake yi bata taba Haduwa da makirci da mugunta irin wannan ba Shekaru Goma sha Shidda Mamanmu ta kwashe tana kassara Rayuwarta ko da da rana Daya bata taba bari ta rabu da Yaya tasan Dadi da Martaban uwa ba shekaru sha Shidda ta kwashe tana Gurgunta Rayuwarta sai alokacin abubuwa suka Dawo mata Daki Daki Tun Farko kovsau Daya mamanmu bata taba Zaunar da ita tayi mata Fada kan wani abu ba sai dai ta rika Fadin yarintace in ta girma Zata Daina Ammh ai Hamida bata mata Haka bama ita ba kaf ya"yanta tana Dorasu kan Hanyar mai kyau tun daga bangaran Tarbiya har bangaran Ayyukan gida da Sauraran abubuwa ashe da gangan ta Sangartata ta Shagwabata Duk cikin Lalata Rayuwarta ne bata sani ba Kaiconta ashe ashe duk wasu abubuwan datake yi ba yin kanta bane tasan wasu abubuwan na tadda Hali ammh wannan Rashin Tsoron da Zafin Zuciyar duk ba nata bane Mamanmu ne taso ta kassara Rayuwar ya Jafar sai abun ya Tsaya akanta ta Godema Allah da abun ya Tsaya kanta Domin daman karamin alhakin daka raina Watarana shi zai tsole maka ido.
Tafara Tunanin yadda ta rika turata sai taje ta ce ma Hajiya ko mallam bazata tare ba batasan Dannallam sai yanzu ta Fahimci komai wato tana Taya Anty Amarya ne kamar yadda ta Taimaka mata ta kashe musu uwa anya Balaraba zata ga Annabi kuwa..?
Idan ta Mutu kila kasa bazata taba karbanta ba ashe ashe bata son tarewarta da ya Danmallan ta Tabbata Auran ma Allah ne yaso da bazasu taba bari ba ta Tuna sanda take tusa mata ra"ayin tace ya saketa Tsoho ne bai dace da ita ba ta tuna yadda take Zaunar da ita tana Dukan ruwan cikinta in taje gidan Danmallan tayi Weekend ta Dawo tasha Turketa ta Tambayeta ko suna waya sai tace mata A"a data ga kuma kamar abun yayi musu yadda suke so ne ta fita Sabgarta ashe Duniyar ce ta Fara Samuwa ba shakka Taga Aba ya Rage damuwa da wasu al"muran sannan ko Jawad sai ya kwana wajen su a ashashen Hajiya Aba bai Damu ba abaya kuwa yana Dawowa sai ya nemi Jawaad inda ya Saka kafa nan yake sakawa shima sai da Mamanmu ta rabasu taji Dadi ashe ashe Sihiri ne ajikinta shiyasa take Fama da Zafin zuciya bata sani ba..!
Sai ta Tuna Aminu sanda yake Fadamata watarana ga Mamanmu din ammh har Abada bazata Shafe mata matsayin UWA BA..ta yarda kuma ta amince a wannan Ranar kewar Uwa ne ya Taso mata da tana Raye da a kan kafadarta zata kwanta tayi wannan kukan ammh ina Duk da Lokacinta ne yayi domin mamanmu bata isa ta yi Ajalin yaya ba tunda ita ba Allah bace ta sani Daman chan kwanakin da suka Rage mata a Duniya kenan

Mamanmu da izinin Lahi sai tayi mutuwar wulakanci sai tayi mutuwar kaskanci wannan Duniyar datake Fatan ta samu bazata taba cinta ba Har Abada tunda har tayi sakacin Datasan sirrinsu tayi alkawarin sai ta Daidaita Rayuwarsu daga ita har Anty Amarya kuma da yardan Allah zama da ya Danmallan yanzu ta fara Zama Daram Kuma Haihuwa da izinin Lahi indai Allah ke badawa sai ta Rokesa ya bata Ta Haifar masa dozin yan Bakinciki da mahasada sai dai su Fadi su mutu Allah Sarki bawan Allah yana chan yana aikinsa a nan an saka sa agaba Allah Sarki Hajiya da mallam kuna Zagaye da makirai da mugaye baku sani ba.
Ita ne nan zata zama sillar Tonuwar asirinsu.
An riga anyi walkiya ta gansu.
Sannan an Dade ana ruwa kasa tana Shanyewa..
Ita nan Amina Aminene ikon Allah badai ta mutum ba sai ta Allah kainuwan Dashen Allah indan Rana ta fito Tafin Hannu bai isa ya kareta ba..Daya bayan Daya sai sun tsinci abunda suka shuka wannan alkwarinta ne..!
Kukan da Amina bata samu tayi ba sai yanzu ya kwace mata sai da Filon Datake kwance akai ya jike da Hawaye kanta ciwo yake yi Idanuwanta sun mata nauyi ga Cikinta na murdamata Har da yunwa tana jin Hajiya ta shigo Dakin bayan ta Dawo daga Falon mallam sukace bata jin Dadi ta shigo ta Dubata ita kuma ta Tusa kanta cikin Hijabi tayi Luf kamar mai barci har ta fita tana fadin Ta samu barci.
Duk tana kwance taji Su Hamida sun shigo sun yi sallar mangariba sai alokacin Hajiya ta leko tana Fadin"Hamida ku tada Mamah mangariba tayi..!
Hamida ta mike ta isa wajen Amina tana tashinta kafarta tataba Taji Jikinta kamar wuta ta Dago tana Fadin"Zazzabi ya kamata jikinta Zafi..!
Hajiya ta kariso Dakin tana Fadin"Asshsha..Mamah Daure ki tashi kiyi sallah sai kici wani abu ki sha mgani..!
Dole Amina ta mike Hajiya sai da ta Tsorata da ta ga yadda idanuwanta suka koma Cikin wani yanayi tace"Amina meya faru kike kuka kinga idanuwanki yadda suka kumbura kuwa..?
Amina ta mike Zaune tana fadin"Hajiya Yaya na tuna..Sai na fara kuka sai kirjina ya fara ciwo da kaina sai Zazzabi ya kamani..!
Daganan kawai ta saki kuka Hajiya ta Dafa kanta Cikin Tsausaya tace"Addu"a zaki mata in kin Tuna ta kin ji ko mamah ba kuka ba..?
Kai ta gyada tana kara sharan Hawayen wasu na ambaliya ita ta mike ta kama Aminar da Jikinta ke Rawa ta kaita Tiolet ta barota ta Fito tana kallon su Hanne da Jikinsu yayi sanyi tace"Zo ki kar ban mata magani ke kuma Hamida shiga kitchen ki zubo mata abinci ga Jawaad ma chan afalo ki zubamai yaci kafin yayi barci.!
Da toh suka amsa mata ta fice suka bi bayanta Hamida tayi yarda Hajiya tace ta Zubama Jawad Jallop din Taliya da Miyar kifi ne ta Zubama Aminata kaimata ta iske tana Sallah a Zaune Hanne ma ta kawo mata mganin da Ruwa suka koma Falo suka barta kada su Dameta.
Tana Idar da sallah ta zauna sai kuka take yi ta rasa addu"an ma da zatayi kawai sai ta Daga Hannu tana rokar ma Mamanmu tabewa da bala"in Duniya kala kala tanayi tana kuka Kafin ta kife kanta ta cigaba Tana wajen aka kira isha"i daga Zaunen ta yi sallar ko abincin bata kallah ba sai da taji kamar Hajiya zata shigo sannan ta Jawo Filet din ta fara ci Turawa kawai take yi ko Rabi bata ci ba Cikinta ya Cuse zuciyarta ta fara tashi ta Nufi Bayi a guje sai amai sai da ta Amayar dashi Duka sannan ta koma gefe tana maida numfashi koiya Fitowa batayi ba sai da Hamida tazo ta fito da ita ta iske Hajiya da Hanne afalon abincin tace a Dauke a Hado mata Tea mai kauri to shi ta dan samu ta sha ya Zauna ta hada da panadol Hajiya ta fice zuwa shashen mallam ta Sanar dashi cikin wani yanayi yace Allah ya Sauwake in ba sauki gobe sai Hajiya ta kaita asibiti tun abunda ya Faru ne Dazu Mallan bai Saki ba har yanzu..!
Awannan Daran yadda Amina taga Rana haka taga Dare domin barci ko barawo bai Saceta ba ga kuncin zuciya ga Zazzabi Cikin Dare kaf Abunda ke Cikinta sai da ta amayar dashi kafin Safe Jikinta yayi zafi sai rawan sanyi take da Haduwar Hakora sallar asuba ma Dakyar ta iya yi tana neman Faduwa Hanne ta jira sai da Hajiya ta Dawo daga Shashen mallam ta Fada mata cewa tayi su sauya ma Amina Hijabi bari ta Fadama mallam ya ma Idi mgana yakai su asibiti.
Mallam na jin jikin Amina yayi zafi Hankalinsa ya tashi ya Kira Idi a waya yace yazo ya kai Hajiya asibiti ba Dadewa sai gashi Lokacin Hajiya har ta Shirya Amina ko Tafiya bata iya yi Saboda yadda Jikinta yayi zafi Hanne da Hamida suka riketa har Bakin mota ta shiga Suka Bita da fatan samun Sauki Cike da Tsausayi mallam ma Sai da ya Tsausayamata ganin yadda ta koma Cikin kwana Daya yace su Hajiya su yi gaba komai kenan ta Kirasa.
Kafin su tafi sai da Hajiya tace su Hanne su shirya su tafi makaranta Harda da Jawaad suka amsa mata da Toh suna masu Tsausayin Amina.
Suka koma Shashen Hajiya suka yi wanka suka karya suka yi shirin tafiya makaranta Harda Jawaad sai da suka fito ne suka ga Aba suka gaisa sai Lokacin ya rike Jaawad yana Fadin ya yi musu yaji shi da balaraba ko Mallam na wajen yace to yaga su Hamida sun dawo ina zai zauna in da ba kowa abunda mallam bai sani ba in Aba baya ga Jawaad bane yanzu mancewa ma yake yi dashi.
Hamida ta shiga gidansu ta gaida mamanmu ta sameta cikin kwalliya kamar wata yarinya ita abun ma sai ya bata mamaki sama sama suka gaisa ta shiga Dakinsu ta Dauki littafinta na Biology data manta Dashi bata ma samu Fadama Mamanmu Amina bata da lafiya ba Shidai Mallam ya sanar ma da Aba sai dai ba gida ya koma ba gidan gona ya wuce Shiyasa Mamanmu bata ji ba Sannan a matan mallam ba wacce ta Bude shashenta ma ballatana tasan abunda ke faruwa..!

General Hospital tace Idi ya kai su suna zuwa ta Kira Nasir a waya ta Fadamai yace bai riga ya shigo asibitin ba ammh gashi nan kan Hanya ba Dadewa sai gashi ya iso ya Iske har Hajiya ta yanki kati suna bin layi Tunda gidan mallam bai Dauki wani Family Doctor ba ba ruwansa da wannan,Duk da ba bangaran yara bane A sanshi a asibitin shi ya karbi katin su Hajiya ya shiga wajen Likita yamai bayani ganin Dr.Isa ne abokinsa ne yamai bayanin Hajiyarsu ne ta kawo kanwarsu ba Lafiya jin haka yace su shigo kawai.
Dole sai Nasir ne ya rike Amina Saboda tana mikewa jiri ya kwasheta ta kusa fadi Allah yasa yana kusa ya Tareta Hajiya bazata iya ba ita kadai
Ganin yadda suka shigo da ita a rirrike yasa Dr Isa yace su shimfidar da ita kan gadon dayake ganin marasa Lafiya nan Nasir ya Dorata shi kanshi ya ji Tsausayin Amina jikinta kamar wuta Saboda Zafin Zazzabi.
Likitan yazo ya Duba bayan ya cire mata Hijabin jikinta ya taba Temprature din jikinta ya gwale mata ido ya kuma Duba Tafin hannunta bayan ya kalleta na tsawon mintina goma kai ya girgiza kafin ya Dawo ya Zauna ya kalli hajiya da Nasir yana Fadin"Zamu dibi jininta za ayi Test..sannan akwai yunwa tare da ita zan kara mata drip da allurai wanda zasu taimaka mata ta Dawo Cikin hayyacinta..!
Ba musu Hajiya tace"Ayi abunda ya kamata likita in ma gado zaka bamu ba Damuwa..!
Yana Rubutu saman wata Takarda yace"A"a mama Ba gado bane zamu dai mu riketa na awa daya ko biyu zuwa uku mu saka mata Drip muyi mata allurai kafin Lokacin Sakamakon gwajin mu ya fito..!
Wata Nurse ya kira tazo yace ta Dibi Jinin Amina aka kai lap yana son abun da Sauri ne Amina duk Tsoron Alluranta bataji ba yau ko Ihun batayi ba tana gama Diba ta fice? shikuma Nasir Likita ya bashi Takardan Daya Rubuta allurai da Driip yaje phamarcy cikin asibiti ya siyo ya kawo mai nan da nan ya saka Handgold ya Hada allura biyu ya yi mata ta Jijiya Biyun kuma tana Cikin Drip din Amina ahalin Datake ciki kuka ma Har ta gaji da yi ashe sai kana da ma natsuwa kake jin zafin wani abu ita ko Zafin Alluran ma yau bata ji ba..
Kamar almara ba Dadewa Amina sai barci ganin haka yasa Nasir ya tafi bangaransa inda yake aiki yace in da wani abu Hajiya ta Kirasa waje ta fita Tana jira domin Dr.Isa ya cigaba da ganin mara sa Lafiya kamar yadda aka saba..!
Hajiya na babban Falo zaune tana jira sai ga Kiran mallam ta Dauka sukayi mgana tace m???? 
  
 !"#$%&'()*+,-./0123456789:;<=>?@ABCDEFGHIJKLMNOPQRSTUVWXYZ[\]^_`abcdefghijklmnopqrstuvwxyz{|}~?ai Amina na ciki ta samu barci yace su dan jira na wani Lokaci Da haka sukayi sallama Idi bai koma ba yana nan yana jiransu.
Awa Biyu da wani abu Hajiya ta kwashe Tana jira sannan wata Nurse tazo ta Kirata zuwa Office din Likita koda ta shiga har lokacin Amina barci take ammh Ruwan ya kare har an cire mata.
Kujera yanuna ma Hajiya yace ta zauna, ta Zauna tana Sauraransa wata Farar Takarda Doguwa ya mika mata Hajiya ta karba Tana Fadin"Likita wannan Takardan fa..?
Fadamin abunda ke faruwa kune yaran zamani yan Boko..!
Mirmishi yayi kafin yace"Amina Sa"idu yarki ce Hajiya ko..?
Hajiya ta Dagamai kai da Sauri kafin ya Cigaba da Fadin"Tana da aure ne..?
Hajiya taji gabanta ya fadi sai ta basar kafim tace"Eh likita..!
Ina fatan ba wata matsala ko..?
Da Sauri yace"Babu Mama..Takardan Dake hannunki Sakaamakon gwajin da muka ma Amina ne..Sakamako ya nuna mana tana Dauke da Ciki kimanin Wata Hudu da kwana goma..!
Hajiya sai taji kamar bata ji da kyau ba ta Zari ido kafin tace"bangane ba..Likita wani irin ciki..,?
Dr Isa yace"Ciki dai na Haihuwa mama .!
Hajiya taji jikinta ya Saki Cikin mamaki ta juya ta kalli Amina Dake Sharan barci kafin ta kalli Likitan tana Fadin"yanzu nan Likita Amina ciki gareta har na Tsawon wata Hudu da wani abu bamu taba ganin alamu ba..?
Dariya Dr.Isa yayi kafin yace"hakan yana Faruwa sosai Mama...naga shekarar ta 17 ajikin katinta ko..?
Hajiya ta gyada kai tana mamakin ikon Allah acikin ranta.
Likita ya Cigaba da fadin"ba abun mamaki bane in baku gane ba..Tana da karancin shekaru sannan Cikin nata irinsa ne Hausawaa ke cema Kurman ciki bai cika bayyana kansa yana karami ba sai ya kusa fitowa Duniya..Sannan in kun lura Cikin yabi Jikinta ne ya kuma yazo Lokacin ta na age din kuruciyarta ne sannan tana da Tsawo sai ya shanye shi ajikinta inbamu masana abun ba, ba lalle ku iya gane tana da ciki ba..!
Hajiya ta jinjina kai kafin tace"Ko fa Laulayi batayi ba Likita sai dai ta rika cin abinci sosai..da yawan barci..!
Dr ya gyada kai kafin yace"Ba lalle sai tayi ba ai kowani Ciki da nasa Salon mama..Ita nata nacin abinci ne da yawan barci kila ko zatayi Laulayin sai nan gaba kadan..!
Hajiya ta sake jinjina kai kafin tace"Sai jiya tayi ma amai sau Daya..!
Dariya wannan karon yayi kafin yace"Normal ne..Mama kila ma Daga yanzu Lokaci bayan Lokaci in taci abund bai karbi Cikin ba Zata iya yin amansa.!
Hajiya ta Damke Takardan Hannunta tana Fadin"Nagode likita yaushe Zamu tafi gida..?
Yace"Yanzu da zarar ta farka..alluran barci nayi mata yanzu zata saketa..!
Suna ma cikin mganar Amina ta Farka tana Kokarin tashi Hajiya ta

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login