Showing 117001 words to 120000 words out of 352722 words
kuma har sunyi bacci sabida kukan da sukayi.
Ita kuwa Ummi tana falo, saida taga dawowarsu sannan taje ta shiga ɗakinta dan yanzu ta dawo da zama a nan kenan ɗakin da Umaymah ke sauƙa in tazo.
Washe gari ranar asabar kuwa,
haka suka wuni gidan shiru ba daɗi gaba e kewar Umaymah ta hanasu jin daɗin gidan.
Ranar ne kuma duban forko na watan Ramadan.
Tunda magriba tayi, al'ummar musulmai keta cekinta labarin ganin wata.
Wannan ya tambayi wancan wancan ya tambayi waccan.
Jira kawai akeyi aji lbri ko gani.
Yayinda duk irin wannan rana duk inda yanki musulmai suke a faɗin duniya suna jimirin da tsumayin lbri.
A wasu wuraren har matasa maza da dattawan kanyi dandazon da fuskanta yamma dan ganin watan
Har dai akayi sallan magriba babu ƙaƙƙarfan lbrin ganin wata.
Bayan anyi sallan isha'i ne, Sarki Nuruddeen Lamiɗo kenan ya tara hakima shi a fada suna jiran ko akwai ta inda labari zai riskesu.
Kasan cewar ana yanayin damuna ne yasa ba ko ina keda yaƙinin ganin watarba.
Sheykh Jabeer kuwa, wanda ranar bai samu yayi salla a masallacin Masarautar Joɗa ba.
Sabida wata ƴar tafiyar da yayi, sai bayan Isha'i ya dawo.
Kai tsaye Side ɗinsa ya wuce.
Yana shiga falon wayarshi dake cikin al'jihunsa ta fara suwa a hankali.
Gefen Ummi ya iso tare dayi mata sallama.
cikin kula tace.
"Sai yanzu?".
Kai ya gyaɗa mata yana mai amsa wayar.
Sannu da hanya tace mishi.
Cikin sauƙe numfashin alamun gajiya yace.
"Yauwa Ummi sannu da aiki".
Sai kuma ya kara wayar akunnen shi cikin nitsuwa yace.
"Wa alaikassalam".
Ɗan jim yayi kana yace.
"Alhamdulillah".
ya ƙarshe mgnar yana shiga cikin falonshi.
Shatu kuwa dake gefen Ummi shiru tayi tare da binshi da ido.
A can falon shi kuwa zama yayi bisa kujera tare da fara zare al'kyabbar daka hannunshi, wayar na kunnenshi yake cewa.
"Eh Jadda Alhamdulillah rahotanni sun nuna cikin Ɓadamaya al'umma da yawa sunga watan Ramadan.
Kuma nima naga watan Ramadan da idona".
Cikin jin daɗi Jadda yace.
"Alhamdulillah, ko yanzu mun samu gamsassun hujjoji daga bakin salihan bayi,
Dan jihar Tsinako sarki Abudulfata da kanshi ma yaga watar ya sanarmin.
Hakama jihar Noki, Jaltarba, Magom, Shibb, da dai sauran jihohi mu na arewaci anga wata sosai tako ina.
Kana yanzu kuma munyi mgna da Sheykh Abdulkareem shima yace anga wata.
Mu nan jihar Leddi julɓe kusan kowa yaga wata."
gyara zamanshi yayi tare da cewa.
"To Alhamdulillah. Allah ya nuna mana ƙarshen sa lfy, yasa muribantu da watar al'farma Annabi da Alqur'ani".
Amin Amin Sarki musulmai Jalaluddin, yace.
Kana ya sallameshi.
Daga nan aka bada sanarwan anga wata, inda shi Sarki Jalaluddin ya kira manyan masarautun gargaji yana shaida musu.
Kana manema labarai duk sukayi dandazon zuwa, nan aka sanar tako ina musamman kafafen yaɗa labarai na yanar gizo.
Nan take ko ina ya ɗauka.
Suna zaune a falon suna cikin hira.
Sukaji wani irin ƙara mai firgitarwa da bada tsoro.
darararam-dam sautin ƙarar bindigar toka mai ƙarfin amo.
Wani irin tsalle Shatu tayi tare da motsowa jikin Ummi, tare da toshe kunnuwanta, sabida sake jin ƙaran.
Gaba ɗaya jikinta kerma da kerketa yakeyi,
Cikin tsoro take cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun, hasbunallahiwani'imanwakil!".
Da sauri Ummi ta riƙon hannunta datasa ta toshe kunnuwanta cikin ɗaga sauti take cewa.
"Shatu ba komaifa, kada ki razana bindigar sanarda ganin watane! Shaidar gobe zamu tashi da azumi".
Cikin tsinkewar zuciya tace zamo daga kan kujerar ta zauna a ƙasa kusa da sawun Ummi, wani irin duka ƙirjinta keyi didib didib, didib.
Murmushi Hibba tayi tare da cewa.
"Aunty Aysha tsoro haka".
Cikin yamutsa fuska tace.
"Ya kamata ku gayawa duk wani baƙo wannan bahugawar al'adar taku in ba hakaba wata rana tsoro zai kashe irina".
Sheykh da tun ihunta na forko yana bakin corridor yana kallon yadda take karkarwa,
wani irin murmushin muguntane ya tsubce mishi.
Sai kuma ya tsuke fuskarsa kamar bashi yayi gajeren murmushi ba, cikin faɗa yace.
"Nifa bana son sakarci sam bafa na son anamin ihu a ka da hargowa a gida".
Cikin tura baki ta bishi da ido.
Shi kuwa fita yayi yana murmushi a cikin zuciyarshi tare da magar zuci.
"Ga rashin ta ido ga tsoro, ga tsiwa da fitsara ga makirin karaya.
Ai da anyi ta sakin sautin bindigar har sai tayi fitsari a zani".
Da haka ya wuce ya nufi fada,
nan suka fara tattauna yadda lamuran zasu tafi.
Ummi kuwa murmushi tayi ganin irin kallon harara da Shatu ta raka Sheykh dashi.
Cikin murmushi tace.
"Taso ki zauna muyi mgna".
A hankali ta miƙa ta hau bisa kujerar da Ummi take ta zauna, Hibba kuwa, tuni ta nufi Side ɗin Aunty Juwairiyya.
Gyara zama Ummi tayi tana fuskantar ta da kyau,
Cikin nitsuwa tace.
"To Alhamdulillah kinga anga wata gobe zamu tashi da azumi in Allah ya kaimu, akwai ƙarin aiyuka a Side ɗin nan wanda ko da can baya ko Sheykh bayanan yana ajiye komai na buƙatar rayuwa akanyi girki a nan kamar akwai mace, sabida anan su Jalal, Jamil, Hashim Sulaiman Imran Affan in yana nan suke shan ruwa."
To yanzu bana Sheykh ba inda zaije sabida a jerin jadawalin malaman tabsir da ake turawa jihohi bana ba'a turashi ko inaba tunda ya girma ya fara tabsir sau ɗaya yayi azumi a nan shekarar da ciwon Jafar ya tsananta, to anane naga zahirin yadda yake gudanar da al'amuran rayuwarshi cikin Ramadan.
To bana ma. Anan cikin Ɓadamaya zaiyi tabsir ɗin shi.
To aiyukan mu sunada yawa.
Dole kisan yadda tsarin komai ke tafiya."
Cikin sauƙe numfashin ta gyara zama ta fuskanci Ummi da kyau kana a hankali tace.
"To".
Itama gyara zama tayi da kyau kana tace.
"Azumi goma sha biyar zaiyi a nan, ƙarishen 15 ɗin a ƙasa mai tsarki zaiyi su.
Ma'ana zai tafi Umrah.
Sannan yanada masallatai uku da yake tabsir a kullum.
Da safe misalin karfe sha ɗaya na safe zai tafi masallacin jumma'a na cikin kasuwa, a can zaiyi tabsir sai ƙarfe shabiyu saura mintuna goma zai taso.
Daga nan kafin ya iso masarautar Joɗa tafiyar mintuna goma ne.
sha biyu dai-dai, zai zauna tabsir masallacin Masarautar Joɗa.
Sai ƙarfe ɗaya na rana zai tashi.
Daga nan bazai dawo gidaba, sai anyi sallan azahar.
To ana idar da salla zai shigo, gida al'adar rayuwarsace tun yana yaro.
Zaiyi baccin awa ɗaya tsakanin azahar da la'asar.
Ƙarfe uku dai-dai na yamma zai tashi zaiyi wonka, ya canza shiga, kafin ya gama an kira salla.
Yana fitowa zai wuce masallacin Masarautar Joɗa, inda yake limanci ana idar da salla zai tafi masallacin jumma'ar dake jami'ar Joɗa. Inda zaiyi tabsir daga ƙarfe huɗu zuwa biyar na yamma zai taso.
Akan hanyar shi ta dawowa yana tsayuwa wurin mashigar laleko zai sayo kayan buɗa baki ƴaƴan itatuwa.
Yana dawowa zai ajiyesu.
Ya wuce Side ɗinsa, wonka zaiyi kana yasa sauƙaƙƙun kaya, ya dawo falonshi ko ya wuce cikin Garden acan zaiyi ta karatun al'ƙur'ani ko kuma wani lokacin ya ɗan konta ya huta.
Kafin lokacin shan ruwa, Ni kuma da hadimar da Gimbiya Aminatu ke bani duk Ramadan ta tayani aiki.
Tuni mun gama aikin buɗa baki. An shirya komai a dinning table, nasu Jalal kenan.
Suma kuma gab da magriba zasu zo.
Shi ma zai fito yakan zauna tsakiyar Jalal da Jamil ko kuma tsakiyar Jalal da Jafar.
Baya cin abu mai nauyi iya karshi dabino da inabi da tuppa, sai ruwan zam-zam wanda dashi yakeyin buɗa baki.
Daga nan zai wuce masallacin Masarautar Joɗa wani lokacin zai fita dasu wani lokacin zai rigasu fita.
Ana shirya mishi abincinsa na musamman a ajiye mishi a dinning table ɗin dake can falonshi a Foodflaks ɗin shi na musamman, wani lokacin Gimbiya Aminatu ke aiko mishi.
In ya fita bazai dawoba sai anyi sallan isha'i Dana asham.
Amman su Jalal su zasu dawo suci abinci kafin isha'i sai su koma masallacin.
Idan ya tashi daga Masallacin kai tsaye zai wuce.
Gidan radiyo ABC Ɓadamaya, inda yake gabatar da shirin.
"Fatawa. Za'a ayi mishi tambaya kan Ramadan dama sauran abinda ya shafi addini yana amsawa, wasu kan tura tambayoyin wasu kuma kira sukeyi a da number da ga suke badawa, suyi tambaya ya bada amsa.
Ƙarfe takwas da rabi ake fara shirin tara dai-dai ake gamawa.
Tara da mintuna ashirin yake isowa gida".
Ɗan tsagaitawa tayi ta kalli Shatu dake cewa.
"Tab agogo sarkin aiki to shi baya gajiya ne, ga azumi ga zirga-zirga ga kuma duk inda yaje dole ba shiru zaiba mgna zaiyi ai ƙishi zai mishi illa".
Murmushi tayi tare da cewa.
"To ai in yaje gidan radiyo tarba ta musamman akeyi mishi, sai dai shi ba ko ina yake cin abinci ba tunma yana yaro.
Ko a gida nan ba abincin kowa yake ciba.
To shiyasa tara da rabin nan zai dawo a gajiye cikin yunwa,
to nan zaici abinci sosai.
Kana yayi wonka zuwa sha ɗaya dai yayi bacci.
To ƙarfe biyu kuma zai tashi, wani lokacin ma biyu bayayi zai tashi yayi ta nafilfilinshi da karatun Alqur'ani.
Daga nan kuma baya komawa bacci.
Har ayi sahur ayi sallan asuba.
In ya dawo yayi Azkar, to nanne yake samun yayi bacci mai tsawo dan tun bakwai da rabi ko takwas na safen zaiyi bacci sai goma zai tashi ya fara shirin tafiya masallacin jumma'a na kasuwa."
Kallonta ta ɗan yi tare da cewa.
"Kin gane lokutan da yake aiki Dana hutuwa dana bacci ko dana cin abinci ko?".
Cikin murmushi tace na gane.
"Da safe zai sha bacci son ranshi, daga takwas zuwa goma kafin ya tashi ya shirya.
Yaje masalacin jumma'a na kasuwa sha ɗaya tayi yayi tabsir ɗin awa ɗaya, daga nan ya dawo masallacin Masarautar Joɗa,
shabiyu ya fara tabsir sai ƙarfe ɗaya ya gama, ayi salla ya dawo.
Ya sake shan baccin awa ɗaya.
Kafin kuma ayi la'asar ya tafi masallacin Joɗa state University. Yaje yayi tabsir in ya dawo, kuma ya lokacin hutawane har magriba.
Daga nan kuma ayi buɗa baki a wuce masallacin daga can a wuce ABC.
Sai tara a dawo.
To yaseen wataran yunwa zata kadashi a hanya, ƙattin rigunan nan da yake sawa sune zasu jashi su kaishi ƙasa.
To ma wai Ummi to yaushe yake zuwa aiki kuma?".
Murmushi tayi tare da cewa.
"To in baya garin an turashi wani state ɗin yana zuwa aikin ne?".
Kai ta girgiza alamun a a.
Cikin murmushin Ummi tace.
"Shiyasa ko yana nan in dai a Ramadan ne baida lokacin zuwa Valli Hospital, bare Genaral Hospital ko kuma Asibitin jami'ar Ɓadamaya.
Shine dalilinshi na ƙin yin aiki a asibitin gwamnati sai ƙarshen sati-sati yake zuwa sau ɗaya, duk wanda zai duba kyautane aiki".
Naɗa hannunta tayi tare da cewa.
"Batun yunwa ta kadashi kuma, yanzu aikin kine, kula da abinda zaici".
Taɓe baki tayi tare da cewa.
"To shi wannan da tsarabe-tsaraben falsafa nasan irin abinda zai cine ma.
Mutun fuska a haɗe kullum kamar mai damuwar rashin jigo".
Miƙewa Ummi tayi tare da cewa.
"To kika sani ko hakanne.
Kuma ai gani duk abinda kike son sani a kanshi tambayeni.
Abincin da yafiso kuma yafi son ganyayyaki, fruits and vegetables sai kuma kayan ruwa, kana yana son nama da kifi in an mishi irin sarrafawar da yakeso.
Sannan yana son abincin gargajiya wasu lokutan musamman a wurin yin sahur.
Kai ta jinjina tare da cewa.
"Uhumm lallai kam, wannan ai yafi Lamiɗo ma iya ƙasaita".
Dariya tayi tare da cewa.
Zo muje store kiga kayayyakin da yasa aka kawo ɗazu."
To tace tare da miƙewa tabi bayanta.
Suna shiga kitchen ɗin suka ɗan haura suka taka steps ɗin da zai sadasu da ƙofar store wanda wani ƙaton freezer ke konce a wurin sai ma dai daicin Fridge.
Hannu Ummi tasa ta buɗe freezer'n.
Motsowa tayi tare da zaro ido ganin yadda aka cika freezer'n maƙil dasu Kabej Karas kokumba green beans, masu kyau sabbi.
Ɗaya sashin kuma nama ne jibge sai kifi a gefe,
Sai ɗaya Fridge ɗin kuma cike yake da ababen sha na ya'yan itatuwa dana kwalba.
Rufewa tayi kana ta buɗe mata drower'n kitchen cabinets ɗin.
Kiret-kiret ɗin kwaine kusa goma suke jere a wurin ɗaya gefen kuma katon ɗin manyan gongonayen madara da millo ne.
Sai katon ɗin sugar irin mai ƴaƴan nan. Sai katon ɗin Lipton. Da ganyen na'ana. Sai can gefe kuma su maggine da sauran kayan ɗanɗano.
dasu kanan fari citta da dai sauransu.
Cikin yin hamma tace.
"Ummi duk yaushe aka kawosu?".
Juyawa tayi suka nufi cikin cikin store tace.
"Ɗazu da yamma kina bacci ya dawo, suda Jalal da Jamil".
Kai ta gyaɗa tare da bin bayan Ummi. store ɗin cike yake da kayan masarufi na buƙatar rayuwa.
Danginsu shinkafa, gero, waken suya, wake ƙosai dasu alale, sugar katon-katon na taliyar manya data yara, da dai sauransu.
Sai kuma doya da dankali dake jibge a gefe, kana sai al'basa da sauransu.
Fitowa sukayi kana suka dawo kitchen.
tukunya Ummi ta ɗaura tare da ɗebo nama tazo ta wonke sabida an yanka wasu dai-dai misalin na miya, wasu kuma anyisu dogo-dogon yanka.
a tukunyar ta zuba shi, kana ta ɗauko al'basa mai girma ta yayyanka a ciki.
Sannan tasa tafarnuwa kaɗan kana tasa garin citta da kanamfari.
Tare da maggi da kori da sauran kayan ɗan-ɗano.
Kana ta kunna Gas ɗin ta ɗaura tukunyar,
ɗanyen kuɓewa ta ɗebo ta miƙawa Shatu tare da cewa.
"Wonke ki yanka min shi".
To tace tare da amsa ta wonke kana ta fara yankawa, ita kuma Ummi al'basa da tattasai da tatuhu kaɗan ta ɗiba ta wonkesu kana ta markaɗesu dai-dai yadda takeso.
Zuwa lokacin kuma gaba ɗaya kitchen ɗin dama Side ɗin gaba ɗaya ya cika da ƙamshin tafashen naman.
Juyeshi tayi a wani kwano.
Kana tasa mai kaɗan tasa manja kaɗan. Tare da watsa jajjagen kayan miyar,
ta soyasu. Kana tasa naman da sauran ruwan tafashen.
ta kuma ɗauko bandan kifin tarwaɗa bandanshi, ta gyara ta wonƙeshi da ruwan ɗumi.
ta watsa a ciki. Sannan tasa ɗan dakekken yajin daddawa kaɗan."
sannan ta rufe tukunyar.
ta amshi kuɓewar tana ƙarisa yankan. Tukunyar data ɗaura ruwan tuwo ta ɗan kalla ganin yana tafasane tace.
"Gacan garin semo na tankaɗeshi ɗibi kiyi mana talge."
To tace tare da juyawa ta ɗebo tayi talgen.
Ita kuwa kuɓewar ta saka, kana ta tsalli ɗan toka ta saka.
Bayan wasu yan daƙiƙu miyar tayi lugub tayi kyau tayi kalar kore mai kyau. sabke tukunyar tayi kana tasa,
man shanu a ciki.
Sannan ta meda tukunyar gefe.
Tuwon ta tuƙa ya ɗan turara kafin ta kwasheshi tana yin mal'mala tana sawa a leda.
Saida ta cika wani madaidaicin Foodflaks mai ɗan girma.
Kana ta ɗauka ruwan zafi.
Ta tafasa tea ta ɗura a flaks tare da tarfa kanumfari da citta sai na'am.
Sannan ta rufe, ta kimtsa komai a kitchen ɗin.
Ganin Shatu nata Hamma ne tace.
"Jeki kwanta tunda mun gama aikin. Sai kuma da asuba."
Cikin alamun bacci tace.
"To Ummi saida safe".
Ta fita tana haɗiye minyau dan ƙamshin da miyar keyi.
A falo taci karo da Hibba Aunty Juwairiyya ta rakota, da Foodflaks a hannunsu alamun abincin sahur ne a ciki.
Cikin baccin da takeji tace.
"Mun yi girki ma, Aunty Juwairiyya".
Kai Juwairiyya ta ɗan gyaɗa tare da cewa.
"A lallai kam sannu da aiki".
Ta ƙarishe mgnar tana ajiye kulolin bisa dinning table.
Ita kuwa Shatu harara ta watsawa kulolin tare da wucewa tayi ciki.
Hibba ce ta biyo bayanta bayan tayiwa Aunty Juwairiyya Saida safe.
Har sun shiga Ummi ta kira wosu.
Falo suka dawo duk suna hamma alamun bacci, ganin Hamma Jabeer na zaune ne, gasu Jalal gaba ɗaya yasa suma suka ƙarasu cikin falon.
Gyara zanshi yayi tare da kallon Hibba da Aysha da duk alamun bacci ya cikasu, cikin sakekkiyar murya yace.
"T....!
Uhummm Ramadan da daɗi, Ya Allah ka nuna mana ka kaimu watan lfy ka nuna mana ƙarshensa lfy ka maimata mana.
Rayuwar Masarautar Joɗa a Ramadan yanada tsari da masifar daɗi da burge duk musulmi.
Kabcen Shatu da Sheykh a kwanakin Ramadan da bikin salla yana sani murmushi da shauƙi.😘🥰🤝🏻
By
GARKUWAN FULANI
"To Alhamdulillah. Allah ya kawomu watan Ramadan, wata mai tarin al'farma da al'barkatu da tarin ni'imomi. Mutane da dama Allah bai basu wannan damarba, da yawa sun rasu.
Wasu kuma basu da lfy, basu san me sukeyi ba ko a ina suke, bare su ribaci wannan dama da Allah ya bamu.
An ga wata wanda haka keda tabbacin gobe zamu tashi da azumi.
Duk kuyi niya, ɗaukar azumi talatin ko talatin ba ɗaya."
Sai ya kuma ya ɗan tsagaita tare da kallonsu Jalal da Jamil cikin sanyi yace.
"Dan Allah Jalal Jamil ku nitsu kunsan halin da muke ciki. Kun san matsalar rayuwarmu kunsan damuwarmu, wannan dama ce da zamu yi amfani da ita wurin tsananta addu'o'in ba dare ba rana.
In sha Allah, Wata rana komai zai dai-dai-ta domin Allahu sami'uddu'a ne.
Jamil kaji tsoron Allah ka ribaci wannan watar, ka raba kanka da zuwa club, ka yayewa kanka masifar nacin liƙewa mata da waya."
Juyowa yayi ya ɗan kalli Jalal kana yaci gaba da cewa.
"Jalal yawon bin yan iska da wani shegen shiga mara kan gado ba tsarine na Musulmin ƙwarai ba.
Aunty Juwairiyya Hibba Ummi Ke uwar bacci".
Ya ƙarishe mgnar da kallon gefenda Shatu da take zaune tana ɗan lullumshe ido,
da sauri ta waresu don a sama taji muryar tasa. Baki ta tura tare da sunkuyar da kanta, shi kuma jenye idonshi yayi daga gefen da take cikin ɗan ɗaga sauti yace.
"Watan Ramadan ya bambanta da sauran watanni.
Domin a cikin watanne daren laylatul Ƙadir yake, kuma a cikin watanne Allah ya sauƙe al'ƙur'ani mai girma.
Kana a cikin watar akwai ranakun da malamai sukeyi hasashen a daren laylatul Ƙadir yake, Daren 21, 23, 25, 27, 29. Sai dai ba'a tabbatar, da sahihin rana ɗaya tsayeyye ba ƙauli mafi rinjaye shine ranar 27.
Abi mafi kyau shine kada mutun ya sake koda dare ɗaya na Ramadan ya wuceshi.
Mu raya dararen da ibada da ambaton Allah, wajibine mutum ya tsare bakinsa, da munanan zantuka walau a baki walau a rubuce a social media,
Domin mu ribanci watar da ambaton Allah da samun ruɓanyar lada, wannan abubuwane da kullum nake gaya muku su, sai dai aiki dasu ya gagareku."
Kusan haɗa baki sukayi wurin cewa.
"In Sha Allah zamuyi ƙoƙarin kiyayewa".
"Allah yasa yace, tare da sallanmansu duk suka fita sai Ya Jafar da Ummi.
Ganin yadda Hibba keta zuba hamma ne ya sashi cewa.
"Muhibbat tashi
Kije ki kwanta".
Kusan a tare ta mike ita da Shatu.
da sauri yace.
"Banda ke". Cikin bacci ta turo baki tare da cewa.
"Ayyah dan Allah fa".
Murmushi Ya Jafar yayi tare da zuba mata ido.
Wanda koda baya mgna ana iya gano yadda yake sonta a ranshi, so kuma irin son da yakeyiwa su Hibba.
Ummi ce ta ɗan kalleta tare da cewa.
"A barta tai bacci aiki mukeyi tun ɗazu".
Shiru bai kulasuba, ganin haka ita kuma tabi bayan Hibba.
A zatonta bai saniba, har sunje bakin ƙofar taji yace.
"Saura ki binƙire kiyi ta bacci, kada ki tashi ki raya daren. Sai gari ya waye ki buwayi mutane da ife-ife da rashin kunya".
Ya ƙarishe mgnar cikin jin haushinta tare da Binta da kallon fitinenneyar yarinya.
Ganin Ya Jafar ya miƙa ya juya zai fitane yasa yayi saurin.
Bin bayanshi ya