Showing 9001 words to 12000 words out of 352722 words

Chapter 4 - GARKUWAAA COMPLTE HAUSA NOVEL

17 Oct 2024

30703

mai martaba sarkin Nuruddeen Aliyu Bubayero, shine sashin GARKUWAN FULANI, wato Sheykh Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero.
Sai kuma na gefen daman Sheykh Jabeer shi kuma na Jafar Habibullah Nuruddeen Bubayero ne, da matarsa Juwairiyya.
Sai na gefen hagunshi kuma na Jalal, ne na kusa da Jalal da kuma na Jamil ne sai dai Jamil yafi zama a sashin Jalal duk da korarshi da yakeyi wasu lokutan kuma lokacin kuma yana sashin Sheykh.
Sai sashin baya kuma sashin Affan.

Daga gefen hagun Masarautar kuwa wasu tamfatsa-tamfatsan plat ne masu girma har guda huɗu, sai kuma wani babban bene dake tsakiyarsu mai tarin girma wanda nanne sashin babban ɗan sarki Habibullah da matanshi.

Sai ta gefenshi can kuma wasu manyan part- part ne kimanin guda biyar wanda duk ƙanne shi ne da iyalansu da ƙananan yaransu a ciki.
Yayinda duk manyan yaransu kuwa kowa nada part ɗin shi a gefen da part ɗin Sheykh yake a ƙalla dai Part ɗin cikin masarautar Joɗa sun kai hamsin da biyar.

Can wurin mashigar kuma wasu ƴan saffan-saffan part-part ne wanda bisa dukkan alamu duka na bayine da hadimai da matansu.

Tsayuwa fasalta cikin ko wanne sashi na masarautar bazai yiwuba, sai a hankali.

Sai dai ko wanne part yanada Garden mai ɗan girma, wannane yasa gaba ɗaya masarautar ke zagaye da korayen fulawowi da bishiyoyi masu kyau.
Fentin masarautar gaba ɗaya iri ɗaya ne, Sky blue and white, mai ɗan karen kyau, a mahaɗar sashukan kuwa wani irin tamfatsetsen sweeminpool mai girma wanda ruwansa ke sky blue.
Can bayan sashin Mai martaba da Sheykh kuwa wani ƙaton filine mai cike da dawakai, da sashin mai rainonsu, gefe ɗaya kuma raƙuma da shanaye ne da makiyaya su, kana ga tumaki, a gefen Sheykh Jabeer ne kuwa akayi wani ɗan madai-daicin gidan zu ta bayan ɗakunan shi wanda yake da tarin tsuntsaye kamarsu, Ɗawisu, jimina, mikiya, agwagin ruwa, tolo-tolo, tattabaru, kana sai Aku. Da sauran tsuntsaye carki, kurciya, hasbiya, caccagi da-dai sauransu, shiyasa sashinsa ya kasance namusamman, don Garden Park ɗin ciki yafi na sauran part ɗin duka girma da kyau, sabida shine asalin Garden ɗin tarihin masarautar Joɗa.
Daga nan mashigar masarautar kuwa akwai wani babban filin sukuwa mai girma.

Daga masallacin Masarautar kuwa akwai miƙeƙƙiyar hanya har cikin masarautar wanda za'a iso gab da fada sannan kowa zai samu hanyar sashinsa.

A tsakiyar cikin masarautar ma kuwa akwai wani masallaci mai girma.

Wannan kenan sai a hankali zaku san mutanen masarautar da sunayensu halayensu dama nasabarsa da danƙantarsu da manufarsu.

A hankali Sarki Nuruddeen da Sheykh Jabeer suke takawa.
Suna shiga cikin gidan waɗannan fadawan suka tsaya a bakin Gate ɗin.

Kana wanda suka samu a wurin suka miƙe da azama wani dogon carpet mai azabar kyau da taushi, ɗaya daga cikin fadawan ya zo ya ajiye gabansu kana ya rinƙa yin baya-baya yana worwore musu carpet ɗin.
A hankali Sarki Nuruddeen Bubayero Joɗa yasa hannunshi ya kamo hannun kekyawan matashin jikan nashi da kab cikin jikokinshi ya fita da ban, hannunshi yake murzawa cikin nasa hannun a hankali a hankali.
kana suna tafiya a hankali, cikin takun sarauta,
Gefen mai martaba Nuruddee bayine da dogarai a ƙallah sun kai Ashirin da biyar, gefen Sheyk Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero kuwa,
Ƴan saffan-saffan fadawane da basu kaishi shekaruba, a ƙalla sun kai goma.
Wanda wannan tsarinsa ne yace bazai iya ganin sa'an mahaifinshi ba ko sa'an Ya Jafar ɗinshi ba suna mishi bauta Babban Yayansu Jafar Habibullah Nuruddeen Bubayero suke kira Yah Jafar.
Kanshi ya ɗan murza ya juya a hankali da gefen ido ya kalli Kakan nashi dake magana cikin yin ƙasa da murya dan ko sarkin dogaren dake gefenshi baiji me yake cewa ba.
"Sheykh yaushe ne tafiyar taku?".
Siraran kyawan Idonshi ya lumshi a hankali ya kuma buɗesu tare da rausayar da kanshi.
Maimartaba bai damu da jiran amsar tasaba yaci gaba da cewa.
"Munyi Magana da Aminina Sarki Jalaluddin yace min Kakarka UmmuKulsum tace tafiyar taku ta ƙara toko?".
Shiru ya ɗanyi har saida sukayi taku uku zuwa biyar kana ya gyaɗa mishi kanshi kai a hankali irin gyaɗa kai na kamala".
Dai-dai lokacin kuma suka iso dab ƙofar mashigar sashin Maimartaba, wanda dama duk ran jumma'a daga shabiyu yake tashi zaman fada,
sanin hutawa yake a irin wannan lokacin ne ya sashi ɗan sake hannun Sheykh Jabeer tare da cewa.
"Sirranta komai a rai yanada wuya, amman kai baya maka wuya, ya zama kamar jininki, akwai tauraro na musamman a goshinka, wanda nake fatan watan wata rana ya haska zuƙatan ahlinka dama talakawan da zaka mulka".

Jin kakan nashi ya sake hannunshi da kalaman da yake jero mishine yasa ya ɗan kalleshi a hankali ya kuma sunkuyar da kanshi.
Sai ya kuma ɗan kalli Sarkin tare dayin mgna.
"Mulki yana da nauyi mai girmi Ni kuwa baya cikin tsarin jadawalin ababen buƙata ko sha'awa a rayuwata,".
Murmushi Lamiɗo yayi tare da cewa.
"Ba sai lallai abinda mutun keso ke samu ba, bakuma dole ka rasa abinda baka soba".
Ganin kakan nashi yaci gaba da tafiya ne yasa shima ya yaci gaba da tafiya.

Inda fadawanshi ke biye dashi a baya.

Yayinda fadawan Maimartaba kuwa suka tsaya a bakin sashin sa.

Sunyi tafiya mai nisa kaɗan kafin suka ratso ta gaban sashinsu mai azabar girma da kyau sashine mai ɗauke da part-part masu tarin yawa da girma wanda tsakanin ko wannensu da ƴar tazara sosaima.

A hankali ya ɗago hannunshi daga cikin babbar rigarsa da zazzafar al'kebbarsa ta rufe,
ɗan ɗaga musu hannunshi yayi alamun su tsaya daga nan.
Cikin abinda bai gaza 18 second ba duk suka rusuna ba tare da sun ƙara koda taku ɗaɗɗaya ba, kusan a tare suke cewa.
"Takarwarka lafiya ɗan Baban yaya Habibullah jikin Sarki Nuruddeen, jika ga sarki musulmai Jalaluddin".
A hankali ya kuma ɗaga musu hannunshi alamun ya isa haka, dan shi dai Allah ya sani har ranshi baya jin daɗi da son wannan kirare-kiraren dan yayi imani da Allah zasu iya sawa ɗan adam ɗagawa da jin kanshi shi wani abune, zasu iya sa mutun yaji kansa a matsayin wani sarki mai iko bayan kuma babu wani Sarki sai Allah.

Yana tsoron ɗagawa ta samu mazauni a zuciyarshi, sam baya son wannan kirare-kiraren na zamanin jahiliyya ina dalili kana mutum ɗan Adam mai daraja azo ana wani ce maka toron giwa ko tozon raƙumi ko dokin ƙarfe yaya Allah ya karramaka yayika ɗan Adam ka bari na ƙasa da kai suna suffantaka da dabbobi.
A hankali yace.
"Ya isa, duk kuje kowa yayi uzurin gabansa in inada buƙatar ku zan nemeku".
Shiru sukayi tare da baje manyan rigunansu suka zauna a inda ya dakatar da suɗin.
Kana sukace.
"An gama".
Shi kuwa a hankali yake taku cikin shigarsa da tafi kama data limamen harami.

A hankali yake taku, har ya iso bakin ƙofar shiga side ɗinsa inda a nan dogari mai tsare mashigar sashinsa sarkin ƙofarsa ke tsaye.
Tuni Sarkin ƙofa ya miƙe yasa hannu zai buɗe mishi ƙofar kenan sai ya kuma ɗan rusunar da kanshi,
Ganin Jamil ya rigashi kai hannunshi ya buɗe ƙofar cikin salonsa na raha ya nunawa Hamman nashi ƙofar tare da cewa.
"Sheykh Dr Malam Hamma Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero Joɗa GARKUWA barka da yamma".
Kanshi ya kauda daga kallon ƙanni nashi, sannan ya kutsa kai ciki,
da sauri shima Jamil ya mara mishi baya,
Cikin wani haɗeɗɗen corridor mai fitinenne ƙamshi da azabebben sanyi suke tafiya a hankali.

Tafiya kaɗan sukayi sai gasu cikin wani tamfatsen falo na al'farma da more rayuwa,
ɗaya daga cikin lumtsuma-lumtsuman kujerun kilisai na manyan sarakunan dake falon ya zauna a hankali.

Ido ya ɗago ya watsa ƙanin nashi su, cikin sauri Jamil yayi ƙasa da kanshi tare da cewa.
"Na tuba Hamma kayi magana ina tsoron hukunci da idanunka gwara kamin duka kon ka haɗani da wannan saggamemen na bakin ƙofar kan nan ya dakani kawai in huta".
Kanshi ya kawar Cikin harshen larabci yace.
"Ban gankaba a masallaci".
Da sauri ya durƙuso gaban Hamman nashi cikin yin wuƙi-wuƙi da idanu cikin sanyi yace.
"Ana Aspet ya Akhi, a matsallacin ƙofar gidansu, Khadija nai sallan jumma'ar".
Kanshi ya gyaɗa kana ya kauda kanshi ya fuskanci wani katon majigi dake liƙe a jikin ginin yana fuskarta kujerar da yake zaune a kai.
Majigine dake ɗauke da full Qura'an, a hankali yake karatun cikin sassanyan murya.
Ganin hakane yasa Jamil ɗan rusuna duk da yasan ba amsa zai samuba cikin sanyi yace.
"Hajia Mama tana son ganinka".
Kanshi kawai ya gyaɗa yaci gaba da karatun shi.
Ganin hakan yasa Jamil ya juya ya fita. Shikuwa Sheykh yaci gaba da karatunshi, kusan awa ɗaya kana ya shiga Bedroom.

Shine bai fitoba sai lokacin da sallan la'asar ta gabato, jin an kira sallane, yasa ya shiga ya sabunta al'wala kana ya fito ba kowa a wurin sun watse kemar yadda ya umsrcesu.
Sai can bakin mafita ya samu mutun huɗu, yana tafe fadawanshi na biye dashi wanda suma sunyi al'walan.

Jamil kuwa daga sashin Hajia Mama ya fito da nufin zaije side ɗinsu yayi al'wala.

A harabar gidan yayi kiciɓis da abokin tagwaicinsa wato Jalal, cikin sanyi ya kalli yadda Jalal ke zagaye da fadawa yana tafiya da yanayinsa da muddin zaka yanke mishi hukunci da ganin zahiri zakace cikekken ɗan iskane, sai dai a baɗinin ba haka abin yakeba.

Kekyawa ne shima dan shi yana ɗibin kamanni da Hamma Jabeer ɗin nasu sosai saɓanin Jamil da yafi kama da Babban yayansu, Barrister Jafar Habibullah Nuruddeen Bubayero.

Tafiya yake cikin shigar tsamari zamani, wondon a saɓule har kana iya hango boxes ɗinshi, kana ga wani irin kafirin aski da yayi mai ɗaukar hankali.
sam a rayuwarsa shi baya ta'ammali da manyan kaya,
Baya tsoro ko shayin ko shakkar kowa a duniya sai Hammansun kaɗai.
tafe yake bayinshi na biye dashi a baya, da wasu kolabe a hannunsu, cikin tsare fuska Jamil yace.
"Kai ku tsaya, kolaben menene wannan a hannunku?".
Juyowa yayi a zafafe cikin halin faɗa yace.
"Kwalaben Giyane ko kanada maganne Akukkuturu?."
Da azaban ƙarfi da tsoro Jamil ya zazzaro ido cikin ɗaga murya yace.
"Kwala ben giya a gidannan Jalal kasan abinda kake cewa kuwa? Kwalaben giya a Masarautar Joɗa".
Ya juyo da masifa kenan yayi arba da Hamman nasu,
shiru yayi tare da yin ƙasa da kanshi, jiki a mace.

Shi kuwa Sheykh Jabeer idanu ya zuba mishi na wasu yan daƙiƙu kana ya juya ya nufi hanyar da zata sadashi da ƙofar tafiya masallacin Masarautar tasu ba tare fitar nan bisa dressing mirror suka ajiyesu kana suka juya suka fita.

Shi kuwa al'wala yayi ya nufi masallacin.


Ƙarfe tara dai-dai na dare. Sheykh Jabeer, ne zaune a bisa wani tattausan carpet mai azabar taushi,
Wata Hamshaƙiyar Gimbiyace mai cikan iko da muƙami, mulki, iko, cikin wani irin kallo mai cike da kulawa tasa hannu ta ɗauki ɗaya daga cikin nonon inabi dake cikin wani kekyawan tray dake gabanta miƙa mishi tayi tare da cewa
"Jabeer Yaushene tafiyar taku?."
Tankwashe kanshi yayi bisa kafaɗunshi kana a hankali ya ɗan kalleta tare da motsa laɓɓanshi a hankali yace.
"jibi".
ya faɗi mgnar a gajarce, gyara kishingiɗarta tayi bisa kilisan tum-tum dake gefenta,
Cikin kulawa tace.
"Da Umaymah zakuje ne?".
Kanshi ya jujjuya mata alamun a a.
Kanta ta rausayar cikin ƙasaita tace.
"Naga kamar bacci kakeji Saida safe".
Kanshi ya gyaɗa kana cikin girmamawa yace.
"Allah ya bamu al'khairi".
Amin tace, shi kuwa daga nan ya fita ya tafi.

Koda ya koma sashinsa. A falo bakin ƙofar ya samu Jakadiya, tana ganinshi ta ɗan rusuna duk da tasan yana hanata hakan a hankali tace.
"Akarmakallahu, Umaymah ce take biɗar mgna da kai, ta kirayi layinka ba'a ɗagawa, shine tace in kawo maka wayar".
Kanshi ya ɗan sunkiyar a hankali yace.
"Ummi kice mata tayi hakuri saida safe".
Cikin mamaki jakadiya tace.
"Lafiya dai ko Sheykh?".
Kanshi ya gyaɗa mata alamar eh lfy.
"To ba laifi zan gaya mata".
Daga nan ta juya ta koma sashinta.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, daga bakin ƙofa ya dakatar da bayinshi.
Kana cikin nitsuwa ya kallesu tare da cewa.
"Sarkin ƙofar ka janye bayin dake bina da bin Jalal da Jamil, kaima ka koma can sashunku, ba'a buƙatar bibikon nan, in inada buƙatar ku Ummi zata sanar muku."
Ciki girmamawa sukace.
"To Sheykh". daga nan ya juya ya nufi ciki.
Su kuma suka juya.

Koda ya shiga ɗakinshi kai tsaye bathroom ya wuce wonka yayi tare da al'wala a cikin bathroom nashi da yafi makoncin wani kyau.
Komai na bathroom ɗin glass ne mai ruwan garai-garai, bathroom ɗin katone, mai ɗauko da babban drower'n glass wanda yake cike da ƙananun kayan sirrin jikinshi kamarsu vets boxes and pants kana towels da rigunan wonka da jalabiyoyinshi masu masifar kyau da tsada da taushi da yawa, sai kuma 3 qtr da kuma turaruka dasu brosh da su makilin da dai sauran kayan buƙata na aske pravet part. Ko ina na kusurwan ban ɗakin da madubai.

Bayan ya fitone, yayi shirin baccinsa cikin wani tattausan jallabiya mai masifar kyau da tsada,
A bakin gadonshi na sarakuna ya zauna,
idonshi ya zubawa woyoyinshi dake kan bedside drower' Woyoyin sun kai biyar,
a hankali yasa hannunshin ya ɗauki ɗaya daga cikinsu data kawo haske, alamun ana kiranshi,
Karawa yayi a kunnenshi tare da yin shiru.
A can ɗaya sashin kuma kekyawar tsohuwar balarabiyace keta mishi faɗan ina ya shiga tana kiranshi bai amsawa.
A hankali ya lumshe idanunshi tare da mirginawa ya konta tattausan gadonsa da shimfiɗar sa, wanda Jamil ke gyara mishi a koda yaushe, cikin harshen larabci yace.
"Sitti raja'an!".
shiru sukayi baki ɗayansu, can kuma sai yaci gaba da magana cikin larabcin,
sawon 32 second yana maga kafin ya katse kiran,
kana yayi laduban konciya bacci ya konta.


Washe gari da safe da misalin karfe sha ɗaya na rana.
Dawawonshi kenan daga fada,
Yana shiga falonshi asalin falon dake gab da makoncinsa kiran Umaymah na shiga wayarsa.
Ganin video call ne ya sashi, amsa kiran kana ya ajiye wayar kan Glass Stull dake gaban kujerar da yake zaune.

Fuskar wata kekyawar Matace ya bayyana a fuskar wayar tashi, cikin sanyi ta zuba mishi idanu ganin yadda ya tonƙoshe wuyanshi bisa kafaɗunshi a hankali tace.
"Jazlaan". Kanshi ya ɗan mirgina cikin wani yanayi ya jujjuya mata kai a hankali yace.
"Jazlaan, Umaymah sai yaushe zan zama Jazlaan? Sai yaushe, Jazlaan zai wadaci rayuwarmu?".
Murmushi mai ciwo a zuciya tayi tare da cewa.
"In sha Allah nan kusa".
A hankali ya lumshe idanunshi cikin sanyi yace.
"Umaymah, kizo kafin mu tafi, ina so mu haɗu".
Cikin tarin kulawa da tsananin ƙauna tace.
"Menene matsalarka?".
A hankali yace.
"Ya Jafar...!




Littafin na kuɗine.
By
*GARKUWAR FULANI*


📝🍇🍇🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘

*GARKUWA*

PAGE 4

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘
*GAREKU MUTANEN NIGER, +22799460151 kuyi haƙuri an samu akasin number da nada bada, wayarta ta lalace. Yanzu ga number da zakuyiwa mgn +22799460151 300 ko 1k idan kun turata mata, saita turo min number ki/ka sai in saki/ka a group ɗin da kika biyawa🤝🏻. Gareku mutanen ƙasata ga number ta 09097853278, turo katin mtn na ɗari uku kacal, ko kimin TRANSFER ɗin darinki uku ko 1k ɗan samun SP Group. In kin biya sai kiyi screenshort ki turo min shaidar biyan kuɗin littafin GARKUWA ta wannan number dai 09097853276*

Cikin nitsuwar da ya kasance halittarsa, ya ɗan ranƙwafar da kai yayinda fuskarshi ta ɗan sauya yanayi murya can ƙasa yace.
"Ya Jafar! Yana buƙatar kulawata, baya son nayi nesa dashi, Umaymah Jalal da Jamil basu da hankali yaran basu da nitsuwa Umaymah basu san ciwon kansuba Affan kuma baya nan".
A hankali wacce ya kira da Umaymah ta gyara zama cikin tarin kula da bege da tausayi da ƙaunar Jazlaan ɗin nata cikin tausasan laffazi tace.
"Daɗewa zakuyi ne Jazlaan?".
Hannunshin yasa yana ɗan shafa sumar kanshi cikin rumtse ido murya can ƙasa yace.
"Sitti tace zamu daɗe a can, kuma Maimartaba ta gayawa kai tsaye, shi kuma ya faɗawa Abba kai tsaye umarni suka bani".
Kai ta ɗan rausayar tare da cewa.
"Ba komai Jazlaan in sha Allah babu abinda zai samu Jafar, in kaje kayi ta mishi addu'o'in kamar yadda ka saba, in sha Allah yana cikin kulawa da kariyar Allah".
Kanshi ya ɗan gyaɗa mata,
Domin bai fiye yawan maganaba in ba amɓaton Allah ba, dan ma ta kasance cikin mutun biyar ns duniya da yake iya yin doguwar magana dasu, musamman Maimartaba da mafi akasari faɗa ke haɗasu, sai ita sai kuma Umminshi Jakadiyarsu kenan wacce tun yana jariri itace uwar rainonshi sai Sitti da Jadda".
shiru ta ɗanyi tana kallon yadda ya lumshe ido tamkar bazaiyi magana ba,
bata dai katse kiranba har tsawon 3 minutes kafin ya ɗan motsa laɓɓansa ba tare daya buɗe kwayar kekyawan idanunshi yace.
"Umaymahhhh".
yadda ya kira sunanra ya tabbatar mata halin da zuciyarshi ke ciki, tafi kowa na duniya sanin matsalarki Sheykh Jabeer Habibullah Nuruddeen Bubayero.
Cikin kulawa tace.
"Na'am Jazlaan".
tashi yayi zaune a hankali ya fuskanci wayar tasa da kyau, hannunshi ya haɗe wuri ɗaya tare da cewa.
"Umaymahhhh Jalal".
Cikin kulawar da ƙanwar uwa shaƙiƙiya kan iya bawa ƴaƴan ƴar uwarta, da tarin son da takeyiwa ƴaƴan ƴar uwarta Tata, musamman shi Sheykh, a hankali tace.
"Me Jalal yayi".
Kanshi ya ɗan ranƙofar tare da cewa.
"Umaymahhhh Jalal bayaji, ya fiye gagara, da son jawowa Ahlinmu abin faɗa.
Ɗazuma kwalaɓen giya fa ya shigo dasu cikin masarautar da ta kasance tsarkakkeya.
Ga Jamil kuma babu nitsuwa tattaredashi, duk inda yaga mace, jikinshi na rawa yakebi ya zama kamar ɗan akuya, Umaymah in nayi nisa da gida, zasuyi abinda zai sasu a matsalar rayuwa".
Wani dogon ajiyan zuciya Umaymah ta sauƙe a hankali tace.
"Kada ka damu, in sha Allah babu abinda zasuyi da izinin Ubangiji rayuwarsu bazata lalaceba kodan addu'o'in da kakeyi musu, da irin tarbiyar da kake basu".
Kanshi ya gyaɗa tare da taune lips ɗinshi na ƙasa yayinda lokacin ɗaya kwayar idanunshi sukayi wani irin kala su ba jaba sunba fariba.
Cikin rauni miskilar muryarshi yace.
"Na sanifa Umaymah babu abinda sukeyi, nasan Jalal ba mashayin giya bane baya shan komai, amman ya rigada duniya tanayi mishi kallon mashayi, tantiri kana taƙadirin yaro.
Haka nan nasan Jamil ma ba mazinaci bane Umaymah amman a idanun mutanen duniya shi tamkar ɗan akuya suke ganinshi,
Kamar yadda Ya Jafar yake ba majanuni bane amman mutanen duniya kallon majanun suke mishi".
Kanshi ya sunkuyar cikin


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login