Showing 135001 words to 138000 words out of 352722 words

Chapter 46 - GARKUWAAA COMPLTE HAUSA NOVEL

17 Oct 2024

30749

Shatu falonta ta fito.
Bisa kujera ta zauna, tare da kiran
number Junaidu wanda Rafi'a ce, ta batashi data tare da bata haƙurin bazata samu zuwaba, sabida yayanta yazo sun koma jiharsu tare.

Ringing ɗaya ana biyu Junaidun ya amsa kiran ganin sabuwar number ne ya sashi cewa.
"Ban gane wake mgna ba".
Cikin jin daɗin yadda taji muryarshi ras alamun ya samu lfy tace.
"Junaidu Adda Shatu ce fa".
Da sauri ya tashi zaune bisa kekyawan gadon asibitin da yake kai tare da cewa.
"Laah Adda Shatu kece? Wlh ban gane muryarki ba, Adda Shatu ya gida ya kwana biyu, ya kewan gida, ya lbrinsu Junainah".
Cikin sauri tace.
"Kai Junaidu duka wannan tambayoyin, ka bari mana in tambayeka ya jikinka, yasu Iri da Laure da Innaji da jikin".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Alhamdulillah Adda Shatu duk jikinmu da sauƙin wasuma duk an sallamesu, yanzu nida Hamidu da Adamune kaɗai muka rage, kuma jikin da sauƙi sosai.
Sai dan Baba Madune yana shan wuya,
Satin daya wucema an sake yi mishi aiki".
Cikin sanyi tace.
"To yanzu su waye ke kula daku".
Kanshi ya rausayar tare da cewa.
"Uhumm mufa yanzu bamu da matsalar komai Adda Shatu kwantar da hankalinki, mun samu gata da kulawar wani babban likita mai mutunci.
An canza mana asibiti ma an kawomu wani asibiti kamar na ƙasar woje".
Cike da jin daɗi tace.
"Alhamdulillah, dama dukkan tsanani yana tare da sauƙi".

Dogon numfashi Junaidu yaja tare da cewa.
"Adda Shatu, ashe mun samu nasara, an kora mana mugun babarbarenen nan,".
Uhum tace a taƙaice.
Shi kuwa Junaidu cigaba da mgna yayi.
"Adda Shatu Ya Salmanu ba lfy, yazo dubamu da jiki shima an kamashi gado.
Shi yake cemin wai su Bappa sun tafi Lardi. Ayyah Adda Shatu yanzu sai yaushe zasu dawo? Kina mgna dasu ne?".
Cikin dariya tace.
"Faɗi gsky dai Junainah kake son tambaya dai. Junaidu.
Suna lfy ina mgna dasu. Sai bayan salla zasu dawo."
Da sauri yace.
"Dan Allah Adda Shatu turo min number su".
To tace tare da gyara konciyarta.
Nan dai suka ɗan yi hira, kana sukayi sallama.
Sannan ta tura mushi number su ɗin.


Suna gamawa ta kira Number Bappa.
Bugu ɗaya ana biyu ya ɗaga.
Cikin jin daɗin jin muryarshi tace.
"Ina kwana Bappa na".

"Lfy lau Alhamdulillah Shatu ya Azumi, da baƙon wuri".
Cikin sanyi tace.
"Alhamdulillah, Bappa yaushe zaku dawo".
Dariya yayi mai ɗan sauti kana yace.
"Bayan salla".
Cikin lumshe ido hawaye na zuba tace.
"Bappa ina jin kewarku, bani da kowa nawa kusa dani.
In na tuno su ya Giɗi hankalina na tashi Bappa inyi ta kuka babu mai sanin irin ciwon da nakeji a raina".
Cikin sanyi yace.
"Kwantar da hankalinki Shatu, su Ya Giɗi suna raye, sai dai suna cikin mawuyacin hali, suna buƙatar addu'o'in ki musamman a cikin wannan mata mai alfarma, na sanki bakya wasa da riƙo da ibada, amman ki ƙara kan yadda kike, in sha Allah wata rana zasu dawo garemu, cikin sauƙaƙƙiyar hanya, addu'a itace abinda suke so, shiyasa na gaya miki abinda Allah ya nuna min a mafarki a kansu".
Cikin sassanyan kuka murya can ƙasa tace.
"Zanyi Bappa zan ƙara zan dage, kuma zan roƙi a tayamu addu'o'in a masallatai da wurin tabsir."
Cikin jin daɗi yace.
"Yauwa Shatu na, ki kwantar da hankalinki, ki zauna lfy da mutanen da kike tare dasu, kiyiwa mijinki biyayya, kiyiwa mayanshi biyayya bana son musu in babba ya gaya miki abu matukar bai saɓawa shariyar musulunci ba."
Cikin sanyi tace.
"To". Da sauri yace mata ga Junainah".
Cikin jin daɗi tace.
"To a bata waya".
Tsalle Junainah tayi tare da cewa.
"Adda Shatu, kizo Lardi garin da daɗi kullum sai an gasa mana zabbi ko Tattabaru, insha nono da zuma inci naman insha zuma, inci su inabi sai na ƙoshi".
Cikin so da ƙauna da shaƙuwar ta da yarinyar tace.
"Allah sarki Junnu ke ko kewata bakiyi bako?".
Dariya tayi tare da cewa.
"Nayi kewarku mana harda Ya Junaidu ma nayi kewarshki".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Na bashi number ku, zai kira ku gaisa".
Tsalle tayi tare da nufar ɗakin Ummey.
Ita kuwa Shatu cikin dariya tace.
"Azuminki nawa".
Da sauri tace.
"Azumi na ɗaya ranan nayi rabi daga safe zuwa azahar jiya kuma na ƙarisa rabin daga azahar zuwa mangriba".
Wani irin dariya ne ya rufe Shatu dariya takeyi sosai.
Kewa da bege da son ƙanwar tata ya rufeta.
Da Sauri ta tsagaita da dariyar jin Junainah na cewa.
"Adda Shatu Bappa yayi aure an samo mana wata Inna mai kirki".
Cikin mamaki tace.
"Ke Junnu ƙarya ba kyau fa".
Da sauri tace.
"To ga Ummey ki tambayeta kiji".
Ajiyan zuciya ta sauƙe jin muryar Ummey cikin sanyi da jin daɗi tace.
"Ina kwana Ummey na ya gida, ya Junnuna nayi kewarku, Ummey wai da gaske Bappa yayi aure".
Murmushi mai faɗi Ummey tayi tare da cewa.
"To duk Alhamdulillah muna lfy eh Bappa yayi aure an bashi ƙanwar innarku, Indo kin santa ai ita take bin innarku, Bata taɓa haihuwa ba, to ashe mijinta ya rasu.
Shine yanzu aka aura mishi ita. Kuma tanada hankali kamar innarku".
Cikin sanyin jiki tace.
"Eh na san Umma Indo tanada kirki, to Allah ya baku zaman lfy yasa kuyi irin zaman da kukayi da Inna".
Amin Amin tace kana tai mata nasiha Sannan sukayi sallama.

Daga nan ta miƙa ta nufi ɗaki dan yin salla.

Ana idar da salla suka fito, kitchen suka nufa ita da Ummi da Saratu da tun ɗazu tana nan.
Suka fara aikin buɗa baki sunayi suna kimtsa komai.


Kafin shida ta cikama sun gama komai.

Yanzu in sun zo buɗa baki ita da Ummi da Hibba tsakiyar falon suke dawowa.
Jalal, Jamil, Imran, Sulaiman, kuma su zauna a dinning table.

Ya Jafar kuwa wani lokacin har can falon Sheykh zai wuce suyi buɗa baki a tare.
Kana su tafi masallacin.

Haka dai komai yaketa wakana cikin aminci da tsari.
A wurin al'ummar Annabi kowa ya nitsu ya maida hankali kan ibada domin neman rabauta.


Ƙarfe takwas dai-dai suka shiga kitchen dan yin aikin sahur.
Cikin kula Ummi ta kalleta tare da cewa.
"Ɗauko kwanu kan nashi".
Kanta ta ɗan juyo ta kalli Ummi tare da cewa.
"Ai bai dawo yaci ba ko?".
Kai ta gyaɗa mata tare da cewa.
"Baya cin ƙosai, kuma kinga doyan ma jiya baiciba, ya gaji dasu ne, ki ɗauko a juyewa su Saratu shi ki ɗan haɗa mishi wani abu kafin ya dawo".
Cikin ɗan kauda kai tace.
"Ummi ai ƙoshi yake shiyasa bazai ciba, a barshi kawai in yaji yunwar yacima wani bai saniba, ai yunwa ba Umaymah bace ko ke bare zaku lallaɓashi".
Dariya Ummi tayi kana kuma ta haɗe fuska tare da cewa.
"Je kiyi abinda nace ko".
To tace ganin kamar ran Ummi ya ɓaci.

Bayan ta dawo da kwanukan ne,
Suka bawa Saratu ta juye, kana ta harhaɗa wonke-wonken ta fara.

Ita kuwa Shatu cikin yin miƙa tace.
"Ummi me zan dafa mishin?".
Juyawa tayi tana haura wurin da Fridge yake tare da ce mata.
"Duk abinda kika iya kika san ba mai nauyi bane".

Kanta ta gyaɗa tare da cewa.
"To".
Cikin ranta tace.
"Bari inyi Special Arish, in yaga dama yaci in yaso ya bari, mutun sai zaɓe-zaɓe kamar mai ciki.
Dankali ta ɗan ɗebo da Nama, kwai, tumatur, kabeji, Bama, maggi, tafarnuwa man gyaɗa, komai dai dai-dai misalin yadda zata buƙata duk ta ajiyesu kusa da ita.

Fere dankalin tayi ba tare da ta daddatsashi ba. Ta wonƙeshi fes kana tasa a ƴar tukunya tare da tarfa gishiri da ruwa dai-dai misali, sannan ta tafasashi.
Kwan ta ɗauka ta fasa ta kaɗashi da kyau tare dasa yankekken al'basa da Curry da maggi da tafarnuwa ɗan kaɗan.

Ganin dankalin yayine ta juyeshi a ɗan kondo ta tsaneshi.
Tare da ɗan barinshi yasha iska, kaɗan.
Kana ta ɗaura Naman da maggi da gishiri da Curry da tafarnuwa da al'basa. bisa wata a ɗan tukunta.
Sannan ɗaura man ta ɗauki dankalin ta tsomawa cikin kwan tana soyashi, saida ta gama ta ajiyeshi gefe.
kafin nan naman kuma yayi lugub yayi laushin.
saida ruwan ya kusa ƙarewa sai ta ƙara wata al'basar da tumatur suka nuna tare sannan ta kwashesu.
Kabejin ta yayyanka ƙanana sannan ta ɗauki dafaffan kwai ta yayyanka shi da ɗan girma.
Kana tasa Maggi da al'basa da Bama ta gauraya kana
Ummi ta miƙo mata ɗan ƙaramin Foodflaks alamun ta amsa ta saka.
Kanta ta jujjuya tare da cewa.
"Bari in sa mishi a plate kawai tunda ya dawo".
Da mamaki Ummi ta kalleta tare da cewa
"Yaushe ya dawo?"
Plate ta ɗauko tare da cewa.
"Tun ɗazu".
Da sauri ta sunkuyar da kanta ganin kamar Ummi na mata kallon Mamaki da tuhuma.
Ita kuwa Ummi cikin Binta da ido tace,
Ya akayi kika san ya dawo".
Kai ta rausayar tare daci gaba da aikin kamar bataji Ummi ba.
Plate ɗin ta ajiyeta, ta zuba Arish ɗin gefe kana tasa haɗin naman gefe, ta kuma zuba na Kabejin shima gefe.
Ta shiryashi yayi kyau sosai.
Ɗaya plate ɗin ta kife kanshi.
Kana tasa spoon da Fork a cikin tray'n data ajiye plate ɗin.
Ɗan madaidaicin flaks ɗin coffee ta ajiye gefe, kana tasa cup da tea spoon a ciki.
Sannan turashi gefe.
Zuwa lokacin kuma tuni Ummi da Saratu su gama aikin sahur ɗin har Saratu ta tafi.
Sauran ta sako a wani plate ɗin tare da cewa Ummu gashi.
Amsa Ummi tayi tare da cewa.
"Ɗauki ki kai mishi to".
To tace tare da ɗaukan tray'n ta fita.

A tsaye ta sameshi cikin wani tattausan jallabiya da alamun wonka ya fito,
Sai wani irin masifeffen ƙamshi yakeyi.

Cikin nitsuwa ta wuce ta bayanshi, inda yake tsaye yana kunna Tv.

Bisa santa table ɗin glass mai garai-garai dake tsakiyar falon ta ajiye mishi.
Kana ta juya a hankali ta fita.

Kai tsaye ɗakinta ta wuce, nan ta samu Hibba tuni tayi bacci.
Wonka tayi da ruwan ɗumi tare da shafa mai kana tasa wata tattausar rigar bacci gajera iya karta guiwa.
Hibaji ta zura a jikinta kana ta haura gado ta konta tare da jawo blanket ta duƙunƙune a ciki.
Sabida ita bata son sanyi, shiyasa takesa ƙaton hijabi kana ta shiga borgo.
Badon Hibba Bama dake masifar son sanyi da kashe AC'n zatayi.


Ƙarfe ɗaya dai-dai ta tashi bacci al'wala tayi kana tai ta nafila hakama Ummi.
Sheykh Jabeer kuwa tuni ya tashi shima.
Ya kira su Jalal ma a waya ya tashesu.

Ƙarfe huɗu da rabi dai-dai ta isa falonshi da tray'n abincin sahur ɗin shi.
Ta ajiye ta juyo kenan shi kuma yana fitowa falonshi.
Tazo tsakiyar falon kenan tana tafiyarta a hankali ba zato ba tsammani taji daram-dam ƙaran bindigar da kullum da asuba sai an saketa sau biyu, ta kuma kasa sabawa dashi bare ta daina tsoronshi.
Wani irin tsalle da zabura tayi tare da ficewa a guje tana cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun".
Bayanta yabi da kallo tare da taɓe baki kana ya nufi Dinnin area.

Washe gari da safe yau Jumma'a kuma, yaune azumi na shida.

Bayan sun fitone, Ummi ta kalleta cikin dariya dan tuno yadda ta fito falon Sheykh Jabeer a guje da asuba, tana jan Allah ya isanmata ana tsinka mata zuciya,
Cikin murmushin tace.
"Ummi dariyar me kikeyi ne?".
Cikin gimtse dariyar tace.
"A babu, yauwa tashi muje ɗazu Gimbiya Aminatu ta aiko, wai tayi kewarki kwana biyu azumi ya ɓoyeki bakije ba".
Cikin murmushin tace to muje Ummi".
Ta ƙarishe mgnar tanayin gaba Hibba na biye da ita a baya.
Cikin sauri Ummi tace.
"A haka zaki fita ba al'kyabba".
Kai ta ɗan dafe tare da cewa.
"Wayyo Allah na, Allah kuwa ni nauyi sukemin wannan tsarabe-tsaraben wuya gareshi".
Murmushi Ummi tai tare da miƙewa ta ɗauko al'kyabbar.
Tazo tasa kana suka fita.

Da Side ɗin Hajia Mama suka fara,
A falo suka samesu.
Cikin fuskar ba yabo ba fallasa Hajia Mama ta amsa gaisuwar Shatu.
Batool kuwa sai auna mata harara takeyi.
Hira suka ɗan taɓa kana suka fito.
Har sun fito Shatu ta ɗan kalli Ummi cikin sanyi tace.
"Ummi jirani anan bari inje in isar da saƙon gaisuwar Ummey na wurin Hajia Mama".
Da Mamaki Ummi tace to kana ta juya ta nufi ciki, ganin Hibba za biyota ne tace.
"A a jirani ina zuwa".
Haka suka tsaya suna jiranta.

A hankali ta turo ƙafar falon.
Da sauri Hajia Mama ta zuba mata ido fuska cike da tsana.
Batool kuwa binta da ido takeyi ganin wani irin takun isa da ƙasaitar da takeyi.
Kujerar dake fuskantar wacce Hajia Mama ke zaune a kai ta zauna.
Ƙafarta ɗaya ta ɗaura kan ɗaya.
Kana ta jingina da kujerar, cikin tsare Hajia Mama da ido tace.
"Uhummmm kin sanni sarai, kar tasan karne, duk motsinki a tsakiyar tafin hannuna kike, dan haka gwara kiyiwa kanki gada ki fita harka da rayuwar mijina! Da ƙannenshi da wanshi. In kuwa kikaƙi zakisha mamakin Shatu."
Tana faɗin haka ta miƙe, tana kallon Batool da tun randa akace Shatu tazo ta bawa Hajia Mama haƙuri da ta shigo tayi wasu kalaman ya ɗaurewa Batool kai ta kasa tantance tsakanin aya da tsakuwa, shiyasa batayi gigin yin mgn ba, sabida tuno abinda Shatu tace mata a ranar cewa.
"Mijina kike so ko, to kizo in ya amince ya kalli inda kike na daƙiƙi biyu rak zan sashi ya aureki".
Da sauri Batool ta dawo daga duniyar tunanin da take jin ƙaran rufe ƙofar da Shatu tayi.

Ido ta maida kan Hajia Mama dake gurnani kamar macijiya.


Jim kaɗan ta fito.
Cike da son gano wani abu Ummi ke binta da ido, amman ta kasa gano komai domin Shatu ta iye takunta, ta fito kamar ba itaba gaba tayi.

Kana suka nufi Side ɗin Gimbiya Aminatu.
Suna shiga ta miƙowa Shatu da Hibba hannu kusa da ita ta ajiyesu.
Bayan sun gaisane ta kallesu tare da cewa.
"Azumi ya boyeku da yake ku ragwagene".
Murmushi sukayi tare da cewa.
"Kai Gimbiya jiya nefa kawai bamu zoba".
Cikin kula Lamiɗo dake shigowa yanzu zai sabunta al'wala zai wuce masallaci yace.
"Shatu matar malam bauɗeɗɗe".
Murmushi tayi tare da sunkuyar da kai.
Hibba ce tace.
"Sai na gaya mishi".
Dariya sukayi kana suka sallamesu suka tafi ganin lokacin sallan yayi.
Har sunje bakin ƙofa Gimbiya Aminatu tace.
"Yauwa Jakadiya kayan miyanku da saura ko ya ƙare?".
Cikin rusunawa tace.
"A'a da saura sosaima".
Kai ta gyaɗa kana suka tafi.
A hanyarsu ba komawane Shatu tace.
"Ummi wanne kayan miyan ne?".
Cikin sanyi tace.
"To ba kince bakya son na Hajia Mama ba, shine ita kuma Gimbiya Aminatu ta haɗo miki komai yanzu dasu muke amfani ai".
Cikin gamsuwa tace.
"To wancan ɗinfa ya akayi dashi?".
"Umaymah ta tafi dashi duka".
Hibba ta faɗa mata.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Ba matsala".

Nan suka tafi suna salla suka shiga kitchen yau harda Hibba.


Sannu-sannu dai bata hana zuwa sai dai a daɗe ba'a jeba.

Yau an cika azumi goma. Gobe za'a shiga goma na wuya, an gama na marmari.


Yau kuma makara Shatu tayi.
Ganin har su Jalal sun zone yasa Ummi ta nufi ɗakinsu.
Ai kuwa kan gado ta hangosu.
Tadasu tayi kana ta fito.
Tana cewa.
"Shatu kiyi sauri kizo ki kaiwa Sheykh nashi".
Kusan a tare suka diro ƙasa.
Brush kawai sukayi suka fito.
Da ƙaton hijabin ta fito.
Tana zuwa Dinning area Ummi ta miƙa mata tray'n abincin nasa.

Amsa tayi ya juya ta nufi falonshi.

Tsaye ta sameshi gaban show glass ɗin dake gefen Fridge ɗinsa dake Dinning area,
Cup ne a hannunshi cike da madarar gongoni da molt a haɗe.
A hankali ta wuceshi kaɗan ta ajiye tray'n.
Kana ta juyo da nufin sauƙowa, taku ɗaya tayi a na biyu ta iso gabanshi kenan.
Aka saki bindigar shaidar huɗu da rabi tayi.
Wani irin zabura tayi tare da af....!



Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta wannan number 09097853276, domin shiga Normal group wanda a wata ɗaya za'a, gama Part one. Ko kima kiyi min TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz bank, domin samun shiga Special Group wanda a sati biyu cakal za'a gama Part two da izinin ubangiji, 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai ki turo shaidar biyanki ta wannan number dai 09097853297.

Ke mai haushi kin turo ɗarinki uku, kinzo kinata haushi, nace ki turo ac no ɗinki in maida miki kuɗinki kin tsaya yimin tumasanci shiyasa nayi Black ɗinki, a rashin Sa'a na haɗa da number ki na goge. Kuma baki Turo ac na na meda miki shi ba. To Alhamdulillah a take a lokacin nayi miki sadaka da ɗarinki uku, ubangijina shine shaidata, banci kuɗinki ba, nasan zakiga PAGE ɗin sabida akwai waɗanda basu san darajar Allah da Manzonsa da iyayensuba, zasu fitar, to kiji ni Shatu na sauƙe nauyin ɗarinki uku.

By
*GARKUWAR FULANI*

Tare da cewa."Lahh Ummi kalli Hamma Jabeer kusa da Uncle Jabir Ali ɗin can".
Cikin Murmushin Ummi tace.
"La ai kuwa, Allah sarki masha Allah, tabarakallah. Allah ka ƙarawa Annabi daraja, Allah ka ƙara bamu hasken addini da imani a zuƙatanmu."
Amin Amin Hibba tace.
Tare da juyowa ta kalli Shatu da tayi kamar bata jisu ba,
Sai tea ɗinta take zuƙa a hankali.
A zahiri zakace idonta kan cup ɗin yake, amman a baɗini kan allon TV'n idonta yake, ta zubawa fuskarshi ido. Duk da bawai kai tsaye shi kaɗai ake ɗaukaba, limamin dake jansu ake ɗauka hakan yasa suma suka fito da yake yana cikin mamun limaman sahun forko.

Sosai take ƙare mishin kallo tare da tsarin shigarsa dana mutanen da yake cikinsu.
Sam bazaka iya bambance shi da suba, Especially ma Sheish Jabir Ali da yake matuƙar kama dashi.
Haka nan taji wasu irin zafafan hawaye masu ɗumi suna tsastsafo mata cikin jijiyoyin idonta.
Ta kuma kasa janye ƙwayar idanunta kanshi. Tana kallon tsarin shigarshi da kullum take ganinshi a matsayin takura.
Lumshe idonta tayi, kana ta buɗe su.
Ummi ta kalla wacce farin cikin ta ya fito fili.
Hakama Hibba. Sai murnar abun takeyi tamkar tayi tsalle ta shiga cikin TV'n,.

Ganin sun sunkuya kai ruku'uh da zasu tafi sujjada ta biyu ne, kuma an ɗaga camerar an maidata ɗaukar samane.
Yasa ta miƙe a hankali bisa santa table dake tsakiyar falon ta ajiye cup ɗin kana ta kalli Ummi tare da cewa.
"Ummi kinji masallacin Joɗa ma sun fara sallan kuma muna zaune".
Da sauri Ummi ta miƙa tare da cewa.
"Farin cikine ya rufeni Shatu,. Muje muyi al'walan mu tafi".
Uhum tace ta juya ta nufi falonta tana mai share hawayenta da har yanzu suke zubowa, tanajin zuciyarta na amsar wani nannauyan abu a kan Sheykh, ta yarda ta gamsu cewa mutun me ibada da imani da ilimi abin sone a zuciyar kowane mutum na gari.

Bayan sunyi al'wala ne suka fito cikin manyan jihabai ƙatti har ƙasa suka nufi woje.
Ananne Shatu tai mamakin ganin yadda kusufa-kusufa matan masarautar ke fitowa, duk suka nufi hanyar zuwa masallacin ta ƙofar dasu Lamiɗo ke bi.

Suna fitowa jikin masallacin sai ga wani ƙaton rumfa na ƙara an lailayeshi da wani irin yashi fari ƙal-ƙal kana ga hasken wuta a cikinsa.
ko wacce da sallaya a hannunta tuni wasu kuma sunma shimfiɗa sallayunsu sunbi jam'i hakanan matan maƙota da sauran matan bayi da hadimai duk nan suke zuwa.
A jeru gaba ɗaya ananne


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login