Showing 15001 words to 18000 words out of 352722 words
Sheykh marfin motar, a hankali ya zuro ƙafafunshi ya fito.
Cikin nitsuwa ya fara taku yana ratsowa cikin farfajiyar Hospital ɗin.
Kasan cewar ta gabas ya fito Aysha kuwa ta yamma ta fito sai ya zama suna fuskantar juna.
Yayinda sai sun haɗu wuri ɗaya zasuyi kwana sun fuskanci kudu inda nanne mashigar cikin asibitin.
A hankali suke takowa suna fuskantar juna.
Sosai ya zuba mata ido sabida ya lura gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi alamun tsananin ciwo takeji gashi a hankali take taku.
Ita kuwa Aysha, tafiya takeyi da kyer sabida azaban ciwo da mararta keyi.
Kanta a sunkuye take tafiya, hakan yasa bata san da mutunba a gabanta.
Da sauri Sheykh ya tsaya sabida wani irin bugawa da ƙirjinsa ya fara. Ganin ta tunkaroshi gadan-gadan, kuma daga yanayin tafiyarta tamkar zata faɗi ƙasa.
Ganin tayi wani irin sunkuyawa tasa hannunta duka biyu ta damƙe mararta da takeji tamkar caccakarsa akeyi da allura.
Gefe ya ɗan tsaya yana kallon ikon Allah, ita kuwa GARKUWA rumtse idanunta tayi da karfi, wata fitinenniyar zuface ke tsastsafowa tako ina,
a hankali ta fara buɗe idanunta jin kartan da mararta keyi ɗin yana ɗan lafawa,
a hankali ta zubawa kyawawan sawunshi idanu, cikin sauri ta ɗago kanta, ganinta tsaye gab kusa da namijin da bata saniba ne yasata ja da baya da sauri tare da miƙe tsawonta cikin firgici murya na ɗan rawa tace.
"I'm very sorry".
Bai kulata ba, sai kauda kanshi da yayi gefe.
Ita kuwa Garkuwa cikin sanyi tace.
"Dan Allah kayi haƙuri".
Kai ya ɗan gyaɗa mata alamar Uhumm.
Ita kuwa cikin sanyi tace.
"Uhumm kaima Doctor Sheykh ɗin kazo ganin ne?".
Da mamaki ya ɗan kalleta da gefen idonshi, sai kuma ya ɗan juyo kanshi kaɗan jin muryarta a sanyaye taci gaba da cewa.
"Muyi sauri mu shiga ance yanada shegiyar ƙasaita da isa, wai ko sarkine yake dubawa in dai lokacin salla yayi tashi yakeyi ya fita".
Cikin tarin mmki ya ɗan waro kyawan idanunshi tare da cewa.
"Umh".
Ita kuwa Garkuwa, hannu tasa ta matse mararta tare da cewa.
"Muyi sauri mu shiga, kaga kuwa kayi sa'a kayi shigar mutunci dan ance shi baya son ganin musulmi da lalatacciyar shiga, ancema in mace tayi shigar banza baya dubata, kaji shishshigin mutunfa ko meye ruwansa da rayuwar wasu ai kowa yayi mai kyau dan kansa ko?".
Rolling Ball eyes nashi yayi tare da gyaɗa mata kanshi.
Kana ya tsuke fuska yaci gaba da tafiya.
Ita kuwa Garkuwa cikin yin ƙasa da murya tace.
"Uhum shidama akace shine shugaban tuzuran ƙasar nan, yana zaune baiyi aureba, ai zama ba aurema ba kyau tunda dai yanada damar yi ko?".
Ɗan tsagaita takunshi yayi tare da cewa.
"Hummh".
A hankali ta bishi a baya cikin yanayin muryar mara lfy tace.
"Dan Allah ka tsaya in rigaka shiga kar yace sai ya dubaka kafin ya dubani".
Dai-dai lokacin kuma suka kutsa kansu cikin asibitin.
Da sauri Garkuwa ta zazzaro idanunta baki ɗaya, tare da dafe ƙirjinta ganin gaba ɗaya Nurses ɗin dake ƙoƙarin fitowa sunyi maza suka koma baya, tare da rusunawa suka haɗa baki wurin cewa.
"Barka da hantsi Sheykh".
Kai kawai ya gyaɗa musu yaci gaba da tafiya, har ya shiga cikin wani ɗan corridor ya shiga wanda zai sadashi da tamfatsetsen Office dinshi ba tare daya ratsa ta cikin Reception ɗin su ba.
Ita kuwa Garkuwa gaba ɗaya tsorone ya rufeta,
Gefen Rafi'a taje ta zauna wanda a take kuma mararta taci gaba da murɗawa da kartawa.
Da ƙarfi ta damƙi hannun Rafi'a.
Cikin tausayawa Rafi'a tace.
"Sannu, in sha Allah bazamu jimaba za'a kiraki, dan na nemi al'farman sauran sun yarda Khadija Nasir Shugaba ce aka shigar, ƴar gwamnan, ba lfy".
Kai kawai ta iya gyaɗa mata, sai taune lips ɗinta da takeyi.
Shi kuwa Sheykh yana shiga Office dinshi, ya fara aikin daya kawoshi cikin ikon Allah kuwa Khadija ta samu sauƙi tunda ya dubata aka bata magunguna.
Mutun biyar ya duba, na shida kuwa, Aysha ce.
Koda aka kira sunanta jiki a mace ta miƙe ta nufi inda take ganin ana shiga.
Nurse namiji na gabanta.
A haka suka shiga,
Ajiyan zuciya taja a hankali sabida tsaruwa da kyau da tsabta da ɗan karen ƙamshin da ya ziyarci hancinta, su sukasa ta son bin Office ɗin da kallo amman ina ciwo bazai bartaba.
A hankali ta iso gaban table ɗin baƙin Glass dake gabanshi.
Ɗaya daga cikin kujerun biyu dake gaban table ɗin ta zauna.
Ƙasa tayi da kanta cikin tarin ciwo da fargaba.
Shiru tayi zaune bisa kujerar tayi ƙasa da kanta.
Shikuwa Sheykh ko kanshi bai ɗago ya kalli inda takeba wanda wannan al'adarsace da wuya ya kalli mutun, mafiya yawan lokuta yafi kallon mutun ta cikin gilashi table ɗinshi,
shiru Office ɗin sai sautin A/C da yake busawa, shima kanshi Nos ɗin sai ya gaza abin cewa,
Ita kuwa Aysha pat-pat haka zuciyarta ke duka, gashi tana jiyo mararta na fara kartawa.
Kusan tsawon 1 minute suna a haka, cikin dakiya da rauni ta ɗan nago kanta ta kalleshi,
Ga mamakinta sai taga asalima hankalinshi baya kanta, yana dai murza yatsunshi da alamun tasbihi yakeyi.
Shi kuwa Sheykh duk abinda takeyi yana ganinta ta kan glass ɗin,
Cikin sanyin murya tace.
"(Jam ɓanɗuna). Ina kwana".
Shiru bai kulataba har sawon wasu daƙiƙun har ta fara zaton ko bai jita bane.
Da sauri ta ɗago kanta jin yayi mata magana, cikin wata sahihiyar murya a takaice yace.
"Suna?".
Cikin fargaba ta tace.
"AYSHA ALIYU GARKUWA....!
*Uhummm wani kayan sai amale, wani littafin yafi ƙarfin a baka lbri ka iya haƙura baka karantaba. GARKUWA YA WUCE ZATON MAI ZATO*
By
*GARKUWAR FULANI*
📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇
🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘
*GARKUWA*
PAGE 5
NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*
📝🍇🕊️🐄🌈🦚🐍🤴🏻💘
*LITTAFIN GARKUWA na kuɗine ga masu buƙatar biyan kuɗin samun damar karantawa al'ummar Niger da kewaye ga number da zakuyiwa mgn +22799460151 biya ɗari uku, ko dubunki ɗaya kacal un saki a group. Gareku mutanena mutanen ƙasata in kina buƙatar GARKUWA ga hankaɗo min ɗari uku kacal! ko dubu ɗaya rak! Ta asusuna na Jaiz bank, 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, sai ki turo min shaidar biyan ki ta number ta 09097853276. Mutanen Ayyah SP Group bana son KATI. Kuma al'ummar 300 in ba dole ba yaseen bana son KATI, to amman in babu yadda zakiyi, nasan akwai irina ƴan ƙauye, ba POS. Kuma kuna son karantawa, to hankaɗo katin mtn ɗinki na darinki uku kisha karatu. Allah ya nuna mana ƙarshensa lfy kamar yadda ya nuna mana forkonsa lfy. ALLAH ya bamu haƙurin zama da juna*
```Fans 1&2 sarakan surutu, Ina gaidaku ina ji daku har cikin ƙoƙon raina. SP Group, inai muku jinjina dubu-dubu.Fans 3
Allah ya rayamu ku cika maƙil. Group ɗin kurame kuma ina sane duku ina kuma jin daɗin nitsuwarku ba surutu. i love all my fan's irin lodi-lodin nan mafa```
```Gyaran amare uwar gidaye masu jego da masu tada komaɗa da sabunta dararen satin forko na amarci. Ku garzayo gani gareku da tsaraba kamarsu, tsumin Tsartai, sa buzu kuwa, garin babambaɗe, garin maɗi mai maɗemaɗin ni'imomi, bunbar ke ɗaya, gumbar Mali mai taken kolli mai sheƙi sai dai gsky ita tanada tsada, gumbar Uku csrmazaƙoi, gumbar haɗin inabi dabino kwakwa riɗi.
Akwai haɗin ilan waddi, duk ba fula tani in yaji ilan waddi uhumm, akwai garin Belɗam yel, akwai tsumin ta baje, akwai kwanon ƙasaitacciyar mace, akwai kirɓeɓɓen tsumin domin mutanen nesa, akwai mgnin sanyi Infection, akwai butar sirri mai. abubuwan dai da yawa, gani ya kori ji, in kina buƙata kiyi min mgn ta wannan number 09097853276 kada ki kira dan ban fiye daga kiraba, gwara kimin mgn ta whatsapp in kinga bana kusa Turo min text message ta in-box```
A hankali ya ɗan ɗago ƙwayan idanunshi ya kalleta.
Kanta a sunkuye hannunta biyu duka na kan mararta cikin wani, irin yanayi take wanda yake nuni da tana cikin wahala.
A hankali ya maimaita sunan cikin zuciyarshi.
"AYSHA ALIYU GARKUWA! To GARKUWAN ina? GARKUWAN meye?."
A fili kuma kauda idonshi yayi daga kanta ya maida idanunshi kan tarin foldan dake gabanshi, wanda sunanta ke rubuce akan na samanshi yaja da yatsu biyu.
Shafin forko ya buɗe a folder kana, yasa hannu cikin wani ɗan abu mai kama da kofi wanda yake cike da biro masu kyau da tsadar gaske.
Tsiraran idanunshi ya lumshe sabida wani irin bugu da yakeji zuciyarshi nayi tun sanda ya hango yarinyar har zuwa yanzun nan da take gabanshi a zaune.
Rubuce-rubuce yayi a ciki irin nasu na Doctors masu kama da tafiyar wahainiya.
Kanshi ya kuma ɗagowa ya kalleta a fizge da gefen idonshi,
sunkuyar da kanshi yayi tare da cewa.
"Meke damunki?".
Cikin shessheƙan wahala da son danne kukan da ke son kabce mata tace.
"Marata, da bayana".
Kai ya ɗan jujjuya tare da kallon shekarunta dake rubuce a cikin folder din,
Yar shekara ashirin kuma da ƙorafin ciwon baya, cikin dakekken sauti yace.
"Yaushe ya fara miki ciwo?".
Hannu tasa ta cikin niƙabin da yayiwa fuskarta ƙawanya ta share hwayenta a hankali tace.
"Shekara uku da suka wuce".
"Meyasa bakije asibitiba tun lokacin?". Ya tambayeta a daƙile.
"Ina zuwa asibiti duk sanda ya tashi".
"Kamar yaushe da yaushe yake tashi?". Ya jefo mata tambayar kamar yadda zuciyarshi ke harbawa da ƙarfin tsiya da kuma sauri-sauri,
Kai ta sunkuyar tare da cewa.
"Duk ƙarshen wata daga 21 zuwa 25". Shiru yayi kamar bai jitaba sai wasu rubuce-rubucen ya kumayi.
Saida ya gama sannan ya tura mata folder ɗin gabanta.
Jikinta na rawa tasa hannu ta ɗauki folder ɗin, ta yunƙura zata tashine, ya basu damar samun kusanci da juna,
da sauri ya rumtse idanunshi sabida wani irin azabebben bugu da zuciyarshi keyi tamkar zaiyi tsalle ya faɗo woje,
cikin zuciyarshi yake maimaita.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun."
A hankali ya buɗe kyawar kyawan idanunshi jin bugun zuciyarshin ya fara yin ƙasa-ƙasa, ido ya zubawa mata ganin ta juya tana tafiya,
wani abin al'ajabin a gareshi shine duk taku ɗaya da zatayi tana nesanta dashi sai yaji zuciyarshi na tsinkewa yana bada wani mugun bugun ras-ras, yayinda bugun tsinkewanta kuwa yaketa dai-dai-ta,
Cikin mamaki ya sunkiyar da kanshi yana kallon yadda takeyin taku, tana riƙe da mararta, taje gab bakin fofar fitane,
Taji wani irin murɗa da kartan da mararta ya farane yasa ta sakin wani sauti mai cike da wuya.
"Wayyoooooooo Allah na, Wayyo Ummeyna cikina".
Da sauri nurse ɗin nan yayi kanta tare da cewa.
"Isah Allah rena joɗu".
Ya ƙarishe mgnar da nuna mata kujerun farin ƙarfe dake gab da bakin ƙofar.
Bata da zaɓin daya wuce ta zauna ɗin, domin gaba ɗaya ƙafafuwan ta rawa sukeyi alamun bazasu iya ɗaukar nauyinta ba ga duhun daya rufe mata ido.
Sunkuyowa Nos ɗin yayi ya amshi folder kana yace.
"Zauna bari inje Pharmacy in amso miki magungunan da alluran sai ayi miki".
Kai kawai ta iya gyaɗa mishi tare da bashi.
Har ya fita sai kuma ya dawo yace.
"Ok sir". Jin Sheykh Jabeer yace mishi ya turo ta gaba
Da sauri ya fita.
Shi kuwa Sheykh Jabeer, tasbihinshi yaketayi da yankan yatsunshi yake ƙidayar, sabida, suma yatsun su kasance cikin bautar Allah shiyasa yake ƙidayar amman ba don wai yasan adadin salati da hailala da istigifarin da yakeyiba, wannan ubangijine kawai masanin adadinsu.
Bayan fitar Nos ɗin da kamar 1 minute wata,
Kekyawar budurwa ta shigo, cikin yauƙi da ƙasaita, sai wani irin masifeffen ƙamshin da take zubawa.
Ƙarasowa tayi gaban table ɗin nashi ta zauna,
cikin yauƙi da korkosa tace.
"Barka da rana Al' Sheykh".
Ko inda take bai ɗaga ido ya kallaba, ya lura ya gane akwai wani abu tattere da yarinyar, dan mafi akasarin ranaku sai tazo, wai bata da lfy, kuma takan zo da ciwuka mabanbanta ne.
Sanin ba musulma bace yasashi ƙara tsuke fuskarsa tamkar zatayi aman wuta, a zafafe yace.
"Name". Cikin yauƙi da son isar da aikin da aka bata tasa hannu ta jawo foldan ta dake sama tura mishi gabanshi tayi,
Cikin harshen hausa da tasan bai fiye son English language ba a rayuwarshi a hankali tace.
"Breast ɗina kemin ciwo, har bana iya sa bra."
Sai kuma tayi ƙasa da mayafinta dake jikinta, hannu tasa kan zip ɗin gaban rigarta tana ƙoƙarin zugeshi ƙasa tare da cewa.
"Kalli Nipples ɗin sun....
Cikin tsananin firgita da tsoro, ta miƙe da azaban ƙarfi, jin yadda yasa hannunshi ya bugi table ɗin da azaban ƙarfi wani irin gigitaccen tsawa mai firgitarwa ya daka mata tare da cewa.
"Tashi, daga gabana".
Karkar jikinta ke tsuma sabida kwarjinshi da tsoronshi sun daki zuciyarta da take cike da fajirci dama dan bata kallon fuskarshi ne ta iya faɗin waɗannan kalaman ma.
Dai-dai lokacin kuma, Nos ɗin nan ya shigo,
ganin yadda AYSHA ta gigice taketa karkarwa, alamun tana son ta miƙe kuma ta kasa tashi.
Shi kuwa Sheykh foldan ɗin Rabeca ya jawo wani rubutu yayi saman foldan ɗin kana ya tura matashi gabanta cikin zafi da tsauri ya nunata mata hanyar fita tare da cewa.
"Fice min daga Office daga yau in kina buƙatar ganin Dr kije gun Dr Ute, shi zakiyiwa duk sakarcinku na al'jihun baya. Ba niba, sannan daga nan ki wuce Zaria kije asibitin Shika domin ina zaton breast cancer kike dashi".
Da sauri tasa hannu ta ɗauki foldan ɗin, gaba ɗaya jikinta na rawa, juyawa tayi ta fice tare da yin magana can ƙasa yadda bazai jitaba tace.
"Allah ya sauwaƙa Ni bani da breast cancer, mugun bakin kawai."
Shi kuwa Sheykh Jabeer komawa yayi ya jingina da jikin kujerar lumshe idonshi yayi a ranshi yake haɗa kalaman da yaci karo dasu a safiyar yau.
Kakarshi tace mishi, aji mgnar Malam kada a duba aikinshi, ta jaddada mishi, wai yayi aure, kana wannan mayyar yarinyar da in tana kusa dashi zuciyarshi ke barazar fashewa, kuma tace mishi wai shine shugaban tuzuran ƙasar nan baki ɗaya.
Tabbas wannan shaidace na abinda ake faɗa a cikin gari a kansa kenan, yaji ya sani Sitti ma da take son suje saudia wai so take ya zaɓi matar aure a can, ga wannan kafurar da ya san turota akeyi ta tallata mishi kanta, don a samu cinikin jarida ya hauhawa ta hanyar buga kanun labarai cewa, Sheykh mazinacine ko kuma mata yakebi shine ya hanasa aure.
Jingina kanshi yayi da kujerar tare da mgn a zuciyarsa.
"Ya ilahi ya mujibadda'awati".
Ta yayane ta inane wa zai gayawa cewa,
shifa yanada banbanci da sauran maza, ba kamar kowa yake ba, taya zai gaya musu ko zai samu a daina binshi da kalmar yayi aure, me zaiyi da mace ta yaya zai fahimtar dasu su barshi ya huta.
Wannan shine nazarin da yakeyi cikin zuciyarshi,
Ita kuwa Aysha ido ta tsurawa, ƙasan kujerar da yake zaune a kai tana kallon wani al'amari mai cike da ruɗarwa.
Ido ta rumtse sabida bazata iya jurar ganin wannan abun ba.
A hankali Nos ɗin nan ya matso gabanshi, magungunan da alluran daya amso ya miƙa mishi su.
Cikin sanyi yace.
"Sir ga magungunan".
Kanshi ya ɗan tankwarar tare da cewa.
"Kira Dr Ruƙayya tazo ta mata alluran".
A hankali yace.
"Sir na duba duk sun tashi, sabida babu kowa. A Reception ɗin, mune kadai muka rage".
Kanshi ya jinjina, don shima yanzu zai tafi, sabida akwai gidajen likitocin a nan kusa koda shi ya tafi Dr Ruƙayya da Dr Ute suna nan cikin makarantar.
Ta gefen idonshi ya ɗan kalli Aysha daketa fama da ciwo,
Ganin Nos ɗin na haɗa allurar ne yasashi, fara tattara woyoyinsh dake bisa table ɗin.
Shi kuwa nos ɗin. Yana gama haɗa alluran ya nufi inda take, tare da cewa.
"Gyara in miki alluran".
Cikin sanyi tace.
"To". Yana isowa gabanta yace.
"Dole ai sai kin tashi tsaye, kinga doguwar rigace a jikinki kuma sai kin naɗeta".
Ido ta ɗan zuba mishi ta cikin niƙabin tare da jujjuya kai a hankali tace.
"Um ummm".
Kanshi ya gyaɗa tare da cewa.
"Tashi mana sauri mukeyi lokacin sallah ya ƙara to".
Shi dai Sheykh ido ya zubawa bayan Nos ɗin yayinda ita kuwa yake kallon gefenta, cikin bada umarni yace.
"Kuzo".
Da sauri Nos ɗin ya juyo ya nufoshi,
hannu yasa ya amshi allurar,
kana ya ɗan kalleta a fakaice yace.
"Zo nan".
A hankali ta taso cikin sanyi takeyin taku tana matsoshi.
A take kuma bugun zuciyarshin ya fara hauhawa yana komawa matakin sama.
Taku biyu tayi ana uku yaji ƙirjinshi ya bar tsinkewar da yaketa yi ɗin, sai kuma bugun da yakeyi da sauri-saurin ne yaketa tsananta.
Taku takwas tayi ta iso tsakiyar Office ɗin, ido ya fara jujjuyawa kan table nashi yana mai jin wani masifeffen bugun zuciyarshin dayasashi hatsala cikin ɗan ɗaga murya yace.
"Ke da Allah kiyi sauri".
Jin hakane yasa ta kara saurinta, ai kuwa da sauri ya dafe ƙirjinshi lokacin da ta iso gab dashi, cikin ranshi ya kuma cewa.
"Hasbunallahiwani'imanwakil".
A zahiri kuwa, da kai ya nuna mata ta kuma matsowa, ba musu ta matso,
yatsarshi ya jujjuya mata alamun ta juya mishi baya,
still babu musu ta juya, a hankali ya murza kujerar da yake kanta, ya juyo ya fuskanci bayanta, dai-dai saman mazaunanta ta sama ta ɗan gefe kaɗan, ya saita, tsinin bakin allurar, cikin iyawa da gwarewa dan salonshi ne baya taɓa yarda ya kalli fatar jikin wanda zaiyiwa alluran ta saman tufafinka yake zira allurar, shiru tayi tana jin yadda, allurar ya ratsa dogon rigar jikinta ya bada sautin tub alamun ya huda rugar, a hankali ta kuma jin ya huda, dogon wondon jikinta tub, sai kuma taji ya sauƙa kan pantien jikinta, daga nan taji ya ɗisa bakin allurar kan fatarta, rumtse idanunta tayi da azaban ƙarfi sabida, wani zafi da taji yana ratsata, bawai tana tsoron Allurar bane, sai dai hannunshi yanada masifar zafine,
kana shina ruwan alluran irin mai, mai-mai ɗinanne kuma duk cikin allurai yafi zafi.
Da ƙarfi tace.
"Wach Allah na zafi-zaffi."
Wani irin azaba taji lokacin daya fara cusa mata ruwan allurar a jikinta, babu zato babu sammani yaji tasa hannu damanta ta cabki hannunshi dake mata alluran hannunta na hagu kuwa yarfashi take tare dasa kuka da sauti tace.
"Wayyo Allah na, ka bari bana so zare Allurar nan zafi nakeji".
Ta ƙarishe