Showing 309001 words to 312000 words out of 352722 words

Chapter 104 - GARKUWAAA COMPLTE HAUSA NOVEL

17 Oct 2024

30735

ya meda ƙofar ɗakinshi ya rufe, tare da amsa kiran Hajia Mama.
Dariya mai sauti tayi tare da cewa.
"Hahaha shegu zanyi mgninsu yau.
Tuni fatar ragon sunan ya shiga hannuna na gama yin shirina har na meyar musu da ita.
Da sauri cikin tsoro yace.
"Toh me kikasa a cikinta".

Dai-dai lokacin kuma sairkin al'adun Sunan masarautar Joɗa ya shigo falon wurinsu Umaymah tare da Gimbiya Aminatu da
Yana riƙe da fatar ragon sunan.

Bayan sun zauna ne ya sun gaisa ya shimfiɗa fatar ragon sunan.
Tare da miƙowa Ummi dake riƙe da Afreen yace.
"Masha Allah kawo Aisha ƴar Aysha jikar Aisha mu cika mata masakinta".
Da sauri Ummi ta miƙa mishi Afreen dake naɗe cikin shawul fari ƙal mai taushi da ɗaukan, ido.

Hannunshi yasa ya fara zare Shawul ɗin yayi kana ya fara cire mata kayan jikinta ya rage daga ita sai Pampers.
Aunty Rahma ce ta ɗanyi ajiyar zuciya tare da cewa.
"Kai wannan masarautar Joɗa taku tanada tsarabe-,tsaraben al'adu masu masifar tsauri.
Allah ya baku cikekken ahlul sunna ya mulki masarautar shine kaɗai zai kauda al'adun ya wanzar da sunna, ina dalili a ninke yarinya cikin ɗanyen fata ayi ta garata a tsakiyar ɗakin mahaifiyarta ai ko ba'ayi hakaba dole zata san ɗakin uwartace".

Umaymah ce ta ɗan gyara zamanta tare da cewa.
"Toh ya zamuyi tunda abu nasune".
Gimbiya Aminatu ce tayi murmushi tare da cewa.
"Watan wata rana dai tabbas al'adun zasu kau sunna ta wanzu in wanda muke zaton ya yarda ya amshi masarautar".

Allah ya sa haka.
Umaymah tace.
Amin Amin sukace baki ɗayansu.
Suna masu kauda kansu kan fatar dan wani irin warin da basu gane kamsaba da fatar keyi wanda dole in kaji zakayi zaton ƙarnin ɗanyar fatarne.
Wanda fiyafiyen ya gauraye dashi sai dai shi kanshi sarkin al'adun sunan kauda kanshi yakeyi dan azabar warin fiyafiyar da Hajia Mama ta turbuɗa cikin fatar.
Kansu suka ɗan kakkauda tare da cewa.
"Dan Allah kayi maza ka gama ka fito da baiwar Allah".
Cewar Umaymah da Mamma.
Shi kuwa Sarkin al'adun suna murmushi yayi tare da naɗa Afreen cikin fatar ragon sunan,
da Hajia Mama ta gama zazzaga mata madarar fiyafiya mai masifar ƙarfi.
Sai dai da yake fatar a ninke take yana kuma warewa ya naɗe da sauri to sai ya zama kamar a rufe yake, shiyasa basu ji wari sosai ba.
Dan duk wari shi ai in a rufe yake bakajin warin sosai.
Cikin murmushi mugunta ya haɗe yarinyar ya ninke ciki ya matse da ƙarfi kana ya ɗagata ya nufi Bedroom ɗin Shatu.
Zaune ya sameta bisa bakin gado.
Tayi masifar kyau cikin wata dakekkiyar Getzner Orange color mai masifar kyau da sheƙi.
Khadija na tsaye gefenta tana ninke ɗan kwalin zatayi mata ɗauri.
Da sauri ta ɗago kanta ta kalli Sairkin al'adun Suna cikin mamaki tace.
"A bawan Allah ya da kawo fatan rago kuma har cikin ɗaki".
Cikin yin ƙasa da kai yace.
"Al'adar ranar suna zamuyi".
Hannunta tasa ta dafe kanta kana ɗaya hannun ta ɗaurashi kan ƙirjinta dake harbawa da azaban ƙarfi da sauri-sauri kuma.

Aunty Amina ce tace.
"Kai gsky yana wani irin wari fa".
Ummi dake biye dashi a baya da ita da Umaymah da Gimbiya Aminatu ne suka haɗa baki wurin cewa.
"Toh ka fara mana".
Juyowa Khadijah kam tayi ta zauna tana kallon ikon Allah.
Itama Aunty Amina hannu tasa ta dafe haɓarta tana kallon ikon Allah.

Dan dagasu har Shatu basuma gane cewa.
Afreen ce a naɗe a cikiba.

Shi kuwa a hankali yake komai yana mai jin yadda yarinyar take mutsu-mutsun neman ceton rai sai ƙara danneta yakeyi.
Ƙarshen ginin ɗakin yaje kana ya sunkuya ya ajiyeta tare da garata ta gangaro har gaban gadon.
Tuni zuwa yanzu numfashin yariyar in ya fita baya komawa.
Gaba ɗaya fatan jikinta yayi jazir idanunta sun ƙaƙƙafe.

A can ɗakin Sheykh kuwa cikin tsananin hatsala da gajiya da dariyar muguntar da Hajia Mama ke kerketa mishi cikin kunnensa tsawon lokaci a tsale yaja tsaki tare da cewa.
"In kin san bazaki gaya minba meyasa kika kirani ina tambayarki me kikasa cikin fatar ragon sunan kina tamin dariya".
Cikin dariyar mugunta tace.
"Hahahahahhh madarar fiyafiyar mai surke da garin sukudaye na turbuɗa cikin fatar da nasan yanzu ana can an naɗe musu ƴar tasu a ciki, kafin miti biyar da za'ayi ana garata ta zama gaw..."
Cikin wani irin tashin hankali ruɗani da firgici da gigita ya cilla wayar ya liƙata da jikin gini a take ta buɗe batir ɗin ya rabu da wayar.
ba tare daya bari ya ida jin me zata ceba.
Cikin tsananin tashin hankali ya fito da gudu.
Gaba ɗaya jikinsa tsuma da karkarwa yakeyi tamkar mazari namfashinsa tamkar zai bar gangar jikinsa.
Daga falonshi yake rabkawa Shatu da Umaymah kira da ƙarfi yana cewa.
"Aysha! Aysha!! Umaymah! Umaymah!!! Ummi! Kada ku bari asa Ƴarinyar nan cikin fatar nan".
Da sauri Aunty Rahma da Aunty Juwairiyya da Haroon da Jannart suka miƙe tsaye.
Da sauri Haroon ya nufi falonshi su Jamil ma kan tashi tsaye sukayi jin yadda yake mgn da azaban ƙarfi.
Kiciɓis sukayi da harun.
Da ƙarfi yace.
"Haroon ina Aysha ina Baby Ina Umaymah?".
Cikin tsoro Aunty Rahma tace.
"Suna ɗakin Shatu ana al'adar fata".
Da ƙarfi ya ture Haroon dake gabanshi.
Cikin tsananin masifar tashin hankali da ruɗani ya nufi Bedroom ɗin Shatu.
Wanda haka yasa suka kab suka bishi a baya.

Da sauri Shatu ta miƙe tsaye tare da cewa.
"Na'am Yah Sheykh".
Sabida jin yadda yake abka mata kira tare da cewa.
"Aysha Aish Ina kike ina ƴata?".

Kiciɓis sukayi a bakin ƙofar shigowa ita zata fita shi zai shiga.
Da sauri tasa hannun shi ya tureta har saida ta faɗa jikin Umaymah sabida hango Sarkin Al'adun suna yana gara Afreen dake cikin fatar a ƙasa a tsakiyar ɗakin.
Cikin wani irin masifeffen tashin hankali yasa hannunshin da ƙarfi ya ture sarkin al'adun sunan
Ya faɗi ƙasa tib.

Cikin rawan jiki da tashin hankali Umaymah da Ummi sukayi kanshi.
Aunty Amina da Khadijah kuwa cikin mamaki suka zuba mishi idanu.

Su Aunty Juwairiyya kusa duk shigowa sukayi cike da mamaki.
Ita kuwa Shatu da sauri ta gyara tsayuwarta tare da nufoshi.
Ganin yadda gaba ɗaya jikinshi ke karkarwar tamkar mazari.
A gigice ya sunkuyo ya zaro Afreen dake naɗe cikin fatar da sauri ya fara worwore fatar.
Gani yakeyi ma tamkar baya sauri murya na rawa hankali a tashe yake cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil Aish zasu kashe mana ita."
Dai-dai lokacin kuma ya gama woreta.
Cikin wani irin tashin hankali Ya juyo a gigice yace.
"Innalillahi Umaymah sun kashe min ita".
Jiki na rawa hankali a tashe Umaymah ta iso gabanshi da sauri tasa hannunta ta amshi yarinyar ganin yadda jikinsa ke karkarwar.
Da Sauri ta juyo gaban Gimbiya Aminatu tare da cewa.
"La'ilahaillaha Muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam.
Ta rasu."
Da ƙarfi Shatu tace.
"Innalillahi Umaymah me kikace kada kice haka dan Allah ku duba da kyau".
Cikin tsananin tashin hankali Gimbiya Aminatu ta amshi Afreen jujjuya yaya tayi da sauri tace.
"Ta...!

By
*GARKUWAR FULANI*


Cikin tarin kaɗuwa Umaymah, Mamma, Ummi, suka kalli juna tare da yunƙura suka tashi a tare.
Sabida jin kalmar da Aunty Rahma ke mai-maita wa, da tsananin ƙarfi da karaɗi.
A guje suka nufo falon sabida jin yadda take ƙara auna musu kira babu ƙaƙƙautawa.

Jalal da Yah Jafar da Aunty Juwairiyya dake Part ɗin su kuwa, suma da ƙarfi suku mimmiƙe tsaye, tare da juyowa suka nufo Part ɗin Sheykhhhh.

Dedde kuwa da sauri ta matso kusa da Ummey da nufin sa hannunta ta tallabeta, cike da al'hini al'amarin.

Junainah kuwa da gudu ta iso gareta tare da da faɗa wa jikinta ta ruggume sawunta tare da sakin kuka da ƙarfi sabida ganin yadda gaba ɗaya jikinta ke karkarwar.

Sheykh kuwa da Shatu kafin kiran Aunty Rahma tayi mgnarta ta forko ruggume da ita yayi da kyau tare da cewa.
"Uhmmm kin san ko wanni sirri nawa, har na aikina da yake sirri amman ni kin gaza fitowa fili ki nuna min waye Bappa a wurinki waye Abboi a gareki".
Hannun tasa ta ɗan shafa sajenshi ta buɗe baki da nufin yin mgn kenan suka tsinkayo. Muryar Aunty Rahma.

Wani irin tsinkewa da bugawa zuciyar Sheykh tayi da masifar ƙarfi wanda hakan ya haddasa wata iriyar fitinenneyar karkarwar zuciya da jiki, da ƙarfi ya sake rumtse idanunshi tare da sa yatsunshi cikin kunnuwanshi ya jijjiga sabida jin abin yakeyi kamar gizo.

Junainah kuwa wani irin masifeffen kuka tasa mai cike da rauni tare da yayyarfa hannunta murya a hargitse tace.
"Wayyo Adda Shatu! Adda Shatu zo kiga Ummeyn mu bata da lfy Adda Shatuuuu".
Tayi kiran da masifan ƙarfin.
Ganin yadda Ummeyn ta tureta tare da jujjuyawa a tsakiyar falon kamar irin wacce hajijiya ke juyawa haka take tafiya tangal-tangal.

Wani irin zabura Shatu tayi wanda yayi dai-dai da lokacin da Mamma da Umaymah da Ummi da suka fito yanzu suka haɗa baki wurin cewa.
"La ha ila ha illahu Muhammadu Rasulullahi Sallallahu alaihi Wasallam".
Sai kuma gaba ɗaya jikinsu ya saki wani irin masifeffen karkarwa da sakewa ya rufesu.
Suka kasa koda ɗaga sawunsu bare su matsa inda suke.
Sabida tsananin kaɗuwa.

Ita kuwa Shatu tsalle ɗaya tayi ana biyu sai gata a bakin ƙofar Bedroom ɗinsa.
Cikin gigita shima ya yunƙuro da ƙarfi ya mara mata baya, sabida yadda yake jiyo falon a hargitse.

Gudu ya farayi ganin yadda Shatu ta fice a guje sabida ihun Junainah da take jiyowa.


Da sauri Yah Al'ameen ya sako kansa cikin falon jin muryar Junainah da abinda take cewa.

Yah Jafar da Jalal da Aunty Juwairiyya na biye
dashi a baya.

Cikin matsanancin tashin hankali Shatu ke kallon Ummey dake tsaye acikin tsakiyar falon, tana me riƙe da kanta dake juya mata sosai, ko mai bibbiyu take ganinsa, hakan yasa numfashinta soma ƙoƙarin ɗaukewa, take kuma idanunta suka rufe rub, hakan yasa ta-ta-fi luuu zata faɗi.

Da wani irin sauri mai haɗe da gudu Shatu da hankalinta yakai ƙololuwa wajen tashi ta ƙarasa wajen da Ummeynta ke tsaye, hakanne kuma yasa Ummeyn ta faɗa jikinta.

Hannayenta duka biyu tasa ta rungume Ummeyn tare da fara jinjigata cikin kiɗima da gigita, cikin muryar kukan da yazo mata lokaci ɗaya ta shiga faɗin.

“Innalillahi Wa’inna ilahirraju’un.
Ummeyna Ummeyna maiya sameki? Ummey ki tashi dan Allah, ki buɗe idanunki!!!”.
Ta ƙare maganar nata cikin matsanancin kuka, tare kuma da sanya hannayenta ta shiga girgiza Ummeyn da ƙarfi.

Sheykh kuwa dake tsaye ganin fuskar matar da Shatu’n nasa ke kira da sunan Ummey ne yasa shi, jin wani irin abu ya daki zuciyarsa da ƙarfi, wanda hakan yasanya shi jin ƙafafunsa sunyi masa nauyi, lokaci ɗaya kuma wani irin rauni ya cika zuciyarsa, wanda har hakan yasa yaji wasu irin ƙwalla masu ƙuna suka bayyana acikin idanunsa.

Ahankali ya ɗan soma taka ƙafafunsa tare da ƙarasawa wajen da Shatu da kuma Ummey'n suke.

Durƙusa guiwowinsa yayi aƙasa a dai-dai lokacin daya iso wajen da suke, cikin wani irin yanayin dake fusgansa, ya shiga ambaton sunan Allah, a dai-dai lokacin daya sanya duka hannayensa biyu ya rungumo Shatu da kuma Ummey’n jikinsa.

Cikin wata irin sassanyar muryarsa wanda amo da kuma sautinta baya bayyana ya shiga faɗin.
“Subahanallah!. Alhamdulillah!! Hasbunallahu wani’imal wakil, innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un, la haula wala k’uwwata illa billahil aliyil azim!!”
Sune tasbihan da yaketa mai-mai-tawa
Shatu dake kuka kuwa jin ya sakasu ajikinsa ne, yasa ta ɗago jajayen idanunta dake tsiyayar da hawaye, cikin matsanancin damuwa da kuma ruɗewa haɗi da tashin hankalin da ta samu kanta aciki tace.

“Hamma Jabeer Ummeyna bata numfashi.
Dan Allah kace ta-tashi, kace ta buɗe idanunta, banason wani abu ya samu Ummey na, ka taimakamin, wayyo Dedde na Umaymah kuzo Ummeyna ...”

Kasa ƙarasa maganar nata tayi, saboda sosai kuka yaci ƙarfinta, sai-dai kuma amma duk da haka bata daina jijjiga Ummeyn nata ba.

Su Yah Jafar Jalal Ummi Mamma Aunty Juwairiyya Aunty Rahma Khadiya Aunty Amina Ishma, Hafsi Yah Al'ameen kuwa gaba ɗayansu zobe sukayi musu, cike da tarin al'ajabi al'hini kaɗuwa da tarin farin ciki.

Junainah kuwa da ta ƙara ruɗewa saboda ganin kukan da Shatu keyi, ƙarasowa jikin Shatu’n tayi ta raɓa jikinta, cikin muryar kuka take cewa.
“Adda Shatu Ummeynmu.
Adda Shatu Ummyen kice ta tashu mukaita asibiti kada wani abu ya sameta!”.

Sauran jama'ar kuwa.
Kowannensu fuskarsa ɗauke da hawaye suka ƙaraso garisu sosai kusa dasu Shatu, Sheykh, da Ummey’n suke.

Sautin kukan Aunty Rahma ne mai nuna tsantsar farin ciki da na Umaymah da Mamma ne suka fito fili, a dai-dai lokacin da sukayiwa Ummey’n zobe, Kowannensu kuka yake, sai-dai kallo daya zakayiwa kukan nasu ka fahimci cewar ba kukan baƙin ciki bane kukane na tsantsar farin cikin da yiwa Allah godiya, domin kuwa acikin muryar kukan nasu suke ambaton sunan Allah, suna me faɗin.

“Alhamdulillah! Alhamdulillah ya Allah!! Alhamdulillahil lazi bi ni’imati hi ala tatimussalihat!!!”

Umaymah kuwa da matsanancin farin cikin mara misaltuwa da take jin kanta aciki ya kasa ɓuya, durƙushewa tayi bisa guiwowinta tare da kifa goshinta aƙasa tayi Soujjadar nuna, matsanancin godia ga Allah daya dawo mata da ƴar uwarta.

Ummey kuwa wani irin Numfarfashi taja sai gata a sume.

Dai-dai lokacin kuma Jamil da jiyo hayaniyarsu ya sashi tahowa a guje, ganinsu cike a falon kowa fuska cike da hawaye kuma sai kalmar Alhamdulillah suke maimaitawa.
Duk sun kasa bin ta kan kalaman Shatu.
Ganin Jamil ne yasata mgn cikin rauni tace.
"Jamil dan Allah taimaka min Ummey na ta suma".
Jin hakane yasa ba tare da ya iso inda sukeba ya nufi kitchen da sauri mai kama da gudu ruwa ya ɗebo kana ya dawo.
Yana isowa gab dasu, ya zaro idonsa baki ɗaya murya can sama yace.
"Mammeyyyyy".
Sai ga ruwan ya kwaɓe a hannunshi shima ya faɗi bisa jikin Yah Jafar a sume.

Gaba ɗaya sun gaza cewa komai sai ambaton Allah.
Da gudu Affan da tun jiya daya dawo dasu Giɗi bai gana da Hamman nasu ba sai yanzu ya nufo Part ɗin.
Jin ƙaran muryar Jamil ne ya sashi shigowa falon da sauri yana cewa.
"Me haka Jamil lfyarka kuwa?".
Turus yayi a bakin ƙofar ganin duk suna cike a falon sun taru wuri ɗaya kowa da irin addu'ar da yakeyi.
Cikin tsaro da fargabar kardai wani abune ya samesu ya nufosu.

Cikin kaɗuwa yace.
"Mamey". Ya kira sunanta da ƙarfi lokacin da idanunshi suka sauƙa bisa fuskar Ummey.
Jiki na rawa ya juyo ya kalli Sheykh dake mgn cikin rawan murya da rauni yake cewa.
"Alhamdulillah! Alhamdulillah!! Alhamdulillah!!! Yah Allah na gode maka bisa wannan rahama da kaimin ko yau ka ɗauki raina burina ya cika, yau gani ga Mameyna a cikin masarautar Joɗa a suffar mutun bani Adam ba tsuntsuwar Boleru ba".
Wani irin kuka ne mai rauni ya kwabce mishi.

Yah Jafar ma kuka yakeyi tare da cewa.
"Alhamdulillah al'ƙadarin Magauta ya karye".
Ummi kuwa da rarrafe ta rusuna gaban Ummey tare dayin ƙasa da kanta cikin rauni tace.
"Barka da dawowa Adalar Uwar gijiyata".
Umaymah kuwa da sauri ta jawo wayar da ta gani kusa da ita.
Saida ta danna sai taga ashema wayar Hibba ce da ta bawa Junainah nayi Game.
Jadda ta dannawa kira.
Yana ɗagawa tace.
"Assalamu alaikum Alhamdulillah Allahu Akbar Jadda! Jadda!! Jadda!!!".
Cike da kaɗuwa Jadda dake kishinƙiɗe ya miƙe zaune tare da kallon Sitti dake yanka mishi lemu wanda tana iya jiyo abinda Umaymah ke faɗa sabida yadda take mgn da ƙarfi.
Wani irin dogon numfashi suka sauƙe a tare jin Umaymah na cewa.
"Alhamdulillah Jadda Aunty Mamey ta dawo Jadda zatonmu da tsammanin mu ya zama gsky Aunty Mameyna ta dawo gata gabanbu Jadda kace Alhamdulillah".
A tare Jadda da Sitti suka fara maimaita kalmar hamdala.

Affan kuwa cikin wani irin sauri ya juya a guje tamkar ƙaramin yaro ya nufi Part ɗin Abbansu.
Yana shiga da gudu yana mai cewa.
"Abba Abbanmu Abbana Mamey Mamey".
Da sauri Gimbiya Samira amaryar Abban ta fito tare da cewa.
"Affan lfy kuwa Abbanku yana fada".
Ai bai kuma bin ta kanta ba ya fito.
Kiciɓis yayi da Hajia Mama tana cewa.
"Kai lfy kuwa kake gudu kamar yaro?".
Ba tare da ya tsaya ba yace.
"Abba nake nema ina yaje Mamye."
Daga nan ya nufi fada.

Ita kuwa Hajia Mama cikin wani irin masifeffen tsinkewar zuciya da fargaban jin sunan da bata ko son jin an kira ta juya ta nufi ɗakinta.

A can fada kuwa bayan sarkin ƙofa yayiwa su Bappa iso cikin ƙaton falon.
Abboi na gaba Bappa da Arɗo Bani da Alhaji Haro suna biye dashi a baya kana sai masu tsaronshi da suka tsaya can bakin ƙofar shiga sabida dakatar dasu da yayi.

Suna shigowa Lamiɗo dake fuskantar Kofar shiga fuska cike da annuri da haiba yace.
"A a a Masha Allah lalle marhabin da Alhaji Abbo lale da zuwa masarautar Joɗa Fulle bandu fullo".
Da sauri Wambai, Dirankadi, Ɗan isa, Ɗan buram, Sarkin fada, Ɗan kade, Galadima Ɗan maliki Chiroma Durbi Ma'aji. Duk suka miƙe tsaye cikin tsananin sakin fuska da alamun sanayya na mutuntaka suka kalli Abboi tare da haɗa baki wurin cewa.
"Marhababika da zuwa masarautar Joɗa".
Sai kuma ɗan zagi ya fara baza rigarsa tare da cewa.
"Sarki ya gaisheka. Sarki yace ayi maka sannu da zuwa fullo Nbandu fullo manyan fada na farin ciki da zuwa ka".
Wani irin murmushi Abboi yakeyi mai cike da kamala ya nufi gaban Lamiɗo.
Har kusa dashi ya isa kana ya rusuna, yayinda Bappa da sauran ke biye dashi a baya.
A hankali ya sunkuyar da kanshi tare da ture hularshi yayi baya da ita.
Cikin alamun shaƙuwa Lamiɗo yasa hannunsa tsakiyar kansa tare da cewa.
"Allah yayi muku al'barka".
Murmushi Abboi yayi tare da cewa.
"Amin ya Allah Baba".
Sabida Lamiɗo yasan Abboi a matsayin ɗansa yake zuwa gareshi yana jin daɗin abokin mahaifin nashi ya sanya mishi albarka".

A hankali ya koma ya zauna ya tanƙwashe sawunshi tare da cewa.
"Barka da hatsi".
"Barka dai".
Lamiɗo yace.
Abba dake gefenshi ne ya kalli Abboi tare da bashi hannu suka gaisa.

Sarkin fada kuwa da sauri ya fito ya umarci hadimai maza da su kawowa baƙin abin taɓawa ai kuwa nan da nan aka cika gabansu Abboi da abubuwan ci da na sha.

Cikin tarin kula Lamiɗo ya kalli Bappa tare da cewa.
"A a Malam liman tafe kuke tare da shine?".
Cikin nitsuwa Bappa yace.
"Na'am tare muke".
Kai Lamiɗo ya jinjina tare da kallon Abboi gyara zama Abboi yayi fahimtar tambayarsa Lamiɗo yayi a hankali yace.
"Ai mutumin ƙasar mu ne zamane da wani babban dalili ya dawo dashi nan ƙasar ku".
Cikin gamsuwa Lamiɗo yace.
"Makiyayinka ne shi?".
Cikin mutuntaka da kunya Abboi yayi shiru dan shi Bappa yafi ƙarfin makiyayinsa a wurinsa Bappa ɗan uwane".
Cikin yin murmushi Bappa yace.
"Eh ni ɗaya daga cikin makiyayansa ne".
Yayi mgnar sabida fahimtar Abboi bazaice hakanba.
Sai kuma suka sake wani sabon gaisuwa.
Nan Babba ke cewa.
"Tare muke da mai ɗauki shi


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login