Showing 312001 words to 315000 words out of 352722 words

Chapter 105 - GARKUWAAA COMPLTE HAUSA NOVEL

17 Oct 2024

30710

da kuma ƙanwata sunzo ganin jikar tamu su sun isa can".
Cikin tarin jin daɗi Galadima yace.
"Masha Allah, Allah ya bada ladan ziyara".
Amin Amin duk suka amsa.
Dai-dai lokacin kuma Affan yasa hannunshi ya ture sarkin ƙofa dake tareshi yana cewa.
"Lamiɗo yana ganawa da manyan baƙi".
Cikin haki da ɗaga murya yace.
"Kai da Allah bani wuri. Abbana nake nema Abba! Lamiɗo!".
Yayi mgnar da ƙarfi tare da kutsa kai cikin falon.
A tare suka juyo suka zuba mishi ido Abba kuwa da sauri ya miƙa tare da cewa.
"Na'am Affan meya faru?".
Cikin haki yace.
"Abba Mamey Lamiɗo Mamey'nmu ta dawo wlh Mamey ta dawo gata can a Part ɗin Hamma Jabeer su Umaymah nata kuwa Mameynmu ta dawo a mutun ba tsuntsuwar Boleru ba".
Kusan a tare gaba ɗayansu suka miƙe banda Lamiɗo dasu Abboi tare da cewa.
"Kai Affan nitsu ka gaya mana".
Cikin kaɗuwa ya kamo hannun Abban nasu tare da cewa.
"Zo muje ka gani wlh Mamey na ta dawo a mutun ba tsuntsuwar Boleru ba".
Ai kafin ma ya rufe baki Abba ya juya da sauri yabi bayan Abbanshi.

Abboi kuwa da Bappa da Arɗo Bani da Alhaji Haro kallon juna sukayi tare da yin murmushin zatonsu ya tabbata jinjinawa juna kai sukayi
Sai kuma Bappa yace.
"Ya ilahi meke faruwa?".
Cikin yin Murmushi Lamiɗo yace.
"An tashi taron fada sai gobe".
Nan take duk sauran suka miƙe suka fita kowa ya nufi muhalli sa cike da alhini.

Shi kuwa Lamiɗo Galadima ya kalla tare da cewa.
"Muje gidan Jabeer ɗin Kuma taso muje ƙofar surkin naku".
Yayi mgnar da yaƙini a ransa su Bappa ne ke tafe da abinda suka daɗe suna tsumayin wato dawowar Mamey (Ummey) kenen.

Ai kuwa da sauri su Bappa suka bi bayansu.
Fadawa na musu rakiya.
Ɗan zagi na baza riga da cewa.
"Gyara kimtsi, sarki ya gaisheku".

A haka suka nufi Part ɗin Sheykhhhh.
Kusan a tare suka isa dasu Abba dan rawan da jikinsa keyi ya hana masa yin sauri.

Lokacin ɗaya kuma duk masararutar Joɗa ta cika da lbrin dawowar Mamey kamar yadda labarin juyewarta da bacewarta ya karaɗe ko ina na Masarautar Joɗa.

Suna shiga Affan yaja hannun Abbansu har gaban Shatu da Sheykh wanda ke ruggume da Ummey har yanzu a sume.
Sun kasa taɓuka komai, duk da shi dai Sheykh ya gane a sumen take.

Cikin haki Affan yace.
"Gata Abba ka gani ga Mameynmu".
Wani irin farin ciki ne mai masifar yawa dake shirin ɗauke masa numfashin sa ne ya sauƙo mishi, jin hakane yasa yayi sauri ya sunkuya a tsakiyar falon ya fuskanci al'ƙibla ya faɗi yayi sujjada gaban Ubangijin talikai sarki buwayi gagara misali.


Dai-dai lokacin su Lamiɗo suka shigo.
Ganin Bappa ne yasa kukan Shatu tsananta murya na rawa tace.
"Bappa Ummey na Bappa Ummey na".
Da sauri irin na sarakuna su Lamiɗo suka ƙara so wurin.
"La ha ila ha illalalhu Muhammadu Rasulullahi Sallallahu alaihi Wasallam".
Suka faɗa a baki a haɗe tare da zama bisa kujera.

Cikin sanyi Bappa ya kalli Shatu kana a hankali ya juyo yankallesu gaba ɗaya hawayene cikin a fuskarsu.
Ga Jamil a sume.
Galadima kuwa da Lamiɗo murmushi sukeyi tare da maimaita ƙalmar hamdala".
Da sauri Junainah tazo ta faɗa jikin Bappa tare da sakin kuka tace.
"Bappa Ummey na ta rasu ne?".
Da sauri ya jujjuya kanshi tare da juyowa ya kalli Khadijah ƙanwar Shatu cikin sanyi yace.
"Khadijah in akwai zam-zam a gidan kawo min in kuma babu bani ruwan sanyi".
Da sauri Ummi ta miƙe kitchen ta nufa tana mai cewa.
"Akwai zam-zam bari in kawo".
To kawai yace mata.
Abba kuwa a hankali ya ɗago kanshi kana ya jingina bayanshi da sawun Lamiɗo ya kife kanshi bisa guiwar Lamiɗo sai ga wani kuka mai rauni ya subce mishi.

Da sauri Bappa ya amshi goran zam-zam mai sanyin.
Matsowa yayi kusa da Shatu.
Da sauri ya buɗe goran zam-zam ɗin ya tsiyayi sassanyan ruwan a tafin hannunsa, kana ya saita fuskarta tare da cewa.
"BISMILLAHI".
Ya watsa mata shi a fuska da ƙarfi tare da sunan Allah.
Shiru babu motsi da sauri ya sake tsiyayo wani ya watsa mata tare da bismillah.
Stiil ba motsi da ƙarfi ya kuma watsa mata a karo na uku.
Da ƙarfi taja wani irin nannauyan numfashin mai tsawo tare da cewa.
"La'ilahaillaha Muhammadu Rasulullah Sallallahu alaihi Wasallam. Astagafirullaha wa'atubu illaik".
Kusan a tare gaba ɗayansu falon suke furta Alhamdulillah.

Cikin wani irin yanayi Jabeer, Jafar, Jalal, da Jamil wanda Bappa ya watsa mishi ruwan ya farfaɗo a firgice suka matso gabanta sukayi mata zobe.
Kana Umaymah da Mamma da Aunty Rahma suna kusa dasu.
Cikin wata iriyar murya mai raunin amo Sheykh ya kamo hannunta murya na rawa yace.
"M...mah..Mam.. Mameyyy".
Da sauri ta ɗago jajayen idanunta da tsananin ciwon kai ya rinasu ta watsa masa su cikin nashi ba tare da ta amsaba.
Cikin rauni ya kuma cewa.
"Mamey Mamey na Jabeer ɗinki ne! Mamey kin manceni ne, gani Ga Yah Jafar ɗina ga sakalallun tagwayenki ga Affan ɗinki ɗan lelenki ga Abba na Ga ƴan uwanki Umaymahna ga Mamma na ga autar Sitti Aunty Rahma Mamey Jabeer ɗinkin ne ga Ummi amintacciyar jakadiyarki mai riƙon amana".
Shiru sukayi baki ɗayansu suka zuba mata idanu.
Ita kuwa ido ta lumshe wasu hawaye masu ɗumi suka zubo mata cikin raunin murya tace.
"Alhamdulillah Jabeer na tunoku gaba ɗayanku".
Wani irin farin cikin ne mai tarin yawa ya cika musu zuƙatansu baki ɗayansu.

Da sauri suka juyo suka kalli Bappa da yake cewa.
"Alhamdulillah baiwar Allah ta tuno baya ta gane ƴaƴanta da ƴan uwanta".

Da sauri Sheykh ya juyo tare da kamo hannun Shatu wacce cikin kuka da rarrafe ta matso gaban Ummey da kyau murya na rawa hawaye na zuba tace.
"Innalillahi shike nan Ummey ta tuna baya kenan Bappa zata mantani kenan?".
Wani numfashin Ummey taja tare da zubda hawaye.
Ita kuwa Shatu kamo hannun Junainah tayi cikin rawan murya hawaye na kwarya tace.
"Ummey ki kalleni Ummey nice Shatunki fa Ummey koda zaki tuna baya kada ki manceni Ummey kalleni fa nice Shatunki kalli Junainah'nki ƴar autarmu Ummey koda zaki manceni dan Allah kada ki mance Junainah ke kika haifeta a cikinku muka reneta bata san kowa ba sai nudake".
Wani irin kuka ta saki mai ƙarfi tare da jawo Junainah da itama kukan takeyi juyowa tayi ta kalli Yah Sheykh cikin rawan murya tace.
"Ummey nane fa da tun inada shekaru takwas a duniya na bar gaban Dedde na da Abboi na na dawo gabanta ita ta raineni kamar Uwa itace ta haifi Junainah itace ta bamu tarbiya sanadinta muka baro ƙasar Cameroon muka dawo Nigeria muka zauna Rugar Bani wayyoooooooo Allah na Ummeyna kada ki manceni".
Shirun da Ummey tayi yasa gaba ɗaya tausayin Shatu da Junainah yasa kowa zubda hawaye sabida fargabar kada fa ya zamo ta tuno baya can ta mance yanzu.
Kuka sukeyi baki ɗayansu hatta Afreeen dake hannun Aunty Amina kuka takeyi.

Cikin rawan murya Shatu ta kamo hannun Ummey ɗaya Junainah kuwa ta kwantar da kanta bisa cinyar Ummeynta a tare suka haɗa baki wurin cewa.
"Ummey kin mance mune?".
Da sauri Shatu ta saki wani irin kuka tare da faɗawa jikin Ummey jin tace.
"Ban mance kuba Boɗɗo na Autata".
Murmushi sukayi baki ɗayansu falon ita kuwa Shatu da Junainah kukan farin ciki sukeyi.

A hankali Bappa yasa tafin hannunshi ya share hawayensa dake gangarowa hakama Abboi sai suke tuno kamar yau suka samu ɓoleru'n nan.

A cikin masarautar Joɗa kuwa gaba ɗaya labarin dawowar Mamey ya riski kunnuwan mutanen cikinta da kewaye.

Cikin wani irin mamaki Gimbiya Saudatu ta miƙe tsaye tare da kallon Babba Basiru daya kawo mata lbrin cike da kaɗuwa tace.
"Kai Basiru muje mu gani".
Ai kuwa da sauri suka juyo suka nufi Part ɗin Sheykhhhh.

Yayinda Babban ɗan ta Yah Hashim da Laminu mai binshi suka mara mata baya.

Gimbiya Samira ma amaryar Abban da Mom mai bin Mamey da sauri suka nufi Part ɗin Sheykhhhh ɗin.

Gimbiya Aminatu da Matar Galadima ma jiki na rawa suka nufi can.

Hajia Mama kuwa wani irin ihu tayi tare da rugawa a guje ta nufi Part ɗin Sheykhhhh a gigice.

Baba Kamal da ɗansa Sulaiman da sauri suka nufi can.

Dr Aliyu ma da matarsa da ƴarsa Rahima da sauri suka nufi can.

A cikin falon kuwa da sauri Shatu ta amshi gorar zam-zam ɗin da Bappa ke miƙa mata, ta sawa Ummey ita a baki.
Sosai tasha kana ta janye goran.

Da sauri ta miƙowa Aunty Amina hannu alamun ta bata Afreen miƙo mata ita tayi.
Ita kuwa amsa tayi kana ta miƙa wa Ummey ita tare da cewa.
"Ummey sa mata al'barka tunda kece kaka mahaifiyar uba da mai renon Uwa sai ki bawa Dedde na ita tasa mata al'barka itama".
Murmushi Ummey tayi tare da amsarta sai kuma ta kalli Sheykh tare da cewa.
"Jabeer na ya girma".
Murmushi dake baiyana tsantsar jin daɗi sukayi.
Nan suka ɗanyi shiru jin Lamiɗo yayi gyaran murya tare da cewa.
"To Alhamdulillah wannan shi ake cewa ƙudurar Ubangiji babu bawan daya isa kaudashi.
Sai kuma ya kalli Bappa da tare da cewa.
"Dan Allah malam Liman bani lbrin yadda akayi Aisha ta kasance tare daku da kuma sanadin haɗuwarku da samun lfyarta?".

Cikin sanyi Bappa yace.
"Bazamu bari ta hutaba tukun?".
Da sauri Ummey ta jujjuya kai tare da cewa.
"A a Bappa gaya musu kawai domin nasan gaba ɗayansu wannan tambayarce a ransu.
Duk da zanso inji ya lbrin Jaddana da Sittina naga kowa sune ban ganiba".
Cikin sauri Umaymah tace.
"Aunty Mamey Jaddanmu da Sittinmu suna lfy suna gab da tasowa zuwa nan suma".
Cikin tarin farin ciki tace.
"Alhamdulillah to Bappa gaya musu ko ince gaya mana meya faru?."
Shiru Bappa yayi sai kuma ya kalli Umaymah dake cewa.
"Dan Allah gaya mana a wacce suppar ka samu yar uwata a wani yankin".
Cikin nitsuwa Bappa ya gyara zamanshi kana ya ɗan yi gyaran murya a hankali yace.
"Ranar wata jumma'a data gabata tsawon shekaru goma sha uku a can ƙasar Cameroon a yanki dake gefen babban birnin Yahunde cikin Rugar Arɗo Babayo...!
Da sauri suka juyo suna kallon bakin ƙofar shigowa sabida jiyo muryar Hajia Mama daga nesa tana cewa.
"Zancen banza zancen wofi kenan ta yayama za'ayi ta dawo mutun har ta dawo nan cikin masarautar Joɗa".
Ta ƙarashe mgnar da ƙarfi tare da banko ƙofar ta shigo a fijajan.

Yayinda duk sauran tawagar masarautar Joɗa ke biye da ita a baya.
Tana shigowa tayi wani irin zabura tare da zaro idanunta gaba ɗaya sai kuma tayi kan Ummey da gudu.
Da sauri Shatu ta miƙe ta tsaya gaban Ummey tare da cewa.
"Da dakuka cutar da ita kuka fitar da ita haiyacinta da halittar ta a zatonku a haka zata tabbatane?".
Da sauri Sheykh yasa hannunshi ya kamo na Shatu yajata ya zaunar da ita.
Ita kuwa Ummey idanu ta zubawa Hajia Mama tamkar zata manna matasu a jikinta sai jujjuya kai takeyi.

Ita kuwa Hajia Mama ganin idon Ummey cikin natane yasa duk wani sihirinta ya dawowa jikinta kamar yadda Ba'ana yace musu zai bawa Ummey mgnin ƙaiƙayi koma kan masheƙiya duk randa tayi Ido biyu da wacce tai mata sihirin zai dawo jikinta.
Bayan kwanaki biyar zata koma tsuntsuwar Boleru kamar yadda sukayi mata.
A lokacin Bappa yaƙi shi dai yace ta samu lfy ta fara mgn amman da gaiya Ba'ana ya bata wannan mgnin sabida zalumcin da akayi mata ya tsananta.

Cikin wani irin gigita Hajia Mama ta kai hannunta ta taɓa fuskar Ummey tare da cewa.
"Kika dawo mutum kenan bokana yamin ƙarya yace min har abadan yadda matacce bazai dawo duniyaba haka bazaki dawo mutunba bazaki taɓa dawowa Masarautar Joɗa ba."
Sai kuma ta kai hannu ta bugi gefen bayanta ta sosa tare da karkata baki kana tasa hannun ta ɗaya ta cire ɗan kwalin kanta ta cillashi gefe tare da cewa.
"Shigayar balarabiya mai nacin tsiya ki aure min miji ki haife mishi zaratan maza harda tagwaye kana ace cikin ƴaƴan ki za'a samu mai gadar mulkin Masarautar Joɗa ai wlh bazata saɓuba".
Sai kuma ta fara yatsuma gashin kanta tare da kurma ihu.

Cikin wani irin yanayi mai cike da rauni kunya tashin hankali kiɗima gigita.
Affan ya kife kansa da jikin sawun Sheykh ya saki wani irin kunyataccen kuka mai cin rai tare da cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun Hamma Jabeer wanne yanayi ne wannan Hajia Mama take ciki wannan wanne ranane mai cike da kunya Allah ya zai nuna min".
Da sauri suka juyo suna kallon Baba Kamal da yake fifita da hularshi tare da kecewa da dariya yace.
"Hahaha ta haukace ta haukace na haukace, zasu haukace duk zamu haukace.
Shegiya muguwar babarbariya ba ke kikayi mata sihiri ta zama tsuntsuwar Boleru ba kika haukata Jafar ba kika sawa Jamil bin mata Jalal bin mutanen banza bw".
Da sauri ta juyo cikin wani irin rawa-rawan haka na sakayyar mugun aikinta tace.
"Tafi daga nan mugun bafulatanin kai kuma ai kai ne kayi mishi ashirin kashe mishi lfyarsa dan kada yayi aure bare ya haihu kana zaton bansan duk abinda kakeyi bane".
Sai kuma duk suka kece da dariyar hauka tare da faɗi ƙasa sunayi harda tafa hannunsu.

Innalillahi wa innailaihi rajiun hasbunallahiwani'imanwakil waɗannan sune kalaman da gaba ɗaya mutanen falon sukeyi sabida fahimtar sakayyace ta riskesu tun a duniya.
Baba Basiru ne ya matso kusa da Baba Kamal tare da cewa.
"Mugu bashi da kama Kamal kaida Hajia Mama tabbas kun cika mugaye masu cikekkiyar manufa wanda har kuka iya ɓoye muguntarku."
Su dai su Sheykh Umaymah Shatu Lamiɗo Abba Bappa gaba ɗaya zuba sarautar Allah ido sukayi.
Affan kuwa kukane mai cin rai yakeyi cike da kunyar abinda mahaifiyarshi ta aikata.

Shi kuwa Baba Basiru a hankali ya matso gaban Gimbiya Saudatu daketa zazzare idanunta cike da mamakin jin tsantsar muguntar mutanen da kullum take faɗa dasu a zatonta masoyan Sheykh ne.
A hankali ya kalleta kana yace.
"Jabeer yau dai ka yarda ka gamsu da abinda nake ce maka ko".
Cikin yanayi gamsuwa Jabeer ya kalli Baba Basiru wanda mutane ke zato maƙiyinshine har Gimbiya Saudatu ta haɗe dashi bata san cewa ƙididdigarta yakeyi ba.
Shi kuwa Baba Basiru a nitse yace.
"Dama na gaya maka Gimbiya Saudatu sha giri girbauce wautace kawai ke damunta da ƴar hasada, sannan kuma da zugan wannan maƙiyin nata".
Yayi mgnar yana nuna Baba Nasiru wanda ita a zatonta masoyi ta ne.
Cikin gyara tsayuwarshi ya kalleta kana ya kalli shi Baba Nasiru daketa karkarwa cikin zubda hawaye yace.
"Ke Gimbiya Saudatu kullum Nasiru na ingizaki da zugaki da cewa Gimbiya Aisha da ɗan ta Jafar ne suka kashe miki mijinki babban yayanmu Yah Aumalu mahaifinsu Hashim da Laminu wan dan Jafar ya gaji sarautar Galadima ko?".
Da sauri ta gyaɗa kanta.
Yayinda suma duk saura suka zuba mishi ido.
Cikin zubda hawaye yace.
"Toh kinga Yah Nasiru ɗan uwanmu uwa ɗaya uba ɗaya shine ya kashe miki mijinki uban ƴaƴanki sannan yanke ingizaki kan su Sheykh da mahaifiyarsu yasa miki tsanarsu kiketa haushi a kansu kamar karya.
Ita wannan muguwar kuwa Hajia Mama da Kamal da Hashim ɗanki da kuke gani kamar yana son Jabeer alhalin ya tsaneshi shi kuwa wai dan Lamiɗo yafi janshi a jikinshi.
Duk sai suka fake a bayanki sunayiwa Sheykh da ahlinsa mugunta yayinda kowani sai yayi zargin kece kinga kin zama bushiya kamar yadda Shatu ta faɗa a zahiri in anganki jiki duk ƙaya amman cikin bushiya namansa ma maganine su kuma suka kasance belbela siffarsa fara cikinta baƙiƙƙirin".
Cikin rauni Gimbiya Saudatu tace.
"Innalillahi wallahi ni dai Allah ya sani ko garin marke ban taɓa nemowa da niyar cutar dasuba..
Yanzu ashe Hashim kaima muguwar zuciya gareka ban saniba har zaka iya cutar da ɗan uwanka."
Ina Affan kam tuni yake kuka tamkar zai shiɗe dan baƙin ciki da takaicin abinda uwarsa ta aikata.

Yah Jafar ne ya gyara zamanshi tare da cewa.
"Tabbas kuwa Hajia Mama da Baba Kamal da Baba Nasiru da Hashim sune manyan Magautan mu".

Da sauri Sheykh ya miƙa tare da kamo hannun Hajia Mama da taketa son kwaɓe kayanta.
Da sauri ya nufi Side ɗinsa.
A wannan ɗaya ɗakin yasata ya rufeta bayan yayi mata allurar bacci.
Kana ya fito.
Nan ya samu Lamiɗo yasa Fadawan shi sun fita da Baba Kamal dake ta ihun hauka.
Sannan Jalal kuma ya miƙa ya damƙi Baba Nasiru dake son guduwa.
Ya miƙashi hannun abokanshi sojojin daya kira bisa laifin kisan kai.

Shi kuwa Yah Sheykh a hankali ya kalli Yah Hashim a hankali yace.
"Ashe harda kai a cikin magautana Yah Hashim. Kai lallai ɗan Adam darene babu mai saninsa sai Allah".
Lamiɗo ne ya kamo hannunshi ya zaunar dashi kana yace.
"Kai Hashim fice mana daga nan bama buƙatar mai muguwar zuciya ko ɗaya a nan".
Ai kuwa da gudu ya fice cike da kunya.

Shi kuwa Lamiɗo gyara zamanshi yayi tare da cewa.
"Jafar bamu lbrin meya faru da kai da mahaifiyarku a dare ɗaya ta sauya halitta daga mutun zuwa tsuntsuwar Boleru kai kuma ka dena mgn".

Gyara zamansu sukayi baki ɗayansu dan wannan itace tambayar da take cinsu a rai tsawon shekaru goma sha uku kenan gaba ɗayansu.

Cikin gyara zamanshi ya ya fuskancesu kana a hankali yace.
"A ranar...!


Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300 babbancinsu a posting ne 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Ta wannan ac no zaku tura kuɗin sai kiyi screenshort na Debit Alert ɗin ki turo min shaidar biyan ki ta whatsApp 09097853276 ku yan 300 in baku da damar biya ta Account zaki iya sayan katin mtn na ɗari uku kacal sai ki copy numbers ɗin ki turo min ta whatsApp 09097853276.

By
*GARKUWAR FULANI*


Cikin tarin kaɗuwa Umaymah, Mamma, Ummi, suka kalli juna tare da yunƙura suka tashi a tare.
Sabida jin kalmar da Aunty Rahma ke mai-maita wa, da tsananin ƙarfi da karaɗi.
A guje suka nufo falon sabida jin yadda take ƙara auna musu kira babu ƙaƙƙautawa.

Jalal da Yah Jafar da Aunty Juwairiyya dake Part ɗin su kuwa, suma da ƙarfi suku mimmiƙe tsaye, tare da juyowa suka nufo Part ɗin Sheykhhhh.

Dedde kuwa da sauri ta matso kusa da Ummey da nufin sa hannunta ta tallabeta, cike da al'hini al'amarin.

Junainah kuwa da gudu ta iso gareta tare da da faɗa wa jikinta ta ruggume sawunta tare da sakin kuka da ƙarfi sabida ganin yadda gaba ɗaya jikinta ke karkarwar.

Sheykh kuwa da Shatu kafin kiran Aunty Rahma tayi mgnarta ta forko ruggume da ita yayi da kyau tare da cewa.
"Uhmmm kin san ko wanni sirri nawa, har na aikina da yake sirri amman ni kin gaza fitowa fili ki nuna min waye Bappa a wurinki waye Abboi a gareki".
Hannun tasa ta ɗan shafa sajenshi ta buɗe baki da nufin yin mgn kenan suka tsinkayo. Muryar Aunty Rahma.

Wani irin tsinkewa da bugawa


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login