Showing 306001 words to 309000 words out of 352722 words

Chapter 103 - GARKUWAAA COMPLTE HAUSA NOVEL

17 Oct 2024

30705

Juwairiyya na tsaye.
A hankali yaja hannunta suka wuce bedroom ɗinsa.
Haka nan yaita maimaita kiran sunanta tana amsawa.

Shi kuwa Jalal juyawa yayi ya fita.

Affan kuwa a hankali ya kalli Hajia Mama cikin sanyi yace.
"Mama ƴan uwan Shatu sun zo, sai kinga wata yarinya mai kama da Mameynmu, ko muryarsu iri ɗaya, anjima kije ki ganta".
Cikin tsuke fuska tace.
"Toh uban marasa zuciya, kullum kai ke cemin in jene".
Da sauri ya kuma juyo ya kalli Rumaisa yayarshi.
Dake jan dogon tsaki tare da cewa.
"Shi bai san damuwar mutane ba, da kishin uwarsa, kana da rashin kunyar da yarinyar nan kewa Mama kake wani cewa taje taga ƴan uwanta."
Idonshi ya kuma juyowa kan Maman tasu jin tana cewa.
"Barshi sakarai ni ko ƴar da aka haifanma banje na ganiba bare wata can baƙuwar ba hillatanar daji, mitssssss".
Cikin sanyin jiki yace.
"Uhumm".
Daga nan bai kuma cewa komaiba, baisan komai kan makirci mahaifiyar tashi ba, iya saninsshi tana son su Yah Sheykh fiye da yadda take sonshi sai dai wasu lokutan yana zargin tana da wani manufa a kansu.
A hankali ya miƙe ya fita ya nufi Part ɗinsa.

Ita kuwa Hajia Mama cikin fidda numfashi ta kalli Rumaisa tare da cewa.
"Sai gobe zanje duba jaririyar, kuma zanje da garin batur, tabbas zan zuba matashi a baki.
Tana haɗiyewa zai tsistsinka ƴaƴan hanjita ta mutu kowa ya futa, shegu masu yawan haihuwa".
Cikin cin daɗin haka Rumaisa tace.
"Dai-dai kenan".


Gimbiya Aminatu kuwa anayi sallan la'asar taje,.
Tabbas itama tayi mmkin kamannin.
Koda ta dawo ta sanarwa Lamiɗo da Abba da Gimbiya, cikin al'ajabi Lamiɗo yace.
"Yarinyar zata kai shekara nawa?".
Da sauri Gimbiya Aminatu tace.
"To gsky bana ceba dan irin yaran nanne masu jiki ɗan cafal ba wawan girma ku ba ƙaramin ruwa da wuya ka iya ƙiyasce shekarunta kai tsaye".
Wani irin dogon numfashi Abba ya sauƙe tare da cewa.
"Shi Muhammad ɗin zai tambayi yayar tata".
Galadima kuwa cikin nitsuwa yace.
"Uhummm babu shakka akwai abinda ke shirin tabbata daga zantu kan Malam Musa, yace ƴa mace mai kama da ita zata fara zuwa kafin ita.
Amman bai saniba ƴartace ko ba tataba, ya kuma ce mana a haihuwar matar Muhammad ne zai sanadin zuwanta.
Tabbas bawai munyi imani da abubuwan daya faɗa bane. Wasu ma mun mancesu.
Sai dai gashi bayan shekaru goma sha biyu abubuwan daya faɗa sun fara baiyana na aure ba fullatar daji.
Sai kuma batun haihuwarta da zuwan yarinyar koda banga ƴarba inaji a jikina itace ƴarinyar dayake nufin".
Cikin nitsuwa Abba ya gyara zamanshi a hankali yace.
"Ni dai yanzu inga yarinya ce damuwa ta, inji shekarunta.
Domin na sani tabbas kafin Aisha ta haɗu da ibtila'in juyewar halinta wlh tanada shigar juna biyu wanda ita kanta bata saniba, saida na gaya mata.
dan lokacin baifi kwanaki ba.
Kuma har bayan ta juye naci gaba da jin abubuwan da nakeji muddin tanada juna".
Cikin rauni ya ƙarashe mgnar.
Daga nan sukaci gaba da tattaunawa kan batun.

Washe gari yau kwanan Baby uku da zuwa duniya.
Ƴan uwa da abokan arziƙi duk sun zo, kab Masarautar Joɗa hatta matar Galadima da take tsohuwa sosai tazo, sai Hajia Mama ce kaɗai bata zoba.


Zaune suke a falon Shatu.
Lokacin suka dawo daga yiwa Inna Amarya rakiya dan Salmanu yazo ya ɗauke ta ya meda ita gida.
Ya rage Khadijah Aunty Amina da Junainah.
Zaune suke a falon Shatu, Ummi ce zaune gaban Shatu ta zuba mata abinci a plate ta bazashi yayi sanyi.
Kana tana jujjuya zumar data saka mata cikin kunun tsamiyar data dama mata mai citta.
Cikin sauƙe numfashi Aunty Amina tace.
"Oh ikon Allah ko ina da al'adarsu mu ai mai jego in dai abinci yayi sanyi to bazata cishi ba".
Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
"Uhum kinga mu kuma nan sai abincin yayi sanyi ƙalau ma kafin mai jego taci, tai wonka da ruwan sanyi, tasha mai sanyi taci mai sanyi kuma babu abinda ke damunsu".
Hannu Shatu tasa ta amshi ɗan ƙwaryar da kunun yake ciki ludeyin dumar tasa ta ɗan ɗebi kunun ta kurɓa, ido ta ɗan lumshe dan tana jin daɗin shi a bakinta.

Ita kuwa Aunty Amina riƙon da tayiwa Babyn ta gyara tare da cewa.
"Gari banban Allah ɗaya kenan".

Junainah ce ta miƙe tsaye alamun zata fita.
Shatu ce ta ɗan kalleta tare da cewa.
"Ina zakije Junnu?".
Ba tare da ta juyo ba tace.
"Zanje kitchen wurin Adda Khadijah da Sara in tayasu girki".
Sai kuma tayi sauri ta ɗan ja da baya, ganin Sheykh da sauri tace.
"Hamma Jabeer ina kwana".
Murmushi ya ɗan yi tare da cewa.
"Lfy lau Alhamdulillah".
Sai kuma ya ɗan juya tare da cewa.
"Yauwa Junainah jeki kira Adda Shatu kice tazo da Baby".
To tace kana ta koma ciki shi kuma ya nufi ɗauki sa.

Bayan ta gayawa Shatu saƙon nashinne ta juya zata fita kuma tayi kiciɓis da Hajia Mama da hadimanta.
Cikin zuba mata ido Hajia Mama ta ɗan kauda kai ta wuce.
Ummi ce ta ɗan miƙe tare da cewa.
"Sannu da zuwa".
Cikin sakin fuska tace.
"Yauwa Ummin Jabeer ina kishiyar tawa kishiya ban haushi".
Ta ƙare mgnar tana zama bisa kujerar dake gefen Ummi ya zama suna fuskantar juna da Shatu.
Cikin sakin fuska Aunty Amina tace.
"Ina kwana?".
"Lfy lau Alhamdulillah ya yar jikallena?".
Hajia Mama ta faɗa.
"Gata lfy lau".
Aunty Amina ta faɗa tana yunƙurin tashi zata miƙa mata ƴar.
Da sauri Shatu tace.
"A a Aunty Amina kada ki bata ita dan Allah".
Da sauri tace.
"Sabida me?".
Ajiye kwaryar hannunta tayi tare da cewa.
"Haka kawai".
Ta ƙare mgnar tana miƙo hannun ta amshi ƴar.
Tare da jan dogon tsaki kana a hankali tace.
"Aniyar kura tabi daji aniyar moɗa tabi randa, wannan dai nan gani nan bari da izinin ubangiji".
Ta ƙare mgnar tana juyawa ta fita ta nufi falon Sheykh.

Hajia Mama kuwa gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi da masifar takaici da tsanar Shatu da abinda ta haifa dama wanda ya bada cikin dan sune gagararrunta.

Cikin takaici ta miƙe ta fita. Hadiman ta na biye da ita a baya.

Wani irin murmushi Ummi tayi tare da cewa.
"Ɗan Adam kenan mugun icce kai dai kaga mutun baka san me accikin zuciya nai ba".
Cikin mamaki Aunty Amina tace.
"Ikon Allah kai wannan gida naku yana cike da sarƙaƙiya".
Da sauri Ummi tace.
"Sosai ma kuwa".

Har bedroom ta wuce.
Zaune ta sameshi bisa bakin gado.
Da sauri ya buɗa mata hannunshi, ba musu ta raɓa jikinshi.
Ruggume ta yayi tare da sauƙe numfashi a hankali yace.
"I miss you so much".
Ƙamshin jikinshi ta shaƙa tare da cewa.
"I miss U to".
Gyara rungumar da yayi mata yayi, tare da amsar Baby cikin manna mata kiss a goshi yace.
"Baki tambayi sunan ta ba".
A hankali tace.
"Kayi mata huɗuba ne?".
Da sauri yace.
"Tuntini ma tun randa nace miki ko kinada sunan da kike son saka mats, kikace insa sunan Mamey duk da ban gaya miki wacece itaba".
A hankali ta manna kanta da ƙirjinshi tare da cewa.
"Toh ai nasan itace mafi ƙololuwar soyuwa da daraja a wurinmu, tunda koda ban santaba baka gaya min komai a kanta ba.
Na fahimci tafi ko wacce mace daraja a garemu, tunda in kaji wuya ita kake kira kana raki in kaji daɗi ma ita kake fara tunowa.
Nasan tanada matsayi na musamman a rayuwarmu".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Aish sarkin falsafa, to nasa mata sunan Mamey kamar yadda kikace".
A hankali tace.
"Me sunan?".
Murmushi mai sanyi yayi tare da yin ƙasa da murya yace.
"Aisha shine sunan Mamey na, kuma sunan matata sunan ƴata ta fari kuma".
Cikin murmushi tace.
"Masha Allah sunan Ummey nama Aisha ne".
Ruggume ta yayi tare da cewa.
"Iye zuriyar Aysha's kenan".
Da sauri ya zaro ƙaramar wayarshi.
Murmushi yayi ganin
3bala'i.
Da sauri ya ɗan janye jikinshi gareta.
Amsa kiran yayi tare da karawa a kunne tare da cewa.
"Uhumm ya akayi ne".
Cikin huci Hajia Mama tace.
"Jahan wlh zan kashe mutanen nan baki ɗaya in huta".
Da sauri ya miƙa ya nufi cikin Bathroom yana juyowa yana kallon Shatu cikin yin ƙasa da murya yace.
"Dame zaki kashesu?".

A hankali Shatu ta bishi da ido, fahimtar kamar yana buƙatar sirrine baison tasan abunda zai tattauna a wayar ne yasa ta miƙe a hankali ta nufi side ɗin ta.
Bayan ta gyarawa jaririyar kwanciya bisa gadonshi.

Shi kuwa Sheykh a hankali ya sauƙe ajiyan zuciya jin Hajia Mama na cewa.
"Wallahi nayiwa kaina al'ƙawarin tabbas ranar suna zan kashe ƴarinyar nan cikin buzun al'ada da za'a naɗeta, tabbas da ita zan fara kafin inbi ta kan uwar da uban su ƙannen dama a tafin hannuna suke, yayan kuwa majanunine".
Cikin danne tashin hankalinsa yace.
"To wai meya hatsalaki hakane?."
A fusace tace.
"Yanzu na baro ƙofar Sheykh wlh naje da garin batur a hannuna zan turawa ƴar shi a baki, wannan fitsarerriyar ƙauyen matar tasa ido cikin ido tace.
Kar a bani ƴarta ita bata so.
A gabana ta amshi ƴar ta fita inaga ɗakin shegen ustazun ta tafi".
Cikin danne dariyarsa yace.
"To bari yanzu ina cikin uzuri anjima zanzo muyi mgnar dake".
To tace kana ta katse kiran".

Shi kuwa Sheykh a hankali ya fito.
Ganin bata ɗakin ne ya sashi sauƙe ajiyan zuciya.
Yana murmushin wautar Hajia Mama
Ya fito falo.

Dai-dai lokacin kuma Junainah data shigo da tray'n breakfast ɗinshi ta ajiye bisa Dinning table.
Shiru tayi tana jin kukan tsuntsayen dake cikin Garden ɗin, a hankali ta juyo ta sauƙa kan steps ɗin.
Ganin tsaye ne yana kallonta yasa ta ɗan matsoshi.
A hankali tace.
"Hamma Jabeer wannan kukan tsuntsayen fa a ina suke?".
"Cikin Garden suke nan baya".
Da sauri tace.
"Ayyah dan Allah ta ina hanyar zuwa wurin yake".
Cikin tsareta da ido yace.
"Zaki jene?".
Kai ta gyaɗa alamar eh.
"Toh me zakiyi a can?".
Ya kuma tambayarta
"Zanje inga tsuntsayen ne ina son kukansu daɗin ji".
Kai ya jinjina tare da cewa.
"Gacan hanyar muje in rakaki".
Yayi mgnar yana yin gaba tana biye dashi a baya.
Dai-dai lokacin kuma Lamiɗo da Galadima da Abbanshi suna ciki can bakin ruwan waya sukeyi da Jadda.

A hankali ya tura ƙofar forko kana ya turo ta biyun.
Cikin sauri ta biyo bayanshi tare da cewa.
"Wow masha Allah".
Sai kuma ta lumshe idonta tare da buɗa hannayenta, tana binshi a baya.
Juyowa yayi ya kalleta bisa alamu duk tana jin daɗin iskar dake kaɗawan.
A hankali ta fara juyi tana gaba.
Da sauri yace.
"Ke Junainah tsaya a nan".
Ya faɗa lokacin data nufi inda ɗawisun su yake, da sauri ya nufota, sanin muddin bawai ya gabatar da ita gareshi bane zaiyi ta yagusheta sai in jinin masararutar Joɗa ce ita to nan babu abinda zasuyi mata.

Ita kuwa Junainah hango ɗawisun a gefenta ne, yasa tayi sauri ta nufi inda yake.
Shima ɗawisun kanta ya nufo gadan-gadan.
Da sauri Lamiɗo da Abba da Galadima suka zuba mata ido.
Shi kuwa Sheykh da sassarfa ya biyota yana cewa.
"Junainah! Junainah!! Dawo nan zai ji miki ciwo".
Da ƙarfi ya rumtse idonshi lokacin daya hango ɗawisun ya iso gab da ita ya buɗe fikafikansa a zatonshi ya guneta zai farayi.

Ita kuwa Junainah wani irin murmushi tayi tare dasa hannun kan ƙunɗun ɗawisun ta fara shafawa, shi kuma fiffigensa ya fara kaɗawa yana jujjuyashi.
Da sauri Sheykh ya buɗe idonshi jin shiru sai dariyar ta da yake juyowa.
Lamiɗo kuwa da Galadima da Abbanshi da sauri suka miƙe tsaye suka nufosu cike da al'ajabin ganin ɗawisun ya fara zagayata kamar yadda yakeyiwa dukkan jinin masararutar Joɗa.

Zagayeta sukayi gaba ɗayansu suna kallon tsananin kamarta da Mameyn Sheykh.
Shi kuwa Sheykh cike da mamaki ya zuba mata.
Ita kuwa idonta a lumshe tana jin yadda Ɗawisun ke goga mata fikafikansa a fuskarta.
Cikin gamsuwa Lamiɗo yace.
"Tsuntsuwa tana shunshunar jinina".
Da sauri ta buɗe idonta jin muryar mutun.
Shi kuwa Sheykh Jabeer hannunshi yasa ya kamo nata, da sauri ta matsoshi tare da cewa.
"Sannunku ina kwana".
A hankali Abba ya ɗan matsota hannunshi yasa ya dafa tsakiyar kanta.
da sauri tasa hannunta kan nashi ta dafe hannun nashi a kanta.
Murmushi mai faɗi Abba yayi tare da cewa.
"Allah yayi miki al'barka".
Cikin jin daɗi tace.
"Amin Amin Baba ngd".
Shi kuwa Sheykh murmushi yayi fahimtar tarbiyyar su Shatu da Junainah ɗaya ne suna masifar jin daɗi in akayi musu addu'a da sanya musu al'baka".
Da sauri
Galadima yace.
"Me sunanki?".
Buɗe idonta tayi tare da cewa.
"Sunana Junainah Aliyu Garkuwa".
Da sauri Lamiɗo yace.
"Shekarun ki nawa ne?".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Kaka shekaruna fa da yawa".
Murmushi Abba da har yanzu hannunshi ke bisa kanta yayi tare da cewa.
"Gaya mana mana".
Cikin nitsuwa tace.
"13".
Wani irin dogon numfashi mai nauyi Abba ya sauƙe tare da cewa.
"Alhamdulillah".
Sai kuma ta janye hannunshi daga kanta cikin sanyi yace.
"Uhumm yanzu abu biyu ya rage, muga ko tanada tambarin jinin masarautar Joɗa a tsakiyar kanta kana muga mahaifiyarta".
Da sauri tace.
"Ummey na tana gida, bata zoba".
Cikin son fahimtar manufar Abba Sheykh yace.
"Kuma kuna irin zaton da nakeyi ne?".
Da sauri Lamiɗo yace.
"Aimu namu ma yafi naka ƙarfi".
A hankali yace.
"Toko dole mubi komai a hankali".

Kai suka jinjina kana Sheykh ya nuna mata hanya tare da cewa.
"Koma ciki ina zuwa".
To tace kana ta juya ta tafi.
Su kuwa zama sukayi.
A nan Sheykh yake basu lbrin batun ƙarar da ya shigar kan case ɗinsu Gaini.
Tuni Affan kuwa ya tattara dukkan hujjoji da shaida a matsayinsa na lawyer mai cikar ƙwarewa.
So yama tafi shida Sulaiman da Malam Abubakar.

Gobe za'a zauna a kotun.


Alhamdulillah yau kwana biyar da haihuwar Shatu.
Anata shirye-shirye bikin suna.
Su Umaymah ma yau tunda safe suka iso, ita da Hibba da Aunty Rahma da Mamma da Ishma.
Sai Haroon da Jannart ɗinsa.
Gaba ɗaya gidan ya cika da ɓakin.

Junainah kuwa tun kafin su iso take Part ɗin Mami matar Affan da yaransu Zahra'n Hamma Yusuf ce da tazo take zana musu lalle.

Gaba ɗayansu cike suke a falon.
Sai hadimai dake can kitchen sunata faman aiki.

Umaymah ce riƙe da jaririyar cikin jin daɗi tace.
"Alhamdulillah yau gani riƙe da Yar Jazlaan.
Alhamdulillah ƴarinya kuwa sak Mamey.
Cikin sauri Aunty Rahma ta ajiye cup ɗin da take shan ruwan da shi tare da leƙo fuskar ƴar tace.
"Alhamdulillah kuce dani take kama".
Murmushi Sheykh yayi tare da cewa.
"Sosai ma kuwa".
Jamil ne ya ɗan jujjuya kanshi tare da cewa.
"Yoh ai ke masu kama dake sunada yawa Adda Shatu ina Junainah ne".
Khadija ce ta ɗan kalleshi tare da cewa.
"Uhumm Junainah kuwa Sarkin yawo tun da sassafe ta tafi gidan Affan har yanzu bata dawoba".
Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
"Tanada saurin sabone ba ruwanta kowa natane".
Kai Sheykh ya jingina jikin kujera yana kallon Shatu dake lumshe idonta alamun bacci takeji.

A hankali Jalal ke tafiya tana riƙe da yatsarsa manuniya tana ɗigirgire da sawunta.
Wanda takalmanta ke hannun Jalal ɗaya cikin yawan surutunta tace.
"Yah Jalal lallena zai ɓaci fa.
Ni mu zauna a nan sai ya bushe mu tafi".
Sunkuyowa yayi ya ɗan kalleta fuska ɗauke da murmushi yace.
"Mun isofa Junnu saura kaɗan".
Tura baki tayi dai-dai lokacin da yasa hannunshi ya tura ƙofar tare da sallama a bakinshi.
"Ni dai bana son Junnu Hamma Jabeer yace ba kyau ace Junainah yafi daɗi".
Tayi mgnar tana ƙara riƙo hannunshi.
Da sauri Umaymah ta kalleta ta kuma juyo ta kalli Ishma dake lafe jikin Shatu.
Ita kuwa Junainah da sauri ta saki hannun Jalal tare da rugowa a guje tare da cewa.
"Lah oyoyo Ummey na".
Tayi mgnar tana nufo gaban Aunty Rahma data hango tamkar Ummey'nta.
Da sauri ta tsaya tare da cewa.
"Laah".
Sai kuma ta juyo ta kalli Ishma kana ta kalli Aunty Rahma.
A hankali ta ɗan matsa kusa da Shatu cikin yanayin jin kunya tace.
"Ina kwana".
Ta ƙare mgnar tana kallon Aunty Rahma da suma duk ita suke kallo.
Da sauri Mamma tasa hannunta ta kamo hannun ta jawota kusa da ita kusan a tare sukace.
"Ikon Allah kenan dan Allah kalli kama".
Murmushi Shatu tayi tare da cewa.
"Ai natama dana Ishma wasane na Ummey na da Aunty Rahma shine gaske".
Cikin sauri Jalal yace.
"Dan Allah yaushe Ummeynki zata zo mana ne kam".
Murmushi Aunty Amina tayi tare da cewa.
"Ai kam zata zo wata rana amman ba yanzuba".
Da sauri Aunty Rahma tace.
"Ai kuwa in sha Allah mu kam zamuje mu ganta".
Junainah ce ta ɗan lafe jikin Mamma tana kallon Umaymah a hankali tace.
"Itama ai zata zo taga Baby".
Murmushi Umaymah tayi tare da shafa fuskarta.

Hibba kuwa Jawo Ishma tayi ta ajiyeta kusa da Junainah hota ta fara ɗaukansu tana cewa.
"Masha Allah tagwayen kamanni".
Murmushi Aunty Juwairiyya tayi tare da cewa.
"Wlh kuwa".

Ranar dai haka suka wuni.
Anata hira da raha.


Ranar suna bayan sallan asuba, aka raba goro da dabino.
Kana akayi yanka yarinya taci sunan Ummey kuma Mamey Aisha.
Jamil na shigowa ya faɗawa Umaymah dasu Mamma dake cike a falon.
Da sauri Hibba tace.
"To da wanne sunan za'a kirata?."
Shiru Shatu dake cikin shiga ta al'farma tayi tana kallonsu.

Khadija ce ta ɗan gyara zama tare da cewa.
"Afreen yayi".
Da sauri Jamil yace.
"Sosai ma kuwa kin iya zaɓi mai kyau kamar yadda kike mai kyau".
Murmushi tayi tare da sunkuyar da kanta ƙasa cikin kunya, sai kuma ta tashi da sauri tayi falon Shatu jin Jamil ɗin na cewa.
"Umaymah tayi ko surkaki ce".
Ya ƙare mgnar yana kallon Shatu.
Murmushi sukayi tare da cewa.
"A tayi sosai ma kuwa".
Sai kuma yace.
"Ko dai baza'a bani ita bane Adda Shatu?".
Da sauri tace.
"A a ni kam banceba ba ruwana, ai ina ganinku bini-bini kuna tare".
Sheykh da yanzu shigowarsa ne yace.
"In ka nitsu mu baka ita in Kuma baka bar ƙelle-ƙellen idoba da kallon mata mu habaka its".
Ƙeyarshi ya sosa tare da cewa.
"A ai yanzu na girma na bari ko Yah Haroon."
Ya ƙarashe mgnar yana kallon Haroon dake bayan Sheykh.
Dariya sukayi baki ɗayansu.
Shi kuwa Haroon zama yayi gefen Mamma tare da cewa.
"Ai kam yanzu ka girma".

Ummi ce ta fito daga kitchen da akoshin cike da hanta gashin tukunyar da akayiwa Shatu.
Sai Jannart kuma riƙe da gashin da tayi musu nasu daban.
Sara da Larai kuwa da sauran duk riƙe da manyan Foodflaks suka shigo dasu a hannunsu.
Kana suka koma suka dauko plates da cups da spoons.
A tsakiyar falon suka ajiyesu.

Nan suka taru gaba ɗayansu suka zauna a falon.
Harda Junainah.

Aunty Amina kuma da Khadijah da Shatu falonta suka tafi.
Shi kanshi Sheykh a nan kusa da Umaymah ya zauna a plate ɗaya sukeci shida Haroon.
Ishma da Junainah.
Jannart da Hibba da Aunty Juwairiyya.
Rahma Kuma ita da Mamma Umaymah kuwa ita da Ummi.
Jalal da Jamil.

Affan kuwa yana can Abuja bai dawoba shida Sulaiman da Malam Abubakar sai dai Alhamdulillah shariya tayi kyau babu jeka ka dawo kasan cewar akwai manyan shaidu kuma ga yawan Addu'o'in iyaye da yan uwa kan su Gaini da Addu'o'in masallatan jumma'a kana ga taimakon gskya. Da samun ƙwararren lawyer da kuma sa bakin babban mutum Lamiɗo da Jadda da kuma shi kansa Sheykh.
A ranar kotu ta wonkesu tsab.
Kana akayi ram da Dineal dama sauran ɓata garin jami'an tsaron kasar da suke da hannu cikin irin wannan kitimurmurar.

Shi kuwa Sheykh Affan ya gaya mishi komai amman yaƙi ya yardama suyi mgnar da Shatu da zaran ta fara mishi mgnar sai ya zille yafi son yayi mata ba zata.

Bayan duk sun gama cin abinci ne, kowa wacce ta fesa wonka da kolliya
Sosai sukayi kyau cikin shiga ta al'farma, Hajia Kubra ma tazo.
Dama sauran abokan arziki.


A hankali Sheykh


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login