Showing 39001 words to 42000 words out of 352722 words

Chapter 14 - GARKUWAAA COMPLTE HAUSA NOVEL

17 Oct 2024

30741

cikin gari ya wuce ɗakinsa bayan ya bawa uwarsa lbri.


Koda aka taso sallan jumma'a, anyi mmkin ganin isa bai dawoba, shiru-shiru dai har akayi sallan la'asar babushi, tofa daga nanne hankali ya ƙara tashi.
Cikin kiɗima suka fara shiga daji a duba ko lfy bai dawoba.

Ai kuwa nan maza matasan Fulani suka watse cikin daji,
Bayan sun gama bulayin nemane babushi babu shanunshi, suna cikin zagayawan ne Sale yayi arba da gawar Isa dake malale cikin jini.
Nan suka ɗauki gawa suka koma cikin gari dashin.

Wannan rana hankali Fulanin Rugar Bani yayi masifar tashi, gaba ɗaya ma sai ba'amaida hankali kam ɓatan shanunba,
Hankali ya tashi, ɗauki ɗai-ɗai da akeyi musu ya fara hautsuna musu tunanin,
Gashi kisane da babu wanda za'a iya kamawa, koda aka sanarwa hukar cikin Numan sai suka korasu da case ɗin, sabida a lokacin da suka zo shigar da report babu musulmi a police cikin officers ɗin shiyasa suka korasu da batun.
Salmanu wanda shine ɗan bokon da kan iya jagorantan lamarinsu, yana gadon asibiti, bisa ƙarƙashin kulawar abokinshi badon hakaba da tuni Ba'ana ya kasheshi.

Koda fulani suka hatsala kamar kullum haka Arɗo Yabani ya tarasu ya taushi zuciyarsu, da kuma shawarar, su kai kukanmu ga sarkin Numan ɗin, tunda ya hanasu samun damar ganin sarkin Nuruddeen Bubayero.

Koda sukaje masarautar Numan ɗinma abin da akayi musu a police station, fiye dashi akayi musu.

Dole suka dawo suka nade hannun suka kai kukansu ga, Allah, sai dai sun ɗauki mataken kare kai da kai, bisa shawarar daddatawa cewa kada makiyayan ko manoma su yarda su rinƙa rabuwa a daji ya zama suje tare su dawo tare da hakane zasu gane mai ke musu ɗauki ɗai-ɗai ɗin.

Yau la'hadi tunda safe, Aysha keta shirin komawa makaranta. Sabida hutunsu ya ƙare.

Tafiyan safe takeso tayi shiyasa ta gama shirinta da wuri.

gaba ɗaya suna tsakiyar gida Yayunta maza sune zasu rakata bakin hanya.

Haka nan taji bata son tafiya ta barsu, tsoro mai yawa ya rufeta Especially in tayi tunani da yadda ake kashe makiyayan.

Durƙushe take gaban Bappa yana yi mata masiha mai ratsa jiki da zuciya ya kare nasihar tashi da cewa.
"Allah ya miki al'barka Shatu, Allah ya kaiki lfy."
cikin sanyin murya tace.
"Amin Amin Bappa ngd matuƙa".
Sai kuma ta kalli Ya Giɗinta da ya zuba mata ido tamkar bai taɓa ganintaba, cikin sanyin murya yace.
"Yanzu shike nan zaki tafi ki barmu, ki tafi can ke ɗaya ki zama baki da kowa naki a kusa".
Haka nan kalamanshi ya karyar mata zuciya, sai kuma taji hawaye nason zubo mata.
A hankali tace.
"Ya Giɗi bazan daɗe ba zanzo".
Cikin sanyi Seyo yace.
"Allah yasa ki samemu in kinzo ɗin".
Da karfi ƙrjinta ya bada wani sauti mai karfi, ta buɗi baki zatayi mgna kenan Ya Lado ya ɗanyi murmushi cikin sanyi yace.
"To Shatu Ni zan tafi inje in kunce dabobbin, bazan samu daman rakakiba, Allah ya kaiki lfy, ya ƙaddara saduwarmu kan al'khairi, ki yafe".
Kawai sai taji hawaye na zubo mata, cikin dariya ya Gaini yace.
"To kunga kun sata kuka, Shatu ko dai bakya son komawane?".
Cikin rawan murya tace.
"Inaji bana son rabuwa daku".
Murmushi inna tayi tare da cewa.
"Ai kuwa dole ki rabu damu, domin lokaci yazo".
Ummey dai ido ta zuba musu.
Shi kuwa Ya Lado da murmushi a fuskarshi ya fita yana ɗaga mata hannu.
Bappa ne ya ɗanyi murmushi cikin sanyi jiki yace.
"Maza tashi ki tafi, ki gaida Aminiyarki Rafi'a, Seyo Giɗi Gaini ku rakata har bakin titi".
Da sauri suka miƙa.
Ita kuwa Aysha kamo hannun Junainah tayi wacce tayi kasake tana kallonta cikin sanyi tace.
"Ƙanwaliya, sai na dawo".
Kai ta gyaɗa mata cikin sanyin da sam ba ɗabi'arta bane a hankali tace.
"Addana, bana son ki tafi".
Shafa kan Junainah tayi, kana ta faɗa jikin Inna, tana zubda hawaye, sake Inna tayi sannan ta faɗa jikin Ummey, murya can ƙasa Ummey tace.
"Tashi ku tafi, Allah ya sadamu da al'khairi, Shatu".
Da kuka ta fita, ta barsu jiki a mace.


A hankali suke tafiya tafiya, suna hira, kayan lambu da suka cika mata bakko dashi na hannun Giɗi, jarkan nonon kuma na hannun Seyo, ya Gaini kuma, jakar kayantane a hannunshi, da kwaryan kwan zabbi, kamar dai yadda suka saba, suna tafe suna, hira suna gab da bakin hanya.
Ba'ana ya isosu aka ci gaba da tafiyar,
suna isa motar da zata wuce cikin Yola (Ɓadamaya) na isa,
saida suka samata kayanta, kafin, tazo har zata shiga taji Giɗi na riƙe da hannunta juyowa tayi ta kalleshi cikin murmushi yace.
"Kinsan abinda zamu iya aikatawa a duniya da abinda bazamu iya aikatawaba".
Kai ta gyaɗa mishi alamar eh, murmushi yayi kana yace.
"To ki ƙara yarda zamu zamu zama GARKUWA'nki muddin muna raye."
Murmushi tayi cikin ɗan jin daɗi tasan akan mgmar auren Ba'ana yake nufi.
Ido ta zubawa Ya Seyo shi kuma sai murmushin shi nan yake mata,
Ya Gaini kuwa hawayene ya cika masa ido shiyasa ya juya ya bata baya.
Cikin sanyi Seyo ya matsota kana a hankali yace.
"Ki sanarwa duniya halinda muka ciki in kin samu dama Aysha, ki sanarwa duniya Fulani ba ƴan ta'adda bane ba ƴan bindiga daɗi bane ba kuma ƴan Garkuwa da mutane bane, wasu kesa rigar Fulani ke wanzar da ɓarna da wasu ƙalilan na mugayen daji."
Cikin rauni ta zuba mishi ido tana kallon kekyawar fuskarsa, da gyaɗa mishi kai.
Ba'ana ne ya ɗan kalleta tare da miƙo mata damin kuɗi yace.
"Mata zanyi kewarki, amman ba matsala duk ƙarshen mako zan ke zuwa."
Drivern ne ya katse su da cewa ta shigo su tafi, haka yasa ta juya da sauri ta shiga, yaja suka tafi tana ɗaga musu hannu, suma basu tafiba saida sukaga motar ta ɓace musu.

Juyawa sukayi suka nufi cikin gari.
Shi kuwa Ba'ana da ido ya rakasu a a baiyane yace.
"Zanga ta yaya zaku zama GARKUWA'nnata, dan na fahimci duk bakwa son aurena da ita, toko zanyi mgninku."

Su kuwa basuma juyo sun kalleshi ba.


Ita kuwa Aysha tana komawa ta samu, Rafi'a ta dawo ta gyara musu komai na ɗakinsu, to samun Rafi'a da tayine yasa ta ɗan samu nitsuwa, ranar kam wuni sukayi suna hira, darema haka sukayi ta hirar yaushe gamo.


A Rugar Bani ( Rugar kikan) kenan nake nufi. kuwa, su Ya Gaini suna komawa suka tafi kiwo, kamar dai yadda suka saba, sukaje kiwo lfy suka dawo lfy.

Washe gari ranar Litinin!


Saudia.
Sheykh ne konce, bisa wani fitinenne gado yayi lib cikin tattausan blanket,
bacci yakeji yasa gaba ɗaya jikinsa yayi lakwas sabida jiya a harami ya kwana ɗawafi, shiyasa yana dawowa ya konta. Yanayin wayarrshi na bada ɗan sassanyan sautin,
wani irin ɗan gajeren tsaki yaja, ba tare daya buɗe idanunshiba ya miƙa hannun kan bedside drower'n glass dake kusa dashi, lalubo wayar, yayi tare da ɗan liƙa yatsarsa kan gilashin wayar ya amsa kiran, kana ya ɗauwara wayar bisa kunnenshi a hankali cikin muryar bacci yace.
"Assalamu alaikum, Umaymah".
Murmushi Umaymah tayi cikin son ɗan yar uwartata tace.
"Na'am Jazlaan ya akayi".
Cikin murya baccin ya kuma gyara konciya tare da cewa.
"Umaymah baki amsa sallamar ba".
Da sauri tace.
"Afwan Jazlaan, Wa alaikassalam".
shiru yayi.
ita kuwa murmushi tayi tare da cewa.
"Naji kamar bacci kakeyi ko?".
Murya can ƙasa yace.
"Uhummmm".
Da sauri tace.
"To yi baccin sai ka tashi muyi mgna nasan a harami ka kwana".
Da sauri yace.
"No Umaymah gaya min menene?".
Dan shi a zatonshi ko akan Ya Jafar ɗinshi ne.
Ita kuwa Umaymah cikin hikima tace.
"Uhum dama batun Jazrah ne".
Fuska ya kwaɓe kamar yana gabanta cikin nuna ko in kula yace.
"Menene kuma hakan? Umaymah".
Kai ta jinjina dan tasan a rina, cikin tsare gida tace.
"Ina nufin Jazrah ƴar Ƴayan Sitti Uncle ɗinmu Aliyu".
Numfashin ya ɗan fidda cikin ƙosawa da zancen yace.
"Ni ban santaba. Umaymah zanyi bacci, kaina ciwo.
Kin yarda in katse kiran Please Umaymah kada kicemin a a dan Allah".
Murmushi tayi wato duk yadda mutun ke zaton Sheykh ya wuce tunanin mai tunani a hankali tace.
"Kashe, Allah ya muku al'barka".
Da sauri yace Amin Amin kana ya katse kiran,
hannu yasa ya cusa wayan ƙasan pillow'nshi.
Kana ya gyara konciyarshi afili yace.
"Ni ina zan kai mace? Toma me zanyi da mace a rayuwata.
Zakuna damuna da wata Jazrah mai koɗeɗden fuska".
Daga nan ya lumshe ido yaci gaba da baccinsa.
Haroo dake bakin kofar shigowane yayi dariya kana yace.
"Uhum zaka san me zakayi da ita ai Ustadz ai ba'a gane maci tuwo sai miya ta ƙare, dama kirarinku ustazu ƙalilan iya shege kasiran, wai me zanyi da mace, hmmm miskilanciba ba".
Daga nan ya koma da baya dan dama Sitti ce ta aikoshi ya kira mata Sheykh ɗin, akan yazo yaci abinci kafin yayi baccin wai.
Koda ya koma sanarwa Sitti cewa yama rigada yayi baccin sai suka zauna na nan sukaci gaba da hiransu...

A nan gida Nigeria kuwa cikin Rugar Kikan.
Tunda safe duk makiyayan garin suka tafi kiwonsu.

Sosai suka shiga irin tsakiyar tsaunuka, wasu na nan wasu na can suna dai hango juna da, sabida abu na kiwo bazai yiwu su zauna wuri ɗaya ba, dama sai in zasu komane suke haɗuwa baki ɗayansu.

Misalin karfe uku da rabi na yamma, duk kowa ya fara ɗan zagawa cikin kwazozzobon dake gefensu da. Yin ɗaharan yin al'wala.

Ya Gaini ne ya fara gangarawa cikin korin babu sanda bare wuƙa a jikinshi. Ko buta babu a hannunshi Don akwai ruwa a cikin kwarin dashi suke al'wala, a hankali ya tsuguna yayi buƙatarsa kana.
Ya dawo wurinda suke al'wala ya tsugana yayi al'wala.
A hankali ya yunƙura ya tashi.
Ɗago kanshi da zaiyi yayi dai-dai da.....!
Wasa farin girki, yanzu ake nutsawa ciki.

Da yawa naga basu fahimci banbancin. Garinsu Parvina da kuma Rugar Bani ba. To ku saurara, Rugar Arɗo Babayo, itace Rugarsu Parvina, kuma a can ƙasar Cameroon yanki Yahunde Rugar take.

Sai kuma ɗaya rugar wacce a nan ƙasarmu Nigeria take yankin Adamawa state, wani dalili yasa na sakaya sunayen garuruwa da ƙasar tamu da masarautun. Amman nasan duk mazauna Nigeria Adamawa zasu gane Rugar Kikan nake nufi nasa Rugar Bani Numan nake nufi nasa Shikan, dama duk sauran jihohinmu na sakaya sunayensu sabida wani dalili Amman nasan duk munsan inda tushen ƙabilar ɓachama suke.
Amman ba mmki in medasu yadda zakufi ganewa.
Ba wata ƙasa bace Kautal Nigeria nake nufi🤝🏻🥰

By
*GARKUWAR FULANI*
[📝🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

🐄🕊️🌈🦚🐍🤴🏻💘

*GARKUWA*

PAGE 11

NA
*AYSHA ALIYU GARKUWA*

📝🍇🐄🕊️🌈🦚🐍🤴🏻💘




Littafin GARKUWA na kuɗine turo katin mtn na ɗari uku kacal ta layin nan 09097853276 domin KARANTASHI daki-daki, ko kiyi min TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa, kana sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta WhatsApp number ta 09097853276. Special Group ne 1k cikin mako biyu za'a gaba wani sashi na littafin.



Ido ya zubawa mutanen da yayi arba dasu, dai-dai lokacin daya.
Ɗago kanshi, yayi arba, da wasu mutanen, da shigar hukuma (police), da sauri ya miƙe tsaye yana ware hannun rigarshi da ya naɗe dan yin al'wala, tare da cewa.
"Lfy? Ku su wayene?."
Basu kulashiba, sukayi kanshi gadan-gadan, cikin dakiya yace.
"Me hakan?". Still no respond.
Sai matsoshi da suƙa ƙarayi, cikin dakiya da jarumtar jinin fulani ya gyara tsayuwarshi, yana binsu da ido ganin zagayashi da suka farayi, da ido yake binsu a zatonsa faɗane shiyasa bai guduba, domin, duk da yawansu bai Karaye ba, dan zuciyar gskya ce dashi kana jinin fulani ke yawo a jikinshi.
Su kuwa mutanen, na gabanshi ne ya ɗan fesa mishi wani abu mai kamar turare a fuskarshi.
Da sauri yasa hannunshin wai zai kare fuskarshi, cikin dakiya da haɗe fuska ya buɗe baki yace.
"Me kuka fesa meeeen."
Sai kuma kawai yayi lu ya lumshe idonshi ya faɗi nan kamar gawa.

Da sauri biyu daga cikinsu suka ɗaukeshi tsallaka korin sukayi sukaje suka ajiyesu cikin motorsu dake can bayan lampon dake bayan korin.

So biyun kuma komawa mafakarsu sukayi.

A can wurin kiwon kuwa, Seyo ne ya ɗan kalli Giɗi tare da cewa,
"Bari in shiga muyi al'walan,in mun fito, sai kai da ya Lado ku shiga mu kuma mu tsare dabobbin namu gudun kada su shiga gonakin manoma."
Kai Giɗi ya gyaɗa mishi daga, nan ya gangara ya shiga cikin korin.


Yadda sukayi Ya Gaini haka sukayi mishi, shima.

Giɗi da Ya Lado sunata jira, shiru-shiru ba motsinsu,
ganin hakane yasa, Giɗi ya fara kiransu.
"Ya Seyo!, ku fito mana, Lokacin sallafa na tafiya".
Lado ne ya kalleshi cikin sanyi jiki yace.
"Shiga ka kirawosu".
To yace kana ya juya ya nufi cikin korin,
har yaje inda zai gangara ya shiga sai kuma ya juyo ya kalli Ya Lado cikin sanyi yace.
"Ya Lado ka kula da dabobbin nan fa kada su cutar da manoma kaga kai ɗaya ka rage mai kula dasu, kada ka bari suyi nesa dakai".
Lumshe ido Ya Lado yayi cikin wata sassanyan murya mai cike da rauni yace.
"Zaku dawo ai, kuɗin sai ku kula dasu da kyau in yaso ni sai in tafi".
Kai ya gyaɗa tare da yiwa yayan nashi murmushi ya shige cikin korin.

Yana shiga ya fara dube-dube babusu babu dalilinsu, cikin ciyawa da kozozzaban ya fara leƙawa yana cewa.
"Ya Gaini! Ya Seyo!! Ya Gaini!!!".
Jin shiru babu amsarsu bare motsinsune ya sashi ci gaba da waige-waige tare da cewa.
"Ya Gaini ina kukene? Yaya Seyo, ina kuke ban gankuba, kuyi mgna mana".
Cikin fargaba yake lelleƙa wuraren, da yake ganin mutun zai iya fakewa a wurin.
Yana sunkuyowa cikin wani sunkurun kawai sai ya koma luuu ya faɗa ta baya sabida abinda suka fesa mishin yasashi bacci.

Daga nan suka ɗaukeshi sukaje suka sashi cikin motar da suka saka sauran yayunshi.

Da suke konce kamar gawarwaki.

Tsaye suke jikin motar, yayinda biyu daga ciki dakeda uniform ɗin police officers, kuma suna cikin motar da itama ta police ɗinne.

Ɗaya daga cikin mutun huɗu dake gaban motarne, yasa hannu ya rufe ƙofar, sannn ɗaya kuma ya kira waya, cikin yaren Ɓachamanci yace.
"Mun sace mutun biyar, uku yaran gidan Malam Liman ne, biyu daga ciki yaran gidan Ahaji Horo ne".
Ɗan jim yayi alamun karɓar umarni.
Tsawon daƙiƙu biyar sannan ya ƙatse kiran kana ya juyo ya kalli, sauran tare da cewa.
"Yace ku, ku tafi dasu a cikin motar, ku wuce dasu,inda kuka shirya, mu kuma yace mu ɗan tsaya nan, yanzu zaiyiwa shanun Rugar Malam Liman kiranye da dogon fito.
To in shanun suka nufi inda yake ba mamaki wasu su biyo shanun daga cikin makiyayan, to yace idan sun biyosu mu kashesu!".
Kusan a tare suka sara mishi tare da busa sigarin dake hannunsu.
Nan mutanen cikin motar sukaja, suka tafi.

Su kuma saura mutun huɗun, komawa mafakarsu sukayi.

Can cikin tsunƙurun dajin kuwa.
Ba'ana ne zaune cikin taron matasan ƙabilar ɓachama da a ƙalla sun kai goma, cikin kausasa murya da bada umarni yace.
"Zanyi fito ɗaya zuwa uku, cikin daƙiƙu 10 shanayen Malam Liman da Alhaji Haro da wasu. Zasu baiyana, a nan.
Suna zuwa ku jasu ku fuskanci gabas, ta ƙasar Jihar Gombe zaku ratsa, kana ku nufi ƙasar chadi daga can."
Shiru ya ɗanyi tare da zuba musu idanu, wani irin azzalumi murmushi yayi cikin barbarci ya kalli biyu dake kusa dashi wanda ƴan ƙanwar Bukar ne su barebari ne, cikin izaya yace.
"Kada ku kauda ido akan ko wacce gonar makiyayin da zaku wuce ta gabanshi, ku shiga gonakin manoma, kuyi kiwo a ciki.
Idan manoman suna cikin gonakin in sun muku mgna ku kashesu, sannan ku gudu da dabbobin yankin wurin".
Cikin barbarci ɗaya daga cikin su yace.
"Ba'ana, tsayuwa kiwon bazai ja mana tsaikoba, har cekiyar ya riskemu ba tare da munyi nisa ba".
Murmushi yayi mai cike da fajirci sumar kanshi ya shafa tare da cewa.
"Ba'akana Ku kiwaci duk gonakin manoma, hakanne zai jawo faɗa tsakanin MAKIYAYA da manoman, daga haka saiku gudu, kaga mun jefi tsuntsu biyu da dutse ɗaya, domin su mutanen duniya sun ɗauka duk wanda suka gani da dabobbi yana kiwo, BAFULATANI NE, sam mutane sun kasa ganewa cewa ba sai Fulani kaɗai ke kiwoba, kaga mun tada faɗa mun kwashi dabobbinsu, mun kashesu mun gudu, kuma in sunje kai korafinsu ga hukuma a kamasu ko a korasu ko azagesu, ace suke haddasa faɗa tsakaninsu da manoma, sun zama ƴan ta'adda a idon duniya. Mun kwashe dukiyoyinsu".
Dariya sukayi baki ɗayansu, kana suka sara mishi, juyawa yayi, ya fuskanci gabas kana ya durƙusa, ya zuba guiwowinsa duka biyu a ƙasa, yatsarsa manuniya ta hannun hagu ya kafa a ƙasa, kana yatsarsa ta hannun dama kuma, ya toshe kunnenshi na dama, da ƙarfi ya rufe idanunshi kana, ya tsuke bakinsa ya rinƙa zuro iskar wata zazzafar fito mai bala'in sauti.
Su kuwa sauran duk rufe ido sukayi dan jin fiton sukeyi tamkar zai fasa musu dodon kunne.

Shi kuwa Ya Lado yana cikin kiwonshi kawai yaga gaba ɗaya, shanun sun juya sun fuskanci gabas, kana sun ɗaɗɗaga kunnuwansu sama, daga baya kuwa sunata karkaɗa binɗinsu.
Cikin mamaki yake ratso tsakiyarsu.
Dan in makiyayi yaga dabbobi suna haka yasan akwai abun da suka gani, ko mutun ko iska, ko maciji ko dai wani abu na daban to sukanyi wannan alamar dan sanar da makiyayinsu.
So ganin hakane yasa Lado ya ƙara kutso kai cikinsu.

Su kuwa dabbobin gaba ɗaya fiton da Ba'ana yake hurawane ya cika musu kunne, ai fa a take suka nausa a guje suka fuskanci gabas, da wani irin masifeffen gudu.
Shanu da dawakai na gaba tumaki da awaki na baya hatta belbelun dake cikinsu, suna kiwo binsu sukayi.
Cikin ƙarfi Ya Lado yayi wani irin ihun wanda dashi suke kiran dabbobinsu, amman ina basu juyoba.

Da gudu ya fara binsu kana yana ihun neman taimako a wurin sauran makiyayan su.

Amman da yake gudun dabba dana mutun ba ɗaya ba,
Sun mishi nisa mai tarin yawa, hakanan


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login