Showing 198001 words to 201000 words out of 352722 words

Chapter 67 - GARKUWAAA COMPLTE HAUSA NOVEL

17 Oct 2024

30800

sashi a wani kulan shima

Kasan cewar da yawa ta ɗan yi shi.
Tana gamawa taje ta jerashi a kan Dinning area.
Sannan tazo ta kimtsa wurin.

Tuni kuma an idar da salla.

Affan dake kusa da Sheykh ne ya ɗan matso tare da cewa.
"Hamma Jabeer gacan ragon an kawo mutane nata son tafiya gida suna jiran kayi yankan."
Da sauri yajuya tare da cewa.
"To muje".

Bayan yayi yankanne ya juya ya tafi.
Yasan na cikin gidanma duk shi ake jira.

Affan kuwa a gefen wurin ya tsaya saida aka gama fiɗan dogarin dake raba naman ya yanko hantan yasa a leda ya miƙawa Affan.
Daga nan Affan ya juya ya tafi cikin gida shi kuma yayi ta rabawa mutanen wurin naman.

Yayinda duk sauran mutane gari kuwa aketa tafiya.

A can mayankansu na cikin Masarautar Joɗa nan Sheykh ya nufa shida Lamiɗo da sauran manyan masarautar baki ɗayansu.

Daga nan ya fara yanka bayi masu fiɗa suna amsa suna feɗewa ko wanne ana kaishi sashin maishi.


Affan kuwa kai tsaye Side ɗin Sheykh ya nufa.

A falo ya samu Ummi da Aysha,
ledan hantar ya miƙa mata tare da cewa.
"Gashi a gasawa Dr Liman Sheykh Akarmakallu Hamma Jabeer kafin ya dawo.
Yanacan yanata yanka zai dawo a gajiye a yunwace".
Dariya Ummi tayi tare da cewa.
"Gsky kam Aysha amshi ki fara da wuri".
To tace kana ta amshi ledar.

Kitchen ta wuce. Ummi na biye da ita a baya.

Juyo naman tayi a roba, ta wonkeshi Sannan tasa wuƙa ta fara yankashi dogo-dogon yanka sala-sala.
Kara lallaɓesu tayi, kana ta tasashi a wata robar, al'basa ta yanka mai yawa, dai-dai yadda zaji mata, citta kanamfari Curry da maggi da ɗan gishiri ɗan mitsilili ta tarfa a ciki.
Ta gaggaureyasu.
Kana ta juye a tukunya sannan ta ɗauka a kan gas, tasa wutan dai-dai misali.

Ummi kuwa al'basan taketa gyarawa tana yankawa a wata roba. Attaru da basufa takwas ba ta, gyara kana ta jajjaga matasu.

Tuni naman kuwa yana tsilala yanata ƙamshi ya tsastsafo ruwan jikinshi, ya haɗe da kayan ɗan-ɗano dana ƙamshi.

Jajjageggen Attaruhu da al'basan da Ummi ta miƙa mata, ta amsa. Kana ta buɗe tukunyar, ta juyeshi ciki ta ɗan motsa naman.
Haɗin duk ya shiga ciki.
maggi da Curry ta ɗan ƙara.
Sannan ta rufe tukunyar nan take tafa bararraka bul-bul sai wani irin ƙamshi yake fesorwa.

Jamil da ya shigo da bayi uku ko wanne da roban kayan ciki a ciki an wonkesu fes, hanji an kitsesu gwanin kyau.
Shima ajiye robar hannunshi yayi tare da cewa.
"Wannan ƙamshi shine ƙungiyar yunwa."

"Allah ko Jamil". Ummi ta faɗa tana kallonshi.
Shi kuwa, kanshi ya jinjina tare da cewa.
"Sosai ma Ummi, gashi wannan nakune Sheyky Aunty Ayshan, Mamey ke, Jalal ya kwautar da nashi wa abokinshi".

"To yayi kyau, bari mu fara aikin."
Cewar Ummi juyawa yayi ya fita yana cewa.
"Afa ajemin wannan gashi na Sheykh da yake ta zuba ƙamshi".

"Kaɗan ba". Cewar Aysha dariya yayi tare da cewa.
"Kai Aunty Aysha rowa ba kyau fa".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Yoh naji Affan yace Hammanku zai dawo a yunwace".

Dariya yayi ya fita.

Ummi kuwa tukwane ta ɗauka kana ta kalli Saratu da yanzu ta shigo tace.
"Yanka min al'basan da yawa.
Ke kuma Larai zoki riƙe min mu yayyanka tunda a gyare suke".
To sukace kana duk suka fara aiyukan da tasasu.

Aysha kuwa buɗe tukunyar tayi ganin. Yadda yayi kauri romon yayi yadda takeso. Yanata ƙamshi sai ta ɗauko wani kekkeyan ɗan Foodflaks karamin.
Ludeyi tasa ta rinƙa korfe romon tana sashi a kular da zafin shi.
Saida ta korfeshi kab.

Kana ta rufe kular sannan.
Ta matso kusa da tukunyar ta fara, motsa naman wuta yanaci daki-daki tana motsashi tana gaurayashi.
Yana ɗan kame jikinshi yana ɗan zama kamar gashi wuta.
saida taga ya tsane yadda takeso.
Ta kwasheshi da zafinshi tasashi a kula kana tasa wani a ɗan madaidaicin kula mai ɗan karen kyau.
Rufeshi tayi sannan ta raba romon biyu, a ƙananan kulan.

A tray'n ta jera Foodflaks masu ɗan karen kyau ɗin kana tasa plate spoon and fork, sannan ta ajiyesu gefe.
Kana ta ajiye mai yawan shima gefe.

Inda Ummi take ta matso kana ta fara taya wonkewa tana tsaneshi tana zubawa a tukunya.
Tare da turbuɗeshi da al'basan da citta kanamfari Curry da maggi tafarnuwa da a dai sauran kayan ƙamshi dana ɗanɗano, saida suka gama komai cikin ƙanƙanin lokaci kana.
Su Sara suka kullace wuri.
Sannan Ummi tace to suma suje suyi nasu aikin.
Ta basu duk wani kayan haɗin da zasu buƙata duk da tasan ana kaimusu.


Falon suka dawo suka zauna.
Bayan Ummi ta zubo musu hanta gashin tukunyar ta yarfa musu romon a samanshi.

Plate ta miƙa Aysha.
Da sauri ta jujjuya mata kai tare da cewa.
"Bana cin kayan ciki".
Cikin mamaki tace.
"Allah sarki Aysha am na manta, da ban haɗaki da aikinshiba".
Shiru tayi ganin ta rumtse idanunta tare dasa hannunta ta kama mararta.
"Sannu baki da lfy ko?".
Ummi ta tabayeta cikin kulawa.
Kai ta jinjina tare da cewa.
"A a ba komai ai da sauƙin".

Jalal, Jamil, Affan, Imran, Sulaiman, Y Jafar ne suka shigo a jere.
Kai tsaye Dinning area suka wuce.
Da sauri Ummi tabi bayansu tana cewa.
"Sannunku an gama yankan ne?".
Baki Jalal ya tsuke tare da cewa.
"Inafa aka gama gajiya kawai mukayi muka gudo .
ALLAH ko Hamma Jabeer har tausayi ya bani mutun kusan awa biyu a sunkuye, ba hutu, fuskarshi kayanshi duk sun cika da jini".

Jamil ne yace.
"Ummi da Allah zubo mana abin ci".

To tace tare da shiga kitchen ɗin gaseshen naman ta ɗauko musu.
Ta zuzzuba musu kana Special Arish ta saka musu da haɗin naman da kabejin da Aysha tayi musu.
Sannan ta ɗauko Drinks ta jera musu, nan suka faraci.

A hankali Aysha tace.
"Shine kuka gudo kuka barshi shi ɗaya a can ko?".
Murmushi Affan yayi tare da cewa.
"No Madam Jabeer ba gudowa mukayi ba shi yace mu dawo da Ya Jafar".


Sulaiman ne yayi dariya tare da cewa.
"Yo gskyanta taga an bar mata miji shi ɗaya duk mun gudo".

Dariya sukayi duka.

Sha ɗaya da rabi. Dai-dai ya shigo, cikin tarin gajiya.

Da sallama a bakinshi, da sauri ta buɗe idonta dake rumtse dan ciwon da cikinta keyi.

Su Jalal kuwa daketa hira suna cin abinci da korawa da Drinks mai sanyi ne suka juyo suka kalleshi tare da cewa.
"Sannu Hamma Jabeer sai yanzu kanshi ya ɗan jinjina kana ya wuce.
Cikin kula Ummi ke ce mishi sannu.
" Sheykh sannu da aiki Allah ya maimaita mana".

"Amin Amin". yace kana ya wuce.
Ita kuwa da ido ta rakashi.
Ɗan juyowa yayi ya kalli bayanshi ko ta biyoshi
Ɗan gajeren tsaki yaja tare da kallon duk jikinshi jini ya tsastsalu ga riƙewa da bayanshi yayi sabida dogon sunkuyo.

A falon kuwa cikin kula Ummi tace.
"Sannu ko Aysha dauki tray'n ki tafin masa dashi".
To tace kana ta miƙe a hankali ta nufi cikin kitchen tana jin mararta na kartawa.

Shi kuwa Ɗan juyowa yayi tare da ɗan buɗe muryarshi a gajiye yace.
"Aish! Aish!!".
Juyowa su Affan duk sukayi suna kallon hanyar falonshi, salon yadda ya kira sunan a kan harshenshi da yadda ya fitar da ƙal-ƙalan yasa amon sunan ya fito da daɗin sauraro da armashi na musamman".

Murmushi Sukayi baki ɗayansu,
wannan salo na manya ne.

Ummi kuwa murmushi tayi tana sunkuyar da kanta.
Affan da Jamil kuwa kallon juna sukayi tare da yin Murmushi.

Ita kuwa Aysha a hankali ta fito da tray'n a hannunta ta nufi falon nashi.
Tanasa ƙafarta kan steps ɗin da zai sadata da corridor'n taji muryarshi ta ratsa mata kunne a karo na ukku yace.
"Ahh'ishhhhh".
Cikin sauri ta haura tare da cewa.
"Na'am Yah Sheykh".

Kai Affan ya jinjina tare yin dariya yace.
"Zuwa gidannan yanzu ɗaukan darasi ne kan sarrafa salon so mai zurfi da inƙanci irin na masana ilimin addini, nasu ba irin namu bane na turawa".

Dariya yayi ganin Ummi ta mishi daƙuwa.


Shi kuwa Sheykh a hankali ya kwaɓe fuskarshi.
Tana shiga ya bita da ido sosai shigar da tayi. Yayi masifar amsarta.

Kan dinning table taje ta ajiye tray'n kana ta juyo.
Gabanshi ta zo tare da cewa.
"Gani".
Zo yace a taƙaice ya nufi bedroom tana biye dashi a baya.

Kai tsaye ƙofar Bathroom ya tura ya shiga.
Juyowa ya ɗanyi ganin ta tsaya tare da ce mata.
"Dan Allah kizo nan".

A hankali tabiyoshi.

Tana shiga ya maida ƙofar ya rufe.

Sai kuma yazo ya tsaya gabanta,
tare da cewa.
"Cire min al'kyabbar".
Cike da mamaki ta kalleshi ganin ya tsuke mata fuska ya kuma buɗe hannayeshi ne yasa ta ɗan matso.
A hankali tasa hannunta ta buɗe al'kyabbar.
Juya mata baya yayi.
Ta zare rigar.
Sake juyowa yayi ya fuskanceta sunkuyowa ya ɗanyi tare da cewa.
"Cire min jallabiyar".
Kauda kanta tayi tare dasa hannun ta kan wuyanshi inda masaƙalin jallabiyar suke.
Boturan ta ɓalle kana ta janye hannunta.
Tsaki ya kuma ja tare da kwaɓe fuskarsa da cewa.
"Kiyi sauri ki cire minsu ƙarni nakeji zasu sani amai kuma fitsari nakeji.
Bana son hannuna ya sake taɓa jinin."

A hankali ta matso gabanshi sunkuyowa ta ɗan yi cike da kunyar wai fitsari nakeji.
Ƙasan jallabiyar ta ɗago kana ya sunkuyo ta cire mishi.
Ta ajiye gefe.
Ƙara matsota yayi dagashi sai fararen tattausan gajeren wondo iya guiwa sai boxes dake can ciki
Sai Senegal fara, daya sata cikin ƙugun gajeren wondon.

A hankali yace.
"Ciremin mana". Yayi mgnar yana matsota, a hankali tace.
"Ta yaya?".
Ƙugunshi ya nuna mata.
Tare da cewa.
"Zaro snglet ɗin daga cikin."

Cikin sanyi ta motso kauda kanta tayi gefe, sabida nauyinshi da kunyarshi da kwarjinshi sun mata yawa.
A hankali ta kai hannunta kan ƙugunshi da nufin ta kamo snglet ɗin ta zaroshi sama.
sai kawai yaji sauƙan hannunta kan Sheykh ɗinsa dake ts....!


Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k Normal group 300 ki sayi katin Mtn ki copy NUMBERS ɗin ki turo min ta number nan da nakeyin whatsApp da ita 09097853276. In Kuma special Group kikeso wanda za'a gama Part two a maƙo biyu, to Kiyi min transfer'n ɗin 1k a susuna na Jaiz bank.
0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta wannan number din da ta whatsapp 09097853276.
Banda VTU bana so in kinyi babu ruwana.
By
*GARKUWAR FULANI*

: Ɗinshi, ta ɗan shafa, wani irin Yar-yar haka tsikar jikinshi ta mimmiƙe a take wani abu yaji yana game jikinshi.
Ita kuwa ba tare da ta fahimci ina ta taɓa ba, ta kuma yi sama da hannun hakan yasa yaji.
Kamar tana mishi wani abune da zai iya tafiya da numfashin sa.

A hankali yace.
"Ha'ahhhhsshh".
Da sauri ta juyo lokacin kuma hannunta ya isa kan gunshin.
Zaro snglet ɗin tayi ta gaba.
Kana ta tura hannunta ta baya ta jawo, ta fito dashi, tare dasa hannunta biyu ta ɗagoshi tayi sama dashi.
Karo na forko kenan da taga surar jikinshi ziraran miraran tana cikin haiyacinta.
Domin wacca ranar da har ta riƙe baki robar wondonshi bata cikin haiyacinta.

Cikin wani irin yanayi ta zubawa faffaɗan kekyawan ƙirjinshi ido, wanda tattausan gargasa tsilli-tsilli ya yi masa ƙawanya.

cire mishi tayi.
Kana yace.
"To sasu cikin washing machine ki wonkesu."
To tace kana ta tattarusu ta juya ta nufi inda washing machine ɗin yake.

Shi kuwa sunkuyowa yayi ya cire gajeren wondon ya rage dagashi sai boxes.

Ita kuwa buɗewa tayi ta sakasu ciki.
Da sauri ta juyo jin yana ce mata.
"Amshi wannan ma kisa".
Da sauri tayi ƙasa da kanta sabida ganinshi haka yayi matuƙar zuwamata a bazata.
Ya razanata.
Rumtse idanunta tayi kirib.

Ajiyeshi yayi a kafaɗanta kana ya juya ya shiga cikin bath ɗin.

Ya fara sakarwa kanshi ruwan ɗumi ya kori duk ƙarnin kana ya fara sa sabulu.

Ita kuwa da sauri ta sasu.
Ciki ta wonkesu a gaggauce.

Ta tsanesu, kana ta shanyasu inda taga ya shanya mata zaninta randa suka dawo, rangadin.
Tana gamawa ta fita.

Shi kuwa kusan awa ɗaya yayi yana murza jikinshi.
Allah yasani baya son ƙazanta ko kaɗan bare ƙarnin jini.

Koda ya fito sha biyu tayi, har ta wuce.
Kimtsawa yayi cikin wasu manyan kayan yadi Getzner mai masifar kyau da tsada lemon green kalanshi, sai aikin da aka yarfawa babbar rigar da zare Royal blue, mai ɗan karen kyau.

Hularshi Royal blue da ratshin lemon green da black blue kaɗan kalanshi mai kyau.
Wasu takalma masu taushi da kyau Black blue, wani turare ya fesa mai ɗan karen daɗin shaƙa.

A hankali ya fito falon sabida ƙarfe ɗaya dai-dai lokacin.
A konce ya sameta bisa 3 str da alamun bata da lfy.
Cikin gajiya yace.
"Yunwa nakeji".
Jin hakane yasa ta taso a hankali.
Bayanshi tabi.
Kujera yaja ya zauna.
Ita kuwa gefenshi ta tsaya,
gasesshen naman tasa mishi a plate kana ta tasa mishi daddaɗan romon.
Sannan ta ɗan ɗebi haɗin kebeji da nama tasa mishi.
Spoon and fork tasa mishi kana ta ajiye mishi a gabanshi.
Hannunta ya zubawa ido yana kallon jan lallen da tayiwa yatsunta, sai kuma ya ɗan kauda kanshi.
Ita kuwa flaks ɗin tea ta jawo.
A hankali tayi taku zuwa jikin show glass ɗin shi.
Buɗewa tayi cup and tea spoon ta ɗauka.

Zama tayi jin cikinta na kartawa.

Tea ta haɗa mishi kana ta miƙo mishi amsa yayi tare da cewa.
"Jazakallahu khairan". Tea ɗin ya kurba ba tare da yaci komaiba.

Ita kuwa a hankali ta kifa ƙirjinta kan, table ɗin tare da rumtse idanunta.
Murya can ƙasa tace.
"Amin".
Ido ya zuba mata, har saida ya shanye rabin kofin.
Sannan ya fara cin naman.
Ido ya lumshe jin ɗanɗanon naman ya ratsa mishi jijiyoyin baki, yawunshi sun tsinke.

Yana kallonta yana ci, har saida ya cinye na plate ɗin data zuba mishi tas, kana ya shanye tea ɗin gyatsa yayi tare da cewa.
"Alhamdulillah".
Miƙa wa yayi ya nufi wurin washing hand Baby, wonke hannunshi yayi kana ya kuskure bakinshi.
Zuwa lokacin har an kira sallan azahar ana gab da shiga Masallacin.

Da sauri ya fito. Ba tare da yace mata komaiba.
Ba kowa a falon, sai dai yaji motsin Ummi a kitchen.
Da alamun ta fara suya ma.

Da sauri ya fita, a can masalacin ya samu su Jalal.

Ita kuwa Aysha a hankali ta miƙa ta tattara plete da spoons ɗin da yayi amfani dasu da kofunan, ta fito falon.
Tanata haɗa zufa.

Kitchen ta shiga.
Nan ta samu Ummi da Saratu suna ta aikin suya
Larai kuma tana can tanayi musu nasun.

A hankali tace.
"Ummi kawo in karbeki jekiyi salla kinga har lokacin ya tafi".

Cikin kula Ummi tace.
"Zaki iya kuwa Aysha nafa lura baki da lfy".

A hankali tace.
"Zan iya jekiyi salla".

To tace kana ta fita ta tafi.

Ita kuwa ta amsheta.

Tana idar da salla ta dawo tace.
"Jeki kwanta ki huta".
Batayi musuba sabida tana jin masifeffen ciwon ciki jikinta har rawa yakeyi.

Wonka ta farayi wai ko zata denajin zufar.

Tana fitowa tasa wata tattausan atampa, riga da siket, kalarta orange mai kyau sai rashin yellow-yellow kaɗan a ciki.
Batayi wata kolliya ba, amman tayi kyau sosai kalar kayan yazo kusan iri ɗaya da kalan fatarta,
ɗinkin ɗan ɗagos.
Ɗaurin ɗankwali mai sauƙin tayi.
Kana ta fesa turare.
Da sauri ta konta jin cikin ya murɗa ko mayafin bata yafaba.


Tana kwanciya kiran Hibba na shiga wayarta.
Da sauri ta ɗauka tare da cewa.
"I miss you Hibba".
Murmushi tayi tare da cewa.
"Nanda wata ɗaya dai zakuzo auren Ya Haroon sai kin mana wata uku muma yadda nayi muku".
Dariyar ƙarfin hali tayi tare da cewa.
"Har biyarma zanyi".

A hankali ta juyo ta kalli Ummi dake bakin ƙofa tana sallama.
"Wa alaikissalam. Ummi shigo mana".

"A a sauri nakeyi ki fito Sheykh ne yace kije".

Fuska ta kwaɓe tare da cewa.
"To".
Hibba ce tace.
"Aunty Aysha bawa Ummi wayar".
Da sauri tace.
"To Ummi ga Hibba zaku gaisa".
Murmushi Ummi tayi kana ta juyo tazo ta amshi wayar.
Sannan suka fito tare, da mayafin a hannunta.
Tana worworeshi ne ta nufi falonshi.

A falon ta sameshi, zaune a Dinning area.
Kujera ya nuna mata, a hankali ta zauna.
Shi kuwa tasowa yayi ya dawo kujerar dake kusa da ita.
Foodflaks ɗin ya buɗe, plate ɗin da ya ɗauka a show glass ɗinshi.
Yasa mata Special Arish da haɗin naman da kwai.
Da kuma na Kabejin.
Tura mata gabanta yayi tare da cewa.
"Kici".
Fuska ta ɗan yamutsa tare da cewa.
"Banajin yunwa".

Tea ya haɗa mata tare da miƙo mata yace.
"Kici ko".
Tea ɗin ta amsa sanin ruwan ɗumi ne.

Shi kuwa ido ya zuba mata dole yasa taci.
Bayan ta ɗanci ne yace.
"Meyake miki ciwo".

Kai ta girgiza alamun babu.
Hularshi ya ɗan tura ya maidashi ƙeyarshi kaɗan tare da cewa.
"Kenan ƙarya Ummi tayi cewa baki da lfy kuma tunda gari ya waye bakici komaiba".
Da sauri tace.
"A a ba ƙarya bane".
"Uhumm!". yace tare da tura mata plate ɗin dole taci, kaɗan kana tace ya isheta.

Miƙewa yayi tare da cewa.
"Meke miki ciwo?".
A hankali itama ta miƙa tare da cewa.
"Ya bari".
Kanshi ya gyaɗa tare da cewa.
"To muje kiyi min tausa bayana ciwo".

Ya ƙarashe mgnar yana kamo hannunta suka nufi bedroom.

Da goran zam-zam a hannunshi.
Bedside drower'n ya buɗe.
wasu magunguna ya fitar, ya ɓalli guda biyu a ciki ya miƙa mata.
amsa tayi,
"Sha wannan sauran na wancan wotan ne". Yace mata.
sashi a baki tayi shi kuma ya miƙo mata goran zam-zam ɗin ta sha ta haɗiye mgnin.

Gariyar jikinshi ya zare ya saƙala cikin durowa, kana ya cire rigarma ya saƙala.
Hakama dogon Wondon da hularshi.

Hannunta yaja suka hau kan gadon.
A nitse yace.
"Ɗan daddanna min bayan".
Ya kwanta a kife.
Shiru tayi sabida rawan da jikinta keyi.

Juyowa yayi ya ɗan kalleta tare da cewa.
"Umarnine fa ba shawaraba".

A hankali tace.
"Yah Sheykh cikina marata ciwofa".
Jawota jikinshi ya kontar da ita, kana ya juyata rigingine.
Hannunshi yasa kan cikinta.
A hankali ya ture rigarta sama kaɗan.
kana yayi ƙasa da siket ɗin.

A hankali yake shafa mararta-ta yanayi yana ɗan lallatse wurin da danneshi.
Shiru tayi sabida tanajin daɗin yadda yake matan.
A hankali ya ɗan manna bakinshi kan goshinta.
Kiss ya manna mata tare da cewa.
"Na sani ai baki da lfy, ɓoye min kikeyi. Sannu".
Kanta ta gyaɗa tare da lumshe ido.
Cikin sanyi tayi bacci tare dasa hannunta kan sajenshi lokacin data juyo ta konta a rigingine.

Gyara musu kwanciyar yayi.
Lokacin ɗaya sukayi baccinsu.

Ummi kuwa da Saratu cikin sauƙin suka gama aikin hajji.
Jannama sai gobe.
Bayan sun gama suyan ne, Ummi ta dama musu kunun shinkafa kyau.
tasa manyan flaks.

Sannan ta koma ɗakinta itama ta ɗan kwanta.

A can jihar Tsinako kuwa, sosai fa shirye-shirye bikin Haroon da Jannart ya kankama.
Tuni an haɗa kayan lefe a saura kaiwa kuma sai bikin yazo a kai.
Haroon ya shiga ribibi.
Yau tunda gari ya waye baiyi waya da Jabeer da Ibrahim ba, sai yakeji kamar shekara yayi baiyi mgna da suba.
Kiran Sheykh ya farayi sai kuma ya tuno, yanzu duk inda yake lokacin baccinsa ne, in kuma baiyi baccinba to yana babban uzurin da bazai barshi ya ɗaga wayar Bama.

Umaymah kuwa tunda safe tayi mgn da AYSHA data kirata tayi mata barka da salla.

Ibrahim ma ya kira Jabeer ba'a ɗagaba.
Wayar Aysha kuwa Rafi'a da sauran ƙawayensu duk sun kikkira.
Bappa ya kirata.
Hakama


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login