Showing 156001 words to 159000 words out of 352722 words
wancan kitchen ɗin dake babban falon ba'a taɓa shi ba, hakama Side ɗin Sheykh.
Sai kuma sama wanda shi a rufe yakema, sam babu kowa a ciki.
Sosai fa su Umaymah suka yaba da kyan shirin da akayiwa wurin.
Nan suka zauna a falon.
Umaymah ce ta kalli Jakadiya cikin sauƙe numfashin tace.
"Alhamdulillah, gobe kuma zakiyi musu jagora shida matarshi su zaga ta gaida ahlin masarautar Joɗa, ta gansu su ganta su san juna, gudun kada a haɗu a wani wurin ba'a san junaba".
Wani gwauron numfashin Ummi ta sauke tare da cewa.
"A nan gizo ke tsakar ko ta ya zamu samu, Sheykh yayi wannan al'adar yadda ya dace ake kuma yinta, kinsanshi mutunne mai kunya, koda yana son abunma bare ba wani son abun yakeyi ba".
Cikin yarda da kai Umaymah tace.
"Kada ki damu yana ɗaya daga cikin dalilin da yasani, na zauna sai naga kamun ludeyin zaman nasu."
Haka dai suketa tattaunawa,
Suna nan zaune Gimbiya Saudatu ta shigo tare da hadimanta, kana da Laminu da Baba Basiru da Baba Nasiru.
Cikin isa da ƙasaita ta nufi kujerar da duk canjin da akayiwa falon ba'a canzashi ba sabida kujerace ta masarautar Jalaluddin, cikin isa take taku yayinda ta bawa ƙofar shiga baya.
Cikin gatsali ta kalli Umaymah data tsareta da ido. Kallon uku saura tayi mata kana tace.
"Duk mutun muna fuki abin tsorone. Amman munafurcin balaraben Mutun yafi na kowa muni da bada tsoro.
In banda salon munafurci ayi aure yau kwana uku a gaza fito da amarya a nunata ga mutanen masarauta, bare a fanshi idonta."
Ta ƙarishe mgnar tana kai mazaunanta bisa, Kujerar.
Sai kuma tayi maza ta miƙa, jin muryar Jabeer da yanzu ya shigo, ko mgnar ta, ta ƙarshe baijiba.
Cikin isa da ƙasaita da rashin tsoronta, da kuma tsare fuska alamun Ni bani da lokacin ki, kuma ni ba sa'an yinki bane ya nuna mata hanyar fita da yatsarshi tare da yamutsa fuska cike da ƙarfin zuciya ya kalleta ita da ƙannen Mahaifin nashi yace.
"Fice min daga gida, bacci na dawo zanyi so banda lokacin jin ihunku na kar...!
By
*GARKUWAR FULANI*
[4/12, 8:34 PM] Maman Aslam: Ta ɗan ja tayi sama da bakin ƙafan wonɗon wanda yake na robane bakin a tsuke yake.
Da sauri cikin tsoro da rawan jiki ta saki robar.
Pat ya fetti a jikinshi.
Ganin ya motsa.
Shi kuwa Sheykh Jabeer wani sassanyan numfashi ya ja mai tsawo tare da fesoshi a hankali kana, ya mirgina a hankali ya juya ya kifu cikin kasalan nauyin bacci ya ɗaura kanshi bisa cinyarta,
Kana ya ware hannayenshi da sukayi ɗan tsami sabida pillow'n da yayi dasu.
Ware hannayen yayi tare da miƙarar dasu.
Ya zama tana tsakiyar hannunshi kana kanshi na kan cinyoyinta.
Haɗe hannuyen nashi yayi ya sarƙafe yatsunshi wuri ɗaya, ya zama ya zagayeta tako ina yayi mata ƙawanya.
Ya cusa hancinsa cikin mayafinta yana mai shaƙar daddaɗan ƙamshin jikinta dana kayanta.
A hankali ya kuma gyara kwanciyarshi da kyau kana yaci gaba da sauƙe sassauƙan numfashin.
Ita kuwa Shatu wani masifeffen tsalle da bugu zuciyarta keyi tamkar zaiyi tsalle ya fito woje.
Gaba ɗaya ida nunta kan sumar kanshi ta zubasu.
Tare da kallon tattausan sajenshi dake kwance lib-lib a gefen fuskarshi.
Wani sassanyan numfashi ta sauƙe tare da lumshe idonta cikin zuciyarta tace.
"Allah shi ƙara".
Sai kuma tayi sauri ta buɗe idonta tana tambayar kanta.
"Allah shi ƙara me ɗin? Ya ƙara ruggumata ko meyeye".
Cikin kauda zancen a ranta ta ɗan muskuta dan janye jikinta. Amman sai ta ji ya riƙeta gam-gam, yana ƙara cusa kanshi cikin jikinta yana mai shaƙar daddaɗan ƙamshin turaren jikinta.
Cikin tsoro murya na rawa a hankali tace.
"Yah Sheykh!".
Karab sautin muryarta ya ratsa kunnuwanshi.
Sai dai ko motsi baiyi ba,
A hankali ta kuma ce.
"Yah Sheykh! Yah Sheykh!!".
Shiru babu amsa sai numfashin da yake fiddawa a hankali yana kuma shaƙan ƙamshin jikinta.
Cikin sanyi ta ɗan ɗago hannunta a hankali tasa taffin tattausan hannunta, ta ɗan rinƙa buge gefen fuskarshi a hankali a hankali tanayi tana cewa.
"Yah Sheykh! Yah Sheykh! ! Tashi wai Affan dasu Yusuf sunzo, shine Affan yace inzo in tasheka".
A hankali ya buɗe idonshi,
Yanayin yadda take ɗan marin gefen fuskarshi da hannunta wanda ke ɗaure da agogo.
A hankali ya ɗago hannunshi ya ɗan kan hannunta ya kamoshi ya riƙe, cikin tsoro ta fara kiciniyar kwace hannunta,
Sai kuma tayi zuru, jin ya ja hannun da ɗan ƙarfi ya kawoshi dai-dai saitin fuskarshi.
Idonshi ya zubawa yatsun hannunta da kullum in ya gansu da jan lalle yake tuna mishi baya.
Da sauri tace.
"Wash Allah na".
Jin ya murɗa hannun ya juyo da fuskar agogon inda zai gani.
Ƙarfe biyu da miti arba'in da ɗaya.
Du-du baccin 40 minutes yayi tazo ta tasheshi.
"Harda zuba min maruka".
Ya faɗa a ransa.
Ita kuwa kan tattausan suman ta ajiye sinsiyar hannunta.
tana jin kanta na sara Especially in ta kalli saitin ƙasan gadonshi."
A hankali ya sake hannunta kana ya yunƙura ya juya rigingine,
ya fuskanci sama, ita kuma tana zaune tana kallon ƙasa hakanne yasa suna fuskantar juna, cikin wani irin yanayi ya zuba mata ido na wasu sakanni.
Shigarta tayi masifar mishi kyau. Kodan tasa kalan kayan da yafi sone.
Cikin muryar bacci yace.
"Shine harda dukana? Meyasa ne ku mutanen garincan kuke son dukan mutun da kallon jikinsa?".
Cikin tura baki tace.
"Cinyana, nagaji kanka nauyi".
Bai janye idonshi a kantaba ya yunƙura ya tashi zaune tare da juyowa ya fuskanceta.
tanƙwashe sawunshi yayi tare da cewa.
"Me zaki kalla a jikina? Woto Kin zama kamar ɓarauniya ko? Me kike son gani? Wani abu kike sone?".
Cikin tura baki tace.
"Nifa tada kai a bacci kawai nayi".
Hannunshi yasa ya riƙo hannunta, yatsunta ya zubawa ido, cikin wata murya mai sanyi yace.
"Masha Allah, kinyi kyau."
Wani irin sanyi taji kalmar tashi tasa mata a ranta, ido ta ɗan ɗago ta kalleshi.
Shima ita yake kallo, ido ya lumshe jin sautin zazzaƙar muryarta a hankali tace.
"Nagode".
Tonƙoshe kansa yayi bisa kafaɗa kana hankali ya sake hannun nata.
Fuskarta ya kalla tare da taɓe baki yace.
"Waya koya miki irin sa lalle Mammeyyyyy nah!? Dan tafi ko wacce mace iya lalle".
Cikin sanyi da nazartar yadda ya kira sunan Mammeyyyyy da yadda lokacin ɗaya idonshi suka fara sheƙin tsastsafo da zafafan hawayen da ba zubowa zasuyiba.
Cikin son gano meke cikin zuciyarsa tace.
"Ummeyy nah ce ta koya min tun ina ƙaramar".
Yatsunta ya jujjuya kana ya miƙe tsaye.
A hankali ya juya ya nufi bathroom sabida baya son ta hango wutar ƙunar dake ransa.
Ita kuma binshi da ido tayi,
tare da langoɓar da kanta tana kallon sharabansa da gargasa yayi musu ƙawanya.
A haka ta shiga wani nazarin tana mai maimaita sunan da taji ya kira da cikekken so shaƙuwa ƙauna tausayi rauni shogoba *Mammeyyyyy.* Ta maimaita sunan a fili.
Shi kuwa Sheykh Jabeer al'wala yayi kana ya fito.
Yayi mamakin ganinta a zaune bata fita ba.
Hararanta yayi ganin yadda taketa kallonshi. Jallabiyar shi ya zura, kana yasa al'kyabbar, tare da sa Hiraminshi.
Sannan ya fesa turare.
Duk inda yayi tana binshi da ido.
Wayarshi da yafi yawan riƙewa ya ɗauka ya zura a al'jihunsa.
Sannan ya nufi bakin ƙofa inda takalminshi suke yana cewa.
"Wannan kallon maitan fa".
Da sauri ta janye idonta.
Cikin daƙilewa yace.
"Kada ki cinyeni da ido fa. Bana son kallo, ko kina bina bashine?."
a hankali ta miƙe tare da lumshe ido ta biyu bayanshi.
Tana gyara mayafinta tare da cewa.
"Ni ban kalleka ba".
"Uhummm." yace a taƙaice.
Kusan a tare suka fito.
Yana gaba tana bayanshi,
Suka fito tsakiyar falonshi.
Tsayawa ya ɗanyi ya gyara masaƙalin Al'kyabbar tashi.
Shiyasa ya zama a jere suke tafiya tana gefen damanshi.
A haka suka fito cikin corridor'n.
Suka doshi Falon cikin kwarjini da dacewa da juna sai ƙamshi da sheƙi zallan kyau sukeyi.
Da Sallama a bakinshi suka kutsa kai cikin falon.
Wani irin dariyar jin daɗi Affan da suke can Dinning area yayi, suna cin abinci da Ummi ta matsa suci.
Wani irin murmushi Yusuf da Aryan ma sukayi tare da miƙewa suka nufi inda uban gidan nasu ke tsaye da kekyawar tauraruwarshi mai haskawa.
Affan kuwa wayarshi ya zaro yana kekkebta musu hoto tare da cewa.
"Ga amarya, ga ango, suna carabki da zallan kyau da ƙamshi".
Murmushi sukayi dukansu, ita kuwa Shatu tana tsaye gefenshi.
A haka su Affan suka iso.
Suna Isa Affan ya ruggumeshi shima Sheykh ruggumeshi yayi tare da make ƙeyarsa.
Da sauri ya janye kanshi tare da cewa.
"Wayyo Allah na yanzu Hamma Jabeer na girma harda yaran nawama ban wuce dukaba".
Murmushi yayi tare da, Ruggume Yusuf da Aryan Allah ya sani yana masifar son yaran nan har gobe bashi da ɗalibai sama dasu yana sonsu so na musamman, duk sanda ya gansu yakan tuna ƙuruciyarsu tun suna yan shekara goma sha biyar-biyar yake tare dasu shi ya horas dasu.
Yana tura irin tarin ƙalubale da suka fuskanta a gasar Polo da kuma irin nasarorin da suka samu Especially Yusuf nashi yana tuna yadda yaran suke sheƙiyanci in sun haɗu, yana jinsu tamkar su Jamil.
Cikin murmushin ya shafa kansu tare da cewa.
"Sannunku da zuwa".
Cikin jin daɗi sukace to.
Bisa kujera ya zauna su kuma suka zauna a ƙasa a gabanshi kan carpet.
Ita kuwa Shatu a hankali ta juya ta nufi kitchen ganin Ummi ta nufi can.
Hibba kuwa na gefensu tana gayawa su Jalal ga Ya Affan fa.
Da gefen idonshi ya bita da kallo.
Har ta ɓacewa ganinsa, Allah ya sani yana son abu blue baya iya cire idonshi kan abu mai kalar shiyasa yake jin baya gajiya da ganinta, da zai samu kada tayi nesa dashi, dan tayi mishi kyau sosai farar fatarta ta fito fes kamar balarabiya ji yake tamkar ya bita duk inda tayi.
Cikin murmushin ya kalli Aryan yace.
"Aryan Ina su Yusuf ƙaramin".
"Alhamdulillah suna lfy Malam".
Kai ya jinjina tare da cewa.
"Masha Allah".
Sai ya kuma kalli Yusuf yace.
"Ina mai sunana baka zomin da shiba".
Murmushi Yusuf yayi tare da cewa.
"Malam baka tambayi Aryan ƙaramin ba da yakeso ya zama kamarka sai ka tambayi mai sunanka".
Dariya sukayi kana yace.
"Ayyah my Aryan, sun kusa tafiya ai in sha Allah Jami'atul Madina zaiyi karatunshi".
Da sauri suka juyo suka kalli Jalal da Jamil da suka shigo da sauri.
Ruggume Affan sukayi suna cewa.
"Oyoyo ya Affan".
Hannu ya basu suka tafa kamar sa'ao',insa ne su.
Cikin dariya yace.
"Tun ɗazu nake kiranku bakwa ɗagawa.
Nace waɗannan ana can cikin hayani ".
Murmushi Jamil yayi tare da miƙawa Yusuf hannu wanda ke cewa.
"Oh wato Affan kawai kuka gani mu ko oho ko".
Cikin ɗan sakin fuska Jalal yace.
"Afwan Hamma Yusuf ya Aunty Zahra da Mama".
"Suna lfy. Sun gaidaku". yace tare da bashi hannun.
Kana suka gaisa da Aryan.
Sannan suka miƙe sukace bari suje wurin Aunty Mami.
Cikin dariya Affan yace.
"Eh kujema kuzo da ita taga matar babban yaya".
Da sauri Jamil yace.
"A a ka kawota da kanka dai".
Ya ƙarshe mgnar suna fita.
Su kuwa cikin yin ƙasa da kai Yusuf yace.
"Uhum dama Malam zamu ɗan shiga wasan daba ne in batsala".
Murmushi mai faɗin Sheykh yayi tare da cewa.
"Wato ku dai har yanzu baku girma da batun doki ba".
Shiru sukayi sai Affan ne yace.
"Tab Yusuf kuma da in ya ga doki bai hauba jikinshi har rawa yakeyi".
Murmushi Sheykh yayi kana yace.
"To muje muyi salla. Tukun tunda sai anyi sallan la'asar za'a fara ko".
To sukace tare da miƙa ganin ya miƙa dan tuni uku da kwata ta wuce.
Affan ne ya kira Ummi tare da cewa suzo zasu tafi.
A tare suka fito kitchen.
Sabbin kuɗi rafa yan dubu-dubu Yusuf ya miƙawa Hibba ƙulli ɗaya dubu ɗari kenan yace.
"Gashi miƙa wa Ummi ta raba muku."
Affan ma ya basu.
Hakama Aryan.
Hibba sai tsalle take tana cewa.
"Yessss my brother's Allah ya ƙara buɗi Amin Amin sukace kana suka juya zasu fita.
Cikin tsare girma Shatu tace.
"Mun gode, a gaida gida".
Gida zaiji sukace kana suka fita suka tafi.
Suma su Ummi wucewa sukayi yin al'wala.
Ana idar da salla kuwa aka fara hawan daba, hawan sarki dama duk sauran shagulgula na gidajen masarautun gargaji yayin wurin taron bikin salla.
MASARAUTAR Joɗa ta cika tayi maƙil da bani Adam.
Haka dai akayi taron lfy aka tashi lfy sai kuma gobe in Allah ya kai rai.
Washe garin ranar da sassafe.
Sheykh ya tafi asibitinshi.
Ko karyawa baiba.
Sai kusan sha ɗaya ya dawo da alamun yunwa da gajiya tare dashi.
A falon ya zauna suna gaisawa da Ummi dan basu gaisaba ya tafi daga masallacin can ya wuce.
Ummi kuwa tasa Shatu ta kai mishi breakfast ɗin shi da yanzu kam in yacima ya zama lunch ne.
Hibba kuwa na can ɗauki tana ƙenƙesa ado.
Cikin isa da ƙasaita Gimbiya Saudatu ta shigo tsakiyar falon babu ko sallama.
Haɗe fuska Sheykh yayi tare da cewa.
"Wannan banzan ɗabi'a na arnatakun baya, dan ko arna yanzu suna cewa konkon, mutun kamar shanu ko mahaukaciya".
Cikin isa ta iso tsakiyar falon.
Dai-dai lokacin kuma Shatu ta fito falonshi.
Cikin shigar doguwar riga mai ruɓi biyu.
Kanta ta ɗago ta kalli Shatu kana ta kalleshi cikin yin dariyar mugunta tace.
"Eh kam tabbas tunda ka auro mahaukaciya dole kasan hali da ɗabi'un mahaukata ai.
Zuwa gaba kaɗan kaima zaka fara ihu da kuka da sume-sume irin na wannan al'janar fulanin daji daka auro ɗin".
Cikin tarin mamaki Ummi ta kalli Shatu ta kuma kalli Hibba da yanzu ta fito, cike da al'hinin ta yaya taji wannan batun ya fasa Masarautar Joɗa yes in dai Gimbiya Saudatu taji to ai shike nan kowa ma zaiji.
Shi kuwa Sheykh ba gane inda soki burutsunta ya nufaba yayi.
Ita kuwa cikin watsa musu kallon ku sakarkaru ne tace.
"Kuna mamakin ta ina naji, cewar ji shekaran jiya iwar haka dai wannan matar tashin tana yashe a sume da ido a wulkice tana ƙarkarwa farfaɗiya kamar mazari ne.
To ai Ni duk wanda yaci tuwo dani miya yasha.
Inada tawa a cikinku duk motsinku ina dashi a tafin hannuna.
Nan gaba kaɗan zamu samu riƙeƙƙiyar mahaukaciya a masarautar Joɗa".
Cikin tsuke fuskarsa yace.
"Yanzu ma ai muna da su mahauka ta kam, ke ɗin me banbancin ki da zararrun".
Shiru yayi ganin yadda Shatu keyin taku a hankali cikin isa ta nufi gaban Gimbiya Saudatu.
Ummi da Hibba kuwa miƙewa tsaye sukayi.
Shi kuwa Sheykh gyara zamanshi yayi tare da ɗaura ƙafarshi ɗaya bisa ɗaya.
Ita kuwa Shatu a hankali ta isa gabanta.
Ido ta zuba mata tare da yi mata kallon tara saura kwata.
Cikin dakkeyar Muryar rashin tsoro tace.
"Toh *Bushiya* mai mugun baya, Bushiya mai bayan ƙayoyi masu kama da allurai, ki buɗe idonki da kyau ki kalleni Ni AYSHA ALIYU GARKUWA ba sa'ar yinki bace uwar mahassadan duniya, in kina cin ƙasa to tabbas ki kiyayi ta curi, ki bar min mijina ya sarara ki far masa rayuwa, ɗan shi ba sa'an yinki bane ki bar min mijina ya huta baya son ihun nan da kikeyi mishi, zan kuma iyan komai dan ganin na kauda dukkan abinda baya so."
Wani irin daɗi ne ya rufe zuciyar Ummi da Hibba Sheykh kuwa ƙafarshi kawai yake kaɗawa yana mai binta da wani irin kallo mai tarin ma'anoni kalmarta ta *Mijina* yake ji tana sa duk wani hudan gashin jikinsa na amsa amon kalmar yana ratsa jikinshi da zuciyarsa haka yasa bai san sanda wani yalwataccen murmushi ya subce mishiba, tabbas Shatu akwai ƙarfin hali.
Ita kuwa Gimbiya Saudatu tsuru tai da ido.
Itako Aysha cikin karsashi tace.
"Na lura ke dabbace, sam bakya gane yarukan mgna na bani Adam, kinfi son sai an miki irin yarukanku na dabbobi.
Kina tsaye da farin yawu a bakinki kina zubda jini.
Yayinda wasu ke bayanki da jini a bakinsu suna fidda farin yawu.
Sokuwar rama mai tsami.
Ni nan da kike ganina da idona tar a buɗe na shigo Masarautar Joɗa, kada ki ganni haka Ni ɗan hakine da zaki iya renawa amman tabbas zan tsole idanun magauta ruwanshi ya tsiyaye.
In kin san fullanci to.
*MIN MI KURORI CITTA NFAMƊA NHEYAH* NI ```DAKKEN YAJIN BORKONE INYI KAƊAN IN KUMA ISHI MUTUN```
Ki tsumayeni tabbas zanyi daka inyi tankaɗe inyi rairaya a masarautar Joɗa!.
Ke ko kallo baki isheni ba domin bata ke akeyi ba da manyan Magauta nakeyi.
Ja mugun bakinki ki fice min a gidana!".
Rab-Rab.
Jalal da Jamil dake da Jafar shigowa ne, suka tafa mata da hannu bibbiyu.
Hakama Hibba. Ummi kuwa ƙasa tayi da kanta.
Shi kuwa Sheykh ƙanƙance idonsa yayi yana kallonsu yana kaɗa ƙafa ya watsa idanunshi cikin na Gimbiya Saudatu yana mata kallon itama ta isheki.
Aunty Juwairiyya kuma da tun ɗazu tana bakin ƙofar shigowa da sauri ta juya ta koma Side ɗin ta.
Ya Jafar kuwa sai murmushi yake tare da dunƙulawa Shatu hannunshi kamar haka👍🏻
Wani irin juyawa Gimbiya Saudatu tayi tare da jan al'kyabbar ta ta fita.
Har taje bakin ƙofa Shatu tace.
"Ki riƙe kalmar mahaukaciya tabbas zakiga mahaukata a masarautar Joɗa zasu baiyana bila'adadin."
Daga nan ta juya ta nufi Dinning area ɗin babban falon.
Ita kuwa Gimbiya Saudatu ta juya ta fita.
Shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya sauƙe ƙafafunshi kana ya miƙa ya nufi falonshi.
Haka nan yaji murmushi na tsubce mishi.
Tabbas ya gamsu da ƙarfin halin Shatu da rashin tsoronta, sai dai yana jiye mata tuggun mutanen da bata san halinsu ba.
Yana shiga yaci abinci kana ya shiga yayi wonka.
Kana ya ɗauki wayarsa.
Jalal, Jamil, Hibba, Ya Jafar, Shatu kuwa zama sukayi a falon cikin mamaki Ummi tace.
"To wacece yar leƙen asirin Gimbiya Saudatu a wannan sashin?
Ya akayi tasan abinda ya faru da Shatu?
Waya gaya mata?
Bayan in banda muyamu.
Ni Juwairiyya, Hibba, Jalal, Jamil, Jafar. Wanda shi baya mgna, ita kanta Shatu bata san meya faruba batasan ya akayi ba.
To waya fitar da wannan zancen a cikinmu?."
Cikin gsky da gsky duk suka ce wlh babu wanda suka taɗawa mgnar Hibba harda ƙollarta tace.
"Wlh ita ko Umaymah ma bata gayawa ba".
To lallai kam akwai buƙatar bincike a tsakanin mu."
Ummi ta faɗa tana mai cike da al'hinin abin.
Ita kuwa Shatu uhummm. Kawai ta iya cewa tayi shiru bata ce komaiba.
Haka dai suka tashi taron.
Sheykh kuwa, number Umaymah ya kira bayan sun gaisa ne yace.
"Uhumm Umaymah wai me kika sani ne ya faru da wannan yariyar shekaran jiya?".
Cikin tsoro da son kauda batun Umaymah tace.
"Wacce yarinyar kuma?".
Fuska ya ɗan tsuke yace.
"Waccar yarinyar dai".
"To bata da sunane ita".
Ta kuma ce mishi.
Cikin gajiya da batun yace.
"To ni ba sanin sunanta nayiba, baku gaya min sunanta ba."
Wani irin murmushi Umaymah tayi tare da cewa.
"Ban gane bafa Jazlaan".
Hannunshi yasa ya ɗan shafi sajenshi.
Yana mai son yasan meya sameta, meya faru da ita, shiyasa a hankali yace.
"Yarinyar dai da kike cewa ɗiyarki!."
Kai Umaymah ta jinjina tare da cewa.
"Laah ni nama mance bamuyi mgnarba, ran sallane tayi aiki ta gaji tunda safe bataci komaiba to ashe tanada olsa shine fa, ta shiga ɗakinka zatayi maka shara ta faɗi ta suma, da kyar aka samu ta farfaɗo suanta kuma