Showing 207001 words to 210000 words out of 352722 words
su jini ɗaya ne, itace bare a tsakaninsu.
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Eh yau kam gani ga Sitti ga Aunty Rahma".
Ta ƙareshe mgnar tana wata mgnar a zuciyarta.
"Uhumm Aunty Juwairiyya kenan, ai dama saida ɗan gari akanci gari da yaƙi, kina matsayin yar uwarsu kuma kike cutar dasu, in da zasu sani da bazasu aminta da keba".
Muryar Ishma ce ta katse mata mgnar zuci da takeyi.
"Aunty Aysha ina Hamma Jabeer".
Kanta ta ɗan shafa tare da cewa.
"Yana Tsinako".
Da sauri tace.
"To shi bazai zo bane?".
Gyara zamanta tayi tare da cewa.
"Zai zo".
"Yaushe?". Ta kuma tambayarta a gajarce.
murmushi ta ɗan yi tare da cewa.
"In Sha Allah gobe zasu zo".
Allah ya kaimu ta tafaɗa tana wasa da jelan gashin Aysha dake bisa kafaɗarta.
Aunty Rahma ce ta ɗan harareta tare da cewa.
"Maza tashi a jikinta ki barta ta huta".
da sauri ta ɗan zame ta sauƙa ita kuwa.
Aysha kai ta ɗan karya tare da cewa.
"Aunty Rahma barta".
Safiyya ce tace.
"Ahyya baki san Ishma bane da shegen surutu da son jiki".
dariya sukayi ganin yadda Ishma ta zumbura baki.
Sitti ce ta miƙe tsaye tare da kallon jikokin nata da yar autar tata, tace.
"Toh maza ku tashi muyi sallan azahar, in mun idar ku isa wurin Jadda ku gaisa."
Kusan a tare suka mimmiƙe, Aunty Rahma ce ta kamo hannun Ishma tare da cewa.
"Jadda ya fita, ai ɗazu ya kirani yace in masa abincin dare, wai ya ɗan fita zai kai dare kafin ya dawo".
Dariya Sitti tayi tare da cewa.
"Uhumm kai Jadda wato ki masa abincin dare. In kun koma kuwa naga wa zai ce ta dafa mishi".
Safiyya ce tace.
"Oh zai ci girgikin yar autarsa".
Ita dai Ramatu murmushi tayi tare da cewa.
Aysha Juwairiyya Jazrah Safiyya mu tafi ɗakina".
To sukace kana suka bita a baya.
Har zasu fitane Sitti tace.
"A a Aysha dawo nan, ke kam baƙuwa tace ga masauƙinki".
Murmushi Aysha tayi kana ta juyo ta dawo sabida tafi gamsuwa da zama kusa da Sitti akan a tsakiyar Juwairiyya da Jazrah dake mata wani irin mayataccen kallo.
Haka dai sukayi sallan azahar,
kana suka fara shirin kamu.
Wanda tuni ango Haroon da tawagar abokanshi sun iso.
Anayin Sallan la'asar suka fara.
Sai gab da magriba suka tashi.
Ranar kusan kwanan zaunen sukayi anata hirar yan uwantaka.
Yayinda Aysha bata gajiya da jin muryar Aunty Ramatu da kallon fuskarta da fuskar Ishma.
Basu samu sun isa wurin Jadda ba.
Sun bari a akan sai gobe da safe in Allah ya kai rai.
A can Tsinako kuwa, gaba ɗaya al'ummar masarautar Tsinako da baƙi abokan Abbansu Haroon dana kakansu Sarki.
Da kuma baƙi na nesa dana kusa duk an kwana cikin shirin, tafiya ɗaurin auren.
Masu tafiya a jirgi ƙarfe tara jirginsu zai tashi.
Masu tafiya a motoci kuma sammako zasuyi.
Sabida sha ɗaya na safe za'a ɗaura auren.
Haka kuwa akayi washe gari da safe masarautar Jalaluddin, ta fara amsar baƙi tako wani saƙo na ƙasar Nigeria.
Fadar masarautar dama farfajiyar ta cika tayi tab da baƙi da ƴan gari, tako ina halarta mutane keyi.
Karfe sha ɗaya dai-dai na safe taron al'ummar musulmi suka shaida ɗaurin auren Haroon da Jannart.
Bayan an ɗan wawwatse mutane duk sun kama hanyar komawa inda suka fito.
Sai Abokan ango da zasu ɗauki ƙawayen Amarya da wasu yan uwa.
Dan amarya dasu Aunty Juwairiyya da Jazrah da Aunty Rahma Ishma da ƙannen mamansu Jannart duk sun tafi a jirgi, da ango.
Safiyyah da Aysha da Azeema da Hibba ne kaɗai suka rage.
Dan Safiyyah ce ta hana Aysha tafiya dasu Auntyr Rahma tace, ita tare zasu tafi.
Haka kuma Sitti ma tace haka yasa koda suke ribibin tafiya ita tana bacci a ɗakin Sitti bisa gadon mulkinta, dan kwanan da sukayi ba bacci yasa duk suna cike da bacci.
Ibrahim da Sheykh kuwa sune suka tsaya da wasu abokan Haroon biyu, sai sunga duk mai buƙatar zuwa ta tafi.
Ƙarfe sha biyu dai-dai Sheykh Jabeer da Ibrahim da Munnir da Mansur abokan Haroon Suka shigo babban falon Sitti.
A nan suka samu Jalal da ya Jafar da Ammar ƙanin Aunty Juwairiyya da Ibrahim wanda shine yayan Jannart.
Sai kuma Goggo Mairo ƙanwar Jadda da kuma sauran yaran Jadda wanda kishiyoyin Sitti suka haifa.
Safiyyah na ganin shigowarsu ta miƙe ta nufi Dinning area fridge ta buɗe ta haɗo musu ya'yan itatuwa masu sanyi, ta gyara kana ta kawo musu.
Bayan sun gaggaisa ne,
Ibrahim ya ɗan kalleta tare da cewa.
"Kun gama shiryawa ko?".
Kai ta gyaɗa mishi al'amar eh.
Sai ta kuma kalli Sheykh dake miƙawa Ya Jafar nonon inabi yana kuma ce mata.
"Sitti fa?".
jujjuya kai tayi cikin falon ta kalli gabas da yamma kudu da arewa.
Gane wai neman inda Sitti takene yasa Goggo Mairo cewa.
"Bata nan ai ta fita".
ɗan miƙewa tsaye tayi tare da cewa.
"Ikon Allah kuma fa da muna nan tare da ita. To ina tayi".
Aunty Salima wacce take itace Babba a yaran Jadda ne tace.
"Nima fa ita nake jira".
Jalal ne ya ɗan kurɓi ruwan sanyi tare da cewa.
"To ko tayi ciki ne".
"Ba mamaki". Goggo Mairo tace.
Cikin nitsuwa Sheykh ya miƙe tsaye, kekyawar al'kyabbar jikinshi ya ɗan buɗa tare da gyara zamanta jikinshi.
Corridor'n da zai sadashi da special Side ɗin Sitti ya nufa, a nitse.
A can bedroom ɗin Sitti kuwa.
Aysha ce tsaye gaban dreesing mirror bayan ta gama ado da kolliyar ta.
Wani dandatsetsen Shadda lace ne mai masifar kyau da taushi tare da sheƙi ne a jikinta, ɗinkin Doguwar rigace.
Ta zauna ɗas a jikinta gwanin burgewa da ban sha'awa.
Kalan kayan sun taimaka kwarai wurin burgewa, dark red wine mai masifar kyau, sai ratsin zare Royal blue mai azabar kyau da sheƙi da aka zubashi suffar zanen ɗawisu.
Turare ta feshe jikinta dashi,
kana ta maida kolbar sannan ta dawo gaban dreesing mirror kujerar ta jawo ta zauna.
Kasan cewar dreesing mirror babbane mai tudu hakama kujerar.
hannu tasa ta fara tsaɓule ribon ɗin da ta tubke himilin gashinta dashi.
A nitse ya iso bakin ƙofar Bedroom ɗin Sitti.
hannunshi yasa ya tura ƙofar,
ɗan wani guntun tsaki yaja tare da sa guiwar yatsunshi biyu ya ɗan ƙonƙosa kofar sau uku.
Kana ya ɗan tsaya gefe.
A hankali ta juyo kanta ta ɗan kalli bakin ƙofar,
har kamar bazata tashi ba.
Sai kuma ta tuna ta rufe ƙofar lokacin da Safiyya ta shigo ta tasheta kan ta tashi ta shirya su tafi.
To da zata shiga wonka ne ta rufe ƙofar dan tana jin kunya kada ta fito tana shiryawa wasu su shigo su sameta.
A hankali ta miƙa tare da juyawa ta nufi ƙofar tana ƙoƙarin warware ɗan kwalinta.
Isowarta bakin ƙofar yayi dai-dai da lokacin ɗaya kuma ɗan buga ƙofar.
Hakan yasa bata gama warware ɗan kwalinba tasa hannu ta buɗe ƙofar dan a zatonta Sitti ce ko Safiyyah.
Tana buɗe ƙofar sai ta ɗan koma da baya, haka yasa bata ganshi ba.
Bai ganta ba.
Kutsa kanshi yayi cikin ɗakin tare da sallama a bakinshi.
kana yasa hannunshi ya maida ƙofar.
Kasan cewar dreesing mirror yana fuskantar ƙofar shigowan ne, yasa. Mutun zai iya ganin abinda ke bayansa muddin yana kallon cikin madubin.
Kanshi a sunkuye da alamu wayarshi yake ɗan lallatsawa.
Haka yasa hankalinshi baya kan madubi.
Ita kuwa Aysha, wani irin sassanyan numfashi ta sauƙe a hankali jin daddaɗan ƙamshin turaren jikinshi.
A hankali ta zubawa bayanshi idanu tun daga kan dudduniyar farar kekyawar ƙafarshi, har zuwa kan tattausan suman dake kwance lib a ƙeyanshi.
Kasan cewar da yasa hiramin yau yayi irin siririn sakun nanne ya tattare gefe da gefen hiramin.
Taku uku yayi ana huɗu ya tsaya cak, ba tare da ya ɗago kanshi ba ko ya juyoba, yace.
"Wannan kallon fa?".
Cikin tsananin mamaki da tsoron al'amarin Sheykh tayi saurin yin ƙasa da kanta.
Shi kuwa Sheykh a hankali ya ɗago kanshi, ya dire idanunshi kan faffaɗan mafubin daya hasko mishi ita ras a ciki.
Shigarta surarta yanayin tsayuwarta da yadda take wasa da yatsun hannunta da kuma sumanta dake zube a kafaɗunta sunyi masifar jirkita mishi jiki da jini da kwanya.
Tabbas jikinshi ne ya sanar mishi ana kallonshi.
Shiyasa yace.
"Wannan kallon fa?".
A zatonshi ma Aunty Rahma ce, ko Sitti dan yasan sun iya tsura mishi ido duk da sun san baya son kallo a rayuwarsa.
Ita kuwa Aysha, Koda tayi ƙasa da kanta digadigin sawunshi ta zubawa ido.
Shi kuwa Sheykh a hankali yaja wani nannauyan numfashi ya sauƙe a hankali.
A hankali ya ɗan juyo fuskarshi ya haɗe tare da cewa.
"Ke da izinin waye kika baro Tsinako kika zo nan?".
A hankali ta ɗan ɗago kanta, kana ta ɗan turo baki,
sannan ta gyara tsuyawarta, tare da cewa.
"Cemin akayi in zo".
Ta ƙareshe mgnar da yin taku biyu zuwa na uku da nufin zata koma gaban dreesing mirror ta ƙarisa shirinta.
Tana isowa gab dashi, da nufin zata wuce da sauri ta rumtse idanunta.
jin ya...
Littafin GARKUWA na kuɗine Special Group 1k a mako biyi huɗu ake gama Part one da two. Normal group Kuma 300 a mako takwas za'a gama Part one da two. Idan kina buƙatar special Group kimin TRANSFER ɗin 1k ta asusuna na Jaiz bank 0005388578 Jaiz bank Aisha Aliyu Garkuwa. Sai kiyi screenshort na shaidar biyanki ki turo min ta wannan number da nakeyin whatsApp da ita 09097853276. In kuma Normal group kikeso na ɗari ukun, shima kiyi min TRANSFER ta ASUSUNA na Jaiz din in baki da halin turowa ta banki to ki sayi katin Mtn na ɗari uku ki copy numbers ɗin ki turo min ta WhatsApp 09097853276. BANA SON VTU KADA KIYI MIN TRANSFER'N DIN KATI BANA SO.
By
*GARKUWAR FULANI*
: Yasa ƙafarshi ya ɗan taɗe mata ƙafa.
Da sauri ta rumtse idanunta tare dasa hannunta ta kamo nashi ta riƙe gam.
Haka yasa bata ida faɗuwar da ta kusa yiba.
Shi kuwa Sheykh fuskarshi ya tsuke tare da sa hannunshi ɗaya ya ɓamɓare hannunta dake ƙamƙame da nashi, kana ya ɗan ture ta.
Da sauri ta kuma riƙo hannunshi jin tayi gefe zata faɗi.
Wani irin ɗan ihun tsoro tasa, jin ta tafi shi kuma ya biyota,
da sauri ta rumtse idanunta jira kawai takeyi taji kanta ya raɗu da ƙasa, sabida tsoro yasa tama mance ta gefen gado take.
Jin ta faɗa kan tattausan katifar gadon Sittine yasa tayi wani irin dogon ajiyan zuciya.
Sai kuma ta buɗe idonta da sauri jin ya faɗo jikinta.
Da sauri ta kuma maida idon ta rufe ganin yadda sukeda kusanci.
Fuskarshi na kan fuskarta, hancinshi na gogan mata gemunshi na bisa haɓarta, goshinsa na kan nata, hakan yasa data buɗe idon nata sukayi kiciɓis da nashi idanun masu kwarjini.
Cikin jan numfashin tace.
"Wayyo Allah na nauyi ƙirjina zai fashe,
Babba da kai zaka fasamin ƙirji".
Ido ya zubawa lips ɗinta yana ganin yadda take motsasu, sai sheƙi sukeyi.
Haka nan yaji yana kusanto da bakinshi ga nata,
da sauri kuma ya maida kanshi tsakankanin wuyanta da kafaɗarta, ya cusa hancinshi cikin tattausan suman kanta da ya baje a kafaɗun nata,
wani irin sassanyan numfashi ya zuƙa tare da ƙamshin gashin kanta da jikinta,
wani irin Yar-yar yaji tsikar jikinshi na zubawa suna miƙewa tsaye.
hannunshi ya cusa tsakanin bayanta da katifar, ya ruggumeta gam-gam a jikinshi.
Shiru tayi tana jin yadda yaketa sunsunar wuyanta yana ƙara matseta tare dasa harshensa yana ɗan lasar fatan wuyan nata.
Tattausan sajenshi na gogar haɓarta, haka yasa tsikar jikinta zubawa.
A hankali ta buɗe idonta ta zubasu kan sajen nashi dake kwance lib-lib tamkar ciyawar dake samun yabanyar safe da yamma.
sai sheƙi yakeyi da ƙamshi,
da sauri ta ɗan maƙe kafaɗarta jin yadda ya manna hancinsa da bakinshi ya manna mata wani irin sihirtaccen kiss mai masifar ratsa jiki da zuciya.
Sosai take jin nauyinshi sabida duk jikinshi ya sake gaba ɗaya nauyinshi ya sakarmata.
Haka yasa tasa tattausan tafin hannunta ta tallabe gefe da gefen fuskarshi cikin jan numfashin tace.
"Ƙirjina kayi nauyi na tuba sauƙa".
Ƙara matseta yayi a jikinshi kana ya maida bakinshi cikin kunnenta cikin dafeffiyar murya yace.
"Waya ce ki jawoni jikin naki?
Kuma da izinin waya kika baro Tsinako kika zo nan?".
Cikin fidda nishi tace.
"Ni ba jawoka nayiba na riƙeka ne dan kar in faɗi.
Zuwa nan kuma ai Umaymah ce tace inzo".
ƙara manna ƙirjinshi da nata yayi sannan yace.
"Na'am wato Umaymah ce Allah yace kada ki fita in ba izinin ta?".
Cikin cinna ɗan bakinta sama tace.
"To ba Mamanka bace".
kanshi ya maido ya haɗe fuskarshi da tata, on expected taji yasa bakinshi kan nata.
Lips ɗin ta na ƙasa ya kama da fararen haƙoranshi na gaba ya ɗan ciza ka ɗan.
da sauri tayi zillo tare da buɗe bakinta zatayi ihu, hakan ya bashi damar lalumar tattausan harshenta yayi mata wani irin masifeffen tsotsa mai gigitarwa.
Ta kasa gane a zahirine ko a mafarki, wani irin kiss yake mata mai masifar ratsa jiki da zuciya.
Tana gaza nazari ko tunanin gane Sheykh wanne iriyar halittace shi a cikin halittun bani Adam komai nashi special ne.
Duk da babu wani ɗan adam daya taɓa sumbatarta tanada tabbacin ba ko wani namiji ya iya irin wannan zazzafan sumbatar Ustazan nan ba.
A hankali tasa tafin hannunta bisa wuyanshi yatsunta ta cusa cikin sumar ƙeyarshi mai sulɓi.
Shi kuwa Sheykh wani irin kanainaye harshenta yayi da nashi ya naɗe nata cikin nashi.
A hankali ya fara zaro nashi cikin nata, wanda haka yasa taji wani abu na mata.
Zir, zir, zir a cikin dukkan sasan jikinta, cikin baƙon yanayin daya cusata tayi wani irin juya harshenta cikin bakinshi ta lalumo harshenshi ta riƙe ƙam ta fara mishi wani irin shan tom-tom har tana bada wani sautin Douh.
Wani irin tsuma da karkarwa jikinshi ya farayi tamkar mazari, hannunshi ɗaya ya zaro ya tallabo kanta da kyau.
Dai-dai lokacin kuma Sitti ta fito daga falon Jadda tazo falonta, nan ta samu su Goggo Mairo duk sun tafi sai Ibrahim da Safiyyah da ƙannen iyayensu.
So bayan sun gaisa da Ibrahim ne take tambayar.
"Ibrahima ina Jazlaan ban ganshi ba tunda kukazo, bai shigoba, ga can jadda ma yace kuje yana nemanku".
Shi dai Ibrahim murmushi kawai yayi yaci gaba da wasa da yaronshi.
Safiyyah ce tace.
"Yana bedroom ɗinki tun ɗazu ma shi muke jira duk kowa ya tafi saura mu.
Su Azeema ma sun tafi da abokan Ya Haroon".
Da sauri ta miƙe ta nufi special Side ɗinta kai saye bakin ƙofar Bedroom ɗinta ta nufa.
Tana isa tasa hannu tana ƙoƙarin buɗewa tare da cewa.
"Jazlaan! Jazlaan!! Jazlaan!!!".
Kamar a wata duniya ko cikin mafarki haka yake jiyo muryar Sitti.
cikin sauyawar tsari ya fara ƙoƙarin janye harshenshi daga gareta, amman ina ta riƙe gam. Cikin sauri ya buɗe idonshi ya zubasu kan fuskarta,
wani irin sanyi yaji yana ratsa zuciyarshi.
Jin motsin turo ƙofarne ya sashi yunƙurawa da ƙarfi ya janye harshenshi tare da janye jikinshi ya miƙe tsaye cikin tsananin kunyar kada Sitti ta shigo ta sameshi a wannan yanayin.
Al'kyabbar ajikinshi ya fara bazawa yana buɗata yana gyarawa.
Ita kuwa Aysha jin yadda ya zare harshenshi da yadda ya miƙene yasata dawowa cikin haiyacinta daga gigitar da ya sakata.
Jiki na rawa ta mike zaune tare dasa tafin hannunta tana goge damshin bakinta cikin tarin azabebiyar kunyarsa.
Sitti kuwa tana shigowa ganinshi tsaye yana murmushi yasata isowa gareshi ruggumeshi tayi cikin tsananin jin daɗi tace.
"Masha Allah. Marhababika ya Habibi, ana Uhubbuk".
Murmushi yayi tare da janye jikinshi gareta kana yace.
"Ana uh hibbuki hubban azeem ya Sitti".
Hannunta tasa ta shafa kansa fuska cike da annurin ganin jika mafi soyuwa a gareta tace.
"Jazlaan me zan kawo maka? me zakaci? me kake da buƙata?".
Murmushi ya kumayi kana ya zauna bisa kujerar sarautar dage gefenshi tare da cewa.
"Sitti na samu komai".
Sai kuma ya ɗan kalli Aysha ta wutsiyar idonshi.
Har yanzu jikinta na tsuma.
Safiyyah ce ta shigo da sallama tare da cewa.
"Ya Sheykh mu tafi darefa nayi".
Kai ya gyaɗa mata alamar to.
Ita kuwa juyowa tayi ta kalli Aysha tare da cewa.
"Kin gama shiryawa ko".
Itama kai ta gyaɗa mata.
har ta buɗi baki zata kuma yin mgna sai tayi shiru jin Sitti na cewa.
"Yauwa to kuzo taso muje Jadda na son ganinku mu tafi ko".
Ta faɗa tana miƙewa tsaye.
Safiyyah ce ta fara binta a baya kana Sheykh.
Har sunje bakin ƙofar fita ya ɗan juyo ya kalleta a fakaice.
Mayafinta take yafawa tare da biyo bayansu.
A falon suka samu Ibrahim, nan ya miƙe yabi bayansu.
Kai tsaye Side ɗin Jadda suka nufa.
Shi kaɗai yake zaune a falon nashi dan ya bar fada yace zai gana da jikokinsa.
Cikin murmushi mai cike da kamala da dattaku, yake kallonsu tare da cewa.
"Lale marhabin da jikokin Sitti da Jadda."
Ya ƙare mgnar yana miƙawa Sheykh da Ibrahim hannunshi, Sheykh ne ya riƙe hannunshi na dama kana Ibrahim ya riƙe na hagu suka zauna suka sashi a tsakiya.
Safiyyah ce ta matso gefen mijinta ta zauna.
Ita kuwa Aysha a hankali ta rusuna zata zauna a gefe, da sauri Sitti tasa hannunta ta kamo nata tare da cewa.
"Matso nan kusa zauna kusa da mijinki shine farin cikinmu.
Yau gamu Allah ya nuna mana matar Sheykh."
Ta ƙare mgnar tana ajiyeta kusa da Sheykh har jikinsu na gogar na juna.
Murmushi mai cike da so da tsammani da zato Jadda yayi tare da cewa.
"Amaryar Sheykh jikar Sitti da Jadda".
Cikin murmushin tace.
"Allah rene Jadda Allah nɓeddu sabbugo".
Wani irin murmushi mai cike da masha hurin daɗi Jadda da Sitti sukayi tare da haɗa baki wurin cewa.
"Amin Amin, tare dake da mijinki".
Cikin tura baki Safiyyah tace.
"Ikon Allah wato banda mu".
Da sauri Sitti tace.
"Wa lakum".
murmushi sukayi dukansu, kana Jadda yasa tafin hannunshi bisa tsakiyar kan Sheykh da Ibrahim tare da cewa.
"Wannan kawuna biyu duk masu ɗaukan rawanin girmane, hakama na ukunku Haroona shima akwai nauyin rawanin bisa kansa.
Ibrahim da Haroon bani da fargaba a kanku.
Amman shi Muhammad Jabeer akwai ruɗu a al'amarinsa akwai firgitarwa, yana tsakiyar Magauta.
Sun kuma rigayemu sanin rawani na bisa kanshi.
Shiyasa sukeyi mishi zagon ƙasa tun yana ƙaramin yaro."
Shiru sukayi dukansu suna jin zantu kanshi, shi kuwa ɗan tsagaitawa yayi kana ya kalli Aysha yafi tota yayi da hannu alamun ta ƙara matsoshi.
A hankali ta rarrafa ta matsoshi, kanta ya dafa kana yace.
"Wata rana kina iya zama a matsayin da Gimbiya Aminatu take a yau.
Ban saniba ko kafin lokacin ina raye, ko na amsa kiran Ubangiji na.
Ga Muhammad Jabeer mijinki ne, kuma uban ƴaƴan kine, in sha Allah, sannan GARKUWArki. Dan Allah Aysha na baki amanarsa ki zame mishi GARKUWA ki kula da damuwarsa tun kan ta riskeshi.
Yanada nauyi a cikin zuciyarshi mafataucine a faɗin duniya yana neman wani abu nasa mafi, ƙololuwar daraja ga ɗan adam daya ɓace matsa tsowon shekaru masu yawa, a hasashen da akayi mana zaki iya haska mishi hanyar da zaibi ya ganoshi".
Kai kawai take gyaɗa Dattijan tanajin hawaye na cika mata ido.
Da kalmarshi