Showing 162001 words to 165000 words out of 352722 words

Chapter 55 - GARKUWAAA COMPLTE HAUSA NOVEL

17 Oct 2024

30785

kafin nan ki gayawa Umaymah in ta amince,
sai inyi aikin amman kada a gayawa Yah Sheykh dan bazai yarda ba."
Cikin tsoro ido cike da hawaye Ummi tace.
"To Shatu me zancewa Umaymah, me kika gani a ɗakin har ya firgitaki yasaki suma?".
Cikin kuka tace.
"Ummi kada ku tsaya bincike a kaina.
Ni dai ku yarda dani bazan cutar da kowaba na cikin Masarautar Joɗa sai wanda ya cutar da kanshi Ummi bamu da sauran lokaci mai tsawo fa, komai zai iya faruwa da Yah Sheykh".
Cikin tsoro da firgici Jamil yace.
"Ba matsala mun yarda dake, ni yanzu taimakon me zan miki?".
Cikin sauri ta share hawayenta tare da juyowa ta kalli shi kana tace.
"Yauwa Jamilu zaka samo mana mai saka tayis, yazo da katon ɗaya na tayis ɗin irin na bedroom ɗin Yah Sheykh sak da sak.

Sai kuma kayi ƙoƙarin mu samu ya Sheykh in ya fita ya wuni sai dare zai dawo".
Cikin sauri yace.
"Tayis da mai sawa ba matsala, batun in ya fita sai dare ya dawo kuma inaga.
Sai zuwa jibi ranar ne zaije asibitin gwamnatin Genaral Hospital.
To in yaje can wuni yakeyi wani lokacin sai dare zai dawo".
Cikin gamsuwa da hakan tace.
"To ba matsala.
Ummi ke kuma ki kira mana Umaymah ki sanar mata, muyi abun da saninta."

To Ummi tace kana a wurin ta kira Umaymah tayi mata bayani.
Ba wani neman ba'asi tace.
"A barta Ummin Jabeer na amince, tayi duk abinda ya dace a kan mijinta da yayanshi da ƙannenshi dama duk wani abu nashi".

Cikin jin daɗi ta jinjina kai lokacin da take jin mgnar Umaymah.

Wani irin dogon numfashi taja mai ƙarfi sai gata ta tafi luuuh kan...!



Wasa farin girki? Shatu kadafa allura ta tono garma.


By
*GARKUWAR FULANI*


Ta konta, kamar maiyin bacci kamar wacce ta suma.
Cikin mamaki suka bita da ido kana suka juya suka kalli juna,
Cikin mamaki Jamil yace.
"Ummi suma ta kumayi ne?".
Kai ta jijjiga mishi alamar a a.
Kana tasa hannun damanta ta gyarawa Shatu'n.
Kwanciyarta.
Tare da cewa.
"Bacci ne tayi".
Kai ya kuma gyaɗawa cike da mamaki yace.
"Wannan baiwar Allah'n, itama da akwai abin al'ajabi tare da ita.
Da akwai abinda yake a duhu wanda bamu sanshi ba a kanta."

Cikin gamsuwa da bayan shi Ummi ta gyaɗa kai tare da cewa.
"Na daɗe da dasa ayar tambaya a kanta, sai dai bani da mai bani amsar dole sai zaman yauda kullum zai ƙara fahimtar dani ko wacece ita.
Yanzu dai Jamil wannan mgnar ta zama sirri tsakaninmu.
Da Allah kada kowa yaji!".
Cikin nitsuwa yace.
"In Sha Allah Ummi babu wanda zaiji".

To da haka dai sukaci gaba da hira a wurin.
Cikin Sa'a baccin nata baiyi nisaba ta farka.

Lokacin sallan azahar nayi suka watse.

Bayan sunyi salla da jimawa ne, ta miƙe a hankali ta nufi ɗakinshi.
A falo ta tsaya, tana nazarin to in ta shiga ta sameshi idonshi biyu fa?
Akwai abinda take son idonta ya ƙara gani dan ta tabbatar.

Shi kuwa Sheykh yana ciki, a kwance kamar mafi akasarin lokuta, waya yakeyi da Aunty Hafsat.
Tana ce mishi ya haɗata da amryar zasuyi mgna.
Cikin sanyi yace.
"Bacci, Aunty Hafsat Bacci fa zanyi, afwan ki bari sai anjima mana".
Cikin sanyinta tace.
"Oho Jazlaan, nace ka haɗani da ita shine wannan magiyar yanzu Yezeed yazo ya nuna min hotunanta wai Hibba ce ta turo mishi.
Tamin kyau sosai, ina son yarinyar.
Zakiya ma tana amshi number ta, wurin Hibba tana kira kuma bata ɗagawa.
Jazlaan haɗani da ita nace ko!".
A hankali ya yunƙura ya tashi zaune.
Cikin sanyin baccin daya fara yi yace.
"To ɗan katse kiran in naje zan kiraki."
A hankali ya miƙe tsaye. Al'kyabbar sa ya ɗauka, tare da nufar bakin ƙofar.
Yana mai sa hannunshi cikin rigar al'kyabbar.
Har yazo bakin ƙofar bai gama sa hannun rigar ba ya buɗata da faɗi.

Ita kuma Shatu a hankali ta tura ƙofar.
Ta sako kai ciki dai-dai lokacin kuma shima ya sako kai waje.
Ba zato ba tsammani sukaji sunyi kiciɓis da juna ta faɗa cikin faffaɗan ƙirjinshi.
Cikin sauri ya sauƙo da hannayeshi dake buɗe kuma al'kyabbar na buɗe da faɗinta sanadin sauƙo da hannun da yayine sai ya zama ya sauƙe hannunshi kanta, yayi mata ƙawanya da faffaɗan al'kyabbar jikinshi ya haɗasu wuri ɗaya ya rufesu.

Wani irin harbawa zuƙatansu suka farayi da ƙarfi-ƙarfi, suna jam junansu i ziwa jikin juna tamkar mayen ƙarfe.

A hankali Shatu taji jikinta na macewa.
Kanta ta manna a ƙirjinta kunnenta na dai-dai kan ƙahon zuciyarshi.
Lumshe idonta tayi tanajin wani irin masifeffen ƙamshi turare mai daɗin shaƙa dasa baccin daɗi cikin ƙanƙanin lokaci, koda yake baccin nata baya rasa nasaba da abinda ke wujijjigata.

Shi kuwa Sheykh Jabeer, shiru yayi yanajin yadda tasa hannunta, ta zagayo ƙugunshi ta riƙe gam-gam da iya ƙarfin ta.
Sai kuma ya ɗan sunkuyo cike da mamaki yakkali fuskarta, tuni tayi bacci cikin ƴan second nin nan.

Cike da mamaki ya zubawa fuskarta kallon tuhuma.
A hankali yasa yatsunshi ya fara ɓanɓaro hannunta,
yanayi yana ja da baya-baya yana komawa cikin ɗakin.

Ita kuwa binshi take amman ba bi irin na takuba,
Cike da mamaki ya ƙara leƙa fuskarta.
Tabbas bacci tayi.
Janyeta yayi daga jikinshi kana ya saketa a hankali ta tafi zata faɗi, bai tareta ba, sai dai yasa ƙafarshi ya tare dai-dai inda yaga kanta zai bugu.
Cikin Sa'a kanta ya sauƙa kan rumfar ƙafarshi.
A hankali ya ajiye ƙafar tashi a ƙasa.
Kana ya janye ƙafarsa, kanta ya konta a ƙasa.

Cike da mamaki, ya juya ya koma can inda yake konciyar.
Bai cire al'kyabbar ba ya konta yana mgnar zuciya.
"Mutun kamar mayya, wannan baccin kuma na meye to".

A haka shima yayi baccin da yasan in bai yishiba, zaiji ciwon kai.

Kiran sallane ya tadashi.
Tanan konce har yanzu.
Al'wala yaje yayi kana ya fito ya kimtsa ya fesa turare.
A hankali yazo kusa da ita.
Ɗan sauran ruwan dake tafin hannunshi ya yarfa mata a fuska.

A hankali ta buɗe idonta, kana ta kuma lumshesu haka tayi kusan sau uku ganin hakane a hankali yace.
"Ke kasa uwar bacci tashi kiyi salla".
Miƙa tayi a hankali tare da cewa.
"To". Shiru yayi yana nazarin muryarta, ba haka muryarta yakeba.
Wannan shine abinda su Ummi basu ganeba, shi gashi ya gane a take,
Su kuwa basu gane cewa muryarna ba tata bace.

Kanshi ya ɗan juya tare da cewa.
"Uhummmm". Daga nan ya fita, ita kuma Shatu da ido ta bishi.
Yana fita ta miƙe kalle-kalle tayi a ɗakin nashi sosai har ƙarƙashin gado ta leƙe.

Tana gamawa ta shiga Bathroom nashi.

Wani irin murmushi tayi tare da cewa.
"Komai nashi mai kyau da tsabta".

Al'wala tayi kana ta fito, a falo ta samu Ummi da Hibba da alamun a nan sukayi salla.

Sosai Ummi tayi mamakin kenan, tana ɗakin Sheykh ne, murmushin jin daɗi tayi a ranta tace.
"Ikon Allah kenan".

Ita kuwa Shatu hijabin Hibba ta amsa tayi salla.
Suna zaune a nan ya shigo.
Wayarshi na kunne cikin nitsuwa yace.
"To Aunty Hafsat gata nan ɗazu bacci takeyi".
Cikin murmushin tace.
"To bata".
A hankali ya iso tsakiyar falon wayar ya miƙo mata tare da cewa.
"Aunty Hafsat ce ƙanwar Umaymah saura kiyi mata rashin ta ido".
Ya ƙarishe mgnar a hankali yadda ita Aunty Hafsat bazata jishiba.

Ita kuwa amsa tayi tare da karawa a kunne cikin nitsuwa tace.
"Assalamu alaikum".
Fuska a sake tace wa alaikissalam ɗiyata, ya gida ya sanyi".
Muryar matar sak irin ta Umaymah shiyasa cikin jin daɗi tace.
"Lfy lau Alhamdulillah Aunty ya gida da aiyuka".

"Alhamdulillah". Tace kana ta ɗora da cewa.
"Sunana Hafsat Jalaluddin Muhammad Sultan".
Cikin jin daɗi tace.
"Eh Aunty na sanki ai Umaymah ta gaya min sunanki ta nuna min hotonki da Aunty Rahma da Zakiya da Yezeed dama duk sauran".
Cikin jin daɗi tace.
"Masha Allah, to ki amshi number ta data Rahma da Zakiya a wurin Hibba, ɗazuma Zakiya taita kiranki ashe kina bacci ne".
Cikin nitsuwa tace.
"To Aunty yanzu kuwa, ngd matuƙa".
Cikin jin daɗi Aunty Hafsat tace.
"Allah ya muku al'barka ya baku zaman lafiya.
In Sha Allah zamuzo auren Haroon zaki gammu mu ganki".

"Amin Amin. Aunty Allah ya kaimu lokacin ya kawoku lfy".
Tace kana sukayi sallama.

Daga nan suka shiga kitchen.
Jamil kuwa tuni yaje yayiwa wani mai musu aikin gidansu.
Yasa ya nemi irin wannan tayis ɗin. Yace gobe da safe misalin sha ɗaya zaizo ya ɗauke shi.

Washe gari da safe.
Misalin karfe tara, Sheykh ya fito cikin shiga ta al'farma, yau ba al'kyabba a jikinshi riga da wondone sai malum-malum gariya mai kyau.
Getzner ce mai masifar kyau Brownish red color mai ɗan karen kyau da sheƙi, gariyar tasha aiki mai ɗan karen kyau da zaren surfani mai sheƙin piash color.
Hular kanshi da red and piash color, takalmin shi kuwa fatar ta kifa kalar red ɗin.
Yayi kyau sosai ya kafa hular nan cas a kanshi. Kekyawan suman kanshi ya konto gefe da gefe da ƙeyarshi sai sheƙi da ƙelli yakeyi.
Sajenshi ya kwanta lib, gashin girarsa dana gemunshi ɗan cas dashi misalin kamu ɗaya, sai sheƙi suke zubawa.
Ɗan madai-daicin bakinshi mai jajayen laɓɓa sai sheƙi sukeyi.
Yar ƙaramar jakar na'urar System ya riƙe a hannunshi, sai wani ƙamshi mai daɗin ji yake fiddawa, ɗan farin siririn Glass irin na manyan Doctors ya manna a fuskarshi kana ya fito.

A falonshi ya sameta, tana jera mishi breakfast.
Ganin zai wucene ta ɗan biyoshi a hankali ya zama suna tafe a jere.
Cikin kallon suman ƙeyarshi tace.
"You are breakfast is ready".
Bai kulata ba yaci gaba da tafiya.
Ita kuma ƙeyanshi ta mannawa harara.
A haka suka fito.
Ya sallami Ummi da Jamil da tunda suka karya bai tafiba.
Da sauri Jamil yabi bayanshi yana cewa.
"Uhum Dakta sai yaushe zaka dawo ne?".
Juyowa yayi ya kalli Jamil sai kuma yace.
"Kanada matsala ne?".
Da sauri ya jujjuya kanshi tare da cewa.
"No. I'm very fine".
yayi mgnar yana jijjiga jikinsa.
Kai ya kaɗa ya juya zai fita,
Da sauri Jamil ya kuma tambayarsa.
"Dakta yaushe zai dawone".
Cikin tsuke fuskarsa yace.
"Ban sani ba".
Daga nan ya fita, shi kuwa Jamil tsalle yayi tare da cewa.
"Yesss, Dakta Allah ya kiyaye hanya, a wuni lfy a asibiti".

Murmushi Ummi tayi tare da cewa.
"Yi maza to ka ɗauki shi".
To yace kana ya miƙe ya fita.
Sanin cewa yanzu Sheykh yana sashin Hajia Mama ne.

Haka yasa ya rigashi fita.

Ummi kuwa miƙewa tayi taje ta rufe ƙofar sabida bata son wani yazo ya shigo.
Kiran Jamil tayi a waya tace in sun isoma ya kirata a wayane zata buɗe mishi.

Tana katse kiran ta juyo ta kalli Shatu dake zaune gefenta tana ce mata.
"Yauwa to Ummi muje mu fara aikin kafin ya iso mun kusa cimma aikin."

Cikin mamaki tace.
"A a keda kikace sai an matsar da gadonshi sannan aikin tono ai bazamu iyaba. Dole sai mazan".
Cikin muryar da har yau Ummi ta kasa banbance shi da asalin muryarta tace.
"A a ba matsala Ummi muje zamu iya".
Ta ƙarishe mgnar tana yin gaba, ganin hakane yasa Ummi Binta a baya.
A hankali suka shiga falon.
Tana mai cewa Ummi.
"A nan ma an mishi wani aikin amman shi bai shiga jikinsa ba, sabida yanada Garkuwar addu'o'in da yakeyi yau da kullum.
Shiyasa duk sabbin sihirurruka basa shigarsa.
Sai dai waɗanda akayi mishi tun bai gama girma ba."
To kawai Ummi ke ce mata sabida jin kamar muryarta na canza mata.

A haka ta kuma nuna mata wani wurin.

Tare da cewa.
"Uhumm Ya Jafar suke nema, su maida majanunin kan bola sai kuma sharrinsu ya zame mishi al'khairi,
Tsawon shekaru baya mgn sai ambaton Allah. Bashi ba zunibi sai tarin lada da yake samu na karatun al'ƙur'ani da ya zame mishi abokin hira.

To ita kuma me take nema a duniya da zata cutar da baiwar Allah da ahlinta duka haka.
In banda lalaci da son duniya na miji ya lalace da bin matsafa yana sawa ana sabauta ɗan uwanshi da yayanshi."
Ita dai Ummi binta takeyi da ido da ƙafa har suka isa bedroom ɗin shi.

Ɗan lungun da ɗaya Bedside drower'n take ta shiga.
Kana ta kalli Ummi fuska a juye tace.
"Naɗe min carpet ɗin nan.
To Ummi tace da sauri ta fara naɗe carpet ɗin.
Bayan ta janyeshi da kyar ne, ita kuma Shatu.
A hankali tasa hannun damanta bisa jikin gadon ba tare da ta ɓallashi ba ko, ta cire wani abu a jikinshi ba, ta yunƙura ta tura gadon tare da cewa.
"Bismillahirahamanirahim".
Da sauri Ummi taja da baya cike da mamaki da tsoron ganin yadda take tura tamfatsetsen gadon mai ɗirkekiyar katifa da ko tura katifar kawai aikine.

Guuuuuuh haka sautin tura gadon yake badawa.

Saida ta turashi har jikin Waldurob.
Kana ta tsaya a tsakiyar inda gadon yake kafin ta turashi.
Dai-dai lokacin kiran Jamil ya shigo wayarta.

Da sauri taje ta buɗe mushi.

Kana suka shigo,. A falon suka bar Ɗalha mai tayis,
kana Jamil ya amshi kayan aikin yabi bayan Ummi yana cewa.
"Yauwa ɗalha ɗan jirani bari inzo mu isa kaga wurin".

To ɗalha yace kana ya fara cin abincin da Ummi ta saka mishi.

Suna shiga suka maida ƙofar falon suka rufe.

A inda Ummi ta barta a han suka sameta.
Da sauri ta miƙawa Jamil hannun tare da cewa.
"Bani gudumar da ma'ɓamɓarin."
Cikin sauri ya iso tare da ajiye ɗan buhun ya fito da gudumar da Maɓamɓarin yana mai mamakin yadda aka tura gadon yace.
"Bari Aunty Shatu nuna min ina zan fasa".
Da sauri tace a a, ku ɗan matsa gefe, musamman ma kai koma can".
Ta nuna mishi gefe.
Sake mata gudumar yayi jin ta fizgeshi.
A hankali ya tashi sabida cewa da tayi ya tashi.
Ido suka zuba mata, ita kuwa, gudumar tasa ta rinƙa buga tayis ɗin dake wurin saida ta fasa uku lafiyeyyu.
Kana ta ture fasassun tasa maɓamɓari tana ɓalle sauran, saida ta ciresu kab.
Sannan ta fara fasa fulon simintin dake ƙasan.
Da mamaki Ummi ke kallon wurin sabida tasan babu wani fulo da akayi kafin asa tayis ɗin.
Fasashi tayi kana ta fara caccaka ƙasan wurin da matonin, tanayi yana fito da ƙasa.

Shiru sukayi ganin ramin yayi zurfi kuma ba komai.

A haka taci gaba da tono tana kuma faɗaɗa ramin ta ƙasa.

Wani irin zabura Jamil da Ummi sukayi lokacin da suka ga wani baƙin hayaƙi yana fitowa cikin ramin.

Ita kuwa Shatu da sauri tasa hannun damanta taci gaba da tonon.
Tare da yin mgna da sauri tace.
"Jamilu buɗe windows da sauri hayaƙin nan ya fita".
Cikin rawan jiki yace to.
Kana ya fara buɗe wa da sauri sabida, hayaƙin ya fara cika ɗakin.

Yana buɗe windows ɗin kuwa hayaƙin ya fara fita.
Tonon taci gaba dayi tare da cewa.
"Inama da akwai wani yardajjen mu a kusa, bayan ku biyun nan da yabi hayaƙin nan zaigane mana ina zai shiga cikin sashukan mutanen gidannan shaidar aiki ya koma kan wanda ya yishi."
Da sauri Jamil yace.
"To ko in fitane inbi hayaƙin".
Cikin sauri tace.
"A a kada ka fita ku tsaya kaida Ummi."

Numfashi suka fara sauƙewa, a hankali lokacin da sukaga duk hayaƙin ya gama fita.
Sai kuma suka fara takowa suna zuwa inda take ganin yadda hannunta dake cikin ramin yake karkarwa.
Ga wata zufa dake keto mata kamar da bakin kwarya.
Wani marfin tukunyar ƙasa ta ɗago.
Kana a hankali ta ɗago tukunyar.
Ta ajiyeta gefe kana ta koma ta jingina tana mai jan numfashin.
Cikin sauri Ummi taje ta kunna sauran wutan ɗakin duka, ya zama kamar farin wata.

Jamil ne ya fara leƙa cikin tukunyar.
Da sauri yace.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun. Ummi zo ki gani".
Ya ƙarishe mgnar yana sunkuyowa da kai hannunshi zai kama tukunyar ƙasan cikin sauri da ƙarfi Shatu ta buge hannunshi da hannunta na hagu tare da cewa.
"Jininka ɗaya da Yah Sheykh in ka taɓa duk abun zai iya dawowa jikinka."

Ta ƙarishe mgnar da ɗago hannun ta na dama tasa a ciki.
Tukunyar da sauri ta rumtse idanunta sabida wani irin masifeffen tsikara da taji an mata a hannunta.

A can ƙasar Cameroon kuwa cikin Rugar Duno dake, kusa da Rugar Malam Babayo.
Ba'ana ne zaune bisa buzun aikinshi.
Da kasko a gabanshi yana kallon cikin kaskon gaba ɗaya jikinshi rawa yakeyi cikin tashin hankali da fargaba yace.
"A'a A a Mata kada ki taɓa, baki amince na baki mgnin kariyar tonar sihiriba, iya ganin idan a zuba sihiri a abinci yake na shayar dake shi nanma a bisa dole baki saniba.
Kada ki taɓa zai cutar dake".
Ya ƙarishe mgnar hawaye na zubo mishi, Allah ya sani baya son abinda zai cutar da Shatu ko kaɗan.

Ita kuwa Shatu a hankali ta fara fito da wasu irin tabka-tabkan layu wanda aka liƙesu da yadin al'kyabba daga gani kasan na Sheykh ne sabida shi ɗaya kesa irinsu a masarautar Joɗa tun yana ɗan yaro matashinsa.
Wani dogon ajiyan zuciya taja tare da fizgo wani dogon maciji a cikin tukunyar ƙasar.
Da sauri Ummi taja da baya, shi kuwa Jamil sai leƙowa yakeyi.

A dai-dai lokacin kuma Sheykh dake cikin Office dinshi na cikin Genaral Hospital Ɓadawaya shi ɗaya, dan yau ba mutane sosai dudu mutun biyar ne kuma ya gama dubasu ya musu komai, yana zaune ko za'a turo wasu.
Wani irin zabura yayi ya miƙe tsaye da ƙarfi tare da cewa.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun".
Sai kuma ya sunkuyo yana kallon yadda babbar yatsarshi ta ƙafar dama wacce zanen maci ke kanta take rawa kar-kar.
Da sauri ya juya ya nufi bathroom ɗin cikin Office dinshi.
Cikin sauri ya zare malum-malum ɗin jikinshi juyowa yayi ya ajiyeta saman kujerarshi.
Kana da sauri ya nufi Bathroom sabida yadda yakejin ana fizgo wani abu kamar jijiya a jikinshi tun daga saman cikinsa kusa da ƙirjinsa, har zuwa kan ɗan yatsarshi.
Da sauri ya cire rigarshi da snglet ɗin, da ido yabi zanen dake jikinshi wanda samanshi zanen kan macijine.
Gaba ɗaya jikinshi rawa ya farayi tamkar mazari.
Duk wata jijiya dake jikinsa saida ta tashi tsaye.
Cikin tashin hankali yake ambaton sunayen Allah da duk addu'o'in da sukazo bakinsa.
Hannunshi yasa ya damƙi bnnarshi data miƙe tayi wani irin harbawa da masifar ƙarfi, riƙeta yayi da kyau jin yadda take tashi tana kumbura da cika tana tsawo tamkar zata faso boxes ɗin shi ta fito woje.
Wannan shine babban tashin hankalinshi dan tsawon shekaru kusan ashirin bai sake ji ko ganin bnnarshi ta miƙe kamar hakaba sai yau.
Karkarwa duk jikinshi keyi, hatta jijiyoyin kanshi dana damatsan hannunshi tasowa sukayi ruɗu-ruɗu jijiyar goshinsa har harbawa takeyi".
Innalillahi wa innailaihi rajiun yaketa maimaitawa, yanajin kamar ana jan jijiyoyin jikinsa.
A haka ya maida kayanshi kana ya fito.
Sai dai bai samu damar maida gariyar ba, zama kawai yayi bisa kujerar yana rawan sanyi.

A haka abokinshi Dr Arabi ya shigo ya sameshi cikin mamakin ganin yadda yake karkarwa yace.
"Dakta Jabeer lfy kuwa meya sameka".
Cikin muryar alamun zazzaɓi yace.
"Zazzaɓi ne Arabi. Sanyi nakeji".
Da sauri ya iso inda yake taimaka mishi yayi ya saka mishi gariyar.
Kana ya kamoshi ya kawoshi bisa tattausan kujerar 3 str dadake cikin Office ɗin ya kwantar dashi.
Aunashi yayi tare


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login