Showing 174001 words to 177000 words out of 352722 words

Chapter 59 - GARKUWAAA COMPLTE HAUSA NOVEL

17 Oct 2024

30808

rusuna tare da cewa.
"Bappa mu isa ciki sannunku da zuwa".
Ya ƙarishe mgnar yana kallon agogon Daimond dake ɗaure a sinsiyar hannun Al'amin wanda ya tabbatar da wuya ba fulatanin daji makiyayi ya cire shanu kusan goma ya saida dan sayar wannan zazzafan agogon."

Cikin sanyi Bappa yace.
"Nanma yayi".

Ita kuwa Aysha da sauri ta miƙe jin muryarshi.
Hannunta ta miƙa mishi tare da motsawa gabanshi alamun zata abka jikinshi.
Da sauri yasa hannunshin ya riƙo hannunta mai lfyar.
Kana ya zauna a ƙasa gaban Bappa sannan ya zaunar da ita.
Cikin kuka da alamun gigita ta manna kanta a kafaɗanshi.
Tare da cewa.
"Yah Sheykh kayi min addu'a kamin tofi zanji sanyi".
Ummi da Umaymah kuwa da Hibba suna gefe suka zauna.
Dan basuma Hausa dasu Bappa ba tukun. Hibba da Umaymah da Ummin sai kallon Al'amin t
Sukeyi sabida kamarshi da Shatu ya wuce zaton mutum.

Shi kuwa Sheykh a hankali ya kamo hannun ya ɗan dagashi sama.
Kana ya fara karatu yanayi yana tofi da ɗan hura mata sassanyan iskan bakinshi.
A hankali ta fara sauƙe ajiyan zuciya.
Tana lumshe idonta hawaye na siyaya.

Shiru sukayi falon gaba ɗaya sai sautin muryarshi dake tashi yana karatun Alqur'ani yana mata tofin.

Cikin ƙanƙanin lokaci komai ya lafa zogin ya bari, Al'farma Annabi da Alqur'ani.

Ganin ta nitsu tayi shirune.
Yasa Bappa sauke ajiyan zuciya tare da cewa.
"Alhamdulillah".

Al'amin kuwa hawaye ya matse yana mai jin tausayinta na ratsa mishi zuciya.

Cikin sanyi yace.
"Parvina!". A hankali ta yunƙuro ta matso gabanshi cikin disashewar muryar da kewar sunan da ya kirata dashi wanda ta dade bata jin an kirata da shiba tace.
"Na'am Yaya Al'amin".
cikin zuba mata ido yace.
"Sannu ko ya jikin naki?".

Murmushi tayi tare da cewa.
"Alhamdulillah da sauƙi, Yah Al'ameen ya ahlin Abboi?".
Murmushi yayi tare da cewa.
"Alhamdulillah". Shi kuwa Sheykh ido ya zuba musu.
Yana karanto wani kamanni dake tsakaninsu.

Juyowa tayi ta kalli Bappa cikin sanyi tace.
"Bappa na. Ina Ummey na, ina Junainah na meyasa baku zomin da itaba nayi kewarta".
Cikin jin daɗi Bappa yace.
"Duk suna lfy Ummeynki da Junainah suna lfy sunce in gaisheki da jiki".

Ciki sanyi tace.
"Ina amsawa ngd".
Sai kuma ta kwantar da kai cikin sanyi tace.
"Yah Al'ameen ina Dedde na?."
Cikin sanyi yace.
"Tana lfy ta gaisheki sosai".
Ido ta lumshe tare da sauƙe numfashi
Sai ta kuma kalli jerin ababen da aka jera musu a kan santa table.

Ummi kuwa cikin sakin Fuska tace.
"Ina kwana Bappa kuzo lfy".

Fuska a sake yace.
"Lfy lau Alhamdulillah."

Sai ya kuma juyo ya kalli Umaymah dake ce mishi.
"Sannu da hanya, ya mutan gida?".
"Lfy lau Alhamdulillah. Ya mai jikin sannunku da jinya mungo matuƙa".
Bappa yace cikin kamala.

Murmushi Umaymah tayi tare da cewa.
"Yiwa kaine ai".
Al'ameen ne ya ɗan kalli Umaymah cikin nitsuwa yace.
"Ina kwana".
Ido ta ɗan zuba mishi tare da cewa.
"Lfy lau ya gida".

"Alhamdulillah ya mai jikin".

"Da sauƙi".

Shiru sukayi dukansu suka maida idonsu kan Aysha data kalli Al'amin cikin shogoɓa tace.
"Yah Al'amin zanci abinci".

Kallonta ya ɗanyi tare da juyowa ya kalli Ummi sai kuma yayi shiru.

A Sheykh ne ya miƙa tsaye tare da cewa.
"Bappa bismillah mu isa can falona."
Ya ƙarishe mgnar yana kallon wayar iphone 12 pro dake hannun Al'amin.
Cikin nitsuwa Bappa yace.
"To bisimilla".
Juyawa yayi gaba kana suka bishi a baya.
Itama Aysha binsu tayi a baya.


Suna shiga shiga falon nashi Bappa ya zauna bisa kujera.
Su kuma duk suka zauna a ƙasa a saban carpet.

Ita kuma Aysha tsakanin Al'amin da kuma Sheykh ta zauna.

Barun kuma ya ɗan zauna gefe.

Cikin girma Bappa ya gyara zamanshi tare da cewa.
"To Jabeer ban saniba ko zaka amince wannan ya duba hannun matar taka, mu gwada nashi mgnin ko Allah zaisa mu dace".
Shiru Bappa yayi tare da zuba mishi ido.
Shi kuwa Sheykh kanshi a sunkuye yana kallon tattausan yadin jikin Al'amin yace.
"Duk yadda kace Bappa ba damuwa, in ka aminta dashi".

Shiru Bappa ya ɗan yi yana nazartan kalaman shi da fuskarshi kana yace.
"In sha Allah ba damuwa".
Kai ya gyaɗa.
Lokacin Umaymah kuma ta shigo da manyan Foodflaks da plate ta ajiye a tsakiyarsu.
Zata fita kenan.
Bappa yace.
"Zauna mana".
To tace kana ta zauna.

Shi kuwa Al'amin cikin kula ya kalli Aysha tare da cewa.
"Matso ya duba hannun ko".
A hankali ta matso kana ta miƙa mishi hannun.

Barun kuwa. Gyara zamanshi yayi tare da kallon su sannan yace
"Wannan ba wani abun tashin hankali bane, yanzu zan mata mgnin kuma zata samu sauƙi sai dai bisa shanu hamsin da nace.
Gsky yanzu ɗari za'a bada".
Ido Sheykh ya zuba mishi cike da tuhuma.
Al'amin kuwa murmushi yayi tare da cewa.
"Kai dai kayi aikinka in ta samu lafi ka faɗi adadin duk shanayen da kakeso bazai gagara ba da izinin ubangiji".
Kanshi ya gyaɗa cikin jin daɗi.
Kana ya zaro wayarshi kamar yadda suka tsara da Ba'ana.
Kiranshi yayi.
Ya saƙala wayar a kunne ya matseta da kafaɗarshi.
Kana ya kalli Umaymah yace.
"A kawo min madarar shanu mai sanyi".
Da sauri Umaymah ta miƙa tare da cewa to.

Shi kuwa Barun. zabirar magungunan da Ba'ana ya haɗo mishi ya buɗe kana ya fara fito dasu.
Jim kaɗan Umaymah ta dawo da madarar shanu mai sanyi ta mika mishi.
Ajiye wayar daya matse a kafaɗa yayi tare da amsar nonon.

Kana ya zuba wani garin mgnin a ciki.
A take nonon ya fara zama kinɗirmo mai kauri.
Kana ya matsar dashi gefe.
Sannan ya fito da wani mgnin yana kwashi da man shanu.
Kiran da akayiwa wayarshi ne yasa ya dakata ganin sunan Ba'ana.
Amsa wayar yayi ya kara a kunne tare da fara mgn ba sallama.
Tsareshi da ido Sheykh yayi ya lura cewa wannan mutumin ba musulmi bane.

Al'amin kuwa hannun Aysha ne riƙe a hannunshi yana mata sannu.

Bappa kuwa shima hankalinsa na kan Barun.

Hakama Umaymah, shi ko Barun.
Kamar yadda suka tsara haka ya fara mgna. Ta tsigar da dole Aysha ta gane waye Barun kuma waya turoshin.

A hankali ta ɗago kanta jin yace.
"Eh naje har cikin gidan an nuna min mara lfyar, to kafin in mata aikin na gaya mata, ƙetaren sihirine.
Nace mata kin mance cewa.
Yana ce miki Mata ki bari in dafaki da kyau gudun kada wata rana wani ya cutar min da ke.
Mata na baki haɗin da idonki zai iya ganin alamun sihiri na mugunta da baƙin hayaƙi tsari ko wani kafiya kuma da farin hayaƙi.
Na gaya mata cewa.
Yace mata Mata kada kiyi gangancin cewa zaki tone wani sihirin tunda kinƙi in dafaki.
Domin zai iya dawowa jikinki ya cutar da ke."

Shiru ya ɗan yi yana kallon cikin idon Aysha.
Ita kuwa tuni Aysha jikinta na tsuma.
Bappa kuwa numfashin ya sauƙe tabbatar da zatonshi hakane wannan ɗan aiken Ba'ana ne.
Al'amin hankalinshi na kan Aysha.
Umaymah kuwa shiru tayi tana kallonshi.
Sheykh Jabeer kuwa idonshi ya lumshe yana sarrafa kalaman Barun da wassafasu da basu cikekkiyar ma'anarsu da jimla a kanshi.
Shi kuwa Barun ci gaba yayi da cewa.
"Eh ogo na gaya mata kuma ta gane.
Don a lokacin tayi shiru.
Na kuma ƙara cemata Ogana yace in cemata duk inda take duk inda ta shiga ko wani motsinta yana cikin tafin hannunshi.
Ya kuma ce in.gaya mata ajiyarta yayi a inda yake, yana son ya gama da aikin da yasa a gabane zai dawo kanta zai kuma ɗauke ta.
Nakuma cemata.
Kace in ce mata.
Duk duniya babu mai bata mgnin ciwon hannunta sai mu, sannan zata worke.
Nace mata kace in gaya mata kana raye tare da ita yana sonki tun kina ƙaramar zai kuma ci gaba da sonki har gaban abadan."

Ba'ana dake can sai murmushi yakeyi cikin jin daɗi.
Yaso ace yana ganin fuskar Shatu to amman wannan mutumin mai shegen hasken ya kareshi.

Aysha kuwa gaba ɗaya jikinta karkarwa yakeyi.
Tana mamaki da tsoron taƙadirancin Ba'ana ya akayi ya samu damar turo jakadarsa masarautar Joɗa har cikin sashinta har falon mijinta har gabanta gaban mijinta.

Ido ta zubawa Barun tana mai haɗa zufa.
Shi kuwa Barun kai ya jinjina mata.


Bappa kuwa cikin sanyi yace.
"Wannan wayar taka ba ƙarewa zatayi ba katse kiran ka shafa mata mgnin, lokacin na tafiya kasan mu yau zamu juya."

Cikin murmushin taƙadiranci Barun yace.
"To Bappa an gama".

Gyara zamanshi yayi tare da miƙowa Aysha kindirmon mgnin daya kwaɓa.

Shi kuwa Sheykh Jabeer gyara zamsnshi tare da watsawa Barun wani irin kallo mai tarin ma'anoni kana yace.
"Bar mgnin nan naka bana buƙatar shi a jikin matata! Bar min matata.
Jeka kawai kacewa. Ogan naka.
Akwai mganin da zai workar da ita ba sai nakuba,
Zata kuma samu sauƙi cikin ƙanƙanin lokaci da izinin ubangiji.
Kace mishi, sama tayiwa yaro nisa.
Duk tsallen da zaiyi bazai taɓoshi ba.
Kacewa oganka ya tsaya inda yake hurumin yafi ƙarfinshi".

Cike da Mamaki Aysha, Bappa, Al'amin, Barun, Umaymah suka zuba mishi ido.
Shi kuwa gyara al'kyabbar jikinshi yayi tare da tsare Barun da idanunshi da suka hantar cikin Barun ta kaɗa cikin iya sarrafa harshe yaci gaba da cewa.
"Muda muke da al'ƙur'ani mai girma ai Allah ya bamu dukkan maganin cutar duniya a cikinsa.
*Kada ku sake zaton samun shigowa masarautar Joɗa*, wannan ɗin ma.
Ni naso ku shigo shiyasa ka samu ka shigo ni na bada dama."
Miƙewa tsaye yayi tare da nunawa Barun hanyar fita cikin dakekkiyar murya yace.
"Tashi ka ɓace min da gani.
In kaje kace mishi idon Muhammad Jabeer a buɗe suke basa bacci. Kada ya sake gigin turo wani ƙazamin kafuru, a tsarkakken.
Masarautar Joɗa Especially nan."
Cikin tsananin tsoro da mamaki da kaɗuwa Barun ya juya da sauri ya fita.
Da ƙarfi Sheykh Jabeer ya buɗe muryarshi yace.
"...!



Kuyi haƙuri dan Allah babban uzurin mgn a wayane ya tsareni sai yanzu.

By
*GARKUWAR FULANI*

Ya ruggumeta da kyau a jikinshi.
Jinyadda taketa fizge-fizgen zata kwance kanta.
Wani irin tsuma jikinshi ya rinƙayi can cikin naman jikinshi yake jin tsuman.

A hankali ya manna kanta, kan faffaɗan ƙirjinshi,
hannunta mai ciwon data ɗaura a tsakiyar kan natane ya zubawa ido.

Sosai hannun yayi jazir sai kelli yaki, alamun kumburin da yayi.
A hankali yasa hannunshin ya tallabo hannun.
Wani irin ihu tasaka da ƙarfi.
Sai dai bai bari ihun ya fito daga bakinta ba, yayi maza ya rufe mata baki da tattausan tafin hannunshi yana ta mai-maita.
"Innalillahi wa innailaihi rajiun".
Tabbas da in ya barta ta kurma ihun shike nan ta tabbata zautacciya,
yin ihun da take son yi dai-dai yake da sihirin ya gama shiga jikinta ya ratsa zai kuma haukatata.
Shiru tayi tana zazzare idanunta da hawaye ke zuba babu ƙaƙƙautawa, shi kuwa Sheykh a hankali ya janye hannun nata data aza a kai ya tallabeshi da tafin hannunshi.
Sannan ya manna ƙirjinshi da nata ƙirjin da kyau.
Har suna iya juyo bugun zuciyar juna.
Sunkuyo da kanshi yayi tsakanin kafaɗarta da wuyatan

Bakinshi ya saita cikin kunnenta.
Hure gashin daya baje kan kunnen yayi ya matsa,
sannan ya kawo bakinshi gab da kunnenta har tattausan lips ɗinshi na taɓa tattausan kunnenta.

Lumshe idonshi yayi tare da gyara tsayuwar nasu da kyau.
Ita kuma sai fiffizgewa take sonshi jikinta duk yana karkarwa ga zufar dake tsiyayo mata.

Hannunta dake cikin hannunshi ya kalla yadda yaketa rawa, gashi zafi jau kamar wuta.

A hankali yayi gyaran murya tare da yin bisimilla.
Cikin ɗan-ɗaga sauti ya fara karanta Suratul Baqra cikin kunnenta cikin fidda harrufan da karsashin yadda zai ratsa kunnuwanta.

Yanashi yana cire tafin hannunshi dake bakinta,
wani irin manna kanta tayi da ƙirjinsa,
ta lumshe idonta wasu hawaye masu ɗumi suka fara kwaranya.
hannunta na hagu dake da lfyar tasa bisa kafaɗanshi ta zagayo wuyanshi da kyau.

Shi kuma hannunshi da ya janye daga kan bakinta ya maida kan ƙugunta ya ruggumeta tsam a jikinshi.

A haka yaci gaba da karatu, in yazo wasu ayoyin yakan maimaita karshensu kafin ya kuma kama forkon na gaba.

A hankali ta fara sauƙe wasu tagwayen numfarfashi, ji takeyi azaba da raɗaɗin yana ɗan lafawa.
*Al'farma Annabi da Alqur'ani kenan.*
A hankali ta daina duk fizge-fizgen ta dawo sai kukan da takeyi mai sauti amman sautin a hankali ne.

Kuka take sosai ganin hakane, ya gyara tsayuwar tasu.
Kana ya tallabo kanta ya kalleta.
A hankali ya girgiza kanshi tare da jawota suka nufi bakin gado.
Yana cewa.
"Uhummm baku samu wurin zamaba a kanta in Sha Allah bazamu zauna inuwa ɗaya dani da kuba, zaku bar jikinta."

Ajiyeta yayi kan gadon kana shima ya hau ya zauna.
da sauri ya riƙo hannunta da take son maidashi tsakiyar kanta ɗin.

Karatu ya fara yanayi yana ɗan hura mata sassanyan iskan bakinshi.
Tub, tub, tub, haka yake ɗanyi tare da fesa iskar, kana ya zuba mata ido cikin idanunta.
A hankali tayi ƙasa da kanta.

Shi kuwa haɗe fuska yayi tare da cewa.
"Ɗago ki kalleni mana".
Kai ta girgiza alamun a a.
Shikuwa hannunshi ɗaya yasa ya tallabo haɓarta, dan ta kalleshi da sauri ta rumtse idanunta.
Cikin kausasa murya yace.
"Buɗe idon ki kalleni!".
A hankali ta buɗi baki cikin irin Muryar da yaji tayi mgna kwanaki dashi tace.
"Bazan iyaba, kunyarka nakeji!".
Watsa mata wani kallo yayi tare da cewa.
"Ƙarya ne, bakiji kunyan Allah'n daya haliccemu ya halicceku ya kuma yi mana iyaka a tsakaninmu ya hanaku cutar damu, ta hanyar mazonsa ya ƙaiyade muku dukkan motsinku, ya hanaku cutar da bani Adam.
Duk bakiji kunyarsu ba, kika shiga jikin yarinya ƙarama, kina sata yin wasu abun da ba halinta ba,
bakiji tsoron Allah daya hanakuba.
Bakiji kunyar iyayenta ba, kina cutar musu da ɗiyarsu sai ni?".
Cikin sanyi murya cike da alamun tsufa, tace.
"Ni bana cutar da ita, Ni ba muguwa bace, ban taɓata cutar da ita ko wani nataba duk tsawon shekarun da nake tare da ita".
Da sauri cikin faɗa yace.
"To meyasa zaki shiga jikinta".
A hankali cikin zubda hawaye tace.
"Ni tun tana jaririya nake jikinta, kuma ni makaran gadone na ahlinsu daga wurin kakarta mahaifiyar mahaifinta".
Da sauri yace.
"Rufe min baki, makaran gado,
Ku kuɗine ko wata kadara ce, ku cikin kadarorin da Allah (S.W.A) ya lissafa cikin jerin jadawalin abinda za'a gada?.
Ko dan kinga ina binki a hankali ne yasa zakiyi min zancen banza na mutanen banza".
A hankali tace.
"Jikana ka kontar da hankalinka muyi mgna".
A fusace yace.
"Waye jikan naki, kina Jinnu ina bani Adam ta ina na zama jikanki.
An ƙi a kontar da hankali tsohuwa dake kinzo kin liƙewa yarinya kina ƙoƙarin sata tana yaye suturar jikinta tana shirin yin ihu.
Ko baki san cewa matar aure bace, baki san daraja da kimar dake cikin aure bako?".
Cikin fushi itama tace.
"Ni bani nasata yarda kallabin kanta ba, zafin ciwo da takeji ne ya gigitata yasata yarda kalkabinta.
Sannan batun ihu da kakeyi kuwa.
Aikin da mugayen Masarautar Joɗa sukayi data taɓane yake shiga jikinta.
Ni kuwa na zone sanadin karatun Rugyan da kayi ta mata, amman duk wancan abun da takeyi ni bana kusa ma.
Kuma ni ba mai cutarwa bace.
Batun darajar aure kuma na fika sani.
Kai kama tsaya inda takene bare ka raya auren ka tabbatar da ita matarka ce kai mijinta ne?.
Kasa sabgogi a gabanka, kana sane da magautanka sun saka a tsakiya kayi, burus dasu, suna neman rabaka da rayuwarka.
Ita kuma dole in taimaketa sannan dama Aysha in dai bata da lfy ko zazzaɓi ne tana kuka haka ciwonta yake."
Cikin haɗe fuska yace.
"Eh wato da ban ƙonaki bane, kikemin baki ko. T taimako bana son taimakonki ki fitamin a jikin matata, bana so, zakisa tayi ihu ta fita tsakiyar masarauta bayan kin san inada magautan to meyasa zaki nemin abinda zaisa magautana farin ciki.
Tai mako kuma bama so, muda mukeda ubangijin taliƙai wanda yasan zahiri da baɗinin shi yake taimaka min, ba tare da yasa mana ciwon kai ko fita haiyaci ko kukaba dan haka fice min a jikin matata".
Murmushi tayi tare da jinjina kai kana tace.
"Matarka kuma yau".
A hatsale yace.
"A a matarki ce, in ba matata ba?."
Sai kuma yayi bisimilla zai fara karatu da sauri tace.
"Tsaya Muhammad Jabeer ɗan Habibullah jikan Nuruddee, Bubayero, Joɗa, Sule Usmanu jinin sarki Muhammad Bello, ni bazanyi faɗa da kaiba kafi ƙarfin haka duk da ni ba cutar daku nakeyi ba. Naga ranka ya ɓaci ina jinin.
Wai matarka kace ko?".
Wani irin kallo yayi mata tare da ɗago hannun shi zai shararamata mari yana cewa.
"Wai ne ma ko?".
Da sauri tayi murmushi tare da cewa.
"Kamar gibtawar ido zan gudu jikinta, ka kwaɗa marin a kanta".
Ai fa a kufule ya kai marin.
Hannunshi na isa fuskarta tana yin atishawa.
Zafin marin ya sauƙa kan fuskarta cikin azaba ta ɓare baki tare dasa kuka tana mai shafa haɓarta ido na zubda hawaye a gigice idonta na ganin duhu sabida zafin marin bata gama dawowa haiyacinta ba murya na rawa tace.
"Wayyo Allah na me nayi maka zaka mareni, ka barni inji da ciwo ɗaya mana".
Hararanta yayi tare da miƙewa ya sauƙa gadon yana cewa.
"Mutun jiki duk al'janu, sai hegen bakin rashin kunya mutun in ba lfy bazaiyi addu'a ba sai kuka".

Ya ƙarishe mgnar da juyawa ya nufi falo.

Ita kuwa Aysha wani irin bacci ne yayi awon gaba da ita,
tana mai jin zafin hannun ya ɗan lafa sai kuma raɗaɗin marin.

A can falon kuwa, wayar Aysha ne dake hannun Hibba yayi ringi.
Bappa am.
Shine sunan da ta gani a rubuce.
Da sauri ta nunawa Ummi shi tare da cewa.
"Ummi ana kiranta".
A hankali tace ki ɗaga.
Kai ta gyaɗa tare da amsa kiran ta kara wayar a kunnenta.

Cikin nitsuwa tace.
"Wa alaikassalam". Sai kuma tace.
"A a Bappa ba Aysha bace.
Hibba ce, Aunty Ayshan tana ɗakin Hamma Jabeer".
Cikin dattaku Bappa yace.
"To Hibba ya jikin nata?".
A hankali tace.
"Bappa hannunta kam yana ciwo sosai, ya kumbura yayi ja, in an taɓashi zafi kamar wuta, bata iya bacci".
Da sauri tayi shiru ganin Ummi na girgiza mata kai alamu.
Ta daina faɗa mishi hankalinsa zai tashi.
Ila kuwa hakane, cikin tashin hankali da kiɗima yace.
"Yanzu kai mata wayar maza, kai mata inji muryarta".
A hankali ta kalli Ummi tare da cewa.
"Ummi wai in Kai mata wayar".
Kai ta gyaɗa tare da cewa.
"Jekiyi sallama ki kai wayar".

To tace kana ta juya ta nufi falonshi.
Tana jin Bappa na cewa.
Yi sauri".
A falo ta samu Hamma Jabeer ɗin cikin sanyi tace.
"Hamma Jabeer gashi Bappa am, na son yin mgna da Aunty Aysha".
Hannunshi ya miƙa ya amshi wayar ba tare da yace komaiba.
Ganin kiran bai yanke bane.
Yasa ya zubawa number ido cike da mamaki ganin code number ɗin bana ƙasar Nigeria bane, na ƙasar Cameroon ne.
a hankali ya kai wayar kunnenshi tare da cewa.
"Assalamu alaikum".

"Wa alaikassalam Jabeer ne?".
A hankali cikin nitsuwa yace.
"Eh Bappa nine, ina kwana ya gida".
Cikin jin sanyi yace.
"Lafiya lau Alhamdulillah. Ya jikin Shatu?".
A hankali yace.
"Alhamdulillah Bappa jiki da sauƙi sosai ma yanzu hakama tana bacci ne".

Ajiyan zuciya ya sauƙe tare da cewa.
"Alhamdulillah to Allah ya ƙara lfy, amman me yake faruwa da hannun ne?".

Cikin sanyi ya miƙe ya nufi bedroom.
A gaban gadon ya tsaya tare da cewa.
"Hannun ya ɗan kumbura amman ba sosai ba, sai kuma yayi ja,


Related Ebooks

Leave a Review

You cannot submit review untill you Register or login