Showing 99001 words to 102000 words out of 352722 words
sai dai taji sunanshi.
Sosai ta shaƙu da Hibba da Umaymah, hakama Gimbiya Aminatu da Ummi.
Lokuta da dama takan shiga Bathroom tai ta kuka sabida begen ƴan uwanta.
Yau kwananta uku cur a gidan.
Idonta ma baiga ranaba.
Umaymah kuwa a sashin Jabeer yana fita.
Wata tirela ta iso har bakin Side ɗin shi.
Nan aka fara sauƙo da kayayyakin ɗaki na amare.
Ana shigarwa ciki. Kana masu aiki na ɗaure komai suna kimtsashi.
Sai kusan la'asar suka gama komai kafin.
Suka tafi kana su Umaymah suka taho.
Suna shiga asalin babban falon, Aunty Juwairiyya da Hibba suka haɗa baki wurin cewa.
"Wow masha Allah, Kai Umaymah ƙara so da sauri kiga falon nan yadda ya zama fadar masarauta".
Da sauri Umaymah da Ummi suka ƙara so.
Masha Allah! Masha Allah!! Masha Allah!!! Shine abinda kawai Umaymah keta mai-mai tawa, sabida kyau da tsaruwan falon yayi masifar kyau.
Kasan cewar falon irin ƙaton nanne mai faɗi da tsawo.
Wasu irin kujeru ne Daimond set masu masifar kyau da tsada, a shirya a cikin tamfatsen falon.masu Golding color mai ɗan karen sheƙi sai surkin Brown color mai sheƙin gaske da ratsin ruwan madara..
Kana haka ma kalan labuyen falon masu tsawo da faɗi da taushin gaske.sai wani table na glass mai Golding color da aka ajiye a tsakiyar falon bisa wani tattausan carpet mai azabar kyau.
Sai wani babban Tv dake liƙe a jikin bongon, kana gefen dama kuwa wani babban majigine manne wanda yake baiyana rubutun Kur'ani reras daki daki.
Can gefen kuwa steps ɗin hawa Dinning area ne,
wanda aka canza Dinning table and chairs ɗin,
Aka zuba wasu masu masifar kyau da tsadan gaske.
Ba'a wani cika falon da tarkace ba, amman yayi matuƙar kyau.
Tafiya kaɗan zakayi ta gefen hakun zaka ratsa cikin wani madaidaicin falo.
Yayinda na Jabeer yake hannun dama.
falon ɗakin da Umaymah ke tsauƙa in tazo kenan.
2 bedroom ne wannan falon yake dashi ko wanne da bathroom a ciki.
Kana sai Dinning area matsakaici daga nan gefen Dinning area kuma akwai ɗan ƙaramin corridor wanda zai sadaka da kitchen da store.
wasu irin datsa-datsan kujeru masu masifar kyau da ɗaukar hankali aka kimtsa a falon wanda komai na ciki.
Peach and white coffee ne mai ɗan karen kyau.
Hakama Dinning table and chairs ɗin.
Still labulayen ma hakane.
Sai kuma cikin bedroom ɗin wanda duk girmansu ɗaya, haka yasa aka shirya wasu tagwayen gadaje masu masifar kyau suma Golding color ne mai sheƙi da ɗaukar ido.
Saɓanin side ɗin Jabeer komai Sky blue and white ne, wanda hakan yasa kana shiga sashinsa sai kayi zaton a sararin samaniya kake rayuwa.
Komai yayi kyau.
Especially kitchen ɗin dake matsakaicin falon.
Domin wancan kitchen ɗin dake babban falon ba'a taɓa shi ba, hakama Side ɗin Sheykh.
Sai kuma sama wanda shi a rufe yakema, sam babu kowa a ciki.
Sosai fa su Umaymah suka yaba da kyan shirin da akayiwa wurin.
Nan suka zauna a falon.
Umaymah ce ta kalli Jakadiya cikin sauƙe numfashin tace.
"Alhamdulillah, gobe kuma zakiyi musu jagora shida matarshi su zaga ta gaida ahlin masarautar Joɗa, ta gansu su ganta su san juna, gudun kada a haɗu a wani wurin ba'a san junaba".
Wani gwauron numfashin Ummi ta sauke tare da cewa.
"A nan gizo ke tsakar ko ta ya zamu samu, Sheykh yayi wannan al'adar yadda ya dace ake kuma yinta, kinsanshi mutunne mai kunya, koda yana son abunma bare ba wani son abun yakeyi ba".
Cikin yarda da kai Umaymah tace.
"Kada ki damu yana ɗaya daga cikin dalilin da yasani, na zauna sai naga kamun ludeyin zaman nasu."
Haka dai suketa tattaunawa,
Suna nan zaune Gimbiya Saudatu ta shigo tare da hadimanta, kana da Laminu da Baba Basiru da Baba Nasiru.
Cikin isa da ƙasaita ta nufi kujerar da duk canjin da akayiwa falon ba'a canzashi ba sabida kujerace ta masarautar Jalaluddin, cikin isa take taku yayinda ta bawa ƙofar shiga baya.
Cikin gatsali ta kalli Umaymah data tsareta da ido. Kallon uku saura tayi mata kana tace.
"Duk mutun muna fuki abin tsorone. Amman munafurcin balaraben Mutun yafi na kowa muni da bada tsoro.
In banda salon munafurci ayi aure yau kwana uku a gaza fito da amarya a nunata ga mutanen masarauta, bare a fanshi idonta."
Ta ƙarishe mgnar tana kai mazaunanta bisa, Kujerar.
Sai kuma tayi maza ta miƙa, jin muryar Jabeer da yanzu ya shigo, ko mgnar ta, ta ƙarshe baijiba.
Cikin isa da ƙasaita da rashin tsoronta, da kuma tsare fuska alamun Ni bani da lokacin ki, kuma ni ba sa'an yinki bane ya nuna mata hanyar fita da yatsarshi tare da yamutsa fuska cike da ƙarfin zuciya ya kalleta ita da ƙannen Mahaifin nashi yace.
"Fice min daga gida, bacci na dawo zanyi so banda lokacin jin ihunku na kar...!
By
*GARKUWAR FULANI*
Ta bugi kofin madarar, ba zato ba tsammani, Jabeer yaji kofin ya tsumbce mishi.
ya faɗi gefenshi.
Tass ya fashe madarar ta kwaranye a ƙasa.
Cikin sauri da tsuƙe fuskarshi ya juyo ya kalleta.
Itama ɗin shi take kallo.
Ido cikin ido sukayi da ita a karo na forko a rayuwarsa duk da yasan sun taɓa haɗuwa.
Kallon kwaɗayye mai irin bakin Junainah, tayi mishi.
Sai kuma ta janye ƙwayar idanunta cikin nashi da sauri.
Sabida wani irin kallon da taga yanayi manata.
Umaymah da Ummi kuwa, kallon junansu sukayi, cikin yanayin son gane ya akayi kofin ya faɗi dan basuga sanda ta ta ɗan buge mishi hannunta.
Hajia Mama kuwa cikin tashin hankali da kiɗima ta kalli Umaymah tare da cewa.
"Akwai matsala, ita batasha, shi nashi ya kwaɓe."
Sai kuma ta maida dubanta ga Shatu cikin alamun damuwa tace kawo hannunki na dama."
Still maida hannun nata tayi baya, ba tare da tace komaiba.
Ummi ce ta ɗanyi ƙasa da murya tare da cewa.
"Miƙa mata hannunki ku gaisa".
Murya can ƙasa tace.
"Yana ciwo". Ta ƙarishe mgnar da jin haushin kanta da ƙaryar da suka satayi.
Batool ce ta kalleta sama da ƙasa kana cikin gyatsine tace.
"Umaymah ai wannan ba irin matar Sheykh bac."
Sai kuma ta haɗiye ragowar mgnar dan ganin wani irin kallon daya watsa mata na alamun.
Ki kama kanki da kiran sunana a bakinki.
Wani dogon ajiyan zuciya Hajia Mama ta sauƙe cikin fargaba tace.
"Tashi Kuje ku gaida sauran. Allah yayi muku al'barka ya baku zaman lafiya.
In sha Allah babu komai".
Kamar jira Shatu takeyi a basu izinin tashi tayi fit ta miƙe.
Da tarin mamaki Umaymah da Ummi suka miƙe, dan abubuwan da suka faru da yanayin Shatu, ya tsaya musu a rai.
Shima Sheykh Jabeer miƙewa,
yayi kana suka jere suka fita.
Sai dai Shatu na ɗan sassarfa.
Cike da mamakin wannan abun suka nufi Side ɗin Gimbiya Saudatu.
A falonta suka sameta tana hakimce bisa kujerar ikonta,
ta ɗaura ƙafa ɗaya bisa ɗaya tana karkaɗa ƙafar cike da izza.
Ummi na gabansu suna bayanta Umaymah na bayansu.
Cikin rusunar da kai Jakadiyarsu ta durƙusa gefenta tare da cewa.
"Barka da safiya Gimbiya Saudatu, ga Sheykh Jabeer ya kawo miki da amaryarsa!".
Cike da izza ta ɗan kallesu sama da ƙasa, kana ta nuna musu gabanta.
Alamun su zauna, cikin sanyi Shatu ta rusuna tare da sunkuyar da kai ta zauna gabanta.
Shi kuwa Sheykh Jabeer wani irin kallo yayi mata, mai cike da ma'anoni,
gefen ta ya kalla inda wata kujerar ke kusa da tata komansu iri ɗaya.
Taku yayi cike da ƙasaita ya isa gaban kujerar, kana ya juyo ya zauna kan kujerar.
Hakan yasa ya fuskanci Shatu da Umaymah.
zaman ƙasaita da isa yayi.
wani mugun kallo take binshi dashi har ya zauna.
Ita kuwa Shatu kanta a duƙe tana murzam ƴan yatsunta.
Umaymah ce ta ɗan taho zata zauna kusa da ita, a hankali ya jujjuyawa Umaymah kai, alamun. A a kada ta zauna a ƙasa.
gane manufarsa ne, yasa ta zauna bisa kujera.
Shiru kakejin falon, sai takun sawun hadimanta dake kawo ababen motsa baki, suna ajiyewa gaban Shatu.
Suna gama jerawa suka koma can gefen.
Jin shiru-shirun yayi yawane yasa Shatu ɗan ɗago kwayar idanunta, ta kallesu.
A ranta take mgnar zuci.
"Ikon Allah, ohoho ni Shatu wannan wanne irin bahagon gidane, mai cike da sarƙaƙiya da tubkar baƙin zare,
To ko dai ita wannan ɗin kurmace."
Muryar Gimbiya Saudatu ce ta ƙatse mata tunani ta,
cikin isa da izza ta kalli Sheykh Jabeer, kana ta juyo ta kalli Shatu, murya a daƙike tace.
"Bakiyi sa'an mijiba, yarinya duk da gashi kamar kinada nitsuwa".
Ido Shatu ta jujjuya cikin hular al'kyabbar jikinta.
Shi kuwa Sheykh Jabeer, ko ta kan mgnar ta bai biba,
sabida ai dama ya tsammaci, hakan
kai ta juyo ta kalli Umaymah cikin ɗagawa tace.
"A buɗe min fuskar amaryar in ganta da kyau, inga wanne irin idone da ita".
Bata rufe bakintaba taji yana cewa.
"Baza'a buɗe ba!."
Murmushi Umaymah tayi sabida tsamar Sheykh Jabeer da Gimbiya Saudatu wani lokacin yadda kasan shi ubanta ne, haka yake mata mgna da yanke hukunci kai tsaye a karan kanta ma bare akan abinda ya shafeshi.
ita kuwa Shatu a hankali take juya ƙwayar idanunta, tana kallon sawun Gimbiya Saudatu.
cikin al'kyabbar ta ɗan juya idonta da kyau ta maidasu, kan kyawawan fararen sawun Sheykh, wanda suke tamkar ka taɓa jini yayi yo tsalle ya fito, sabida taushi da laushin fatar
Wanda duk mutun mai zama da al'wala da yawan karatun al'ƙur'ani tafin hannunshi da ƙafarshi sukanyi wani kala mai masifar kyau da ɗaukar hankali koda baƙin mutun ne sai fatar hannunshi dana ƙafarshi sunyi kyau na musamman, hakama kuma fatar jikinshi wannan shine baiyanennen darajar zama da al'wala da yawan ambaton Allah kenan.
Da ƙarfi ta rumtse idanunta tare da buɗe su.
kan babbar yatsar kafarshi ta zubawa ido, sosai da sosai.
wani ɗan zane baƙi mai suffar tafiyar maciji ta gani.
sai dai bata samu ganinshi ras yadda take soba, shiyasa taketa zare ido,
shi kuwa Sheykh Jabeer a hankali ya ɗan turo ƙafar damanshi gaba.
Dan ya gyara zaman ɗayan a kanta.
Hakanne ya bawa Shatu damar zubawa yatsun nashi ido, suna nan zara-zara alamun mutum ne mai matsakaici tsawo.
Ras zanen bindin maciciyar nan yake kan babbar yatsarshi.
har zuwa bisa rumfar ƙafar kamar zanen dayis,
cikin tarin mamaki da al'ajabi take bin zanen da idanunta.
har inda igiyar takalminshi ya tsare zanen.
Wani irin sassanyan numfashi ta sauƙe a hankali.
sabida rashin ganin ƙarshen wannan zanen, da kuma inda ya nufa, da kuma ganin ya saman zanen yake.
Hankalinta kab ya tafi ga zanen shiyasa bata jin ta ƙaddamar da Gimbiya Saudatu ke zubawa ba.
Muryar ta taji da ɗan ƙarfi tana cewa.
"Bata da sunane? Ke me sunanki".
Ta ɗago kai da nufin yin mgna kenan sai kuma tayi shiru.
jin Umaymah na cewa.
"Sai kisa mata naki sunan, ba sai kiji namu ba".
A gyatsine ta kalli Umaymah kana, ta ɗan matso bakin kujerar,
hannu tasa ta ɗauki tupa cikin jerin ƴaƴan itatuwan da aka jera a gaban Shatu.
miƙa wa Shatu tayi tare da cewa.
"Kici kada ki tafi bakici komaiba,".
A hankali tace.
"Alhamdulillah!". Cikin sauri Gimbiya Saudatu tace.
"A ni ba'a zuwa sashina a tafi ba abinda akaci".
Hannu ta miƙa ta amshi tupan kana ta riƙe shi.
Shi kuwa Sheykh Jabeer miƙewa tsaye yayi alamun tafiya hakane yasa.
Suma suka miƙa suka fita.
Daga nan kai tsaye Side ɗin.
Baba Nasiru suka nufa.
A falo suka samu matarshi da yaranshi dama shi kanshi.
Bayan sun zaunane.
ya kallesu sama da ƙasa yace.
"Dama baku zauna ba, a hakama na ganku.
ba sai kun zauna ba".
Cikin sanyi ƴarshi Jamila ta ɗanyi ƙasa da murya tare da cewa.
"Ayyah Baba ka barsu mu gaisa".
Haɗe fuskarshi yayi sabida yasan irin masifeffen son da Jamila keyiwa Jabeer lokuta da dama, takanyi ta kuka in taji abubuwan da mahaifinta yakeyi mishi.
shi kuwa Sheykh Jabeer tuni ya zauna ya harɗe ƙafa,
Jamila kuwa cikin nitsuwa ta gaidasu kana.
Ta kawo musu abin sha,
Ummanta ku ko kallo Bata ishesuba yadda itama bata lallesu ba.
Haka dai suka fita suka tafi.
gidan Baba Basiru kuwa suna shiga ya tashi ya bar musu wojen.
Daga nan suka shiga gidan Barrister Kamal
Baba Kamal kenan.
Yana ganinsu ya tashi ya ruggume Sheykh tare da cewa.
"Masha Allah, Alhamdulillah yau dai Allah ya nuna min ɗana da matarsa".
Zama sukayi bayan sun gaisane yayi musu addu'o'in al'khairi.
Daga gidanshi gidan Dr Aliyu sukaje,
wanda yake mutun mai mutunci da kamar Barrister Kamal.
Sosai suka jima a sashinsa,
yayi musu addu'o'in da sanya al'khairi da al'barka.
Daga nan kuma sai Sashin Mom tsakar gidan Abbanshi.
Maman Imran, ba yabo ba fallasa ta amsa musu.
Daga nan wurin Amryar Abbansu sukaje, wanda suka sameshi a can.
Daga nan sukaje gidan Ya Hashim da sauran ƴan bappanunsu.
Gida na ƙarshe dai gidan Aunty Juwairiyya ne, can suka samu Hibba da Ya Jafar.
Bayan sun gaisane,
Umaymah ta ɗan matso kusa da ita cikin sauƙe numfashin gajiya tace.
"Ɗago kanki Shatu kinga nan ƙofar Aunty Juwairiyya ce, ga mijinta shine babban yayan Jabeer, kuma yanada matsalar ƙwoƙolwa.
Yanzu daga nan Side ɗinkin zamu wuce, wanda yana nan kusa da nasun. Sai gefen nakun kuma nasu Jalal ne."
A hankali ta ɗago kanta ta kalli Ya Jafar, yana riƙe da hannun Jabeer yana karatun shi a hankali.
Cikin sanyi tace.
"Ina kwana yaya!".
Kafaɗarta Umaymah ta dafa tare da cewa.
"Baya mgnar komai a duniya inba karatuba, sai dai yanajin komai kuma yana gane komai in an gaya mishi amman fa baya mgna kam in ba karatuba."
Cikin tsananin rauni da tausayawa,
idonta cike da ƙwalla tace.
"Allah sarki, Allah ya bashi lfy".
Karon forko kenan tunda suko fito dashi taji ya amsa addu'a duk da tarin addu'o'in da akayi ta musu sai yanzu taji yace.
"Amin ya Allah". Hakama Umaymah da Jakadiyarsu da Hibba sai dai duk ya riga su amsawa.
A hankali take ɗan satan kallonshi a fakaice.
Hibba ce ta janye mata hankali da cewa.
"Aunty Shatu kin gaji kam. muje ki huta, gashi azahar ta kusa ma."
Ɗan guntun murmushi tayi tare da cewa.
"Uhum".
Umaymah ce ta miƙe ita da Ummi kana sukace.
Taso mu tafi, yanzu Hibba zata cikaki dan zance."
Cikin murmushi Aunty Juwairiyya tace.
"Ayyah Umaymah ku bar mana ita mana".
Ummi ce tace.
"Lokacin sallafa ya ƙara to".
"Hakane kam". Juwairiyya tace tare da ɗaukar Foodflaks dake kan dinning table, tabi bayansu tana cewa.
"Hibba ɗauko sauran!".
To tace kana ta suggumi sauran tabi bayansu.
Nan suka bar Jabeer da Ya Jafar ɗin.
A babban falon suka zauna.
Aunty Juwairiyya da Hibba suka ajiye Foodflaks ɗin bisa Dinning table,
kana suka dawo tsakiyar falon.
Umaymah ce ta miƙe tare da kallon Shatu, tace.
"Taso mushiga ciki, kiga tsarin wurin naku".
Miƙewa tayi cikin alamun gajiya, domin zagaye masarautar Joɗa babban aikine mai zaman kanshi. Donma su sun saba, ita kuma bafulatanar dajine tafiya baya bamu tsoro.
Bayan Umaymah tabi, ta gefen Dinning area ta ɗan ratsa da ita,
Suka shiga cikin kitchen, juyowa tayi ta kallesu Ita da Hibba,
"Nan shine babban kitchen ɗin ki, dake babban falonki.
Shine wanda in kinada aiki mai yawa, kamar na salla ko azumi, ko zakiyi ki aikawa surakanki.
Hadimai zasu iya shigowa su tayaki."
cikin fahimta tace.
"Toh". Hibba ce ta ɗan ƙara so shigowa ciki tare da cewa.
"Kai wanga kitchen badai girmaba, gashi komai a tsare gonin kyau. Kalarsa green and white komai na ciki gwanin kyau".
Murmushi suka ɗan yi kana, Umaymah ta juya dasu.
Daga nan cikin kitchen ɗin ta gefen dama akwai wata ƙofar da sai ka hau stpes huɗu.
A gefen ƙofarne wani datsetstsen Fridge mai girma yake kwance.
Haurawa sukayi kana Umaymah ta tura ƙofar ta shiga.
Store ne mai zaman kanshi.
akwai komai na buƙatar rayuwa, sai dai ba mai yawa bane.
Shatu ta ɗan kalla tare da cewa.
"Ga kuma store ɗinki. Nan za'a ke aje miki duk wani abun buƙata".
Kai ta gyaɗa, kana suka fito.
Wata ƙofar daketa hannun hagu ta nuna mata suna buɗe wa suka fito.
Sai gasu bisa wata baranɗa mai girma, kana can ƙasan barandar fulawine da kuma pompona ke jere iya ganinka,
Daga sama kuma igiyoyin shanya ne da a ƙalla sun kai huɗu.
sai saman barandar kuwa, injin wanki ne.
Nan dai ta nuna mata komai na wurin kana suka dawo cikin gida.
Suna shigowa falo. Sheykh na shigowa.
A nitse yake taku, kanshi na sunkuye yana kallon wayarshi da yake lallatsawa.
Umaymah ce ta ɗan bi bayanshi tare da cewa.
"Zo nan Shatu".
Cikin zuba bayansu ido. Ta ɗan gyaɗa kai, tare da taka sawunta a hankali tabisu.
Hibba kuwa gefen Aunty Juwairiyya ta zauna.
Shi kuwa yana shiga falon nashi, ya juyo ya ɗan kalli Umaymah cikin kwaɓe fuska yace.
"Umaymah, Dan Allah ni bana son ana shigomin da wasu ababen cikin Side na, bare rayuwata, me wancan abun da kika kira zaizo yi anan?".
Ido ta kafeshi dasu hakane, yasa yayi ƙasa da kanshi.
tare da shigewa bedroom yana cewa.
"Dan Allah iya kar abun can falo".
Ƙeyanshi Umaymah ta zubawa ido.
"Wato ma wai wancan abun, lallai ma Jazlaan".
Juyawa tayi ta ɗan leƙo a corridor ta hangota, murmushi tayi tare da cewa.
"Taho mana".
Kai ta kuma gyaɗawa tare da ƙara saurinta tafiyarta a hankali.
Suna shiga falon, tayi wani irin ɓoyeyyen ajiyan zuciya mai sanyi,
sabida wani irin masifeffen sanyi mai gauraye da ƙamshi mai ɗan karen daɗi da taji ya bugu jiki da zuciyarta.
lumshe idonta tayi, kana ta buɗe su a hankali jin Umaymah na ce mata.
"Nan falonshi ne, namusamman ba kowa ke shigo mishi wurin kai tsaye ba.
dan ko Juwairiyya bata shigo mishi nan, kana akwai ƙannenshi ƴan uba maza da kuma Jalal basa shigo mishi nan.
Jamil kan shiga in baya nan in zai dawo shikeyi mishi shara da gyaran wurin.
Jalal kuwa yakan iya shekara ƙafarshi bata tako nanba.
Sai kuma Ya Jafar ɗin sa, shi kam bashi da hijabi da Side ɗin Jabeer, yakan shiga har cikin Bedroom nashi wani zubin har bathroom.
Sai kuma Haroon da Ibrahim su dama, dan su yasa aka gina sama wai masauƙinsu in sunxo.
To ammanfa in sunzo a ɗakinshi suke ko motsi zasuyi tare zasuyishi.
Sai kuma yayan Hibba, Hibbab shi na hannun damanshi ne.
Dan haka daga yanzu in dai yayi tafiya kece, zakiyi aikin da Jamil keyi".
A hankali tace "to".
Haura step ɗin Dinning area ɗin shi dake falon wanda akayiwa ƙawanya da wani irin labule mai masifar kyau.
Labulen ziri-zirin igiyoyine masu sarkafe da jeren duwatsu masu kama dana Daimond. wasu farare wasu Sky blue wasu Royal blue. suna da wani irin haske mai wal-wal. Cikinsa kuma.
Wani badaidaicin Dinning table ne mai kujeru shida nan uku nanma uku sai wani fridge ma daidaici. Gefensa show glass ne mai kyau wanda yake ɗauke da cups and plates and spoons and forks Mug. Da dai sauran ƙananan abeben buƙata.
sai woshing hand Baby, dake liƙe a can gefe.
sosai tsaruwan wurin yayi kyau, komai Sky blue and white. Abun sai ya zama kamar a duniyar taurarin yake yadda walwalin ke haska ko ina.
Falon kuma yanada ɗan karen duhu, domin saida Umaymah ta kunna musu wuta.
Bedroom nashi ta nuna mata da yatsa.
"Ga makwancinsa, sai kuma wancan ɗakin shi ba mai kwana a cikin ɗakine na musamman babu mai shiga ciki sai shi ni Lamiɗo Galadima, domin ɗakin aikinshi ne".
Ita dai da to